Qamshi Complete Hausa Novel

Qamshi 56-60

Sponsored Links

*✨QAMSHI 56-60✨*

 

 

✍🏿Rashow

 

 

WANNAN PAGE DIN NAKI NE MY SIS.

ILHAM MUHAMMAD.

 

 

Da sauri na fito daga sashin Diddy naje na Gaishe ta sabida qa’ida ne kafun naje gidan gona se nabi na gaishe ta ita dasu Jiddy sannan na shiga na gaishe da su Diddy da matan Baba na idan nayi sa’a Baba me Zuma bai futu da wuri ba sena gaishe shi,Sosai atamfar jiki na wanda akayi min dinkin sitiret fitat ya min kyau ya zauna das a jiki na kamar wanda aka dinka a jikin nawa,karamin mayafi na yana geten kafada na don ko yafawa banyi ba, hill shoes me igiyar belt na Sanya ma kafa na hakan seya qara qawata tafiya na ya dada fito da tudun mazaunai na suna wani irin Kara cikowa suna jujjuyawa acikin rigan,dan yamutsa fuska na nayi tare motsa karamin baki na ina tafiya da dan sauri inayi ina lissafi hakan ne ya dauke min hankali da ko lura dasu Safeena da suka tawo zata yima Hatim rakiya zuwa gurin motar shi banyi ba,Cak naja na tsaya ganin yanda na kusa buge kafadar Safeena sabida Sam ban lura dasu ba,kallon juna mukayi ido cikin ido ni da Safeena sannan na dan juyar da Kai na gefe na saci kallon Hatim wanda yake sanye cikin wani black half jamfa me ratsin zanen milk Kala Kan shi kuma babu hula se gashin kanshi da yake kyalli sabida gyaran daya sha,karamin bakina nadan turo gaba kamar wacce akace dole se nayi maganar a hankali nace “Yaa Hatim kayi kyau” ba Safeena kadai ba hatta Hatim da kanshi yake kallon agogon hannun shi Seda ya dago kanshi ya zuba min ido ba tare da yace min komai ba ya Kafe ni da idon shi, giftawa nazoyi zan wuce nayi tafiya ta a zafafe Safeena ta Sanya hannu ta kamo rigana ta baya ta dawo dani saitin ta tana min wani mugun kallo tana wuci tace “uban wa ya baki daman kallon muji na har ki bude wannan kazamin bakin naki ki yabi miji na a gaba na?” Kara turo baki na nayi na juya ido na  ina Kara shagwabe fuska na kamar wacce zanyi kuka da shagwaba nace “to ai shine yayi kyau da yawa, kuma ni ai sabida don kalan kayan mu daya zabar min yayi kala daya da nashi ne yasa nace yayi kyau fa” na karasa maganar tare da sake juya ido na, wani irin yarrrr Hatim yaji a jikin shi tsikar jikin shi yana wani irin tashi ya kara tamke fuskar shi ya sakar min harara yana kokarin gota mu ya wuce yana lasar leban bakin shi tare da Sanya hannayen sa duka a aljihun wandon shi,ganin Safeena ta juya tana kallon Hatim ne wanda idon ta yake mata gizo inba karya idon nata yake mata ba kamar har wani murmushi taga Hatim yake yi,wani fushi ne ya taso mata a ranta tace wato shi an yabe shi har wani dadi yake ji yana wani munafukin murmushi,wato kayan ma shi yaje ya zabo mata amma idan sun hadu a gaban mutane se ya ringa shan qamshi yana bata rai ashe zagawa yakeyi yana danne yarin yar nan yana cinta a boye to wallahi bazan yarda da wannan rainin wayon ba,a zafafe ta juyo tana kudura a ranta cewar yau wallahi seta koya ma yarinyar nan hankali se ta cire mata duk wani iskancin da yake kanta, wayam taga bani gurin ta kuma juyowa ta kalli Hatim wanda ya daga kafadar shi yayi gaba abun shi,sake juyawa tayi ta hango ni ina tafiya ina jujjuya duwawu na gashi har na kai kofar da zai shigar dani gidan gona.

Seda Safeena ta tabbatar Hatim ya futa a gidan ta jujjuya taga babu kowa a haraban gidan se megadi da yake can bakin gate yana Jin gidan radio,da sauri Safeena ta nufi gidan gonar ta shiga bata iske kowa a bakin kofar shigan ba sakamakon officer Marry ta karbi handbags dina ta biyo ni dashi female part don zan canza kaya na kafun na fito na fara aikin canza ma kifi ruwa na kuma zuba ma kaji abinci sabida har yanzu ban dauki sabbin ma’aikata ba.

Sosai Safeena ta zaga ko ina bata ganni ba haushi da takaici ne ya Sanya ta bude kofofin dakin kaji duk suka firfito waje ta nufi gurin ramukan da kifi suke ciki ta bude gurin futar ruwan ta yanda ba’a budewa sabida kifi sukan futa ta gurin take ruwan ya shiga fucewa da qarfi kananun kifi wanda basu gama girma ba suka fara futa ganin hakan da Safeena tayi ne ya sanya ta dawowa a zafafe ta shiga yin ball da kajin da suke ta Karan kuka, ba tausayi ba komai Safeena take ball da kajin nan wasu ta shuresu da kafar ta wasu ta takasu ga kajin turawa daman basu da wani kwari take wasu suke faduwa ko shurawa basu sakeyi.cusa waya a aljihun wandon jikin ta merry tayi ta matso kusa da Safeena tace “Maa you are under arrest”jin abunda wani muryan da Safeena bata San dashi ba ta dago fuskar ta da duk ta hada gumi take taji faduwar gaba Sabida ganin police mace a gaban ta sake kajin da suke hannun ta tayi a zafafe ta hauro wa officer merry murya a kausashe tace”uban wa ya baki damar shigowa har cikin gidan mijina kice zaki kamani? to kiyi gaggawar fucewa anan inba so kikeyi ki rasa wannan karamin aikin naki ba, ke kinma san waye miji na a qasar nan kuwa? “Kara matsowa kusa da ita merry tayi tana me ciro handcuffs daga gefen wandon uniform din jikin ta ta sake cewa “Maa you are under arrest. tayi saurin kama hannun Safeena wacce take daga hannun sama don karta kama mata hannun ta hadesu duka biyu ta sanya mata handcuffs din ta tura ta suka matsa daga cikin kajin, da sauri merry ta kwala ma officer din da take Zama a bakin gate kira “yes sir am here ” tayi maganar tana Sara ma officer merry dan juyowa merry tayi jin muryan officer din a kusa dasu kafun merry tace komai ma dayar officer din tace “sorry sir kukan kaji naji yayi yawa ne shi yasa na taso daga bakin aikina don na duba naga ko lafiya” kai officer merry ta daga mata tace “is ok kije ciki ki sanar ma madam.”sake Sara ma officer merry officer gate din tayi ta juya da sauri ta nufo kofar female part Cak ta tsaya tare da Kamewa ta Sara min sabida gani na da tayi na fito da mugun sauri don jin kukan kaji ya cika gidan.turus naja na tsaya ina kallon kaf kajin gidan wanda suka cika ko ina da sauri na fara tawowa don ganin wasu kajin a kwance a qasa kamar basa motsi, da sauri officer ta biyo bayana tana min bayani,banko dago kaina ba cikin tashin hankali ina dago gawar wata kaza nace “a wuce da ita station amata duk abunda ya dace kafun nazo kuma Kar a yarda a bada Belin ta.” sake Sara min officer tayi ta juya da sauri ta sanar ma officer merry abun da nace ta wuce da Safeena ta get wanda se a lokacin Safeena tasan ma da akwai wani get a cikin gidan gonar sabida girman da yake dashi.da sauri Rabe daya shigo gidan gonar hannun shi dauke da takardun shi na neman aikin a gidan gonar ya juya ganin kaji a kwance a kasa basa ko motsi ga wata mata can kuma an wuce da ita wacce baiga fuskar ta ba, bai tsaya a ko Inaba se a tsakiyar falon Jiddy wanda suke zaune da Diddy da Zafeer da Zunnurain,duk Rabe suka kalla wanda ya shigo musu falon a hargitse babu ko sallama yana haki yama kasa magana Diddy ne ta mike tsaye tana ruqo zanin ta tace “shi Kenan kuma nawa ya kare shin Rabe wane ne ya mutu a wannan tsakiyar ranar?” kan shi Rabe ya girgiza yana haki yana nuna hanya da hannun shi yace “qamshi ne Diddy! qamshin kine” wani kalan zabura kowa na dakin suka yi suka mike sukayo kan Rabe suna tambayar shi “meya Sami qamshin?” suna rige rigen tambayar Rabe,Diddy Kam sumar tsaye tayi ta Kame daga yanda take tsaye Zunnurain ne yayi jarumta ya tare ta don karta fadi.cikin haki Rabe ya Kalle su yana nuna waje yace “wata ne tazo gidan gonar qamshi ta kashe mata duk kajin gidan gonar harma da kifi yanzu an tafi da matar police station.” ajiyar zuciya Diddy ta sake me karfi kamar wacce aka mata shocking ta dawo hayyacin ta ta ture Zunnurain wanda yake rike da ita tace bani guri ka gani.” tayi hanyar waje suma duk futowan sukayi suka bi bayan Diddy suka nufi gidan gonar.

a durkushe suka iskeni ina daga kajin da suka riga suka mutu ina matsar wa gefe, Jiddy ne ta dafa kafada na da sauri na dago kaina na Kalle ta ta sanya hannu ta shafa kaina tace” ki daure komai zai zama dai dai”  kaina na daga mata don jin makoshi na nakeyi a toshe zuciya na yana min zafi amma na daure na dubi Diddy da take ta zagaye kajin tana daga kai tana girgizawa na juya na kalli su Rabe suma duk sun shiga tashin hankali murya na a sanyaye wanda bai futa sosai nace “Zafeer kaida Rabe ku maida kaji masu egg daku nan su kai kuma Thariq kai da officer lidi ku Kora  fararen kajin suma dakin su na kalli Diddy data kasa tsayuwa guri daya nace” please Diddy ga rumfa can ku koma inuwa ku zauna keda Jiddy bari mu gyara gurin”  na kalli Zunnurain nace “Nurain zomu Kwashe wanda suka mutu mu maidasu gefe.” hannun rigan shi ya nade muka fara dagawa Diddy da Jiddy ma hannun suka sanya muka shiga Kwashe wa, dake muna da yawa zuwa azahar muka gama kwashe komai muka koma gurin kifi muka gyara murafen da Safeena ta ciccire na sake zuba musu sabon ruwa na barsu su huta kafun na basu abinci, kallon su Jiddy nayi nace “Jiddy ku koma ciki haka ni zan tsaya idan sun huta na basu abinci kajin da suka wahala kuma zuwa anjima in Sha Allah zasu wartsake tunda na sanya musu magani a ruwan shan su na kalli su Zafeer nace” nagode dukan ku da taimakon ku a gare ni. murmushi sukamin Thariq ya kwafe fuska kamar zaiyi kuka yace “sorry qamshin Ammy dazu na Kira Ammy a waya na sanar mata abun da ya faru tace itama gata a hanyar dawowa gidan kai kawai na daga mishi.

Ammy da kanta ta kawomin abinci gidan gona ta rungume ni tana jajan tamin abunda ya faru, bata bar gidan gonar ba har Seda ta tabbatar naci abinci wanda ita da kanta ta ringa bani a baki har Seda na koshi tukum ta barni ta tafi dakyar don taso mu tafi cikin gida tare nace mata zan jira kifi su huta ne na basu abinci tukun na tawo gida.

Safeena tun tana ganin abun kamar wasa taga an shiga yi mata wani irin mugun duka ne yasa babu shiri ta amsa laifin ta sabida ko zata samu su kyaleta haka fuskar nan nata daya gama babbakewa da man bleaching yayi jazur ya kumbura wani gurin har tambara tambarar baqi baqi yayi gefen bakin ta ya kumbura yayi simtim.

Se dab magrib na shigo sashin Ammy ban samu kowa a falon ba sedai ina jiyo maganar su daga cikin dakin Ammy daki na na wuce sabida inason nayi wanka kafun a kira sallar magrib, da ruwa me zafi na gaggasa jiki na kuma naji dadin hakan da nayi,na dauro alwala ina futowa daga bathroom ana Kiran sallar magrib gaban mirror naje na tsaya ina goge ruwan jikina na fesa turare na sanya doguwar rigan barci na shinfida mat din salla na kaffara harama, Koda na idar da salla ban tashi a gurin ba har Seda nayi sallar Isha sannan na mike na nade abun sallar hijab din jiki na ma cirewa nayi na nade shi tare da mayar dasu yanda suke na ajiya na zame dogon rigan dake jikina na isa gaban mirror na tsaya ina shafa khumra na kamar yanda na saba don Sabo da shafawan da nake yine akoda yaushe har qamshin sa ya kama jikina koda ban shafa ba zakaji ina kamshin,ba tare dana sanya komai a jiki na ba na isa gaban durowa na bude ina kallon kayan ciki wani Bikini pant wanda gaban pant din yake da wasu ring guda biyu ta baya kuma idan ka kalli mazau nai na zaka zaci ban sanya pant bane sabida dan siririn igiyar pant din yabi ramin duwawu na ya shige ciki se manyan mazau nai na da suke kyalli a waje wani fele felen riga na dauko na sanya wanda ya tsayamin iya cibiya na ga kan nipples dina baro baro ana gani,gaban mirror na dawo na dauki turare na shiga feshe jiki na dashi a firgice na sake turaren da nake fesawa na juyo a mugun razane don jin wani irin  magigicin buga kofan dakin akayi tare da bude kofar kai dagaji kasan bana lafiya bane hakan.

Cak Hatim ya tsaya yana bin jiki na da wani irin kallo tun daga kafa na har zuwa sama ya tsaida kallon shi akan nono na da sukayi cirko cirko suna tsole idon me kallon su.

 

 

 

*Rashow* 07052100719 chat me up.

Leave a Reply

Back to top button