Furar Danko Book 2Hausa Novels

Furar Danko Book 2 Page 42

Sponsored Links

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣2️⃣

…….Bai samu ganawa da Abba ba sai bayan sallar isha’i ya samesa a falonsa. Bayan sun gaisa cikin dakewa Abban ya ce, “Aliy!”.
    Ya amsa da “Na’am Abba”.
  “Aliy!”
Ya sake ambata. Shima sake amsa masan yayi kamar farko. Malam Mika’il bai gajiya ba ya sake kiransa a karo na uku shi kuma ya amsa masan dai kamar yanda yay na farko da na biyu.
         “Na kiraka sau uku ko?”.
    Kai ya gyaɗa masa alamar eh.
“Na kiraka badan tisa maka sunan da ni na saka maka ba ne, na kiraka ne domin a yau zan tabbatar maka da magana ta ƙarshe ne akan aurenka. Dan duk maganganun da Yahanasu ta faɗa ɗazun akanka sun sosama mahaifiyar ka da nima kaina zuciya. Kuma mun ɗauki alƙawarin bazaka sake rufa wata anan gidan babu matar aure ba. Dan haka a yanzu ina son jin ta bakinka, idan kana da wadda kake so sai ka faɗeta, idan kuma babu mahaifiyarka ta maka mata, nima kuma na maka sai ka zaɓi guda a ciki.”
       Sai da ya ɗan rumtse idanunsa da jan numfashi, sannan ya ɗago a hankali ya kalli mahaifin nasa. Sai kuma ya sake maida kansa ya duƙar. “Kuyi haƙuri Abba duk ni ne na ja muku, amma insha ALLAH komai yazo ƙarshe, ba sai kun nemomin mata ba ni da kaina ma na samota”.
     Wata irin ajiyar zuciya Abba ya sauke a hankali, sai dai cikin dakewar san nan ya ce, “Wacece? Ƴar wanene? A ina kuma ta ke?”.
           Duk da yawan tambayoyin bai gazaba wajen amsasu ga mahaifin nasa. Ya ce, “Yarinyar da nake aiki gidansu. Ɗiya ga Alhaji Isma’il Jiƙamshi. A yau suma kuma suka buƙaci na turo iyayena dama in har na shirya”.
      “Alhamdullahi. Aliyu Hydar ka daɗe baka faranta min rai irin yau ba. ALLAH yay maka albarka. Ya yaye maka dukkan damuwarka. Ya ɗauraka akan maƙiyanka. Ya kawo maka mafita ga al’amuranka. Na amshi zaɓinka badan ta kasance ɗiyar Alhaji Isma’il Jiƙamshi ba, ko dan yana da kuɗi, sai dai dan nasan kai nagartaccen mutum ne da bazai taba yin zaɓen tumun dare ba.”
     (Abba ka gafarceni wannan dai kam zaɓen tumun asubace ma ƙarewar dare) ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam murmushi kawai yayi da faɗin, “Nagode Abba. ALLAH ya ƙara lafiya da nisan kwana mai amfani. Ku gafarceni akan dukkan abinda nai muku ba dai-dai ba kuma insha ALLAHU zan cigaba da zama a fiye da yanda kuke buƙata”.
     Sosai Abba yay murmushin jin daɗi, Aliyu na cikin ƴaƴan da yafi ƙauna a cikin ƴaƴansa, sai dai shi kansa a wasu lokutan bai san mike danne soyayyar ba yayta kyararsa da hantararsa a dalilin ƙaddarar da wani bai isa ya canjata ba. Albarka sosai ya saka masa sannan ya sallamesa. Koda yabar wajen Abba cikin gida ya shiga, sai dai kai tsaye ɗakin Ammah ya shige yau bai gaida kowa ba a matan gidan. Ya samu tana shirin fitowa kaima Abba abinci dan yau itace da shi. Ya fahimci tana cikin damuwar da ya san babu makawa akan abinda ya faru ɗazune tsakaninta da Umma. Ƙannensa kansu yau basa cikin walwala. Suna gama gaisawa Ammah ta fice, annan ne Hawwah ke bashi labarin faɗan da akai sosai ne ai yau ɗin kuma duk a sanadinta ne. Da ga ƙarshe aka ƙare da musu goron halin da yake a ciki. Sosai ya ƙara jin zuciyarsa ta Zafafa. Sai dai komai bai ce ba yay musu sallama ya tafi makwancinsa……

          *_WASHE GARI_*

     Washe gari batare da sanin kowa ba Abba da tawagarsa suka nufi gidan Alhaji Isma’il Jiƙamshi nemawa Aliyu Hydar auren Mawaddat Isma’il Jiƙamshi. Sun sami tarba ta mutunci dan har Baba ma yazo gidan shima. Abinda zai birgeka babu ƙyama ko hantara irin ta mai kuɗi ga talakawansa. Abin farin ciki da mamaki ashema Alh. Sufi Ado Garko school mate ɗin Abba ne ma a secondary school. A take hira ta kaure a tsakaninsu har zuwa kan abinda ya tarasu. Sai dai kuma bayanin da shi Baba yazo da shi ya girgiza su a wajen. Dan a ganinsu babu wani shiri ai tare da su game da haka. Baba ya kwantar musu da hankali tare da tabbatar musu da dalilansa masu ƙwarin gaske ta yanda su duka suka gamsu da hakan. Sun ɗan ƙara tattaunawa sannan sukai musu sallama cike da jin daɗin karramawar da suka samu suka suka taho akan sai anjima idan sun haɗu ɗin….

★★……

Sam Smart bai san mima ake ciki ba. Dan hatta zuwan nasu Abba bai san da shi ba saboda yau bai ma fita aiki ba. Tunda ita tace ta koresa da kanta a ganinsa babu amfanin ya koma su sake raba hali. Dan haka ya zaɓi yin kwanciyarsa a ɗaki yayta buga game ɗinsa hankali kwance har lokacin sallar juma’a ya gabato. Yana shirin shiga wanka Ahmad yazo gidan. Zuwan Ahmad gidan ba sabon abu bane garesa dan haka bai damu ba. Haka koda ya bashi shadda sabuwa fil yace ita zai saka bai kawo komai a ransa ba dan Ahmad ɗin ya sha musu ɗinki irin hakan, haka shima kansa yasha yi musu ɗinki a taren.
     Bai wani ɓata lokaci ba ya fito a wankan, Ahmad na zaune har ya kammala shirinsa. Yayi ƙyau matuƙa kamar ka sacesa ka gudu. Ahmad ya wani shiga masa ruwan turare. Warce turaren Smart yay yana hararsa da faɗin, “Kaifa a duniya kamar baka san wahalar kayan duniyar nan ba. Anata wannan yanayin zaka ƙaramin turare haka dan neman hanyar talautani”.
           Dariya kawai Ahmad yay masa da kashe ido ɗaya ya furta “Am sorry Zakin zaki”.
     Shima dariyar yay a karo na farko. Dan duk sanda ya kira shi da Zakin zaki yana nufin shi ɗin na Coach Hameed kenan yayansa. Cikin nishaɗi da farin cikin tsokanar juna da suke na kiran tuzurai suka fita. Jan Ahmad yay suka shiga ciki gaida Ammah. Ta saka masu albarka tare da addu’a data so tsayama Smart a rai. Amma sai ya danne ta a ƙasan rai da tunanin Ammah tayi addu’ar ne kawai domin gabansa. Daga haka suka taso suka fita acewarsu zasuje sallar juma’a su dawo nan suci biranuskon da Amma keyi matsayin abincin rana…
        “Wai wane massalaci zaka akaimu haka ne?”.
    Cewar Smart yana kallon Ahmad dake drivering a nutse. Murmushi Ahmad yay masa idonsa a titi ya bashi amsa da “Mi kakeci na baka na zuba? Zaka gani ai”. Baki Smart ya ɗan taɓe da cigaba da game ɗinsa a waya. A haka suka cigaba da ƴar hirarsu har suka iso massalacin juma’ar. Zamansu babu jimawa aka fara khuɗuba, dan haka suka nutsu wajen saurare har aka kammala. Ana ƙoƙarin tada salla ya hango Uncle Yousuf da Coach da ke isowa yanzu, da alama sun makara ne. Baice komai ba ya gyara tsaiwarsa aka tada salla. Kasancewar bayan idar da sallar juma’a yin ɗaure-ɗauren aure a massalacin normal ne yasa bai kawo komai a ransa ba. Sai dai haka kawai yake jin sa wani iri yau kamar wani abu na shirin faruwa da shi. Ga kansa da ke ciwo ƙasa-ƙasa amma dai sai ya daure tunda bawai ya matsa masa da yawa bane. Wani irin harbawa da dokawar ƙirji ce ta samesa a lokaci guda a dalilin jin sunansa matsayin angon da aka ɗaurama aure da amarya mai suna Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Shi al’ajabi ne ma ko ruɗani yama rasa ganewa. Ya dubi Ahmad da ke kallonsa yana dariya, “Kai nifa ban ganeba wlhy, wai waye haka mai irin sunana komai da komai fa”.
       Sake tuntsirewa da dariya Ahmad yayi har da riƙe ciki. Sai da yaga Smart ya turɓune fuska har yana harararsa sannan ya ɗan sassauta. Sai dai maimakon amsa masa sai ya miƙe dan yau dama ɗaurin auren biyu ne kawai ma, bayan an ɗaura na farko da ya kasance Smart da Lulu na biyun kuma aka fahimci shima dai da amaryar farko ne da wani angon, dan kuwa dai Alh. Sulaiman ne ya ƙulla, abin mamaki kuma babu shi a massalacin sai Tajuddeen kawai da gayyar abokansa. Yana jin kuma an ɗaura auren Lulu da Smart ya yanke jiki a wajen ya faɗi. Su dai mutane basu fahimci minene matsalar ba, haka ma su Abba magabatan Smart dan sai da aka tashi idonsa ya gane masa mahaifin nasa da tawagar dattijan anguwarsu. Sagade kawai yay yana kallonsu kamar television. Abba da ke kallonsa da murmushi ya ce, “Ɗan nema daina kallona ni, ko duk murnar ce ta saka sumar tsaye”.
       Dariya dattijan suka sanya har da Baba. Uncle Yousuf da ke jin ALLAH ya gama masa komai a yau ya matso ya kama hannun Smart cikin nasa ya jasa ya rungume. “FATAN ALKAIRI SURUKINA”. ya faɗa cikin kunnensa. Kamar wanda aka farkar a barci Smart ya ja nannauyar ajiyar zuciya. Cikin marairaice fuska alamar yaya haka.. yake kallon Uncle Yousuf. Shiko ya sake faɗaɗa dariyarsa da ɗan ɗage kafaɗa alamar nima ban sani ba. Coach ma rungumesa yayi yana mai jera masa addu’oi. Shi gaba ɗaya ma ya kasa iya furta komai. Sai da Ahmad yaja hannunsa gaban su Baba sannan ya motsa gaɓɓansa da ƙyar. Rissinawa sukai suka gaida Baba da ke zagaye da manyan mutane ciki harda gwamna. Abin zai baka mamakin yanda har aka iya haɗa mutanen bayan auren babu wani shiri a cikinsa. Koda yake ba abin mamaki bane idan akai dubi da girman Alh. Sufi Garko ɗin da ƙarfin ikon da yake da shi wajen manyan jihar. Sosai manyan mutanen nan suka dinga saka masa albarka kowa na jansa jiki ganin yanda Baba ya damƙe hannunsa cikin nashi shima. Daddy ma sun gaisa yana ƴar fara’arsa dai. Daga haka suka ringuɗa zuwa government house. Dan sakamako gwamna ne ya bada auren Mawaddat matsayin waliyyi yasa shi shirya liyafar cin abinci bayan ɗaurin auren. Smart dai ya zama kamar wani butun butumi. Komai ɗaukarsa yake kamar a mafarki. Ga kansa dake ƙara nauyi matuƙa har idanunsa na ɗan rinjayar ganinsa. Amma dai yanata dakewa kodan fidda mahaifinsa kunya. Dan duk da Malam Mika’il Idris Mawashi ba mai tarin dukiya bane. Dattijo ne nagartacce mai cikar kamalar da masu kuɗun dole suga girmansa da jin shakkar kawo masa raini. Shi da kansa ya biyama ɗansa sadaki naira dubu ɗari biyu. Sai dai Baba ya ce ɗari kawai zasu amsa ALLAH ya sanya albarka. Hakan ya ƙara sakama Abba jin kimar mutanen. Dan shi mutum ne mai girmama mutumtaka fiye da dukiya. A Government house mutanen da suka taru har sunfi na massalacin yawa saboda wasu sun iso a makare sai dai walimar zasu samu kasancewar sakon gayyatar ɗaurin auren yazo musu a ƙurarren lokaci dan a jiya jiyan nan da dare duk Baba yasa aka watsa shi a waya ta hanyar contacts ɗinsa dana Uncle Yousuf da na Daddy. Amma da ace shirine na musamman ai sai ma an rasa masaka tsinke. Sai dai hakan ma Alhamdullah, dan basuyi zaton taruwar mutanen kamar hakan ba amma sai gashi kamar wasa a kaso uku da suka gayyata kaso kusan biyu sun halarta bayan wanda sukaje massalacin salla kawai. Anci ansha anyi asuwaki da kaji yanda ya kamata, sai dai ango ya gagara cin komai. Ga abokansa ko nace teammate ɗinsa na ball zagaye da shi sunata masa shaƙiyanci da masa ciwon bakin jin auren a ƙurarren lokaci da sukai. Haka dai yayta daurewa har aka kammala cin abinci aka shiga hotuna. Nanma dauriyar yay tayi kasancewar duk wanda zai ɗauki hoto sai an jajubosa musamman ma manyan mutanen nan da ke nanuƙe da Alh. Sufi Garko. Shigowar lokacin sallar la’asar ne yay belinsa. Da ga salla kuma kowa zai kama gabansa……….✍️

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

Leave a Reply

Back to top button