Hamshakiya Complete Hausa Novel

Hamshakiya 15

Sponsored Links

*🌸HAMSHAƘIYA*🌸

 

 

Na

_Jiddah S Mapi_

 

 

*Chapter 15*

 

 

 

“da kafa har ta isa bakin titi ta tari me taxi ta sanar mishi inda zai kaita, shiga tayi tana tsaki a ranta dan har yanzu tana jin zafi a jikinta, bayan sun iso ta biyashi kuÉ—inshi ta shiga ciki, ta gaji da zirga-zirga between gidanta da gidan marayu ya kamata tasan abinyi, tana wannan tunanin har sukaci karo da shugaba, kallonta tayi “Amrish daga ina da sassafe haka?”

kai kasa tace “wallahi shugaba naje neman kosai ne”

 

murmushi tayi tace “Amrish rigima dakin aika yara ai zasu siyo miki”

“ba zasu dawo da wuri ba siyasa naje da kaina”

 

“to hakan yanada kyau ya kamata ma a fara soya kosai da safe dan nasan mutane dayawa suna son kosai”

 

“eh wallahi shugaba ko Unty sadiya ma tanaso”

 

“to shikenan yau zan faÉ—awa masu girki su rinÆ™a sa kosai a ciki”

 

taji daÉ—i sosai matan tana son su, batasan itace take É—aukan nauyin gidan ba amma ta saki jiki da ita harma tana cewa zatasa a fara yin abinda suke so na breakfast hakan ba karamin darajan matar bane ya karu a idonta.

 

Bayan ta shiga office ita kuma Amrish ta wuce cikin gidan, da kallon tuhuma Unty sadiya ta bita, cikin ranta tace “na shiga uku”

 

zama tayi a gefenta tama murmushi, murtuÆ™e fuska unty sadiya tayi tace “aina kika kwana?”

 

“gidan shugaba” ta tsinci kanta da faÉ—an haka, sai a lokacin ta saki fuska tace “meyasa baki sanar min ba?”

 

“wallahi na tafi ba shiri ne time data kirani ina can bakin pompo, kuma banyi tsammanin zan kwana ba dan aikine ya rikeni nida Æ´arta mukayi ta gyaran naman da zasuyi miya dashi yau shiyasa na zauna acan”

 

“okay ai na zata wani wuri kika je har na kwana cikin fargaba”

 

“a,a babu inda naje”

tayi magana tana É“oye jikinta ta yadda ba zataga shatin bulala ba, É—aukan najma tayi wacce take mata dariya tace “kin sanni ne? kikemin dariya”

wasa ta fara yiwa yarinyar da haka har ta samu ta sulale daga wurin bataso unty sadiya taga shatin bulala a jikinta, É—aki ta koma ta zauna tareda kwantar da najma a jikinta tana tuno abinda ya faru tsakaninta da umar ne ko faruk bata sani ba, abin ba daÉ—i dan da bai É—aureta ba da yau yana kwance a kabari.

 

so take kota halin kaka ta gane wayene me laifi a cikinsu, ga kuma tunanin yadda zatayi da tulin kayan data É—ibo daga gidan gomnati, da manyan masu faÉ—a aji, so take ta cire ta siyar ta gina babban makarantan marayu amma ta rasa yadda zatayi ta fara.

 

tayi kwana biyu bata leka gidan can ba tana gidan marayu a zaune abinta da Æ´an uwanta yau tasa a ranta zataje ta duba gidan, da yamma sosai ta sulale ta fita, taxi ta shiga har kofan gida ya kaita, saida ta biyashi ta shiga gidan.

 

 

a falo ta ganshi kwance sanye da boxer yana karanta jarida, kallo É—aya tamishi sannan ta watsar tace “kasa riga”

yi yayi kamar bai jita ba itama bata kuma yin magana ba ta shiga É—aki ta duba komai yana mazauninshi sannan ta fito taga yasa jallabiya maroon tace “zaka iya tafiya a duk lokacin daka so”

 

ya bari ta iso bakin kofa zata fita yace “bazan tafi ba sai kinyi hukuncin daya dace dani”

 

“ba zanyi hukunci ba saboda ba kaine me laifi ba, hukunci yana kan mai laifi ne”

 

“nine mai laifi kawarki teema nine na fara É“ata mata rayuwa, Umar nine doctor shikuma faruk shine soja ki daina wahal da kanki”

 

“ba wahal da kaina nake ba, abinda naga ya dace nakeyi, zaka iya tafiya a duk time É—in da kaso”

fita tayi daga ɗakin ta wuce bayan gidan inda yake ɗauke da lambu kayan itatuwa dayawa, wani bowl ta ɗauka ta fara tsinkan inibi da saitun, ayaba da rabina shima ta tsinka ta cika bowl ɗin dashi take bakin swimming pool ta ɗibi ruwa ta wanke, komawa gefe tayi ta zauna kan grass carpet ta fara ɗauka tana ci, sunada zaƙi lumshe ido tayi, rayuwar duk ta fita a ranta dama burinta ta gyara gidan marayu ya shiga hannun mutane masu imani to Allah ya cika mata buri yanzu batada wani burin daya wuce ta gina school wanda zasuyi karatu kyauta ba tareda sun biya ba, daga nan saita miƙa kanta wa ƴan tsaro suyi mata duk hukuncin da sukaga zasu iya, domin itaɗin mai laifi ne, ba zatayi haka ba saita cika burinta ta miƙa kanta wa ƴan sanda.

 

hannu tasa ta share hawayen fuskanta sannan ta kalli gidan da take zaune a ciki, anan ya dace tayi nursery da primary idan yaso sai a nemi inda za’ayi secondary, sunan nursery zatasa Na’eem and Aliyu nursery school, yaran da manya suka yiwa fyaÉ—e ta hanyan luwaÉ—i har suka mutu, na primary kuma zatasa Manal and Feenah primary school, manal wacce akayi kawalcinta har tun tana yarinya akayi mata fyaÉ—e da feena wacce suka yankewa hannu suka tafi saudiyya da ita har yau babu ita babu labarinta , sai secondary kuma tasa zainab and teema secondary school, zainab wacce ta bada rayuwanta domin taimakon yara Æ™anana, zatayi high institution shikuma zatasa Orphans university ma’ana jami’an marayu”

 

tana tunanin hawaye yana wanke mata fuska har yana jiƙa gaban riganta, kai ta ɗago ganin yana miƙa mata tissue, kallonshi tayi bata karɓi tissue ba taci gaba da kuka tana sharan hawaye, zama yayi a gefenta yasa hannu cikin bowl ɗin ya ɗau ayaba ya ɓare sannan ya kai bakinshi ya fara tauna hankali kwance yana kallonta tana sharan kwalla.

 

saida ya cinye kusan uku kafin ya É—au inibi ya fara sha, saida yasha kusan rabin bowl É—in ya É—au zaitun yanaci yan lumshe ido, batayi mishi magana ba taci gaba da kukanta, bai bar komai a bowl É—in ba ya cinye tass yana kallonta ya kara sa hannunshi a roban bowl É—in ganin ba komai cikin mamaki ya É—ago kai yace “laa ya kare”

kallonshi tayi, yayi murmushi wanda ya kara fito da asalin kyaunshi na bafulani yace “kinga yadda na cinye wannan fruits É—in ba tareda na sani ba kuma ban Æ™oshi ba? to haka rayuwarki zata kare, bakisan me kikayi ba kina tunani kina kuka, abu É—aya da zakiyi kiji daÉ—in rayuwa shine jajircewa da dauriya da kuma yadda da Æ™addara mai kyau ko mara kyau, saÉ“anin haka zaki kare rayuwarki ne cikin kunci akwana a tashi kizo kina tsanan kanki, tabbas mutane sun miki laifi to ai laifin da mutane suka miki shine rayuwa, idan kina zaune ba’a É“ata miki rai kuma ba’a yimiki laifi ta yaya zaki É—au darasi a cikin rayuwa?

Amrish zama na kwana kaÉ—an da nayi dake na gano ke É—in macece jaruma keba raguwa bace kinada zuciya kuna kina aiki da hankali, kamar yadda kikayi kika É—ibo wannan tulin dukiyan daga gidan manyan mutane haka zakiyi amfani dashi ko gina rayuwan mutanen da suke da bukata koda kin mutu babu wanda zai manta dake.

 

nasan akwai zafi maraici dan nima na tashi ba uba, to amma babu maraya sai rago, ki tashi ki daina kuka ki manta da baya ki fuskanci gaba, sawa a rai sai kin É—au fansa ba shine ba, ni nan da kike gani na daÉ—e da sanin kece kike kisan barinki kawai nayi dan nasan kinada hujjan yin hakan.

 

na gano hakan ne ranan dana fara duba cctv footage a gidan Alhaji hamza naga duk yadda kukayi dashi kuma nasa a kunnena naji duk yadda kukayi, hatta lokacin da kikaje gidanshi na sani, na kyale abin ne saboda nasan kinada hujja kuma ya cancanci kisa, amma fa É—aukan doka a hannu ba kyau, zoben hannunki na gani a gidan hajiya Halima ranan da aka kasheta, da kaina na É—au zoben na kai kofan office nata a gidan marayu ina sa ido naga wanda zai É—au zoben sai naga kinzo wucewa, a tsorace kika É—aga zoben kika sa, tun daga lokacin na fara bibiyanki duk inda kikaje, akwai ranan da akayi sanyi sosai kika wurga dutse masu gadi suka bar mutum É—aya nine naje wurin na nuna musu id card nawa na jasu da hira dan ina jira ki fito ki tafi ba tareda an kamaki ba, sai kuma naga kin fito kin gudu daga nan nayi musu sallama na tafi, bakisan wannan zancen ba amma ni nasan komai a kanki Amrish, abinda ya bani mamaki shine yadda ke É—aya kika zama mutum biyu wato Ameera da Amrish”.

 

 

“da kanki kuma kika kara sanar min ke É—in kina kisa kuma kina sata, a lokacin na yadda da magananki Amma na nuna miki kamar da wasa kike, kinsan dalilin da yasa nayi hakan?”

 

shiru tayi ta zuba mishi manyan idonta tana kallonshi cikin mamaki da tsoron abinda yake faÉ—a mata, murmushi yayi yace “saboda na wanke É—an uwana a wurinki wato Umar”

 

nasan Umar yayi laifi hakan yasa na karÉ“i hukunci a kanshi, ina son Umar sosai banason abinda zai taÉ“ashi domin shine babba akaina, a haka ya hakura ya barmin girman ya zama nine babba, ni nake amsa sunan babba akan Umar, dan Allah ki cire idonki akanshi kinji?”

 

ba zato ba tsammani yaji ta faÉ—a jikinshi ta fashe da kuka sosai tana Æ™ankameshi, zubawa bayanta idanu yayi yana jin sautin kukanta yana ratsa jikinshi, a hankali ya É—ago hannu yasa a bayanta yana É—an taping, cinin muryan lallashi yace “is okay”

 

“dama kasan wannan labarin kayi shiru akai? meyasa baka mikani wurin Æ´an sanda ba? meyasa ka rufamin asiri?”

 

“ki daina kuka nasan an zalunceku shiyasa na É“oye komai daya shafi case É—in, duk wani alama ko shaida na kawar dashi nasan idan an kamaki dole zaki ambaci suna yayana a cikin masu laifi”

 

sakinshi tayi tace “kenan kayi haka ne dan ka kare yayanka?”

 

“bakiyi laifi ba idan kince haka, amma ni nayi ne domin nasan bakuda laifi”

 

share hawaye tayi “ta yaya zan yadda da kai? ta yaya zan yadda cewar ba tuggu kake haÉ—amin ta yadda zaka mikani wa Æ´an sanda kai tsaye ba tareda wani fargaba ba?”

 

“ta yadda kika yadda dani ta haka zaki yadda dani”

 

bata gane zancenshi ba, zuba mishi ido tayi tace “to meyasa ka yadda ka zauna dani?”

 

“na yadda ne saboda nasan kina cikin kaÉ—aici zama ke kaÉ—ai zai iya sa miki wani tunani wanda bai dace ba, kizo ki aikata abinda zakizo kina dana sani”.

 

 

 

_hauwa shu’aibu jiddah 08144818849_

Leave a Reply

Back to top button