Hausa Novels

Adade Anayi

Sponsored Links

COMPLIED BY ESHAAAT SMILER

HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS

WATSAPP 08066360176 FOR MORE

 

 

 

?A DADE ANA YI….sai gaskia💭

Bismillahir Rahmanir Rahim

1⃣

Sarita Vihar, New Delhi, India

12:08pm

School bus din St Paul’s High School ya

tsaya daidai bus stop din Sarita Vihar,

Yanmata biyu suka sauko daga bus din, kallo

daya zaki musu ki san cewa ‘Yan Makaranta

ne, sanye suke da Uniform doguwar riga

wanda da kadan ya wuce guiwa, ko waccen

su rik’e take da Jakkar makarantar ta

(School bag) da kwandon Abincinta

(Lunchbox) wasu daga cikin ‘yan Bus din

suka lek’o ta Window suka ce da yanmatan

da aka sauke “Alvida Kaveri, Alvida

Najwa” (Goodbye Kaveri Goodbye Najwa),

Kaveri da Najwa su ka daga musu hannu

suna Murmushi har Bus din ta k’ule da

ganinsu, da6i’ar su kenan, duk wacce aka

sauke sai an mata wak’ar bankwana.

Najwa da Kaveri ‘yan unguwa daya ne, tun

suna Kg suke zuwa Makaranta tare har

yanzu da suke High School 11th class.

Shekarunsu ba zasu wuce Sha bakwai zuwa

sha takwas ba.

Sun gangaro cikin unguwansu daidai gidansu

Kaveri suka tsaya, suka rungume Juna

Kaveri tace “NAJWA Kala milathe hai’n

(Najwa sai mun hadu gobe)” Najwa ta kalli

k’awarta Kaveri da murmushi har kumatunta

na lobawa tace “Sighra Milate hai’n Kaveri

(sai mun sake haduwa Kaveri)” suka dagawa

juna hannu ko wannen su yayi hanyar

Gidansu.

Ba tayi taku 15 ba ta isa gidansu, kamar

kullum maimakon ta shiga gidansu sai ta

tsaya a shagon dake daidai gidan, daga waje

take k’walawa mai shagon kira “Vijay Bhaiya

main bapaas aa gaya hoon(Brother Vijay, i’m

back)” bata tsaya jin me zaice ba ta

shigewarta gida, Lek’owa Mai shagon yayi ta

windown Shagon har ta kusa shiga gida ya

bude murya yace “ghar me svaagat haai

Najwa(Welcome Home Najwa)”.

Ta k’arasa ciki daidai k’ofar Tag ne mai

dauke da sunan Babanta a jiki SADA ABU,

hannun k’ofar ta murda ta shiga da Sallama,

ba amsa,kutsa kai tayi inda ta san zata ga

Mahaifiyarta, kamar yadda take zato hakan

ne, tana dakin Yayanta gaban tamfatsetsen

Hoton Yaron da ba zai wuce shekaru goma

zuwa sha daya ba, ajiyar zuciya ta sauke, ta

k’arasa gun mahaifiyarta tare da dafa

kafadunta, firgigit ta juyo a lokaci daya ta

goge hawayen da ke sintiri a idaniyarta gami

da k’ak’ulo murmushi.

“Maa, kukan kikeyi kuma?” Najwa ta fada

cike da damuwa, da Sauri Mahaifiyarta ta

girgiza kai tana murmushi tace “Aa Najwa ba

kuka nikeyi ba wani abu ya fada min a ido”.

Najwa tayi murmushi bata son jan zancen ta

ja hannun Maa suka bar dakin, ranta ba

dadi, duniya in akwai abun da ta tsana be

wuce hawayen Mahaifiyarta ba, kuma tun da

taso da wayonta take ganin Hawayen

Mahaifiyarta sakamakon wannan hoton da ke

mak’ale a dakin Yayanta.

Bayan Najwa tayi wanka ta shirya cikin kaya

Riga da Wando na Indiyawa ta yana gyalen a

kanta ta fito k’ofar gida wurin Vijay

Bhaiya,yana zaune a cikin shagon yana

ganinta ya fadada murmushinsa, ganin

fuskarta yayi ba walwala, cike da damuwa

yace “Kya huwa Najwa?(Meya faru Najwa?)”

ta rausayar da kai tace “Meri Maa abhee

bhee phir se ro rahee hai(Mamata na chan

na kuka kuma)” cike da tausayawa yace “ki

mein chitr abhee bhee use rona bana?(Hoton

nan na sata kuka har yau?)” tace “vah

hamesha ke lie jab tak vah us tasveer ko

dekhata hai rona hoga(Har abada zata

cigaba da kuka in dai tana ganin hoton nan)”

da sauri yace”ise door le jao(to a dauke

mana) tace “yah aasaan nahin hai(ba abu

mai sauk’i bane)” yace “prayatn(ki k’okarta)”

ta sauke ajiyar zuciya mai k’arfi ta mik’e

sannan tace “theek hai, main koshish

karoonga(Okay zan k’okarta)”.

“Waalaikum Salam” Maama ta amsa

Sallamar Paapa tare da mik’ewa ta k’arasa

gareshi,ya tarbeta da murmushi a fuskokinsu,

jim kadan fuskarshi ta koma na damuwa,

cikin sanyi muryar sa yace “Yesmeenah!

Kuka kikayi ko?” da sauri ta girgiza kai ta

kasa magana. Najwa ta fito daga daki tace

“Sannu da zuwa Paapa, Maama kuka tayi, ta

sake shiga dakin Yaya” Ran Daddy ya b’aci

yace “haba Yesmeenah, na zata mun wuce

gurin nan,ba kin min Alk’awarin ba zaki sake

shiga dakin kiyi kuka ba? Ashe ban isa in

rok’eki ki bar abu ba? To shikenan, Vijay

zansa ya fiddo komai na dakin ya k’onasu

tunda ba zaki bar zubar da hawayenki ba”.

 

Da sauri ta goge idonta tace “kayi hakuri na

bari” be ce komai ba ya wuce dakin yaron

su, duk suka bi bayanshi, Kinkimo

Enlargement din yayi ya fita dashi, da sauri

Maama ta bi bayanshi ta kamo rigarshi, tana

ja yana ja, kawai sai ta fashe da kuka tana

fadin “Sada! Ina zaka kaimin yarona? Ina

zaka kaimin shi, ka dawo min dashi, ba zan

yarda a sake rabani dashi ba” cikin zafin

nama Paapa ya fizge rigar ya cigaba da

tafiya, ta durk’ushe k’asa tace Wallahi ka

fita da hoton nan i will never forgive you,

kuma i will leave you”.

Chak ya tsaya, Najwa ta fashe da kuka bata

taba ganin Mahaifanta haka ba, Maama ta

tashi ta isa inda Paapa ke tsaye, ta

rungumeshi ta baya tace “DonAllah Papi kar

ka rabani da hoton nan, kar ka rabani da shi,

i’m only linked to him throught this picture”

Paapa ya rungume ta yana hawaye yace “i’m

Sorry Yesmeenah, bana son kina tada

hankalinki, nafiso ki mik’a Alamuranki ga

Allah, yana sane damu, shi zai bayyana

mana Zaid idan yana raye, zai kawo shi har

inda muke, idan kuma ya riga mu gidan

gaskia sai mu rok’i Allah ya gafarta mai”

Maama ta saki wani kuka mai sauti, Najwa

ta tako har gaban Mahaifanta ta rungume su

duka suna kukan tare ba me lallashin wani.

Can cikin Study room ta iske Paapa zaune ya

rafka uban tagumi, da yana da halin maido

dansu gida da yabi ya maidoshi ko don

kwanciyar hankalin matarshi, kusa dashi

Najwa ta zauna, tana me tausayin

Mahaifanta tace “Paapa?” firgigit ya zabura

ganinta ya sa shi k’akulo murmushi yace ”

Najwa, are you okay? menene?” ta hadiye

miyau tace “Paapa,bana son Kukan

Maama,kukan ta na daga min hankali,

ganinta a hali irin na yau ya sa na tsorata

Sosai, hankali na ya mummunar tashi” cikin

damuwa Paapa yac e ” Najwa Maaman ki na

da rik’o, as long as tana ganin hoton Zaid,

ba zata ta6a daina kuka ba.

Najwa da damuwa tace “Paapa, bamu san

ko yana mace ko raye ba, to meyasa ba

zamu koma Nigeria ba? Meyasa ba zamuje

mu nemo shi ba? Only then Maama will

have peace” ya girgiza kai, idonshi ya kawo

ruwa yayi saurin maidasu yace “Saboda ba

zamu iya ba, we cannot go back” da mamaki

tace ” maganar kenan kai da Maama, sai

kuce ba za mu iya zuwa Nigeria ba, to wai

Saboda meyasa?” yace

“We are not allowed to go back there” tace

“Waya hanaku zuwa Fatherland dinku?

Saboda me?” Murmushi yayi yace “We

cannot say, amma all we know is that we

cant ever go to Nigeria”.

Najwa kanta yayi zafi, Hakan na nufi zata

cigaba da ganin kukan Mahiafiyar ta kenan?

Da gudu ta tashi ta nufa dakinta

sakamakkon kukan da ya zo mata. Kan

Gadonta ta zube tana kuka, bata San

Yayanta ba, iyakar sanin da ta mai shine

wannan hoton da Maama ke ma kuka, hoton

ma Zanensa ne, bayan nan bata san komai

game dashi ba, ta ya zata tsaida ZUBAR

HAWAYEN Mahaifanta? Ta ci kukanta ta gaji,

a bayyane tace “aap kahaan hain Bhaiiy?

(Where are you Brother?).

Rivers Port Hacourt, Nigeria.

Murmushin nan da ke kashe ‘Yanmata yayi

wato Murmushin gefen baki, a ganin

‘Yanmata don su yake yin wannan

murmushin don ya rikita su, amma shi a

wajenshi duk sanda yayi wannan Murmushin

to ya ga Nasara ne ko alamun cin Nasara,

Wayarshi ya ciro yayi dialing wani number ya

kara a kunne, muryar shi cike da nuna isa

yace “AbdulMajeed’s on his way to Abuja

from Kano, Stop him in Zuba, I want all the

Documents, Money,Assets, inshort i want the

Clothes he’s wearing, Hell i want Everything”

Daga chan 6angaren aka ce “Okay Boss” har

zai yanke wayan yayi saurin cewa

“Armstrong, Beat the hell out of him but dont

kill him” Armstrong daga dayan 6angaren

yace “Consider it done” kafin Wayar ta

yanke.

Sake latse wayar yayi ya kara a kunne cike

da iko yace “Kidigo, kanaji ba, kaje Gidan

Abba Abu wurin 12, ka bi Motar da zata fito

daukar Yara a Funtaj School Asokoro, Idan

an dauko yaran ina so ka min Abducting

Macen ka bar Namijin, Call me as soon as

you do as i said and i’ll tell you what to do

next”.

Sai da ya kwankwadi gwangwanin Gulder,

kafin Ya zube kan Gado ya lumshe ido tare

da sakin murmushin shi, ta fara gaya mai

k’arya, yana jin dadin yanayin da yake ciki,

kusan minti uku yayi a haka kafin ya ji ana

shafa mai kai, nan da nan fuskarshi ta

chanza kala, fuskar daure tamau ba annuri, a

hankali ya bude ido ya zube su fes kan

Dame.

Murmushi tayi tace “Zed, are you Alright? i

didnt see you the whole of Yesterday, i

decided to come check on you” wani mugun

kallo ya mata, bata damu ba don ta saba

ganin haka, tace “Zed talk to me please” a

tak’aice yace “Go out” ba tare da ta mai

gardama ba ta juya da sauri ta fita, yayi

tsaki yace “Stupid i’m ZAID not Zed” ya

maida idanunshi ya rufe, be son komai ya

bata mai jin dadin shirin shi na fara daukan

fansan, wannan Shu’umin Murmushin yayi a

hankali yace “Baba Abba, Payback is a b*tch

(Ramuwar Gayya tafi ta gayya Zafi)”.

Toufa! Wasa farin Girki

Tambayoyi da yawa a kanku ko? Sannu a

hankali zaku amsa tambayarku da kanku.

To Jamaa ga Babi na Daya, ya kuka ganshi?

Yayi kuwa?. A Cigaba?.

To gani nan da k’ok’on barata, ina baran

k’urioinku ta hanya danna tauraron nan na

k’asa, sannan ku bada naku gudummuwa ta

hanyar fadan ra’ayoinku game da wannan

Babi , Lol i’m simply saying Please do Vote,

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg2⃣

 

11:17am

 

A daidai hanyar Zuba wanda ya baro Kaduna wanda zai Sadaka da Abuja,Cikin wata Mota k’irar Mercedez Benz, mai dauke da number Kano, Matashin Saurayi ne wanda ya hada komai a zahirance ke tuk’insa cikin kwanciyar Hankali da k’warewa,ba zai wuce shekaru 28 ba, kasancewar ranar Ranar Aiki ne, jefi jefi kake ganin motoci na wucewa.

Bai san ya akayi ba, ya dai ga motoci biyu sun sha gabanshi,ba tara da tsammamni ba ya taka birki k’ii gami da yin Salati ganin ya kusa kai ma Motar farko karo, be gama tunanin me ke faruwa ba ya ji ana k’wank’wasa windown Moatarshi da Bindiga daidai saitin kanshi, k’ululu cikinsa ya kada,hanjinsa ya duri Ruwa, nuni suka mishi da ya fito, hannu na rawa ya fito bakishi be daina ambaton Allah ba. Maza sunfi Goma suka yayi6eshi, dukkaninsu sanye da facial Mask.

 

Umurnin da aka bashi ne ya sa shi tunanin wannan wasu irin yan fashi ne? Inda Armstrong ke ce mai “Take off your clothes” da sauri yace “What?” saukar wani abu me k’arfi yaji a gefen fuskarshi, da sauri yayi k’ara tare da dafe gefen kanshi yaji danshi danshi Alamun jini, cikin daga murya yace “take off your clothes,i wont ask again” da sauri dan saurayin yayi yanda sukace, ya rage daga shi sai gajeren wando da guntun singileti, harta Takalmanshi Zobe da Agogo, sai da ya cire,  wani ya durk’usa ya kwashe kayan ya zube su a bayan motar.

 

Armstrong yace “Nelly take the Car go through the bush and start working” da saurin dan saurayin yace “Please dont, i’ll give you anything you want, name your price but Please just dont take the car”. Marinshi akayi ta gefen hannu” beyi shiru ba yace “if you want the car, just let me take somethings in it and i promise you all you want” Bindiga yaji a kanshi,fitsari ya zo mai saboda firgici Armstrong yace “You are not supposed to talk, talk again and i wont hesitate to pull the trigger” da sauri ya hadiye maganganunshi. Armstrong ya ma Nelly alamu da ido.

 

Dan saurayin na gani Nelly ya shiga motar dan saurayin ya juya Akalar Motar ya shiga cikin dajin gurin,wani ya bishi da wata motar, Armstrong ya tasa k’eyar Dan Saurayin su ka shiga Motarsu, sauran guys din suka ware.

 

Chan cikin dajin Nelly suka shiga, gindin wata bishiya suka tsaya, suka fito da kayan Aiki, suka tada Injin Penti(painting) nan da nan suka chanza Kalar Motar nan daga Ruwan Madara zuwa Bak’i, sannan suka chanza Lambar Motar daga ta Kano State zuwa ta Rivers State, ba su tsaya Motar ta bushe ba Nelly ya sa Handgloves dinsa ya bude Motar ya shige bayan sunyi waya da Boss yace “Ya kawo Motar da abunda ke cikinta Porthacourt” sukayi sallama da sauran guys din, sai bayan minti Ashirin yayi kiran Armstrong don yace mishi ya wuce PH.

 

Bayan sunyi tafiyar minti ashirin Wayar Amstrong tayi k’ara ya kara a kunne “Okay” kadai yace, kafin yayi umurni da direban ya tsaya, suka fito da dan Saurayin, suka mishi Mugun duka da hannu da k’afa, suka mishi dukan yan ‘yanwanki, sai da suka ma dan saurayinnan Jina jina kafin suka yasar dashi a gefen titi.

 

ABUJA NIGERIA

12:15pm

FUNTAJ SCHOOLS

 

“Mtsww” tsaki Zinatu ta saki a karo na 3, sam bata son jira, Muhsin yace “Sorry Zeenah, yanzu Falalu zaizo” haushi ya hanata tanka ma k’aninta da ke rik’e da Foodflask da Folder dinshi a hannu, yanda take cika tana batsewa sai kayi zaton wata uwar mata ce, amma shekarunta dudu ba su rufe 10 ba, ajinta 5, daga chan sai ga Falalu Direba da saurin shi ya k’araso inda take,Yana zuwa ya zube k’asa don sarauniyar fa cika tayi fam, “donAllah kuyi hakuri Zinatu, wallahi holdup ne ya rik’eni tun wurin 11 saboda yau Friday” harara ta buga mai tace “Muje gida Mommy sai ta koreka” ba ta tsaya jin magiyarshi ba ta yi gaba, k’aninta Muhsin ya bi bayanta don shi sam bai da damuwa, Jikin Falalu sai rawa yakeyi har suka shiga Mota ya ja Motar suja bar Haraban Makarantar.

 

Kamar daga sama Falalu ya taka birki sakamakon wata Mota da ta sha gabanshi, Maza biyu suka fito dauke da dumaduman Bindigogi nan take Falalu ya sake fitsari. Zinatu da bata lura da abun da ke faruwa ba cike da Masifa tace da “Falalu wani irin Wulakancine haka zaka taka birki har mu buge goshi?” be amsata ba sai ji tayi an sa6eta sama, sai a sannan ta ankara da abun da ke faruwa, ihu ta sake da k’arfinta, Muhsin ya fashe da kuka, suna ji suna gani aka sa Zinatu a mota suka wuce da ita. Da Fallalu ya rasa abunyi kawai sai ya fashe da kuka  don ya san yau Hajiya Mairo sai ta halbeshi.

 

Hajiya Mairo Zaune kan Kujera mai alfarma, ta daura k’afa daya k’an daya tana cin Apple, ta daga kai ta kalli agogon da ke mak’ale kan bango, a ranta tace “Boy should be home” numbern shi ta latso, ringing daya aka dauka, “Boy, yadai? Kana ina ne,ko goslow ne ya tareka? Gashi har an kusa Sallahn Juma’a, ko sai ka tsaya an idar zaka k’aroso gidan?” Armstrong yace “Shuttup kin kira kin isheni da surutu” da sauri ta cire wayan daga kunnenta ta duba don ta tabbatar da wanda ta kira, tabbas numbern Boy ne, to ya akayi haka, da karaji tace “who are you? And why do you have my Son’s phone? Where is he?” Armstrong yace “i’m an armedrobber” Mommy tace “What? Ina yarona?”yace ” he’s beaten up” ya mata kwatancen inda suka barshi kwance helplessly, ya shaida mata dama kiranta yake jira, ya kashe wayar tare da cire sim din ya yar.

Ihu take tayi, da gudu Ziyada ta fito da masu aikin gida, “Mommy? Me ya faru” ta daura hannu akai “Shikenan sun nakasa min Boy, yanfashi suka tare shi a hanyar Abuja, yana chan a Zuba”Salati Ziyada da masu aiki sukayi. Ziyada ta rungume Mommy Suna kuka, Mommy ta fita hayyacinta, ta ja mayafi zata fita, Ziyada ta rik’ota Mommy ina zaki? “Zuba” Mommy ya zaki je Zuba ke kadai? Ki kira Daddy atleast, please Mommy” da sauri ta dialling Numbern maigidanta. Ringing na ukku ya dauka “Hello Abba, Mun shiga ukkun mu, yan fashi sun tare Boy a hanyar dawowanshi Abuja, yana nan yashe kamar bola a bakin Titi”ta kwashe yanda sukayi da Danfashin ta gaya mai, Alhaji Abba ya rude iya rudewa yace “Barin mu tafi yanzu, ki kwantar da hankalinki, da mun shigo Abuja zan kiraki, calm down Maryam, AbdulMajid will be fine tunda sun tabbatar miki dukanshi kadai sukayi kuma a

Ka makami ba” ina ita ba wannan ba “Abba ka maido min yarona” yace “Ga mu mun dau hanya”.

 

Wata Sabuwa inji ‘yan cha-cha, ihu ta sake tare da cin kwalar Rigarshi tace “What?? Fallalu kana da hankali kuwa? Kasan me kake cewa? Wasu ‘yaniskan ne suka dauke min yarinya? Har kana zuwa da bakinka kana gaya min an tare ku a dauke Zeena? Donubanka ina diyata,Uban me kakeyi da aka dauketa? yau sai na kasheka, Fallalu ko ka fito da diyata ko nayi gunduwa gunduwa da kai” Fallalu da ke k’ak’arin wahala ya fasa ihu, “Hajia wallahi ban san ya akayi ba, ganin su kawai nayi a gabana, ki tambaya Muhsin kiji” Muhsin na kuka ya na dukan Mommynda yace “Mommy sun tafi da Zeenah, sun sa ma Fallalu Gun a Kai, zasu kashe shi idan ya bisu” cikin zafin nama tace “Oh shine ya basu diyar tawa su kasheya, to ni zan kasheka” Ziyadatu da hankalinta yayi k’ololuwa gun tashi, fuskar ta tayi Ja saboda Kuka, ga abunda ya faru da Ya Majeed ga kuma Sace Zeena da akayi, jikinta ba k’wari ta janye Mommynta, tace da Fallalu ya fita.Mommy ta zube k’asa, tana birgima.

 

Ziyada kuka,Muhsin Kuka, ba mai lallashin wani, Mommy fa abun ya cita k’ara ta sake me k’arfi tace “Na shiga Uku ni Mairo,Allah idan hukunci zaka min ka hukunta ni ba ‘yayana ba, ba su maka komai ba, saboda me?” Ziyada tayi saurin toshe bakin Mahaifiyarta, tace “Haba Mummy, karkiyi sa6o mana, k’addara ce, Ya Majeed will be fine, and Zeenah nasan kidnappers ne sukayi kidnapping dinta,Kudi kawai zasu ce a basu, donAllah ki kwantar da hankalinki, Mommy ta tashi kamar an tsunguleta ta kira Police Headquater. Yanda take yi kamar zararriya, Zafi Biyu, ga ‘yanfashi sun tare Abdulmajeed baa san halin da yake ciki ba, ga 6arayi sun sace mata mafi soyuwar diyarta, kai da sakel ihu ta sake sakewa, hawaye ya gangaro kuncin Ziyada a baiyane tace ” Me ke shirin faruwa da mu?”.

 

Porthacourt

 

“Good,ina Zeenatu din?” yace “na bugas da ita, tana bacci, cikin daga murya Zaid yace “Are you Crazy? Ka buggar da ita da uban me?” “Oga Kawai Sleeping powder na shak’a mata, she wouldnt stop shouting, tana ta ihu ne,kuma i needed to act quick don zata sa a kama mu lokacin muna kan hanya,shine har yanzu bata tashi ba” Zaid ya sauke numfashi,”Shes too young for that,kar kuyi abunda zai cutar da ita, kaje ka siyo mata komai da zata buk’ata har kayan wasa, if you hurt my little cousin, i’m gonna kill you, take care of her, call me when she wakes up, i’ll make the call” dif ya latse wayar.

 

National Hospital Abuja

3:45pm

 

Accidents and Emergency aka karbi AbdulMajeed, aka shiga duba shi,

“he’s lucky don ba karaya, ba gocewa, its obvious tunda ba da wani abu suka buge shi ba, da hannu ne, yanzu we’ll move him to a private room” cewar Doc.

Suna zaune su duka a dakin da aka kwantar da AbdulMajid, Suna kuka, Daddy ya shigo da wani inspector aka ma AbdulMajid tambayoyi ya basu amsa yana me cije gefen bakinshi saboda azaba, Ziyada na kan gadon da yake kwance tana shafa kan yayanta. Mommy tace “nifa Officer ba wannan ba ina so in san inda Diyata take” yace “Hajiya kiyi hakuri, mu jira kira daga Kidnappers din, da sun kira ku sanar damu zamu fara aiki, but for now zamu fara binciken yanfashi da makamin da suka tare Yaronku, zamuyi saurin kamasu tunda sun tafi da motarshi, za mu sa matakan tsaro har sai mun ganosu.

 

Inspector ya fita bayan yace dasu su sanar dasu idan sun ga kira daga bak’uwar number.

AbdulMajid yana tari yace ” Daddy, kayi hakuri, i lost those files and documents, i lost everything” Mommy tayi saurin isa gareshi tace “yi shiru Boy, lafiyar ka ta fiye mana komai, Alhamdulilah ba su maka wani mugun abu ba, ba komai” Daddy yace “kar ka damu AbdulMajid, ba wani abu bane 10% kadai mukayi loosing, inshaAllah ma zaa kamasu” kafin wani daga cikinsu yayi magana wayar Mommy tayi k’ara, bak’uwar number ce, Mommy ta nuna ma  Daddy ta mai alamun da yayi alerting inspector, Mommy ta dauka tare da sa Handsfree tace “Hello”

 

Cike da gadara, da nuna isa aka fara magana “Hajia Mairo, muna lafiya? kafin kuyi tunanin linking call din don tracking dina, kar ku manta rayuwar diyarku a hannuna yake, kuka kuskura kukayi abunda be min ba, zan kasheta kuma na kashe banza, kuma i’ll make sure ko gawarta ba ku gani ba” da sauri Mommy tace “dont please, zamuyi duk abunda kuke so but dont hurt Zeenatu, zamu baku ko nawa ne” Zaid ya murmusa kamar suna gabanshi yace “good” AbdulMajid da k’arfin hali yace “ta ya zamu tabbatar da bakuyi mata komai ba, ta ya zamu san shes alright” Zaid yace “Majeed Abba, jikin da sauk’i kenan, i’m glad you are found, well Idi let her talk to her Family” Idi daga dayan 6angaren ya cire selotape din bakin Zeenatu da ke jin duk abunda ke faruwa, “Mommy, Daddy, Ya Majeed, ku taimakeni ina jin tsoro”  Zaid daga dayyan banagaren yace ya isa Idi, they’ve heard enough” duk suka rude suna kiran sunan Zeena, amma ba daman amsawa tunda idi ya maida Selotape din bakinta.

 

Zaid yayi disconnecting call din Idi, dama Conference call ya hada, kafin ya cigaba da magana “Kun san tunda ta farfado take ta kuka, ta ki cin Abinci, har chocholates aka bata duk ta k’i ci, tana ta ihun kiran Mommy, well idan Mommynta na sonta kamar yanda take tunani she wont dare mess with me,  she wont involve the Police” da sauri Mommy tace “wallahi we wont, just tell us how much you want” kai tsaye yace “Naira Miliyan Goma” a take tace “Done, turo account number” yayi dariya yace i’m not stupid, zan kiraki gobe da safe i will tell you what to do” da sauri tace “Okay, okay, please dont hurt her” yace “it depends, the moment kukayi informing police zan sani, and i wont hesitate to kill her” cikin rudu tace “Wallahi ba zamu sanar da Police ba, wallahi ba zamuyi taking risk dinnan ba, na maka Alk’awaro” Zaid ya murmusa yace “Good, kinsan meyasa na kiraki? Ban kira Alhaji Abba Abu ba? Saboda nasan kece da gida, sai yanda kikayi dashi, Mijin tace, so tell your baby husband and your baby boy not to do anything foolish”. “They wont i promise”

Kai Kai Abun ya ishe Ziyada, hakurinta ya k’are, wannene wannan da yake gaya ma Iyayenta magana san ranshi? Daga ji ba babba bane, duk da a dake yake magana amma kana iya jin muryar k’uruciya a tattare dashi, tayi amanna ba zai wuce tsaran Ya Majeed ba amma ji yanda yake magana kamar ya sansu duka, tace “Kai Matsoraci, ashe kai dan k’aramin dan iska ne? Ashe akwai abunda kake tsoro? Ka fito ka tare mu gaba da gaba mana, dont be a coward” da sauri Mommy ta rufe bakin Ziyada, “haba kiyi shiru mana, waya saki magana?kar ki bata ranshi ya kashe ‘yaruwarki a banza, donAllah bawanAllah kayi hakuri”.  Ziyada cikin daga murya  tace “Mommy wannan ba Allah a ranshi” Zaid yayi murmushi sosai, yace “Hello Ziya, i’m coming for you, i cant wait to see you too, my regards to Zaineema”. Dif ya latse wayar tare da cire simcard din, dukkansu baki hangame, a hankali Ziyada ta sab’ulo da ga kan gado, tace ” He knows us All(ya san mu duka)”.

 

“Ohhhh, to ga Zaid ya faso, me suka mishi haka da yake neman hallaka su duka? Shin yana cin Nasara? Waye Zaid? Meye Asalin Zaid? Who is he? Who? Who?

 

Wattpad@biebeeisa, they gt every post first.

If you are enjoying this

Show me some love by Voting and  Commenting .

 

#Nagode

#1love

#ADAY

#Bibiliciousfreakingfans

[11:29, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg3⃣

 

Mamaki ya cika su ko waye wannan ya ma Familynsu Farin Sani, Daddy yace “Dole mu sanar da Police, dole a kama su, dole a hukuntasu, hukuncin Kidnapping a k’asar nan yanzu daidai yake da wanda yayi kisa” Mommy tace”Aa, ba zamu sanar da Police ba, ba zamuyi gangancin nan ba, ka manta sharuddanshi? Yace zai kashe Zinatu, Daddy yace “Yanzu Maryam sunci bulus kenan? Miliyan Goma? Ga fargaba? Ba ma wannan ba, kina nufin haka zaa bar maganar? Ina da tabbaci sune sukayi ma AbdulMajid haka, ina mamakin ko waye, gwara dai ayi bincike” Ziyadat tace”gaskia Mommy a sanar da Hukuma, abi mana hak’kinmu, idan account number zai turo tsaf zaa kama su a sauk’ak’e” Mommy tace “Sai dai ya kira goben, Unless my Daughter comes back to me, we wont inform anybody, “Abba, muje mu fara processing hada kudin” Daddy yace “Maryam, there’s a way to get her back AbdulMajeed be ce komai ba don zuciyar shi na zafi, Mommynsu bata jin shawara, dole abunda take so zaayi,suna haka ne Nanah ta shigo da gudu tana kuka, ba ta fada ko ina ba sai kan AbdulMajid, har sai da Ziyada ta matsa da sauri don k’iris ya rage ta fado kanta,tana kuka tace “My Majeed are you Okay?” tsaki yayi tare da cije baki, Mommy tayi saurin zuwa gunta tana murmushin k’arfin hali tace “Nana, hakuri zamuyi, jikin da sauk’i” Nana ta daure fuska tace “Wasu tsinannun ne suka Mashi haka? Matsiyata, in kudi suke so ba ya basu ba? Har sai sun taba lafiyar jikinshi? Yanzun nan Momcy ke fada min, anfara investigation din?” Mommy tace karki damu an fara, nan ba da jimawa ba asirin su zai tonu” ba tare da k’ara cewa wani abu ta juya tana shafar fuskar Majid, Ziyada ta kauda fuska, Mommy da Daddy suka fice.

 

NewDelhi India

 

Najwa ta bushi iska, hankalinta a tashe, kamar ba jiya Maama tayi Alk’awarin daina kuka ba ma gashi ta cigaba, ranta na k’una ta kalli k’awarta tace

“main kya kar sakata hoon usake aansoo ko rokane ke lie Kaveri? (What can i do to stop her tears Kaveri?)”.

 

Kaveri ta jinjina kai tace “usakee khushee vaapas jaane ke lie ek raasta khojane (Find a way to return her happiness)” Najwa tace “How Kaveri?” Kaveri tace “Everything is easy with the internet(komai na zuwa a sauk’ake ta yanar gizo)” tunanin be taba zuwa mata ba, da sauri ta bude laptop dinta da ke kan gado yana chargy, ta kunna bayan ya kunnu ta sa Modem dinta ta ta shiga Searching a Google, ‘Zaid Sada Abu’ tayi Searching wasu sunaye ta gani da suka fara da Zaid, ko Sada, dayan bayan daya ta dinga bincika amma no match found ake nuna mata, Najwa ta sa kanta k’asa a hankali ta furta “Ya Rahman” Kaveri tace “it means he’s not on any Social Network” “It appears so” inji Najwa, don da yana wani Social networking kamar su ‘Facebook’ ‘Twitter’ ‘Instagram’ da anyi recommending a goggle, kanta ya kulle, sai gaf da Maghrib Kaveri ta tafi gidansu.

 

Najwa bata saduda ba, sai da ta gwada searching ’email’ me dauke da ‘gmail’ da ‘yahoomail’ wani wuri ta sa ‘Zaid Sada Abu’, wani gun kuma ‘Zaid Sada’ duk ba nasara, haka tayi registering facebook ta dinga Searching masu suna Zaid, ta dinga bi amma ba ta samu komai ba, ta gama ta shiga Instagram, duk wani dubaranta ya k’are amma ba wata nasara, haka fa zube kan gado tana hawaye mai dumi, a hankali tace “Ya Rahmanu, what do i do now?” Diary (littafin sirri) dinta ta janyo ta bude ta fara rubutu kamar haka;

 

Dear Diary

 

I am on a mission to stop my Mother’s tears, i searched for my Brother thoroughly through the internet but to no luck,Me zanyi? Ya Zanyi?”

Ta daga kai kamar me tunani, hankalinta ya tsaya a tunaninta na k’arshe, ta san abu ne mai wuya, amma hakan kawai zatayi Allah zai taimaketa, ta cigaba da rubutu “Diary, i’ve decided, i’ll go to Nigeria, I’ll find my brother, and i’ll bring him home, So Help me God, Allah ka bani saa, ka kawo min komai a sauk’ak’e Amin”.. Ta rufe ta mayyar ta gyara kwanciyarta kan gado bayan tayi Addua don yin bacci.

 

Bacci ya k’aurace mata, sam ta kasa bacci, gabanta na ta fadawa, tsoro ya mamaye ranta, amma idan ta tuna abunda take shirin yi zai faranta ran mahaifiyarta, sai ta ji ta samu k’arfin guiwa, tana ji Mahaifanta suka turo k’ofa, da sauri ta rufe ido tayi kamar me bacci, tofeta sukayi da Adduoi suka juya suka fita, Adduar k’arshe tayi tana rok’on Allah ya sa ta iya baccin, ba dadewa ba bacci yayi awon gaba da ita. Asuba ta gari Najwa Sada Abu.

 

KANO Nigeria.

 

Karfe 6:30pm a k’asar Nigeria daidai yake da 10:30pm daidai a k’asar India, Hajjo ta fito daga bandaki dauke da buta a hannu, ta zauna a ganan kewayen idanunta suka kawo ruwa, rabon da taci abinci har mantuwa ta manta,sai Zogalen da take ci, Zogale shine abincinta, Ta siya Zogale, ta dafa ta saida ta kuma ci ma cikinta,ta daga kai ta kalli gidanta, kallo daya zaka ma gidan ka fahimci gida ne mai kyan gaske, amma zaka gane tsohon gida ne, don ba kula ba gyara, Allah ya jik’an Sada, Allah ya gafarta mai, da yana da rai ba zai taba bari ta wulakanta haka ba, Allah yayi wadaran Abba, Arzikki da dukiyarshi bai amfana mai komai ba, wai ace tana da D’a Kamar Abba, wanda sunanshi ya kauraye gidan Talabijin da Radio don dimbin Azzikinshi amma ya wofintar da Uwarshi Mahaifiya, ba komai, Akwai Allah, ko da yake bata fiye ganin laifinshi ba,tunda tun Asali shine mafi soyuwa a gareta,ta So shi kamar ta bashi ranta, gashi kuma Mace ta shiga tsakaninsu tayi musu Iyaka, AbdulMajid din da take gani tana jin sanyi kwana biyu ta bar jinshi, ta zama bata da kowa, ba ta da wani gawa, ina ma Mutuwa zai zo mata yanzu, da ta fi farinciki, sai da ta ci kukanta kafin ta hakura tayi Alwala don gabatar da Maghrib.

 

Porthacourt Nigeria

 

Bayan yayi Sallahr Asuba ya zaro wayarshi tare da chanza simcard, ya latso numbern Hajia Maryam.

Abuja Nigeria

Ringing biyu ta dauka tare da sa lasfika, dama jiran wayarshi suke, a lokacin suna nan zaune gabaki daya a Parlo har AbdulMajid, jiya da su Mommy zasu dawo gida ya saka daru sai da Dr ya sallamesu.

 

Mommy tace “Hello”, Zaid yace ” Hajia Mairo Muna lafiya?ya mai jiki AbdulMajid, naji ance an Sallameshi”. “Uhm” kadai Mommy tace, yace “Ina Kudina?” da sauri tace “ga su nan an hada komai” yace “Good, zaa zo har gida a karba, and Zeenatu will be returned to you” cike da Murna AbdulMajid ya gyada kai don zasuyi amfani da wannan damar su chafke wanda ya zo amsar kudin har ya kaisu ga Ogan su.

Kamar yana gabansu ya sake shuumin murmushin shi yace “Hajia Mairo, barin baku dan guntun labarin wanda zai zo karban kudin, Sunanshi Dogara, Shi ba Musulmi bane, shi kuma ba Christian bane, bai da addini, hasalima bai da wani mamora, yana da Mahaifiya da yarinya mai shekara daya, wahalar duniya ta musu yawa har wata rana da yaga baida amfani a rayuwa yayi alwashin kashe kanshi, cikin ikon Allah sai gani nazo na cece shi na hana shi aiwatar da abunda yayi niyya, na bashi kudi mai yawa nace yaje ya ciyar da Mahaifiyar shi da diyarshi, tun daga nan,he does everything i ask him to, he owes me his life” Zaid ya tsuke muryanshi ya cigaba da cewa “Dalilin da ya sa na baku labarin nan shine, idan har kuka kuskura kukayi gigin setting dina up by informing the police don nace zaizo gida ya amsa, akace zaayi Interrogating Dogara don ya tona min asiri, ba zai ta6a ba, kun son irinsu ba butulu bane, sai dai ku kashe shi, he has nothing to loose don nayi mai Alkawarin kula da Maman shi da diyarshi, kama Dogara will be the biggest mistake of your life, don zan kashe Zeenatu bayan maza 3 sun mata fyade” Mommy da Ziyada suka sake k’ara don ko tantama babu zai iya abunda yace, Mutumin nan be da Imani ko kadan, AbdulMajeed wani irin Zufa ke keto mai, Daddy mai saukin zuciya har ya fara guntun hawaye.

 

Farinciki ya ziyarci Zuciyar Zaid da yaji Firgici tattare dasu, Babban burinshi shine ya k’untata ma Familyn Abba Abu, yayi murmushi yace “So abun nufi shine, Ba zaku ga Zeenatu ba har sai Dogara ya kawo min Kudina, ku ka sa aka kamashi to a bakin ran Zeenatu, So Hajia Maryam, dont mess with me” da sauri Mommy tace “Wallahi we wont, safely zaa maka delivering kudinka” yace “good,6am Dogara zai zo karban Kudin” dif ya latse wayar.

Shiru sukayi gabaki daya kowa da sak’e sak’en zuci. AbdulMajid yace “Mommy, yana wasa da hankalinmu ne, a gaya ma Police” da sauri tace “No Boy, wallahi ba za a gaya musu ba, ba zanyi chacha da rayuwar diya ta ba”. Daddy ya jinjina kai yace “gaskia ne, mu basu kudin kawai” AbdulMajid ya gyada kai,Mommy ta yi Zipping Biggest sized Ghana Must Go da Wani Jakka.

 

6:00am

 

Maigadi ya k’wank’wasa parlorn k’asa, jiki ba k’wari Daddy ya mik’e ya bude, Yace “yadai Bagobiri?” cikin hausanshi yace “Akwai bak’o a waje, nace mishi kuna bacci yace kun san da zuwanshi” kafin Daddy yace komai sai Mommy tayi saurin cewa “Ka barshi ya shigo” da hanzari ya juya Gate.

 

Bayan sun bashi jikkunan kudin,ya loda su a yar motarshi Golf 3, da yake har rakiya suka mai, ba wanda ya mai ko kallon banza, har ya kunna mota zai wuce, a tsorace Mommy tace “zeenatu fa?” Dogara yace “Oga Zaiyi waya, make sure you dont do anything foolish”. Mommy ta gyada kai.

Ya ja Mota ya wuce, su kuma suka wuce ciki suna jiran Tsammani.

“Oga, kudin are in possesion, i’m cleared” daga bangaren Zaid yace “Good, ka zo PH yanzu” “Okay Oga”.

 

11am

“Ki tsaya nan, Mommyn ki zasu zo daukanki, kar kije ko ina kinji? Cewar Idi, Zeenatu baki ya mutu, tace “DonAllah ka kirasu” yace “kar ki damu, zasu zo nan ba da dadewa ba” ya wuce warshi, Tsohon Gidan Mai ne, amma ba kowa, jefi jefi take ganin gilmawan mutane, daga mafaka Idi ke kallonta, kiran Zaid yayi yace “suna Gidan Mai” Zaid yace “i’ll make the Call”

Zai

Wayan Daddy ya kira wannan karon,da sauri ya dauka ganin ba suna, Zaid yace “Kuje Total Filling Station na shehu shagari Way,Zeenatu na chan na jiranku” da sauri suka fita ba tare da an kashe wayar ba, yace “kuyi Sauri temperturen garin da Sanyi kar tayi Mura” Ziyada tace “daniska kamar ka damu” yayi Murmushi, yace “Hello Again Ziyada, i will see you soon” dif ya latse wayar, ta Allah bata ka ba.

Haka suka dunguma cikin motar Daddy, Daddy ke tuk’in.

Ko da suka iso gidan Mai, tana chan ta dunkule guri guda, tana dagowa taga motar gidansu, da tsalle ta tashi, Mommy bata bari an tsaida motar ba ta bude murfin k’ofar ta nufo Zeena, itama da gudu suka rungume Juna suna Kuka, “I’m so so sorry my baby, i wont let anything come between us again” kuka dai zinatu keyi, Ziyada ta rungume k’anwarta, Daddy ma. AbdulMajid yace “Oya lets go home”.

 

NewDelhi India

 

Bayan dawowarsu Makaranta, wurin Vijay Bhaiyya suka nufa, bayan sun gaisa kamar kullum, ta sanar dashi buk’atar ta na zuwa Nigeria neman Yayanta, karon farko yace “sam ba dashi ba” ta dinga mishi magiyan ya taimaketa, yace “Najwa main apane moorkhataapoorn yojana ka hissa nahin hoga (i wont be part of your silly plan)” sai da suka sha mahawara kafin ya amince, don shima yana son yaga Madam Yesmeen cikin farinciki, don sosai take kyautata mai, ya tambayeta idan tana da kudi, tace eh tana da piggy bank guda 5 tun tana yarinya take savings ciki, kuma tana da Sark’a suje su siyar, Kaveri ma tace zata bada nata gudummuwan haka ma Vijay bhaiyya duk sai a harhada, haka dai suka yanke hukuncin gobe za suje Nigerian Embassy don fara neman Visa. Hmm najwa Allah bada saa..

 

Rivers Porthacourt Nigeria

 

Dogara ya iso Lafiya, ya gabbatar da kudadden nan gaban Zaid, Zaid ya bude jakkun nan, kawai sai yaji sam baiyi farinciki ba, to ya amsa Million Goma wurinsu to sai me? Sai me? Miliyan Goma zasu maido mishi Mahaifanshi? Zasu maido mishi Farinciki da ya rasa for the past 19years? Zasuyi making up wahalhalun rayuwan da ya shiga? Miliyan 10 ba abunda zasu mai,Ko Ownership documents din Shares din Familyn Abba Abu wanda dududu ba zai wuce 10% ba cikin dukiyoyinsu? These wont change a thing, harbi yayi da jakkan kudin, yace “ma Dogara ya tafi zai nemeshi” Dogara na fita Zaid ya durk’usa k’asa ya fashe da kuka, Kuka mai ban tausayiai tsumma zuciya,Rayuwarshi tun yana yaro ya shiga dawo mai tiryan tiryan kamar a lokacin komai ke faruwa, yafi awa daya a hakan kafin ya tashi da sauri kamar an mintsineshi, ya share hawayenshi kafin yayi shu’umin murmushin shi, yace ma kanshi “I’ve waited for this my whole life, i cannot be weak now,I’m Zaid Sada Abu, i do what i want and say what i want with no apologies” ya sake Murmushi da ya tuno wani abu “lokaci yayi da zan gana da Nana Asmau Mati Nakowa” ya dauko yar nokia dinshi ya latso Armstrong ringing daya ya dauka yace “Hello Oga” a dakile Zaid yace “Are you tired?” da sauri Armstrong yace “No not for you”, “come over” kadai yace”.

 

Bayan Arstrong yazo suka shiga Mota suka dau hanya, sai da suka kusa fita cikin gari Armstrong yace “ina Zamu?” a takaice Zaid yace “Keep Driving”. Armstrong yayi gum da bakinshi yana Mamakin Zaid, shekararsu bakwai tare amma kullum ji yake kamar bai sanshi ba,kullum a stranger yake, ga yanda ya fahimce shi; Yana da jin kai,Miskili ne na gidan gaba, da wuya ka ganshi cikin mutane, wani irin baudadden mutum ne, ba ka ta6a gane inda ya dosa, baida yarda ko kadan, bai son tambaya ko kadan, ko aiki ya saka kar ka tambayeshi don me?duk da ya san Waye Zaid da kuma Motive dinshi na destroying Familyn Abba Abu. Chan k’asan mak’oshi Zaid yace “Abuja zamuje”.

 

Hey Lovers! Me Zaid zaije yi Abuja?

 

Shin Najwa zataci Nasaran zuwa Nigeria?

 

Wattpad: @biebeeisa

Please Dont Forget to Vote, Comment and Share.

Thank you.

 

#1love

#ADAY

#nagode

#BibiliciousFreakingFans

#anatare

[11:30, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg4⃣

 

Zeenatu ta basu labarin abubuwan da ya faru tun daga ranan da aka dauketa, ba laifi ta danyi ladab ta nutsu ta bar rawan kai duk da ba a mata wani mugun abun ba, Bayan Sallahr Isha AbdulMajid ya sami Daddy a parlo zaune yake tambayanshi ko akwai wanda yake zargi da yake son ganin bayansu, a iya tunanin Daddy, zuciyarshi ba ta hango mai kowa ba, don shi yana da kyakyawan mu’amala da mutane, Mommy tayi charaf tace “Ai Boy in gaya ma, wannan aikin abokan gaba ne, sun ga Allah ya daukaka Mahaifinku, so suna hassadarshi, shi yasa suka bullo ta haka, amma ta Allah ba tasu ba, zamuyi tightening Security kan ku duka, you shall no go out without an escort” dariyan ba zaiyiwu ba AbdulMajid yayi, yace “sai kace wani dan jariri, aa, i dont need anyone to guard me, Allah shi zai kareni” Mommy ta rude tace “Haba Boy, kar kace haka, ka manta abunda aka maka jiya jiyan nan? Ka manta abunda aka ma k’anwarka? Ko bakaji lokacin da yace ‘he’s coming for us all?’ dole sai munyi taka tsantsan” yace “Mommy, don yayi threatening dinmu sai kar mu cigaba da hidindimun mu? Don kar ya sake mana wani mugun abun? Kar ki manta, duk abunda ya samu bawa daga Allah ne” Daddy yace “haka ne Majeed, amma zaman lafiya yafi zama dan sarki”.

 

“Hello, Nana” a yangance Nana tace”yes, who is this” irin muryar da ke rikita yanmata Zaid yace “Erhm, you shouldnt worry about who am i, rather worry about what i have for you” da mamaki tace “tell me” yace “its about AbdulMajid Abba Abu” tana daga kwance ta mike tsaye tace “meya sameshi?” yace “bakomai, nasan baki da wani burin da ya wuce ki aureshi, i can make that happen”nan da nan ta rude tace “gaya min danAllah” yayi murmushi yace “ki sameni a Silverbird, by 9” dif ya latse wayar. Daga kai tayi ta kalli agogo 8:12pm, da sauri ta fada toilet don yin wanka,da yake guntun tunani gareta, bata tsaya tunanin waye wannan ya kirata ba, kuma don me yake son taimaka mata, sam bata wasa da abun da ya danganci Majeed, don Son shi take sosai tana ji zata iya komai donshi, bayan ta fito daga wanka ta chanchara kwalliyarta,ta dauki makullin motar ta ta bar gidan ba tare da ta nemi izinin kowa ba, ba tare da damuwan dare ba.

 

Nana Asmau Mati Nakowa diyace tilo a gun Senator Mati Nakowa,ita kadai suka haifa,Sen. Mati da matar shi Sayluba sun dorawa Nana soyayyar duniya, suna mata duk wani abun da take so shiyasa take cin karenta ba babbaka, Nana irin Spoilt brat din nan ne wanda bata da me tsawatar mata,ba tajin magana ko kadan,ba abunda ba ta sha na daga kayan maye, ta bi maza ta bi mata,So Daya ne Tak, shi take wa AbdulMajid Abba Abu wanda kwatakwata ba ta gabanshi, sam bata burgeshi banda Mommynsa da take sonta, duk gidan daga Mommy, Zaineema sai Zeenatu ke sonta, ba da wani abu Mommy ke sonta ba sai don ita diyar Mati Nakowa ce, kuma Hajia Sayluba Aminiyarta ce, idan suka hada yaransu aure, zaiyi raising Standards dinsu, Mommy akwai son Abun duniya gashi su ba matsiyata ba, a cewarta da kudi ake neman kudi, bata abu don Allah, sai don neman suna, shiyasa yake abota da matan Senators, Gwamnoni da masu hannu da shuni, garin shishiginta ne ta shige ma Hajia Sayluba, ganin Nana na ma dan Mommy mahaukacin So ne yasa ta neman ma diyarta auren Majeed, Mommy kuwa tace Aure anyi an gama, duk yanda ta bi da Majeed don ya amince da Nana ya k’i, ya bujire mata, tayi tayi amma a banza,Daddy ya sa baki amma Majeed yace “ba kalarshi bace, bata da kamun kai” Shekaru biyu kenan ana bin Majeed ya Yarda yak’i, ita kuma Mommy na da san ‘yaya, bata so ta tilasta mai, tace a bari ya sauko har ya amince da kanshi sai ayi. Wannan kenan.

 

Inda ya mata kwatance a Silverbird din ta nufa, sai dai ta duba bata ganshi ba, ta latso last call dinta, tace “Hello banganka ba, kana ina?” cikin yanayinshi yace “turn around” tana juyowa ko taga mutum a bayanta har tana niyyar bigeshi, ta dan ja baya,kallo ta bishi da shi sama da k’asa,”Wow, guy dinnan ya hadu sosai,na k’wadaitu dashi, don dai Son gaskia nake ma AbdulMajid da shi na aura, amma shi wannan din sai na huta dashi ko so daya ne” cikin sakwan da be wuce goma ba tayi tunanin nan, a zahiri kuma tayi wani shuumin murmushi tace “Ouch, ka ban tsoro” a dakile yace “lets talk shall we?” be jira amsarta ba ya wuce kan kujerun da suke jere a gun ya zauna, ta ta6e baki tace “shi kuma wannan wani iri ne” ta bi bayanshi ta zauna. Ya fara magana ba bata lokaci, “idan kin koma gida, kice da Babanki, da ya ba AbdulMajid gudummuwan 20million,idan ya tambaya na meye sai yace saboda 6arayi sun tare shi suyi robbing dinshi ne, shiyasa ya bashi gudummuwa ya maida abubuwan da ya rasa bayan nan, sai ki ritse AbdulMajid ofcourse bayan kinsha ‘yan abubuwanki in otherwords ‘drugs’ yanda zakiji dadin aikinki, ki danyi making Scene na idan be aureki ba zaki kashe kanki,and kawo kunnenki” ya rada mata wani abu a kunne, shewan murna tayi, wow, meyasa bata taba tunanin hakan ba, lallai this guy gt the brains,har ta fara murnan ta auri Abdulmajid,chan kuma sai ta kalli Zaid tace “Ya Sunanka? And why do you want to help me?” murmushin da ke sa ‘yanmata raina kansu ya mata, yace “i love helping people” tace “dagaske? Maybe zaka iya taimaka na” ya mik’e kai tsaye yace “kiyi abunda nace kiyi, zaki ban labari”.

Ya wuce ya barta Zaune, bata wani damu ba, babban burinta ta mallaki AbdulMajid Abba Abu.

 

Grand towers Hotels

 

Idonshi lumshe cikin kwamin wanka, da alamun yana jin dadin ruwan nan, ya gama da Abuja kuma, be yi zaton abu zai zo mai da sauk’i har haka ba, amma bayan tataunawar shi da Nana ya ga Alamun cin nasara, kara shiga cikin ruwan yakeyi, Jijiyar gefen kanshi tayi tsaye yayin da abubuwan da suka faru a baya suka shiga dawo mai kamar a lokacin suke faruwa.

 

TUNA BAYA

 

Mallam Abubakar Dikko asalin mutumin K’asar Sudan ne, Hijira yayi ya dawo Nigeria don k’uncin rayuww, Mutum ne mai wadatan zuci, yana da hangen nesa, yana da kuma da kirki sosai, ‘Yar fillo Hajjo da ke kawo mai fura yana siya a kasuwa inda yake sai da Azurfa da Zinari ya Aura, Hajjo mace ce mai tsananin Kyan gaske irinsu ne a ke kira da sadaka yalla, a nan cikin Unguwar Rigiyar Zaki ya kama musu gida, Bayan Aurensu Mallam abu ya bude makarantar Allo a k’ofar gidansa yana koyar da Almajiran da basu wuce 10 ba.

Bayan Shekara daya, Allah ya azurta Hajjo da Juna biyu, dadi kamar ya kashe Mallam Abu ji yake kamar ya hadiyeta don dadi, kula ta musamman yake bata, da wuri ma yake tasowa daga kasuwa, bayan Allah ya sauketa lafiya ta sa mu Danta namiji lafiyyaye, ran suna yaro yaci sunan Mallam Abu inda aka mai inkiya da ABBA  haka suka cigaba da rainon Abba har Allah ya k’ara ba Hajjo juna biyu bayan Haihuwar Abba da wata 1, ji take kamar tayi kuka amma da lallashi da bin baki ta hakura, Mallam Abu ya samo mata wata tsohuwa mai kula da ita, bayan wata 9 ta sake haihuwan Namiji, ran Suna yaro yaci sunan Baban Hajjo wato SADA.

 

Wata Goma tsakanin Abba da Sada amma sai kayi zaton shekarunsu daya, don girmansu daya wayon su daya, haka suka dinga Kula da yaransu har suka kai munzalin shiga makarantar boko, wani Firamare na cikin unguwa Mallam Abu ya kaisu, dama tun suna shekaru 3 yake fita da su gaban gidanshi ya hadesu da Almajiran da yanzu sun fi 30 ya koya musu.

A halin yanzu zaka gane banbancin Abba da Sada, Abba yaro ne da ka ganshi kasan dan fari ne, gele ne sakarai, baya maida hankali a karatun shi, Mallam Abu kuwa na hukunta shi tare da wanda ba sa maida himma, haka zaije gida yayi ta ma Hajjo kuka, wai Mallam baya sonshi,yafi son Sada, hankalinta na tashi idan yace hakan, haka zata dinga janshi a jiki tana lallashi don dai ya bar jin wani iri, Abba na da tsokanan fada kuma idan ya jawo fada Sada ke shigan mai, baida wani wayau sai yanda abokan su sukayi dashi. Sada ko yaro ne mai wayau mai himma, ga tattali, duk k’ank’anta kudi sai ya tara su, Abba ko da ya cinye kudinshi zai bi na Sada ya dauke, Sada be magana. Mallam yafi Jan Sada a jiki saboda yafi himma kuma yana son yaron saboda ya san ya kamata. Hajjo kuwa a baiyane take nuna tafi son Abba, don a ganinta Mallam na nuna dayan biyu, shiyasa take jan Abba jiki,ta goya mai baya kan komai, zai lallata abunsa yace na Sada yake so, Sada sarkin hakuri yana gani zata kwace nashi ta ba Abba kamar bashi bane Yaya. Wannan kenan

 

Har Girmansu, suna aji 5 na Sakandire Allah ya ma Mallam Abu rasuwa, wannan Mutuwa ta girgiza duk wanda ya sanshi, saboda mutum ne mai Hakuri da iya zama sa mutane. Abba da Sada sunyi Kuka, ya zamana su ma ke lallashin Mamarta su. Kwanaki sun ja, duk cikin Abokan Marigayi, Mallam Iro kadai ne ke taimaka musu, shi yasan sirrin Mallam Abu, yanzu haka Dukiyoyin Mallam abu da duk wani abunda ya bari na wurin Mallam Iro, a cewarshi sai yara sun gama Sakandiri zaa raba musu su kama Sana’a,  Kafin nan duk wani ci da sha din gidan Mallam Abu  ya koma kanshi, bayan Sun gama Sakandiri ne Mallam Iro ya kira limamai masana rabon gado ya durfanar da komai gabansu yace a raba, haka aka raba mudu Gado kamar yanda addini ya tanada. Cikin Gadon Sada ya dauka wani Fanka yace da Mallam Iro, “baba ga fankan nan ka dinga shan iska” yace “Anya Sada, hakkinka ne” a takaice Sada yace “Na baka” yayi godia Sosai, yace da Hajjo”Hajjo in ba zaki damu ba, ina so in Aureki, ina sonki” fuskar Sada ya nuna farinciki na Abba ya nuna akasin hakan, Jim Hajjo tayi, ba zata k’i Mallam Iro ba saboda kirkinshi ya kuma tsaya musu tun bayan rasuwar Mallam, amma ganin bacin rai kan fuskar Abba ya sata ce mai zatayi shawara. Bayan  fitar Mallam Iro, Abba ya bishi da harara yace “Munafikin Baba” Sada yayi saurin cewa “Subhanallah, haba Abba, meye haka? Mutumin da yake kula damu yana bamu ci da sha kai har sutura in Allah ya hore mai, sai ka nuna bacin rai don yana son auren Uwarmu? Abun farinciki ne Abba” cikin  tsawa yace”dama ba danAllah yake kula damu ba, bana son wannan Auren, Umma danAllah karki aureshi, bana son ki aura kowa, duk munfukai ne, ni zan kula dake har k’arshen rayuwata, zanyi kudi Umma” ba dan tanaso ba tace “dama ba na son Auren kowa, Mallam shine Mijina na farko kuma ma k’arshe, kune farinciki na, kun isheni” Abba yayi murmushi mun gode Umma, girgiza kai Sada yayi ya fita, da wannan aka bar batun Auren Hajjo.

 

Hajjo ta musu maganan fara Sana’a, itama zata fara danwake da shinkafa da mai da yajin sayarwa, Abba ya rufe Ido yace “sam bai yarda ba, ya zaayi ace mamarsu tana abincin saidawa, shi gaskia sam, kuma shi kar a takura mai da fara sana’a,zaiyi idan lokaci yayi” Sada yayi mamakin Hajjo da tace ta fasa, da kuma zuba mai ido da tayi. Burinshi yayi karatu kuma InshaAllah sai yayi, ya gaya musu cewa zai ba Mallam Iro gadonshi ya dinga juya mai, Abba yace kai wallahi baka da wayau nan ya kushe hakan, Sada be damu ba tunda Hajjo bata hanashi ba, haka ya kai ma Mallam Iro Gadonshi, Mallam iro ko ya kira shaidu yace “ko bayan ba raina wannan na Sada ne, zan dinga juya mai da ribar da uwar”. Sada ya gaya mai yanason ya cigaba da makaranta, Mallam Iro yace “ya jira fitowar takardun shi kafin ya shiga jami’a zai tsaya mai InshaAllah” Mallam Iro ya shiga da Sada wurin Koyan Kayan katako (Carpentry work) da abunda yake samu a gun aikin koyan Kafintan ne ya ke siyo Omo,sugar, ashana, da cingam yana k’uk’k’ulawa a tray yana zagayawa, Allah ya dafa mai ya bude mai kasuwa nan da nan ya ke k’arewa yana siyan wasu, sai kuma ya hada tebiri a gun aiki, yazo yana jera kayan Sana’ar shi a kan tebirin k’ofar gida, Abba ko da kudin gadonshi,sai dai ya siya banza ya siya wofi yana kashe ma abokai kudi,ya zama dan fafa.

 

Haka Sada ya k’ware a harkan Kafinta, yana zuwa gidaje yana gyara musu kujeru da makammancin haka, tradern shi kuwa ta cika mak’il don yanzu ya bar tebiri ya buga Container duk da Abba na shiga na daukan abunda yake so,ko a jikin Sada don a ganinshi abunshi na Abba ne, ya zamana cikin Gida ma Sada ke ciyar dasu. Haka Rayuwa ta cigaba har Sada ya ja raayin Abba suka koma Karatu.

 

Ko da suke Jami’a ana garin Kano, Sada da kudinshi sosai, don shi yake hidimar makarantansu da ta gida, Abba k’arya ta k’are tunda gado ya k’are, Sada bai da ganin k’yashi ko mai Abba ke so zai mishi, haka suka dinga karatu ba tare da wata matsala ba, har yau Sada bai bar kafinta ba, don yanzu likafa ta ja har kujeru da gadaje yakeyi.

Bayan Shekaru biyu

 

Ganin shi da kudi da kyaunshi Mairo ‘yar mutanen katsinawa ta ganshi,Asalinsu ‘yar kamaru ce, tana karatu itama a Kano,sosai take sonshi, ta sha kaimai kanta na ya sota, amma shi san bata mishi ba, ya bata hakuri, ashe idonshi ya k’yallo mai Yesmeen shu’aibu yar mutanen Yola, yarinya ce mai hankali itama nan take karatu fannin lafiya, a lokacin ba ko wani Uba yake barin diyarshi mace zuwa karatu wani gari ba, amma da yake Yesmeen na da kamun kai haka babanta ya barta tazo karatu Kano. Ajinsu daya da Mairo, duk yanda Mairo ta so ta shige ma Yesmeen amma ta k’i yarda, don yanayin Mairo da k’awayenta bai mata ba. Haka su Mairo suke jin haushinta don ta fiye girman kai a cewarsu.

A lokacin da su Sada zasu gama Makaranta,har lokacin Mairo bata bar yi mai Wasik’u ba, don har gida take binshi, a lokacin ne ya baiyyana ma Yesmeen son ta da yakeyi,ba wuya ta amince mai. Wannan kenan.

 

Ya kuka ga tuna Bayan?

 

Wattpad : biebeeisa

Please,Biko,donAllah dont forget to Vote, Comments and Share.

 

#1love

#ADAY

#anatare

#Bibiliciousfreakingfans

#nagode

 

BiebeeIsa

[11:31, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg5⃣

 

Ba 6ata lokaci Sada ya sanar ma Mallam Iro ya samu yarinyan da yake so yar mutan Yola ce, yana so ya Aureta kuma,Mallam Iro ya tattara Abokan Mallam Abu su uku suka tafi chan Yola neman aure, ganin Sada ya samu mata, hannu bibbiyu danginsu Yesmin suka karbi Mallam Iro, Baban Yesmin ma yace gwara ayi Auren ta karasa karatun gidan Mijinta, hankalin shi zaifi kwanciya, nan aka Ajiye maganan cewa idan zasu sake dawowa su dawo da Sadaki a daura Aure, Sosai Baba Abba shima ya baza rudun neman mata,Hajjo tace “Abba da ka bari ka fara tara abunda zaka rik’e matar dashi sai kayi auren” ai fa shikenan Hajjo ta gama dashi, don me zata cemai sai ya tara kudi zaiyi aure? Wato shi Sada baa ce mai komai ba da ya tashi Neman Aure, sai shi da ba’aso, dama ya san ta fi son Sada, in banda haka, don me k’aninshi Aure, nan da nan Hajjo ta rude, ta fara lallashin Abba, tace ya samo mata ko diyar wacece zata aura mai shi.

 

Soyyayar Sada da Yesmeen ya zagaye ko ina, da Mairo taji labarin dangin Sada sunje Yola neman auren Yesmin komai ya kwance mata, ta shiga damuwa sosai don sosai take son Sada, Abba ko Allah ya daura mai son Mairo, don Mairo na da kyan jiki, dirin ta na fizgar Maza, ya nuna mata So amma ta nuna mai ita Sada take so, kadan kadan yake jin kishin Sada, amma da yaga cewa bata gaban Sadan sai hankalinta ya dan kwanta, da Mairo taga ba sarki sai Allah, soyayyar Yesmin da Sada sai gaba yake k’arawa, ta maida wuk’aken Har Abba ya samu ya dinga chusa kanshi gunta har ta fara bashi hadin kai ba don ta hak’ura da Sada ba, sai dai don kar tayi biyu babu,a yanda take cema k’awayenta “gwara dan Abu daya, da ace na rasa su duka” har wa yau tsanar Yesmin dank’are a ranta.

 

Bayan Shekara 1

 

Wata 4 kenan da Aurensu duka, Sada na zaune da Yesmin a nan gidan Hajjo, inda ya buge Soro da dakinsa ya gina musu Ciki da Parlo wadattace, Abba ko Hayan ciki da parlo  Hajjo ta kama mai a sharadda, a cewar shi nan Gidansu ya musu kadan ga Sada sa Iyalinshi, amma a zahirin gaskia Mairo ce tace ita ba zata iya zama da Uwar Miji ba, da yake yana sonta sai ya biyo ma Hajjo ta haka.

Duk hidima da shagalin da akayi da biki Sada ya dauki nauyin, harta lefen Mairo shi yayi, abunda ya ma Yesmeen, shi ya ma Mairo, be nuna bambancin ba. Hajjo suna zaune lafiya da Yesmin, yesmin tana girmamata don har wanki take mata, hakan kuwa na faranta ran Sada, yana son Mai kyautata ma Uwashi.

A haka bayan sun gama Makarnata,k’offofukan Alherin Sada sai budewa sukeyi, Don yanzu Provision Stores dinshi Guda Biyu,ya Mallaka ma Abba na K’ofar Gida,a Kasuwa kuwa yana da Shagon Saida Yankunne masu daraja,  Aikin Kafinta kuma be bari ba, don ya zama Ogan kanshi yara ne dashi. Kasancewar ya gama karatu da Matsayi mai kyau, wani Mallamin su ya bashi shawarar zuwa Zaria neman aiki don ya gani a Newspaper ana Neman wanda suka gama Makaranta,ya samu Abba yace “suje Zaria neman Aiki” Abba yace “Wallahi Sada baka da Godian Allah, Aikin me zakaje nema? Kana da Sana’oinka, yo ko ni da Shago na daya a ba zanje neman wani aiki ba, balle kai,Mallam kawai ka zauna tare da matarka, nima hakan zanyi” Sada yace “ai ba laifi idan aka k’ara hanyar Samu” a tak’aice Abba yace “to ba yanzu ba nidai Allah ya baka Saa”. Fir ya k’i bin Sada Zaria, Sada ya tafi da takaddunshi, cikin ikon Allah, aka dauki Sada Aiki, kuma zaa dinga bashi Albashi mai tsoka.

 

Ran Juma’a yake zuwa Kano ya koma ran Lahadi, sosai yake kula da Matarshi da Hajjonsu, harda Abba, duk abunda zai siyo ma gidanshi sai ya siyan ma Abba, dalilin haka ne Abba yayi relying kan Sada,har ya zama raggon Mutum, zuwa da dawowan da Sada keyi na daga hankalin Hajjo, don ta kanji a Radio Hadarin Motoci daga wannan gari zuwa wannan gari, wannan zuwan da Sada yayi ta mishi magana “Yanzu kai Sada, baka jin wahalan tafiya ko? Baka gudun Sharrin k’arfe?” Yayi murmushi yace “Umma, Allah zai kare, tunda ina daku ai dole nake zuwa ganinku” Hajjo ta jinjina kai, tana son Halaiyar Sada, yana da kula sosai ba kamar Abba ba, shi da yake cikin gari sai yayi kwana 8 ko fi bata dorashi a idonta ba, ta nisa tace “Sada, tunda matarka na hutun Makaranta, ka dauketa ku koma chan gun aikin ka, alabasshi in ta koma Makaranta ta dawo” dadi kamar ya shide shi, dama kunya ce ta hanashi tafiya da Yesmeen, yace “Umma kefa?” tace “in dai ta nine kuyi zamanku chan ka maida hankali gun aikinka, amma na san ba zaka iya ba sai kazo ganina da danuwanka, to ko zuwa bayan wata1 haka sai ka dinga lek’omu” yayi godia yaje ya sanar da Yesmin, itama sosai taji dadi don tana kewan Mijinta.

 

Zuwa yayi ya gaya ma Abba shawarar da suka yanke, yace “ai dama hakan yafi, zuwa da dawowan nan akwai matsala, gwara ku koma chan” nan suka danyi fira kadan har ya ke gaya mai Mairo na da juna biyu wata 3, murna kamar me gun Sada,ya zaro dari biyar ya ba, yace “ga goron Albishir” Abba ya yi dariya, yace “ai ka shiga ciki kai mata sannu don tana ta kwaikwai, ba don yaso ba suka shiga gidan Abba, kawai shi har yau hankalin shi be kwanta da ita ba, tana zaune ta tara uban miyau a baki, yace “Madam ya jiki?” cike da yatsina tace “da sauk’i” Allah ya k’ara sauk’i” Abba na murmushi yace “Gobe zaya wuce Zaria da Yesmeen” ta dan yi yastina kafin tace “au haka zata tafi bata mana Sallama ba?” Sada yayi adria yace “maida wuk’an zamu biyo da safe kafin mu wuce” bata ce komai ba, din har yanzu bata daina jin wani abu game da Sada ba, haka suka fita, har k’ofar gida Abba ya rakashi yace “to a gaida Umma da Yesmeen”.

 

Bayan Wata Daya

 

Kwana biyu kenan ta ke jinta wani iri, tashin zuciya da k’warnafi ke damunta, bata yi k’asa a guiwa ba Sada na zuwa ta sanar mai, yace ta shirya suje Asibitin Shika, haka ko akayi, gwajin farko ya nuna tana dauke da juna biyu wata daya, Fadin farincikin Sada bata baki ne, haka ya dinga Addua. Washegari yaje Kano ya sanar ma Hajjo, Hajjo tayi adduan Allah ya raba lafiya, a lokacin Cikin Mairo na da wata huddu, fi’ili da iyayi dai Mairo nayi, ita bata son kaza ba ta cin kaza, kullum sai ta ci tsiren Hansin,shi ko Abba ya ta biye mata.

 

Lokacin da watan Haihuwan Mairo ya tsaya, lokacin Yesmin suka koma Kano, Yesmeen tayi ja sosai, cikinta na wata biyar yayi dabas a jikinta, ta zama abar shaawa, da taje gidan Mairo kai mata Akwatin da Sada yayi na Jariri, baki Mairo ta bude tana kallon Yesmeen, kasa boye hassadarta tayi, ko murnan ganin kayan batayi ba kamar yanda take mamakin chanzawar Yesmeen.

Don bala’i, saboda da damuwa a ranar ta fara nak’uda, bayan yan wasu awanni ta haifo yaronta dan Jazir dashi,daga Asibiti tace ita a wuce Gidan Hajjo da ita,

Hajjo ta tarbeta sosai. Yesmin ta kama zanin da Mairo ta bata wurin haihua ta wanke su tas.

Haka a ka dinga tarairayar Mairo da Jaririnta.Rago Sada ya Siyo, ran Suna yaro yaci ABDULMAJID.

 

Yesmeen ce Rainon AbdulMajid, Allah ya dora mata son yaron, itace wankin kayan kashin shi,har Abba kance mata Ummin AbdulMajid.

AbdulMajid na da wata 4 Yesmin ta haifo danta Namiji,Farinciki gunsu ba a magana, har Yola Sada yaje ya gaya ma Iyayenta,da zai juyo aka hado shi da tsohuwan da zata kula da ita, Akwati guda Sada ya yi ma Uwar Jego da Jaririnta, harta Mairo sai da ya siyan mata Atamfa da Lifaya na fitar suna, ran Suna Yaro yaci ZAID.

 

Jim kadan bayan Haihuwan Zaid Mallam Iro ya rasu, Mutuwar ta girgiza Sada,yayi kuka sosai, Allah sarki tun kafin a rufo shi babban danshi yace akwai dukiyar Sada a gun Mahaifinsu, Sada yace “a bari a gama zaman makoki sai ayi magana” amma shi Dan yace “aa, Baba yace da ya rasu a damka maka Dukiyoyinka” Mukullin Shagon Kasuwa ya ba Sada, kasa karba yayi sai Abba ya karba, haka aka suturce shi aka kaishi gidanshi na gaskia.

 

Sada ya dauki nauyin gidan Mallam Iro don ba zai taba manta Alherinsa gareshi ba. A na haka ne Sada suka tattara ina su ina su suka koma Zaria, Zaid na da Wata daya, sam ba haka Mairo ta so ba, so tayi su zauna tare tayi ta ganni abubuwan da suke ciki.

Bayan 40 ne Sada ya samo ma Yesmeen makarantan Ungozoma(Midwifery),Goggo na nan, Haka suka cigaba da Rainon Zaid.

 

Bayan Shekara Hudu

 

Alhaji Abba Abu ya kalli k’aninshi Alhaji Sada Abu yace “Gida yayi kyau sosai, Allah ya sa Alheri, sai ayi Sauka ku tare” Alhaji Sada ya murmusa yace “InshaAllah, yauwa sai maganan Makarantar Abdul dina da Zaid,tunda bakinsu bude yake ya kamata a sakasu a Boko da Islamiya”  Alhaji Abba yace “to ai sai a saka sun”.

 

Alhaji Sada ya Gina Gidanshi a Sharadda, Gidane hadadde wanda sai wane da wane ke mallakan irin gidan,yana da motarshi mercedez 190, da ya siya Motar nan ne ya ba Alhaji Abba tsohon Motarshi starlet, bayan ya siya musu gidan da Alhaji Abban ke Haya, duk sun zama Alhazawa, don shekaru biyu da suka wuce Alhaji Sada ya biya musu Makka su 5 har Hajjo, sukaje suka rage farali. Kudi gareshi amma ba su rufe mai ido ba, ba su sa ya dau rawanni tsiya ya daura ma kanshi ba don har Yau yana aikin Kafinta. Yana kamantawa duk abunda yayi a gidanshi yana ma gidan danuwanshi, da Mahaifiyarshi. AbdulMajid kuwa kawai zaa ce Mairo ta haifeshi amma shi dan Yesmeen ne, don ko da yaushe yana gunta, Mairo ta bugeshi ta yi fadan ya bar zuwa amma ina, Alhaji Abba kance “ki rabu dashi kowa ya san AbdulMajid dan Yesmeen ne” zuciyarta sai tayi bak’i.

 

Da doki Alhaji Abba ya shiga gidan shi yana k’walawa ma Hajia Mairo kira, da sauri ta fito da tulelen cikinta, tace “Abba Lafiya?” cikin Zumudi yace “daga Sharadda muke, baki ga gini ba, ba kiga Gidan Sada ba, yanda kika san gidan kansila, gida ya hadu wallahi” ya karashe cikin d’oki, “tsuut” ta buga tsaki, da mamaki ya kalleta yace “ya akayi?” tamau ta daure fuska tace “Ya fa? Kai yanzu baka jin kunya? Ace k’aninka na da gidan kanshi kai baka dashi?” shima fuskan ya daure yace “Wannan gidan naki ne?” tace “aa naka ne, amma waya siyan maka?” yace “Sada, kuma lokacin da ya siyan min ya zama mallakina ko shi bai da iko akanshi” “hmm, haka dai kace, amma abun kunya ne ace k’aninka shine Ja Gaba a kan komai, Sada ya maka Fintink’au, kai kana nan zaune gida kamar hoto sai an dauko an baka, kaine fa babba ya kamata ace kai ne Gaba yana bin ka baya, amma ya maida ka sakarai, sai abunda ya dauko ya baka, gashi da Manyan Shaguna har da na saida gwal, gashi da shagin kafintoci, ga Aikin gwamnati yanayi, kai ka k’are a teaching” ran Alhaji Abba yayi matuk’a gun baci, yace “Ke Mairam, ki fita ido na, ai Arzikki na Allah ne, kuma da ni da Sada duk daya ne, tunda Allah ya bashi, kamar ni yaba, ba wani abu kuma zan cigaba da gode mai, ai naga da Arzikkin Sadan ne muke takama ko? Naga har Makka ya kaiki, kuma yake kula da danki kamar nashi, to kinga bansan Sakarcin banza da na wofi, ina sane da duk abubuwan da kikeyi cikin gidan nan, ki kiyayeni, So kike ki samin bak’ar Hassadanku ta Mata, to Allah ya tsareni da yin hassadan danuwana” yana kaiwa nan ya wuce fuuuu ya barta ranta na k’una, kawai dai ta fashe da kuka bakin ciki, jin Zafi da kishin Yesmin ya turniketa, yanzu ya zatayi??..

 

 

Wattpad:biebeeisa

Toh wannan pagen sai aslow, ban samu nayi editting ba, nevertheless Dont forget to Vote, Comment and Recommend.

 

#1love

#ADAY

#anatare

#Bibiliciousfreakingfans

#nagode

 

 

Biebee Isa

[11:32, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg6⃣

 

Alhaji Sada ya dauki AbdulMajid da Zaid ya kai su wani IMAN Nursery and Primary School nan k’asan Sharrada phase 2, Makarantar mai hade da Islamiyya ne, a wurin interview “Whats your name?” Headmaster ya tambayesu, AbdulMajid yayi wuf yace “My name is AbdulMajid Sada Abu” Zaid ko yace “My name is Zaid Sada Abu” Headmaster yace “Wow ashe twins ne” shidai Alhaji Sada bece komai ba, don ba yau ya fara jin Abdul na amfani da Abdulmajid Sada ba, burgeshi yakeyi shiyasa yake sonshi kamar Zaid.  Makarantar mai hade da Islamiyya ne hazak’ar su da basirar su ya sa aka basu Aji biyu(Nursery 2), nan take Ya biya kudin makarantan duka, ya kwashe su ya zube su a Mota suka wuce gidan Baba Abba. Tijara sosai Mairo tayi, wai don me AbdulMajid zaiyi using sunan Sada bayan Ubanshi na da rai, ita sai taje ta chanza mai suna, Wulakanci Sosai Alhaji Abba ya mata, k’ila da ba don cikin da ke jikinta ba da ya maketa. Wannan Kenan.

 

Bayan wasu shekaru

 

Kwanci tashi ba wuya gun Allah, yara suna ta zuwa Makaranta har sun kai Primary 5,idan Abdulmajid yazo na daya, Zaid zai zo na biyu, next term Zaid zai zo na daya AbdulMajid yazo an biyu, haka sukeyi.

Hazak’arsu na ba mutane Mamaki, akwai wani rana da Zaid na kwance kan cinyar Mamanshi, kamar an tsunguleshi ya mike yace “Maa, wani abu kamar Y din da ke kasan wuyana ciwo ne?” tayi murmushi tace “aa Zaid ba ciwo bane, Y ne ni, na maka shi da razor” ya zaro ido, yace “Maa, kin kusa yankani?” tace “aa Zaiduna, akwai dalilin da ya sa na maka, kuma idan na haifa maka k’anne suma zan musu” da alamun tambaya yace “saboda mene?” tace “saboda duk inda aka ganku an san ku ‘yanuwan juna ne” ya dan yi nazari yace “kamar in kanina ya bace,idan mun kai girman Baba da Baba Abba da mun hadu zamu gane juna ko?” mamaki ya bata sosai, kawai tayi murmushi ta gyada kai, yace “to Maa, bazai goge ba?” tace ba zai goge ba har tsufa, baka san ana zane a fuska ba? Ko a ma mutum bille ko a mai fashin goshi, har tsufa ba zai taba gogewa ba, kaima naka kamar haka ne, amma naka a gefen wuya ne na zana maka ‘Y’ a bayan hannunka kuma na zana ma ‘S’,da sauri ya juya bayan hannunshi,yace “ina ‘S’ din?bangani ba” tayi dariya ta cire mai riga ta nuna mai zanen ‘S’ dinshi a wurin da ake Allurar rigakafi, yace “lahh, ya akayi ban taba gani ba?” tace “ya akayi ka ga na wuyanka?” yace “rannan ina duba mudubi nagani” tace “wannan kuma saboda kana sa riga, kuma hankalinka be kawo akwai wani abu a gun ba shiyasa baka taba gani ba” yace “Eh Mami,idan kin haifa min k’anenna, i will take care of them” tayi daria ta saba jin haka daga bakin Zaid, tace “to Zaid kayi ta Addua, Allah ya kawo masu Albarka” Zaid yace “Ameen, Maa ‘Y’&’S’na nufin ke da Baba ko?” tace eh Zaid, kana da kaifin basira, “Allah ya sa har girmanka” yace “Ameen” haka ya cigaba daa mata tambayoyi ita kuma tayi ta bashi amsa.

*

A kullum burin Zaid be wuce yazo gidan Baba Abba ba,yana son Baba Abba, yana son  AbdulMajid,ba don komai yake son zuwa ba sai don k’anwar Abdul Zaineema da ke da shekaru 4, tun tana jaririyarta yake son ta, yana son yara, da yazo yake daukarta, in gaban Hajia Mairo ne sai ta daka mai tsawa, “Donubanka ka ajiyeta, kai yaushe aka gama daukan ka da kai zaka dauki wani? Salan ka kada min ita” dariya kawai zaiyi yace “Mama ai na iya daukanta, zainee bata da nauyi dagaske ba zan kada ta ba” Rankwashi take sake mai a kai, da sauri yake ajiyeta yana yak’e me kama da kuka, gobe hakan bazai hana shi daukan ta ba, baida zuciya ko kadan, so da yawa sai Abdulmajid yace “Zaid, donAllah  kar ka k’ara daukan Zaineema, bana so Mama na rankwashin ka akai, ka kyaleta, nima bana daukanta” Kamar Sakarai dariya kawai zaiyi bawai don yaji ba, abubuwan

da Mairo ke mai, in wani ne ba zai sake marmarin zuwa Gidan ba, gabanshi zata kira AbdulMajid ta bashi wani abun marmari, ta hana Zaid, sai dai AbdulMajid ya bashi a bayan idonta, ko kadan abubuwan da take mai bai damun Zaid, ko don yarinta ne be san kanshi bane oho.

Watarana sun dawo Makaranta, Zaineema na tashi daga bacci ta gansu suna wasa, da gudu ta dauko Zani ta nufo Zaid dashi, da yake itama sosai take son Zaid, cikin gwarancinta take cewa “Zaid, Zaid ka min babu” tashi yayi daga wasan da sukeyi da AbdulMajid, yace “Zo in goyaki” AbdulMajid yace “danAllah kazo mu cigaba da wasan mu, Zaineema kai ma Mama zanin ta goyaki” Ina Zaid beji ba, ya durk’usa ta hau ya zo daura zani kenan Zaineema ta subuce mishi ta fadi gwaram a k’asa, wani irin Ihu tayi wanda da ta ja ihun, sai da tayi seconds kafin ta sake shi, Zaid tuni ya kidime, nan da nan ya fara kuka, AbdulMajid yayi saurin zuwa ya dagota, yana cewa “sai da nace miki kije Mama ta goyaki,yi shiru” ina sam Yarinya ba tayi shiru ba, ihu takeyi sosai. Zaid ya kasa motsi, kuka yakeyi yana bin AbdulMajid a baya suka yi cikin Gida, daga ciki Mairo taji kukan Zaineema, da gudu ta fito, mai ya faru? AbdulMajid yace “Faduwa sukayi da Zaid” ba ta tsaya jin meye ba’asin ba ta hau Xaid da duka, duka bana wasa ba, dukan da ko kai babba akayi ma irinshi sai kaji jiki, balle yaro dan shekara 9, AbdulMajid ya dire Zaineema k’asa yaje yana kama hannun Mamanshi, saidai ta hankade shi, kuka sosai sukeyi duka su ukun, Zaid yana ta kuka har muryanshi ya dishe, kiyi hakuri “Mama, ba zan sake daukanta ba” ina Mairo bata bar dukanshi ba, duk fushi,kishi, jin zafi, hassada, da bak’incikin Yesmin da Sada da ta ke ta fa dashi fiye da shekaru goma, Mairo ta fanshe shi a jikin Zaid yau. “Kashe min ita zakayi? Eyi?in ta mutu ya zakayi? Zaka iya biyana? Ko an gaya maka juyar uwarka zata iya haifa man wata?(Tun bayan Zaid, Yesmeen ko 6atan wata bata sakeyi ba, Mairo ko kafin Zaineema, 6arinta 3, sa ma kanta damuwa da hassadar Yesmin ke barar da cikin).

Kamar daga Sama, Allah ya jefo Alhaji Abba, da alamu duk maganganunta a kunenshi, da gudu yaje don ceton Zaid, harda Mari lafiyayye ya ba Mairo, a razane ta kalleshi, yace “ba tun yau ba na san kin tsana Zaid, ko me ya miki wannan dukan yafi k’arfin shi, Allah zai saka mai” ya dauki Zaid ya sa6eshi a kafada, yayi lamo jikin Baba Abba, yana kuka a hankali, AbdulMajid na kuka ya bi Babanshi a baya. Bakinciki ya turnik’e Mairo, itama daukar Zaineema tayi tana mulmula mata goshinta da ya dan kumbura, amma har yanzu bata daina kiran “Zaid ba”.

 

Gidan Hajjo Baba Abba ya wuce dasu don chan ya baro Yesmin, a Mota AbdulMajid ya gaya mai abunda ya faru, girgiza kai yayi yace “Mairo akwai Azzaluma, kayi hakuri Zaid Allah zai saka maka” yanda ya shiga da Zaid a hannu ne ya sa Yesmin faduwar Gaba, Alhaji Sada na nan shima zuwanshi kenan daukan Yesmin.

A tsorace suke su duka 3, Hajjo tace “lafiya? Me ya samu Zaid din?” karaf AbdulMajid yace “Mamanmu ce ta dukeshi don sun fadi da Zaineema” Yesmin ta kawar da kai don jin ba’asin dukan, ba tun yau ba ta ke lallashin shi kan hakuri da daukan Zaineema sai ya girma, amma bayaji, rai a bace Hajjo tace “sai ta bugeshi? Da gangan zai kadata ne? Meyasa Mairo bata da tausayine? Anya kuwa Abba, anya nan gaba zaa je gidanka?”. Zuciyar Sada duk ba dadi yace ” Aa Umma, ai laifi yayi, don ta hukuntashi ba wani abu bane, shima ina shi ina daukan Zaineema” Alhaji Abba yace “Sada Maryam bata da kirki, hakuri na ya k’are, wallahi nagaji da ita, ta maidani sakaran Namiji, don taga ina mata shiru-shiru, zan sauwak’e mata gaskia”. Hajjo tace ” ka sawwak’e mata, tayi hankali” da Sauri Sada yace ” Aa danAllah, hakurin zaka cigaba da yi, da Nasiha da lallami zata daina InshaAllah ” Hajjo ta kumbura tayi fam ba tace komai ba. Sada ya da cigaba da bashi baki har ya hak’ura,  kafin yace da Yesmin “Ki shafe shi da Robb, ai sai ku tashi ku tafi kafin Maghrib yayi, AbdulMajid mu tafi gida” Abdul ya mak’e kafada Alhaji Abba ya gane nufinshi, cikin bacin rai yace”zaka zo mu wuce ko sai na sa6a ma” Alhaji Sada yace “kasan dai ba zai yarda ba ko, kai dai kawai ka tafi”.

 

Bayan komawarsu Gida, Yesmin ta dafa ruwan zafi, ta ma Zaid wanka dashi, lokaci zuwa lokaci yake sakin Ajiyar Zuciya, duk shattin hannuwan Mairo a jar fatarshi, muryarsa a dishe yace “Maama, ki haifa min jaririya kinji? Ba zan kada miki ita k’asa ba” wani kuka ya kubce mata, ta rungume danta, tana tausaya mai, tana tausaya ma kanta, ta son Mairo bata sonta bata son danta, Mairo na kishi da ita, Kishin Sauri wanda hausawa kece ma yafi Kishin kishoyoyi masu auren Miji daya Zafi (Kishin sauri:Kishin da Matan ‘yanuwa{Matan Ya da Matan K’ani} ke yi da junansu).

 

BAYAN  SHEKARA DAYA

 

Alhaji Sada Abu mutum ne mai Amana da Gaskia,ga aiki da kwazo ba Ha’inci, Alheririkan Allah sai samunshi suke tayi ta k’ofofi da dama,baya ganin k’yashi yake taimaka ma gajiyayyu, duk mai ya ta6a Allah na dafa mishi. Alhaji Abba na aiki a wani board na Trust fund wanda samun aiki a gurin sai kana da mai maka Alfarma, Alhaji Sada ya sama mishi aiki gun, don yana da connections da yawa.

 

Bayan  gama Primary dinsu Abdulmajid, Alhaji Sada ya saka su a secondary boarding, makaranta ce mai ji da kanshi kuma sai dan wane da wane ke ciki wato HASSAN IBRAHIM GWARZO, yanzu haka suna chan JSS1 komai dinsu daya. Cikin Abubuwan Alherin da Alhaji Sada ya samu a shekarar nan sun k’unsa da Tamfatsetsen gidanshi da ya gama ginawa a hotoro, Gida ne Wakeke, wanda zaa iya ginin gida uku ciki,randa ya gama Ginin, rannan Ya Mallaka ma Alhaji Abu gidan ya tashi daga ciki, bayan ya mai gyaregyare duk da ba wani abun da ya samu gidan don du du gidan be wuce shekara 6 ba.

Sannan ya siya Shaguna 5 a bakin Titi ya rushe su ya Gina k’aton Shago inda zai zuba kayan Kafintoci, Shawara yayi da Abba na yana son Fita k’asar waje inda zai Siyo kayan aikin Kafinta, da kattakon su, ya zuba a shagon” nan da nan Abba ya bashi goyon baya na cewa ya tafi Italy su ke da irin kayyayakin nan, kuma ya bashi shawara ya tafi da Yesmin suna dawowa kawai sai su wuce sabon Gida, Sada ya Amince da batun Abba ko da ya gaya ma Hajjo ta sa ma abun Albarka, Yesmin ta ji dadi sosai, zata fita kasar waje, duk da tana zuwa Makka.

 

A ranar da Mairo taji cewa Yesmin zata tafi k’asar waje, Ihu ta saka don ji take kamar tayi hauka, kasa boye bakincikinta yayi har Abba na mata dariar mugunta yace “ba yanda zakiyi uwar Hassada, haka zaki ta kallo har zuciyar ki ta fashe”.

Haka sukaje K’asar Italy sukayi sati biyu kafin sukayi sarin abubuwan da suka kaisu aka turo ta Ship, tsaraba sosai tayi ma Zaid da Abdul komai iri daya, daga Italy suka wuce Makka sukayi Umra kafin suka dawo Nigeria kai tsaye Sabon Gida suka tare.

Washegari zaa yi Waliman bude Sabon Shago da Sabon Gida.

Hankalin Mairo a tashe da taga Babban Gida kamar wannan, Hassadar ta ya motsa ta shiga kushe gidan wai gida kamar gidan yan yankan kai,yan walima suka bita da ido, kallon ko wani lungu da sak’on gidan takeyi zuciyar ta ba dadi, wani zazzabi mai zafi take ji, zuciyarta  bata farfado daga tashin hankalin da ta shiga ba aka dunguma a kaje Sabon Shago. Daga nesa ta hango Wani katafaren Gini wanda ya k’awatu da hasken Fitila, idonta ya kai ga SADA ABU AND SONS FURNITURES, a tare aka shiga, Alhaji Sada baki har kunne, Alhaji Abba da Yesmin na gefenshi yana nuna ma mutane wurare a cikin shagon, wurin sai kanshin Italian furnitures yake tayi, wurin ya k’ayatu, ga maaikata, baki wangale Mairo ke tunanin yaushe Sada yayi Acheiving  haka,  bata damu da yawan mutanen da ke kallonta ba ta daura hannu a ka tana zubda hawaye, harsada ba zai barta ta sake mintuna ko daya a gun ba, da sauri ta juya ta fita daga shagon, ta tsaida taxi tace a kaita Dorayi.

*

“Hmm kin ban mamaki, wai yanzu akwai abunda zai gagareki Mairo Sani?, duk kaifin basirarki? Har yanzu baki gama da Yesmin ba?” wlh da nice ke da tuni na yarda k’wallon Mangoro na huta da k’uda”Mairo tace”uhmm Wallahi Aliya abun sai a hankali, duk na rasa yanda zanyi,Sada na controlling Mijina, Mijina na k’arkashin shi, sai abunda Sada yace yakeyi, rannan harda marina yayi saboda Sada” Laiya ta rik’e baki, Mari? Mari fa kikace, Dank’ari Mak’ari, nan gaba mugun bugu zai miki ya barki kwance” “ya zanyi Aliya?” Aliya tace “tsaya kiji in baki labari,Mijina ke da Arziki duk cikin familynsu, kowa ya kwaso shara kan Mijina yake zubarwa, yayi Hidiman Gidanshi, yayi na yanuwanshi,daidai da ruwansha shi ke siyan musu, komai yake musu, ni ko inda akwai abinda na tsana be wuce yanda yake musu bauta ba, don a guna bauta ne yake musu, aiko na yi shige da fice na, na rusa lamarin, yanzu da nike miki magana, Ba uwar da yake musu, ya tara daga ni sai ‘yayana, In gaskia tazo a fadeta, kin ga da Mijinki ne k’anin Mijina da ba zan dinga barinshi yana muku Hidima ba, kowa yaci gashin kanshi, Lallai Yesmin na k’ok’ari da har ta ke bari ya muku Hidima” da sauri Mairo ta katseta, ta san halin Aliya, yanzu zata gaya mata magana tace “Hegia, nima ina mamakin kauda kai irin na Yesmin, yanzu dai gaya min, ta ya kikayi shige da fice har Mijinki ya zama me jin maganarki?” ko shakka Aliya tace “gyara zama ki sha labari, bani kunnenki” nan ta mata bayani a kunne, suka kwashe da daria suka chafe hannu.”Shegia Aliya Bashir, ba Allah a ranki” tace “tsaya nan,kallon ruwa kwado ya miki k’afa” Mairo ta nisa tace “yanzu kina tunanin akwai halin Abba ya mallaki dukiyar Sada gabaki daya?” Aliya tayi wuf tace “tsaflillahi” ke dai kawai ki shirya gobe Asabar na rakaki Marmara.

*

WASHEGARI

K’arfe Biyu da Rabi ya ma Alhaji Sada, Yesmin da Hajjo gidan Alhaji Abba, sun zo daukarsu zasu tafi Visiting dinsu Zaid,dama Alhaji Abba ya shirya,ya fito da Zaineema,Yesmin tace “Zainee ina Mamarki?” Abba yace “Mairo bata jin dadi tun safe, tace a gaida yaran”. “Allah sarki in mun dawo ma dubota” cewar Alhaji Sada, ya ja Mota suka nufa makarantar HIG.

Tana jin tashin Motarsu ta sa6i gyalenta, ta kwashi kudi mai yawa ta kulle gidan ta fice, taxi ta hau ta nufa Dorayi gidan Aliya Bashir.

*

K’aton Carpet aka shimfida a k’asa k’ark’ashin Bishiya, duk suka Zube a k’asa, Sosai Zaid ya rame, dama tunda AbdulMajid ya dan fishi kumari, Zaid kwance jikin Mamanshi, Baba Abba yace “yadai yarona?” AbdulMajid yace “Baba tun jiya Zaid yake ta kuka,kuma yace baisan meke damunshi ba” Hajjo tace “nidai ince bai jin dadi don tun da yazo be yi wani magana sosai ba kuma be dauki Zaineema ba” Sada yace “abunda zai hana Zaid daukan zaineema ba k’aramin abu bane” Yesmin ta kalli danta tana karantar shi, shirushiru ba halinshi bane, a hankali ta lumshe idanunta ta bude tace “Zaid baka da lafiya ne?” Kai ya girgiza, tace to me ya sameka? Yace”Mama ni gida nake so, i want to be with you” tace “haba Zaid, ko term daya ba kuyi ba, kayi hakuri, baga danuwanka ba kuna tare? Kanaso babanka yayi asaran kudin Makaranta?” ya girgiza kai, yace “nidai ku tafi dani yau ku dawo dani gobe”ina so inje gida ne” Baba Abba yace “Zo, ya tashi ya je gunshi yace “Bakason boarding?” ya gyada kai yace “na ma Alk’awari ba zaka dawo 2nd term na, zan chanza ma makaranta a dawo da kai kuda da mamanka” nan ya danji dama a ranshi, abinci Yesmin ta zuba musu duka sukayi lunch, har yanzu Zaid bai warware ba, har Lokacin tafiarsu, ya shiga kuka sosai, Visting dinsu na farko beyi kuka ba, sai wannan, Yesmin hankalinta tashe amma daurewa takeyi balle da ta ga ya mak’alk’aleta yana kuka sosai kamar bazai sake ganinta ba, itama hakan takeji kamar ba zasu sake haduwa ba a hankali ta rada mai a kunne “I love you Zaid, dont you ever forget that, take care of yourself” kai ya daga mata ya sake fashewa da kuka, ya karya musu zuciya duka, Sai da Alhaji Sada ya tsawatar mai kafin ya saketa, sannan ya rungume Babanshi shima, haba Sojan Baba Abba, ka bar kuka mana, bakaji yace zai cireka ba? Ya gyada kai, “maza share hawayenka” ya kalli AbdulMajid yace ku kula da junanku” suka juya suke wuce, Yesmin na waigen danta, sabon kuka yazo ma Zaid ya ruga da gudu cikin makaranta, waiyo ji take kamar ta bi bayanshi.

 

Marmara

 

Mallam danlami yace “Naji bayananki, me kikeso ayi?” ta kalli Aliya, Aliya ta mata alamun kiyi magana tace “Ina so Mijina ya daina min gardama, ina so yayi duk abunda na sashi, ina so yayi duk abunda nikeso, ba ma shi kadai ba, dukkan su, duk wanda nace kar yayi abu, kar yayi, inaso ,su zama mai jin maganata a ko yaushe” Mallam yayi dariya yace “angama sai me kuma?” tace “aa Mallam a fara da wannan, in an ci nasara sai in dawo” Mallam ya daka mata tsawa yace “kina da tantama ne? Kina tunanin aikina baya ci?” da sauri ta girgiza kai, Aliya ta mata nuni da ta badhi hakuri, nan ta sake bashi hakuri, ya hakura ya buk’aceta da ta sake tambayan wani abu, tace “So nake duk dukiyoyin Sada ya dawo k’asan Abba, komai da ya Mallaka ya mallaka ma Abba” yayi dariya yace “ke da kikace bakya son kowa ya maki gardama, ai wannan aikin kine, ke zaki sa shi duk abunda kike so, kuma dole duk suyi abunda kikeso, tashi kije komai zai tafi kamar yanda kikeso, ni aikina ban bada magani, ban bada komai, ni zan miki aikin da kaina ku tashi ku tafi zan fara aiki”. Suka mai Sallama bayan ta Zube mai duk kudin da tazo dasu tace zata dawo bayan aiki.

**    **   **

Ghen! Ghen! And this is just the begining.

 

Hello Bibilicious Freaking Fans, show me love Please Vote and comment.

 

#1love

#ADAY

#Bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

 

[11:32, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg7⃣

 

Komai ya Chanza a ranar nan, Rayuwar su ta chanza a ranar nan.

Mairo na daga daki ta lura da chanjin Abba, da ba ta isa ta sa shi yin komai ba, duk magiyarta in beyi niyya ba bayayi,da ta lura da alamun da Mallam danlami yace mata zata gani, sai tace bari muga in aiki ya fara ci ta bude baki tace “nagaji wallahi, barin huta In miki wanka Zainee” da sauri Alhaji Abba yace “barin mata” tace “to ba dai ruwan zafi, barin tashi in daura” da sauri ya tashi yace “bari na dafa, huta”. Yana fita ta daka tsalle tana murna, ah bari ta ga yanda komai zai tafi cikin kwana biyu kafin ta fara aiwatar da aikinta.

*

Duk yanda take zaton aikin Mallam ya kai to ya wuce nan, sai ga Baba Abba da wanke wanke da shara daki, a cikin kwanaki biyun nan, yanda ka san rak’umi da Akala haka yake binta da duk abunda takeso,sannan taje gidan Hajjo, tace da hajjo ” tanaso ta ci danwake” rannan Hajjo bata dan jin dadi amma haka ta tashi ta jefa ma Mairo danwake tana zaune tana karkada k’afa. A nan ne dai ta tabbatar da aikin Mallam yayi sosai, don haka zata aiwatar da Ayyukanta, Burinta ya kusa cika.

 

Kamar ko yaushe,in Alhaji Sada na gari sai yazo gidan Alhaji Abba bayan Sallahn Asuba, haka yau ma ta kasance, suna k’ofar gida suna fira Mairo ta fito, Abba ta kalla tace “koma ciki” ba musu ya tashi ya shige ciki, Sada da mamakin abun da ya faru, ya dai wayance da cewa “Barka da Safiyya Maman Zaineema” fuskarta daure ta kalleshi ido cikin ido tace “ina important documents dinka? Ina ownership documents dinka na Sada’s furnitures, ina Makullan Shagunan ka da ka ta6a mallaka? Ina duk wani takaddu masu amfanin da ke gareka? Ina suke Sada?” samun kanshi yayi da cewa “wasu na gida, wasu na office, wasu na company” murmushi tayi tace na baka lokaci nan bayan Azahar, ka tattaro min duk wani abu da kasan ka mallaka, duk wani abunda zaka iya dauka, ka dauko ka kawo min,sauran kuma kar ka damu yanzu dai kayi yanda nace”.

 

Yana isa gida ya fara tatare tattare, Yesmin ta farka tace “Papi me kake tattarawa?” da sauri yace “ina zuwa, sauri nake” haka ya kwashe takardun Mallakar supermarkets 3, da Makullansu,har mukullin Motoci 3 duk da na Yesmin, ya wuce Kasuwa,daga nan ya wuce Office kafin ya je Company.

Kafin Azahar tas ya kwashe komai, ji yake ba zai iya jira ba har bayan Azahar, ji yake umurnin da Mairo ta bashi idan ya wuce minti daya ba zai iya rayuwa ba, so sai ya wuce gidan Abba kawai.

Zaineema na ganinshi ta rugo da gudu ta rungume shi, “Baba Sada ka kaini Zaid” dariya yayi yace “karki damu kinji yarinyata, Zaid ya kusa dawowa” Mairo ta murmusa tace “Zainee, je ki kira Baban ku a daki, kice mai Baba Sada yazo” da gudu yarinyar ta shige daki, ta kalli Sada, tace “har ka dawo da wuri haka?” yace “ai ba wuya na gama kwaso su duka” tace yauwa, ta mik’a mai Biro, yace gashi, ina so ka maida sunan duk Takaddun nan daga Sunanka zuwa sunan Abba, a hankali ya amsa biron, ya dinga chanza Sunanshi zuwa sunan Yayanshi jiki a sanyaye,yace “nagama” Abba da sai yanzu ya samu bakin magana yace “Meyasa? Don me zaiyi haka?” ta kalleshi tace shuttup, baka son ka mallaka Dukiyoyin Sada?” yace “ai yana bani dukkan abun da na buk’k’ata, hakan yayi” ta girgiza kai tace “aa, beyi ba, kana son dukiyan Sada” a hankali Abba ya furta ” beyi ba, ina son dukiyan Sada” murmushi tayi ta kallo Sada tace “good, yanzu ka bar komai nan zuwa gobe ka dawo da Yesmin, da kuma Aminnan ka wanda ka yarda dasu su 10, zaka gaya musu ka mallaka ma Abba, dukiyoyinka, zaka gaya musu cewa Abba shi ya gajeka, zaka gaya musu baku san mai zai faru gobe ba, amma kasan ko bayan ranka Abba mai kula da duk wani abun da ka tara ne, yafi ka adani, ya fika kula, ya fika bukkata shiyasa ka mallaka mai komai, Abba zai kula da ku da Al’umma, kana so duk su ba Abba irin goyon bayan da suka baka, and duk wanda ya maka tambaya game da hakan, zakace its your decision,and its final do you understand Sada.” a hankali ya gyada kai yace “na fahinta Maman Zaineema” tace “and kar ka ce ma kowa komai” yace “ba wanda zaiji” ya juya ya tafi tsalle ta daka da ta ga komai ya dawo karkashin Mijinta bari dai gobe tayi ayita ta k’are, har Party zata hada na Celebration, ta kashe ma Abba Ido tace “kayi Celebrating mana” Murmushi kawai yayi.

 

Zaune gabaki daya a parlorn Alhaji Abba, Aminnan Alhaji Sada suna Zaune suna mamakin dalilin tarasu da yayi, don kiransu yayi yace “su hadu gidan Alhaji Abba akwai muhimiyyar maganan da yake son sanar da su”. Bayan sun nitsa duka Alhaji Sada ya fara da Bismillah, yace “nasan kuna Mamakin taraku da nayi anan, ba wani abu bane, na tara ku ne don na gaya muku cewa, Duk Dukiyar da Allah ya Mallaka min, komai da na tara, kasancewar Abba ne ‘Next of Kin’ dina, na mallaka mai komai, na maida komai k’ark’ashinsa”nan ya fara lissafo musu abubuwan da ya Mallaka wanda ya chanza izuwa Sunan Abba, da mamaki suke dubanshi, har Yesmin da ta gama rudewa, bawai don ya mallaka mai take jin Zafi ba, amma ta yanda yace “komai da komai, to saboda me?” ji tayi Alhaji Ashiru yace “Alhaji Sada, komai fa kace, to saboda me?” Murmushi yayi yace “ko bayan ba raina Abba shine Magaji na, shi zai Gaje ni a komai,Wa ya san Gobe? Wa ya san mai zai faru gobe? Nasan ko bayan raina Abba mai kula da duk wani abun da na tara,zai kula da komai, yafi ni adani, ya fini kula, ya fini bukkata, ya kuma fini chanchanta, shiyasa na mallaka mai komai, Abba zai kula da ni da Al’umma gabaki daya, sabida haka ina so duk ku ba Abba irin goyon bayan da kuka bani” Alhaji Sani yace “Amma Alhaji Sada” ds sauri ya dakatar da shi, yace “its my descision, and its Final” duk sukayi gum da bakinsu suna juya maganan a ransu, Yesmin da bata san hawaye na zuba daga idaniyarta ba, ta san this isnt right, something is wrong somewhere, tana kallo Alhaji Sada ya dauki kwallin da ke dauke da da komai nashi ya Mik’a ma Abba, Mairo ta hau tafi raf raf tana cewa “Allah ya tayaka rik’o” Abba yace “Sada, ba zan baka kunya ba, yanda ka yarda dani ka mallaka min komai, inshaAllah zan baka Mamaki, i wont let you down,Allah ya saka da Alheri ya bar zumunci” Sada yayi murmushi yace “bakomai Sada, abu na naka ne, komai yanzu kuma naka ne” suka rungume juna. Ya kalli jama’an dake gurin yace “InshaAllah ran Jummaa zaayi ‘yar gutun walima don taya Abba Murna”. Da haka aka watse

 

Ranar juma’ah aka sha Walima a Company da yanzu Ya koma ABBA ABU & SON’s FURNITURES,inda Alhaji Sada ya k’addamar da taron ya shaida ma Mutane cewa komai yanzu na Alhaji Abba ne. Mairo na jin mutane da yawa suna tsegumin abun, har wata na cewa “ina aka ta6a irin haka? Komai fa ya mallaka mai, anya an bar Alhaji Sada haka kuwa?” dayar tace “me kike nufi?” tace “gaskia wannan aikin asiri ne, ba cikin hayyacinshi yake ba, waye don zumunci zai yi kyuata da hardwork dinshi gaba daya, kuma da ranshi da lafiyar shi, bawai ya ba shi manager ba, gabaki daya fa ya mallaka mai?” dayar tace “gaskia da alamar tambaya,Aikin Asiri ne” hankalin Mairo ya tashi, nan tazo ta musu tatas, ta kore su daga wurin waliman, ba a gama Waliman ba ta wuce Dorayi gun k’awarta Aliya Bashir.

*

“Ina zaton nagama mai wuyan, ashe da yawa mutane sun dago ni”. Aliya tace “Ai muddin Mutane na ganinsu, to tunanin da zasuyi tayi kenan” Mairo tace “anyi baayi ba kenan” Aliya tace “kawai a kiyi mai gaba dayan” Mairo ta kalleta da alamun tambaya tace “Mai kike nufi?” a takaice tace “ki shek’e su duka” Mairo ta gwalo idanuwa tace “kai, aa, ba zan iya ba, rashin imani na be kai nan ba” daria sosai Aliya tayi, tace “aiko ya kai nan, tunda kikayi abunda kikayi, ai Mairo, kwatakwata baki da Imani, hakan kawai ne mafita, in ko ba haka ba, Mutane zasuyi ta surutu har Asirinki ya tonu” Mairo tayi kasak’e tace “yanzu dai meye abun yi?” tace “gobe ki shirya muje gun Mallam sai ya baki maganin da zaki shek’esu” da haka sukayi Sallama suka rabu.

*

“Anya zata iya kisa?” zuciyarta tace “da Asirin ki ya tonu fa?” nan da na Shaidan yayi mata busa, zuciyarta ta bushe ta yanke hukuncin gobe zasu koma gun Mallam.

Jin muryar Abba tayi a Kanta inda yake cewa “Maryam tunanin me kikeyi haka?” a tak’aice tace “tunanin Kashe Sada da Yesmin nikeyi” ya zaburo yace “Saboda mene Maryam? Sun ba mu duk abunda muke da burin samu a rayuwa” tace “hakane, amma zamansu a doron k’asa barazana ce a rayuwata, shiyasa na yanke hukuncin kashe su” da sauri ya rik’o hannunta, “Kiyi Hakuri Maryam, ba sai kin kashe su ba DonAllah, Sada danuwa na ne, kuma ina sonshi sosai” tayi tsuri tana kallonshi, kar fa soyayyar danunwan nan ya bata mata shiri, kar fa Abba ya fara mata musu, a dakile tace “sai ka za6a ko ni ko shi” da sauri yace “ke na za6a uwar ‘yayana, ina sonki, kece farincikina, zan iya rabuwa da kowa don in zauna dake, amma Sada danuwana ne, akwai Babba Alaqa tsakaninmu, ina neman Alfarma da ki barshi raye,in bakya bukatar ganinsu zan sa shi su bar garin,amma kar a kashe su donAllah Maryam” tausayin Mijinta ya kamata amma ta dake tace “in kuma hakan zai bani farinciki fa?” yace “da hannuna zan kasheshi don baki farinciki, amma ina rok’onki da kiyi hakuri” shiru tayi tace “zanyi tunani, har k’asa ya durk’usa yana mata godia”. A Wannan daren bai runtsa ba, kwana yayi yana kuka, tana sane dashi amma tayi banza ta kyaleshi, ainun ya bata tausayi, nan ta yanke hukuncin da safe zata koma gun Mallam.

*

“Mallam yayi dariya, yace “Mairo, kin raina aikin da na miki, aikin da na miki babban aiki ne, zaki iya sa duk wani mai jinin Mijinki abunda beyi niyya ba, kawai fadan yanda kikeso abun ya kasance ne kawai naki” tace “Mallam, yanzu kana nufin duk abunda na sa Sada da Yesmin zasuyi?” yace “da kikace ya mallaka ma Mijinki komai yayi gardama?” tace “haka ne,yanzu dai da nayi niyyan kashesu, amma na fasa, kawai ina so su shiga duniya, chan k’ololon duniya, kar su sake waiwayen inda muke, suyi nesa da har abada ba zamu sake haduwa ba balle wani ya shaidasu, ina so su zama tamakar mattatu a gun kowa” Mallam yayi daria yace “hakan kawai zaki kallesu kice musu, zaki sha mamaki” tace “naji wannan, amma ina so kaima ka k’ara da naka aikin yanda aikin zaifi ci, ko sunan K’asa Nigeria sukaji gabansu zai fadi balle suyi niyyar zuwa” yace “ki tashi ki tafi, baki da matsala, daga ranar da kika sa su suka bar garin,ki k’addara kamar an sa su a k’abari ne an rufe”. Sukayi godia duka suka bar wurin Mallam.

A hanya Aliya ke tambayan Mairo “Shin dansu fa Zaid?” Mairo tace “wannan tsinannen yaron, da yana nan da harda shi duk zaa hada, amma ban iya jira har ya dawo,bari a fara da uwayenshi, ni da hannuna zan murk’ushe shi, ke dai sa min ido”. Aliya tace ” kai Mairo ba Imani” tayi daria tace “gunki na koya komai”.Suka chafe suka saka daria.

 

*

“Na yanke shawara Abba, zaa barsu da ransu, amma zan sa su suyi nisa su bar kasar, ba za su sake dawowa ba” jim yayi gabanshi na faduwa, ta lura da hakan tace “ko ka fi son a kashesu?” da sauri ya girgiza kai yace “a saka su suyi nisa da mu din” tayi Murmushi to tashi muje gidan”.

*

Yesmin na ganin Mairo taji gabanta ya fadi, murmushi ta k’irk’iro tace “Sannunku da zuwa Yaya Abba ina kwana?” yayi murmushi cike da tausayin su yace “Lafiya lau Yesmin” a dakile Mairo tace “ina Sadan?” cikin Sanyin Jiki Yesmin tace “yana ciki” cike da tsana tace “ai sai kije ki kira mana shi” shigewa tayi sai chan suka fito tare, Jikinshi sai rawa yakeyi ina zai sakasu, “sannunku da zuwa, Maman Zaineema ina Zainee?” Abba ne yace “tana gidan Hajjo” “Allah sarki” Mairo ta tashi tayi tattaki har gaban Sada tace “Ina so ka dauki matarka, da wasu ‘yan kudi, ku bar k’asarnan, kuyi nesa da k’asar nan, kar ku sake waiwayen Nigeria, duk inda ka san muna iya haduwa ko ba dade ko ba jima kar kaje gun, wurare kamar Makka da Madina, Ina so ku manta da Mahaifarka, ku tashi ku tafi yanzu” hawaye ya sulalo ma Sada, Abba ma kuka ya fashe dashi, Yesmin da ta daskare tana jin umarnin Mairo gabanta ya fara dukkan chalugude,ta bude baki tace Mairo, me kike ji dashi? Me kike tak’ama da shi da zaki ce mu bar k’asa? Baki da hankali ne?” Mamaki ya cika Mairo, ta ya akayi Yesmin ke kawo mata gardama?kar fa ta bata mata shiri, da sauri Sada ya zo ya ja hannun Yesmin suka shiga daki “hada kayanki” kadai ya iya ce mata, kuka takeyi sosai, tace “haba Sada, nagaji, ba inda zani, ba inda zanje, ina nan, nagaji da cin kashin da Mairo take mana, ina take so mu tafi mu bar Zaid?” da sauri Sada ya dawo gaban Yesmin, ga mamakinta Kuka taga yana yi, ta tsorata sosai ganin bawaye kwance kan idon Mijinta, yace “Yesmeen, i’m not loosing my mind, thing is, ina kasa yi ma Mairo gardama, yanzu maganan na da mukeyi, delay din da nakeyi ban aiwatar da abun da ta sani ba, ina ji kamar ana sara min duk wani gabobin da ke cikin jikina, DonAllah help me, be my strength, ki hada kayanki Yesmin, muje, we’ll come back for Zaid, inshaAllah, i want you to trust me right now” idonta ta lumshe cikin zafi ta tashi, ta hada akwatinta,yace “Nagode Yesmin, i love you” da sauri ya hada komai ya dauki E passports dinsu,ya dauki Akwatinshi da na Yesmin suka fito Parlor inda har yanzu Mairo da Abba na nan zaune, Abba na ganinsu, ya tashi tsaye yana kuka, kasa hakuri yayi sai da ya rungume Sada, Sada yace “mun tafi, Abba, ka kulan min da Mama da Zaid, kace ma Zaid za mu dawo daukan shi for now, we’ll leave” Mairo tayi wani shuumin murmushi tace “zaku samu Jirgin Lagos yanzu, ku tafi, ku bar k’asan, like i said, kuyi nesa da mu, ku bar k’asan, GO and NEVER, come back” gyada kai Sada yayi yace “InshaAllah, ya ja hannun Yemsin suka bar parlorn suna waiwayen Gidan, k’asa Abba ya durk’ushe yana kuka mai tsuma zuciya, kallo daya Mairo ta mai, tace “ka tashi ka bar kuka” kamar wanda akayi programming  ashi tare da share hawayenshi, tace “daga yau wannan ya zama gidanmu” kai kawai ya daga mata alamun ya fahimta.

 

Kwana yayi yana kuka sosai, kuka yakeyi, tsawa ta daka mai tace “kar na sake jin kukan nan” da sauri ya shanye kukanshi kamar karamin yaro,ganin babanta na kuka,Zaineema ta fashe da kuka, hankalin Mairo ya tashi,ta dauka Zaineema ta fita da ita waje ta hau lallashinta, sai da tayi bacci ta kwantar da ita, ta dawo daki, yana ganinta ya firgita ya tsorace, bata ji dadin yanda ta ganshi ba, ta lura tsoronta yakeji, ha’an, ita fa ba haka take son Mijinta ya kasance ba, ba ta son Mijinta ya zama mai tsoronta,bata so ya zama wani sakarai solobiyo wanda sai yanda tayi dashi, bata so ya zama ‘Mijin tace’, amfanin hakan ya wuce, yanzu tana so Mijin ta ya dawo yanda yake da, ta na so su shimfida sabon Rayuwa, taci Alwashin yi ma Mallam Asubanci gobe, don daidaita lamura.

 

Washegari ta nufi k’auyen Marmara, ko gun Aliya bata je ba, Mallam yace “Aiki yayi kyau ko?” tace “eh Mallam, amma ina mamakin yanda Yesmin ta so kawo min gardama” Mallam yace “ai ce miki nayi Masu amfani da jinin Mijinki kadai ne zasuyi abunda kikeso, kamar Uwar Mijinki,danuwan Mijinki, sai yaran Cikinki ke da Mijinki”.”haba nidai ince, yanzu dai Mallam, ina tsoron kar Yesmin ta kawo min matsala, Ina so a sa musu a ransu cewa sun bar Nigeria a ganin damansu, ba su da abunyi a Nigeria, sun bar dansu Zaid wurin Abba,babu abunda zasu dawo yi,duk runtsi ina so ka sa Sada da Yesmin suk’i dawowa, Duk yanda suke son zuwa Nigeria su ka sa” yayi dan zanen shi a k’asa ya dade yana siddabaru sai chan ya dago yace “yanzu suna garin Lagos, na tura ma su Almatsutsi,Sada baida matsala daman, Yesmin din zaa ma aiki, ba su ba zuwa Nigeria” tace yauwa “sai maganan Abba, na kasa ganeshi, kuka yake tayi, ya ki walwala, yanayin yanda nace amma sam bana son shi cikin damuwa, ya ki hakuri da Sada, Ina so a yi mai faraqqu a mance shi tsaf ya mance shi” dariya sosai Mallam yaui kamar boka, ko da yake bokan ne ai yace “wa yace miki Jini wasa ne? Ai ba zaiyiwu ba, kawai abu daya zaki iya yi, zaki sa shi ya yarda cewa sun mutu ne, daga shi har uwarshi, amma babu yanda zaayi su shafeshi daga zuciyoyinsu” tace “to taya zasu yarda sun mutu?” yace “ki kona gidan nan kice suna ciki wuta ta cinye dasu” tace “kai ba zaiyiwu na k’ona gidan nan ba, sai dai wani abu” yace “wannan matsalarki ne kuma, na miki aikin da kikace na Mijinki da Sada da Yesmin su mance da komai, su mance komai Umarninki ne, yanzu dai ki samo hanyar da zaki nuna ma duniya cewa Sada ya mutu kinga ba wanda zai yi mamakin 6acewar shi,daga nan idan Abba ya yarda K’aninshi ya mutu, sai ku fara gina Sabon rayuwanku ba tare da wani Matsala ba”. Ta jinina maganar sukayi Sallama.

A mota take ta tunanin ya zata nuna ma duniya cewa Sada ya mutu?” Salati da ‘yan cikin Motar ke yi ne ya dawo da ita hayyacinta, ta farga ta duba abinda ake ma Salati, Daga nesa ta hango wata Mota hade jikin Bishiya tana ci da wuta, mutane sun kai dauki ana ta watsawa Motan ruwa, amma kamar ana Zuba Petir, sai k’ara ci take tayi. Drivern Motar su Saude yayi parking ‘yan cikin tasin suka fito don su ma su taimaka, da k’yar aka samu aka kashe wutan motar, Mutane biyu ke cikin Motar, da alamu Miji da Mata ne, ba dai a shaidasu don gangar Jikin sunci wuta, Mairo ta tsaya tana ganin ikon Allah, ji tayi wani yace “yanzu ina zamu fara neman dangin Bayin Allahn nan? Ba a shaida komai” wani “yace daga ina suke ne?” “ta hanyar Zaria suka fito kagani” wani yace “yanzu dai mu k’arasa Kano, a shaida ma polisawa”.

*

Ta shiga duniyan tunani, tsuntsu daga sama gasasshe, kilan opportunity ta samu, bari tayi amfani da damar nan, ba zata bari damar ta kubuce mata ba, Mairo ta daddage ta fasa ihu, ta zube k’asa tana birgima,ta nufo Motar kamar zata fada ma gawarwakin da ke shimfide k’asa, wasu maza su ka kamata, kafin kace kwabo mutane sun mata chaaa an zagayeta, ana tambayarta ko ta san su , da kyar aka samu tayi shiru tana kuka tace ” k’anin Mijinta ne Sada Abu da Matarshi” take wurin ya kaure da Salati.

•••••°°°°°°

Ya mu Mata, muji tsoron Allah, kar mu zama masu bauta ma zuciyoyin mu, Zuciya na kai mutum ga halaka, Allah kasa mufi karfin Zukatanmu Amin.

 

Hello Bibilicious freaking Fans,P.S dont forget to Vote and Comment.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

[11:33, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg8⃣

 

Wani Mutumi yace “yanzu kina nufin Alhaji Sada Abu da matarshi ne wadannan?” da sauri ta gyada kai,nan da nan Mutumin ya daura hannu a kai yace “shikenan munyi rashin mutum mai kirki da sanin darajan dan Adam” wani yace “yanzu dai ko a k’arasa da si kano, ko a kira Police, su dauki report a damk’asu ga danginsu a Sallahce su”. Wani ne yace da Mairo ta shigo ya kai ga gida don fada ma ‘yanuwanta, ba musu ta shiga motar suka kama hanyar Kano, Gidan Hajjo suka fara yi inda tana shiga ciki ta sake fashe wa da sabon Kuka, Hajjo ta taso da sauri dama tun jiya take jin wani abu zai sameta ko nata,cikin sanyin jiki take cewa” Mairo, lafiya? Meya samu Abba?” Mairo ta fashe da wani kukan tace “Sada, Allah yayi ma Sada da Yesmin rasuwa, sakamakon hadarin da sukayi, Motarsu ta ci wuta, suka da k’yar aka shaida su ne” kan Hajjo ya shiga juyawa “Inalillahi wa ina ilaihir rajiun” take maimaitawa, “Sada? Yesmin? Sada mai jin kanta?” wasu zafafan hawaye suka soma kwaranyowa daga idaniyarta, Mairo na tayata. Hajjo ta daure tace “Ina Abba?” “yana gida, be sani ba dai” Hajjo tace “Ina tausayin Abba, ina tausayin halin da zai shiha in yaji mutuwar danuwanshi, ku kaini gun Abba, in gaya mishi Sada ya rasu, ku kaini in lallashi Abba, ku kaini in kasance da Abba a yayin da zaiji mutuwar danuwanshi”. Kuka sosai Hajjo keyi, Mairo ta kamo hannunta suka fita daga gidan.

*

Jinyake kanshi ya mai nauyi, he cant remember a thing, tun bayan Waliman da aka gudanar a Abba furnitures, yana ta son tunano wani abu amma ya kasa, to me zai tuna? Me yakeyi a Gidan Sada? Shifa ya kasa tuna komai, kururuwan Mairo da yaji a tsakar gida ya sashi fita a guje, ganin ba Mairo kadai bace harda Hajjo da wasu mata biyu ya sashi karasawa garesu. Gabanshi na dukan uku-uku, da k’yar bakinshi ya lalubo “mai ya faru? Umma meyasa kuke kuka?” Hajjo tayi shahada tace “Abba sai dai muyi hakuri, Allah ya ma Sada da Matarsa rasuwa sakamakon hadarin Mota da ta riskesu a hanyar dawowa daga Kano” “Inalillahi wa ina ilaihir rajiun” ya dinga maimaitawa a ranshi, sai wanda ya ta6a rashin danuwa zai fuskanci halin da Abba ya shiga, dama Sada yayi tafiya ne? Tambayar da yake tama kanshi kenan, harda Yesmin? Allah sarki Zaid, sai da ya tsagaita kukan yace “Ina gawar? “Mairo na kukan munahinci tace ” an tafi a dauko su” Mik’ewa Abba kawai yayi ya shiga toilet.

**

Bayan an kawo Gawarwakin, Abba ya tsura ma Gawar Ido yana kuka, ya kasa shaida danuwanshi ko matarshi, Hajjo Bayan Hajjo ta gama musu Addua,tace “Abba, mutane suna jira ya kamata akai su gidansu na gaskia, in yaso in ka dawo sai ka kira Mahaifan Yesmin ka shaida musu Rasuwar”. Hawayensa ya share ya mik’e zumbur.

Kamar yadda akeyi, nannade su kawai akayi a likkafani ba tare da wanka ba(Saboda k’onewa sukayi, anfiso a rufe su hakan ba tare da wankan gawa ba) aka dauki Gawarwakin nan, aka tafi dasu Mak’abartan k’asan layinsu a k’afa, Mutane ko sunzo da yawa, Manyan Mutane, yan Kasuwa da dai sauran su,haka aka rufe su kamar yadda Addini ya tanada, sannan suka dawo Gida a ka cigaba da zaman karban gaisuwa.

 

Kafin kwana Biyu Mutuwar Alhaji Sada Abu da Matarshi Yesmin ya zagaya k’asa baki daya, don Babban mutum ne, wanda ake damawa dashi a k’asarmu Nigeria,dai cinciridon zuwa gaisuwa akeyi, Manyan Mutane suna ta zuwa ma Iyalan Sada Abu gaisuwa. Kowa yazo sai ya tausaya ma Abba, don cikin yini daya ya zabge ya jeme, su Mairo kamar dagaske, ana ta karban gaisuwa. Tun ranar rasuwar Abba ya kira chan gidansu Yesmin ta Landline ya sanar dasu Rasuwar, Washegari sukazo aka yi ma juna gaisuwa yau kuma suka juya Yola don karban gaisuwa, suma suna zaman Makoki. Wannan kenan.

 

LAGOS Nigeria.

Bayan barinsu Gida, ticket din Jirgi suka siya na Lagos,ko da suka iso, wani katafaren Hotel suka je, kwanan su daya, a halin yanzu duk wata damuwar su ta yaye,kamar an dage su daga K’aya, ba sa jin komai, ba sa tuna gida, sunji kawai sun gaji da Gida be shiyasa sukace zasu chanza Environment, to ina suka dosa? Tambayar da Sada keyi a zuciyarsa kenan, don shi ya k’agara ya bar k’asar nan,fuk wani numfashin da yake daukar wa a Nigeria ji yake kamar ana sassake shi.

 

Yesmeen na kwance kan Gadon Hotel din, tana Kallon TV tashar B4U kamar bata da wani matsala, Sada ya fito daga toilet ya kwanta kusa da ita “Yesmeenah, kina son India, kina ta kallonki” Murmushi tayi tace “Ina son Indian film, ban gajiya da Kallonsu” wani dan guntu tunani Sada yayi,yanda bai san zama a Nigeria, gwara suyi chan da Nesa, irin Asia dinnan, bari dai ya shawarci Yesmin yace “Will you like it if we move to India?” cikin doki tace “Like? I’ll love” sukayi daria, yace “then lets make it Happen” ta tashi da doki suka fita don fara processing tafia India.

Ba kamar yanzu bane da ake shan wahalan Visa and all, nan da nan suka samu ticket din EGYPT AIR, wanda zai sa dasu da k’asar Egypt kafin sun wuce India.

Tafiar ta kasance gobe, kawai Sai Yesmin ta kasa bacci da daddare, zuciyarta ya mata nauyi, tada Sada tayi, ya tashi yace “Yesmeenah lafiya?” ta dan matse k’walla tace “Papi, Zaid fa? Ya zamu tafi mu barshi? I hate thid place, muje Kano mu dauko shi mana” Sada ya tashi zaune, yace “Yesmeenah ba mun gama maganar Zaid ba,ba yana Makaranta ba? So kike mu datse mishi karatu? Zamu dawo mu tafi dashi idan sunyi hutu,Abba da Mairo zasu kula dashi, zai ma fi jin dadin zama dasu ga Zaineema ga AbdulMajid, kar ki damu, zamu dawo mu daukeshi kinji?” shiru tayi don ta kasa gardama mai, ta koma ta kwanta.

Washegari suka bar kasar, suna barinta zuciyarsu tayi musu nauyi, ji sukayi kamar an kawo Boader an saka tsakaninsu da Nigeria.

 

NewDelhi India

 

K’asar ta burgesu sosai, Tun a cikin Jirgi suka hadu da wani Indian Family, suna fira jefi jefi da turanci, inda Sada ke shaida musu “they are new, suna son Gida haka dan Self-contained, Mutum ya shaida masu Shi Landlord ne, yana bada haya, yana kuma saida Gida, Sada yace “yana so ya siya Gida, mutumin yace “bari su isa, sai ya kaisu suyi magana sosai”.

 

Suna isa suka tsaya restaurant suka ci Abinci kafin landlord Vikash Joshi da Matarshi suka shiga nuna musu Gidaje da kudaden gidan a Laptop, nan dai Sada da Yesmin suka ga wani Gida a Sarita Vihar wanda yafi sauran saukin kudi, “We can live here, we can start a new life here” Yesmin ta jinjina kai, sukayi ciniki, inda Vikash ya sanar da su cewa suna iya biyan Kudin rabi da rabi har tsawon Shekara 3, nan da nan Sada ya bada kadan daga cikin kudin in dollars, kafin Suka kaishi wurin chanza Kudi from Dollars to Rupees.

 

Suka shiga Taxi suka nufi Saritar Vihar, chan tsakiyar Gari Unguwan yake, sun dade suna tafiya kafin suka iso Gidan, Unguwa ce shirushiru,  ba za dai a ce ma Unguwan na masukudi ba, dan lowcost ne.

 

 

Komai yaji a gidan, sai dai yayi k’ura, Vikash ya shaida mai, akwai Yaran unguwa da ya fita zai gansu ya sasu tayashi ya basu 50 rupees, yace “to shikenan” zasu tafi Sada yake cema Vikash yana so ya fara aiki, nan ya buk’aci ganin takardun shi, don ya yaba da Sada, da sauri ya dauko mai, Ya dudduba yace “Gobe zaizo ya daukeshi suje gun Aikin, zai taimaka mai” Sosai sukayi ta ma Vikash da Matarshi Godia har suka rabu, Yesmeen  tace “Suna da kirki, na zata zasuyi mana k’abilanci, don naji ana cewa ba sa son bak’ar fata” Sada yayi daria yace “to ke bak’ar fata ce? Kina ganin ki Ja, duk kin saje da Indiyawan” Daria tayi sosai, tace “Allah dai ya taimake mu ka samu aikin nan, nima da zaka barni da na nema aikin” kallonta yayi sosai sonta na shigar shi, yace “Anything for you, in har zaa dace, zan amince ki fara aiki” da sauri ta rungume shi tana murna”.

Fita Sada yayi yace bari ya nemo wanda zasu tayashi gyaran Gida, Yana fita ya ga wasu yara na wasan k’wallo, da hannu ya ya fitosu, su biyu ne maza matasa ba zasu wuce shekaru 18 ba, dama sunga wucewarsu a Motan Vikash sir, sun san sabbin shiga ne, Sada yace “I want you to help me clean my house?” duk sukayi daria, dayan yace “No English, Hindi , Hindi” Sada ya dafe kai ya ja hannunsu suka shiga Gidan, ya musu nuni da su gyara gidan, Wanda ya fi dan wayewan yace “Sweeping?” da sauri Sada ya daga kai yace “Yes sweeping” dayan da ya lura ba indiyawa bane, ya girgiza kai yace ma dayan “su tafi kawai yan pakistani ne, musulmai ne, su tafi kar su taya su komai” dayan ya girgiza kai yace “ba wani abu su tayasu kawai” dayan ya girgiza kai ya wuce ya bar dayan a ciki, dayan ya kalli su Yesmin yace  “Ek Minute” ya fita, Sada ya kalli Yesmin yace “toufa, me hakan ke nufi?” Yesmin tace na daiji wannan yace “(1 minute)”. Kafin suce wani abu sai gashi ya shigo, da tsintsiya da Bokiti da liquid soap, ya kusta kai cikin Gidan, su kuka suka zauna a kasan Bishiya, Yesmin tace ” Ina ganin kamar dayan yace ba zaiyi bane, don naga wani kallon da yake mana” Sada yace “aiko zan ma wannan Alheri Sosai”.

 

Yaron Ya dade yana aiki, ya shiga nan ya gyara, ya wanke chan, komai sai da ya gyara, Aiki dai yayi ba ha’inci, ya fito ya musu nuni da ya gama, suka lek’a, suka ga komai yana shining, Sada yaji dadi sosai, ya bude Wallet ya ciro 200 rupees ya ba shi,200 rupees daidaid yake da Naira dubu 1 a kudin Nigeria, sosai dan saurayin yaji dadi, daga yanda yakeyi zaka san yaji dadi, be iya cewa komai ba sai “thank you, thank you”. Yesmin tayi murmushi tace da Sada “barin ga ko na iya indianci” ta kalli Saurayin tace “Aapka Naam kya hai?(Ya sunanka?)” da Murna yace “Mera Naam Vijhay(Sunana Vijhay)” nan ya shiga rantafo zanttutuka da Indianci, suko sai daria suke tayi.

Vijhay ya rakasu Kasuwa sukayi siyyayan abubuwan bukatarsu, na Abinci, da sauransu.

 

Washegari Vikash yazo ya tafi da Sada Maaikatansu, cikin ikon Allah aka daukeshi Aiki,Vikash yake tambayar shi, “ita Yesmin ba zata fara aiki ba? Ko su a country dinsu Mata ba sa aiki?” Sada yace “sunayi, in sunyi settling itama zata nemi aiki” yace “me take iya yi?” Sada yace mai “Medical Practitioner ce” Vikash yace “Wow, aikuwa zai kaita wani Private Hospital, idan sun mata Interview zasuyi employing dinta”. Ko da ya gaya ma Yesmin yanda sukayi da Vikash taji dadi sosai.

Washegari Vikash yazo ya dauke su suka tafi Indrasptha Appolo Hospital da yake a nan Sarita Vihar. Bayan wani dogon bayani da wasu abubuwa aka dauki Yesmin aiki a Asibitin.

 

Tun daga ranar da suka dawo Unguwar, kullum Vijhay sai yazo yace “room sweep?” sai dai suyi daria, in akwai wani aiki sai Sada ya bashi ko wanki, ko makamancin haka, har suka fara sabawa duk da ba wani fahintar juna sukeyi ba, in ta dafa Abinci tana zuba mishi yaci. Haka Yesmin da Sada suka fara Sabon rayuwa ba tare da wani damuwa ba ko matsi.

 

BAYAN WATA BIYU

KANO NIGERIA.

 

Yau Asabar, yau ‘yan HIG ke hutu, Alhaji Abba Abu da Matarshi da Zaineema ne suka zo Hassan Gwarzo daukan su AbdulMajid, da gudu suka rugo suka rungume Alhaji Abba, Kafin suka rungume Mairo, Zaid ya dauki Zaineema da take ta tsalle tana fadin Zed Zed ko kallon Abdul batayi ba,abunda ya k’ona ran Mairo kenan,wai don me Zainee zata fi murna da ganin Zaid,ba Yayanta Abdul ba, Alhaji Abba yayi daria yace “Ahh, Zaineema baki manta Zaidunki ba, to ku shiga mota mu tafi gida” bayan sun saka Jakkandu cikin Booth, suka shige mota suka nufi gida.

Murna gun Zaid da ya ga an doso Gate din Gidansu, ya k’agara ya ga Maminshi da Babanshi, sosai yayi missing dinsu, Alhaji Abba na parking, Zaid ya bude murfin Motan ya dira ya sa gudu ya na kwala kiran “Maama, Baba, mun dawo” Abdul ma ya rufa mai baya da gudu, gaban Alhaji Abba ya fadi, yana tunanin ta yanda zai sanar da dan k’aramin yaron nan Rasuwar Mahaifanshi,tsayawa yayi yana tunani ya kasa shiga ciki, Mairo ko ta6e baki tayi ta shige ciki.

Ko wani daki da sak’o na cikin Gidan Zaid ya bincika amma wayam, ina Maaman shi, ko suna gidan Kaka Hajjo ne?

A Parlor ya iske Mairo, ya k’arasa gunta yace “Mama, ina Mamana da Babana?” a tak’aice tace “Sun Mutu” Ido ya fiddo, Zaid na da wayau, haba dan JS1 ai ya san Mutuwa ko? Cikin firgici da tsoro yace “Mama danAllah kiyi hakuri, suna ina? Ko sunyi tafiya ne?” ihu ta datsa mai tace “Ajiyar su ka bani?nace maka sun mutu ko?ko baka san mutuwa ba?” hawaye ke zuba a idonshi, kanshi na juyawa, Mamanshi ta mutu? AbdulMajid ma ya fara kuka, Alhaji Abba ya shigo, da sauri Zaid ya k’arasa gunshi yace “Baba Abba, wai Babana ya mutu?da sauri Alhaji Abba ya kalli Mairo, yace ” haba Mairo, yanzu sai da kika gaya mai mutuwar nan? He’s just a kid” tsawa ta daka mai tace “yi min shiru, ko basu mutu bane? Boyeboye na meye?gwara a gaya mishi ya sani tun wuri” Alhaji Abba ya fara hawaye, yace “ba dai ta hanyar nan ya kamata ya sani ba” tace “naje na gaya mai, don ma ban gaya mishi ta irin hanyar da suka mutu ba?” tambayar da Zaid ya mata ne ya basu mamaki, ita dai tasan Zaid yasan ba ta sonshi, bata son Yesmin, ta tsanesu duka amma bata taba zaton wayonshi zai kai ga ya mata irin tambayar nan ba Kallonta yayi ido tsaye yace “Ke kika kashe su ko?” tamkar saukar Aradu Mairo taji abun, haka kurum taji tsoro ya kamata, yaro k’arami kamar Zaid ya sa ta fargaba karo na farko. Baba Abba yace “Zaid, kar kace haka, ka bari kaji, nine Babanka Maryam itace mamanka yanzu, AbdulMajid kuma Yayanka, Zaineema kanwarka, kar in k’ara jin maganar nan a bakin ka” Kuka yakeyi sosai, AbdulMajid ya matso kusa dashi yana share mai hawaye, Zaid ya sa duka hannayenshi ya ture AbdulMajid ya fadi kasa warwas,”Mamanka ta kashe min Mama, nima sai na kasheta in na girma, kuma wannan Gida na ne, sai na koreku duka, bana sonku ku fita ku barmin Gidan Babana, Allah sai ya saku a wuta dukanku” Alhaji Abba ya daka mai tsawa yace “Zaid ka min shiru, baka da hankali ne? Wayace maka mu muka kashesu? Baka san kowa zai mutu ba? Lokacinsu ne yayi, nima da na ji rasuwarsu i acted like you did, nasan kai yaro ne, you wont understand, amma Baba Abba is here for you kaji yarona?” da k’arfi Zaid yace “I hate you all” ya ruga da gudu cikin dakinshi ya danna Jamlock ya fada gado yana kuka mai tsuma rai “Maamaaa, Baaabaa, ku dawo, Allah ka dawo dasu, Allah ka dawo musu da ransu, Allah ba zan iya rayuwa ba su ba, Allah nima ka kasheni” haka yake ta fada har bacci mai nauyi ya dauke shi.

Hankalin Mairo yayi k’ololuwa gun tashi, ta rasa ya zatayi, nan da nan ta kira Hajia Aliya ta landline din gidan, tace mata akwai Matsala, Hajia Aliya ta sanar da ita zata zo bayan Laasar.

 

Ba zaman lafiya cikin gidan, gida kamar gidan rainon yara, Kuka Zaineema, da Abdulmajid keyi, tunda suka ga Zaid na kuka suma suke ta kuka,Hankalin Abdulmajid ya tashi, Allah ya daura mai son Zaid, haka ya k’i cin Abinci gashi yana jin yunwa, shi sai an bude kofa ya shiga gurin Zaid, kuka Sosai suke tayi da abun ya ma Mairo yawa sai ta sa chazar fanka ta zane Zaineema da AbdulMajid kafin sukayi shiru, sukayi baccin dole.

 

Tunda ya tashi bacci yake jin yunwa, rabonshi da Abinci tun wanda yaci a School karfe 9 na safe, gashu yanzu past 4, bude k’ofar dakin yayi zaije kitchen yaji magana K’asa k’asa dakin Mamanshi, cikin sando ya karasa yaji me ake cewa,

“Yanda Allah ya rufa min Asiri, don uban yaron nan so yake ya tona min Asiri, inshaAllah I got rid of Yesmin and Sada for good, sun tafi kenan” Aliya tace “Amma da mamaki, wai haka kurum ya tambayeki ke kika kashesu? Ko kin taba gwada kashesun ne a gabanshi?” “Wallahi Aliya, yanda kikaji haka, nima haka naji, ban taba ba, nima ya ban mamaki” Aliya tace “gaskia akwai matsala, yaron nan zai baki matsala nan gaba,tunda kinji ya fara claiming in ya girma zai kasheku, nan Gidan Babanshi ne,waye-waye, wata rana Allura zai tono garma, gwara tun wuri ki san nayi” Mairo tace “Wallahi na tsorata,yaro ya hargitsa min gida, sai da na zane su Abdul kafin suka shafa min lafiya sukayi bacvin dole, Abba ko tausayin yaron ya sashi fita, bansan ya zanyi ba, Aliya ya zanyi?” tace kawai “ki murkushe shege cikin dare, ko kuma muje gun Mallam ya baki maganin da zai shek’eshi”

Be tsaya karasa jin me suke cewa ba ya fara ja da baya-baya, duk da wasu kalmomin sun mai girma, hakan be hana shi fahintar komai ba, wato sun kashe Iyayenshi, shima zasu kashe shi ko, dile ya ceci kanshi?” a hankali ya shiga dakin Baba Abba, ya ko ci saa Wallet dinshi na kan dressing mirror, budewa yayi ya cire kudin da ke ciki duka ya sa a Aljihu, da sauri ya fice daga gidan a guje, yana gudu yana waigen Bayanshi, Yanayin unguwan shiru, kowa na cikin gidanshi sai da yayi gudu mai nisa kafin ya samu machine, mai machine ya kalleshi yace “ina zaka?” inda zan bar gari, Mai machine din Yace kana da kudi? Zaid ya bude Aljihunshi yace “gasu nan” ganin yawan kudin ne mai machine ya waiga gefe ya ga ba me kallonshi ya fizge duk kudin ya burka machine dinshi yace “yaro koma Gida” Zaid na kallo mai machine ya gudu, Zaid ya sake fashewa da kuka, mutane ba Imani, haka ya cigaba da tafia yana kuka, be sanin inda yake jefa kafanshi, ga Wani Uban yunwa yanaji,har ya fito bakin titi har bayan Sallahn Maghrib, Zaid na tafia, da yaga jiri na dibanshi ya samu wuri ya zauna, daga nesa ya hangi wani Mutum mai kama da Babanshi, ya fito daga wani Supermarket din da a zahiri na Babanshi ne, sai yanzu ya ga nisan tafiar da yayi, cikin zafin nama ya tunkari Mutumin da ke k’okarin sa Ledoji cikin Mota, Zaid ya fada kan K’afan Mutumin, a firgice Mutumin ya dago yana cewa “lafiya yaro?” baki bushe Zaid yace “Babana..” daidai da digowar hawayen mutumin, a ranshi ya maimaita kalmar ‘Babana’, Zaid ya karasa maganar da ta sark’e mai a baki “ka taimakeni” luuu jiri ya dibi Zaid ya fadi k’asa sumamme….

 

Wanene wannan Mutumin?

One word for Mairo,

And Zaid’s journey begins…

 

Hello lovers show some love, Vote, Comment and share..

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

[12:01, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg9⃣

 

Da sauri Mutumin ya k’araso gun Zaid tare da fadin “Ya Salam” waigawa yayi gefe ya ga kowa na ta kanshi don dare ya soma yi, da sauri ya cicibe Zaid ya saka a mota, ya shiga ya Motar shi sai wani Asibiti mai suna Garkuwa Clinic.

Nurses suka shiga da Zaid, nan da nan aka soma taimaka mai,bayan wasu lokkutta, Dr ya fito ya samu Mutumin zaune daga waje, yace “ka kwantar da hankalin ka, stress ne ya ma yaron yawa, mun saka mishi drip. Alhajin ya sauke naunayar Ajiyar zuciya, yace “Alhamdulilah”.

*

Lura yayi da Wallet dinshi a bude kuma a k’asa, da mamaki ya karasa ya dauka, wayam ba ko sisi, yana da tabbacin akwai kudi a cikin Wallet dinnan, kudi ne ko da suka zarce dubu bakwai, abun da mamaki,gun Mairo ya nufa yace “Maryam, waya shigo min daki? Banga kudina ba” tace “ka dai duba, wa zai shigar maka daki? Duk muna nan” sharewa kawai yayi, don ya san kudin na cikin wallet, definitely daukan kudin akayi, to wa ya dauka? Share magaanar kawai yayi. AbdulMajid zaune kamar dan maraya, ba uhm ba uhm uhm, Abba ya dan rausayar da kai yace “Maryam,wai har yanzu Zaid na cikin dakin nan, ya ki fitowa?” baki ta ya6e tace “Yo ya fito? Tunda mu din ne bai san gani? Ga dai Abdul nan yanda kasan ni na mutu be da wani walwala saboda Zaid” Baba Abbs ya mike ya nufi k’ofar yana mita “Haan anyi yaro da taurin kan tsiya, ya fi awa hudu ciki fa, ni yunwan nan nake jiye mai kar ta mai lahani” cikin hali na ko in kula, Mairo tace “Yo ai Yunwa ba k’anwar uwa bace bare na uba, da yaji yunwa zai fito yaci Abinci”. Alhaji Abba yace “bari dai inje in gani, ya shiga k’wank’wasa dakin, ji yayi kamar k’ofar bude take, yana turawa kuwa kofa ta bude, da sauri ya kutsa kai, ya na neman Zaid, shiru, haka ya lalube har toilet ba Zaid ba alamunshi, da sauri ya fito, yace ” Mairo be ciki, wallahi baya nan” Dam gabanta ya fadi, to ina yaron nan zaije? Kar dai ya tafi tona mata asiri ne?” da sauri ta mik’e suka shiga nemanshi duk gidan ba shi ba alamunshi, hankalin Baba Abba ya tashi matuk’a, Mairo ma ta dan tsorata, Baba Abba ya fita k’ofar Gida yana tambayar masu Gadin gidaje ko sunga gilmawar Zaid, duk sukace ba su ganshi ba, Da sauri ya tari taxi yayi gidan Hajjo yana mai rok’on Allah ya sa yana chan.

 

Hajjo ta ji zance bambarak’wai, “Abba ba kai kace min yau zaka dauko su a Makaranta ba?name zaka zo kana tambaya na in Zaid yazo” Cikin rudewa yace “ba a ganshi bane, ba wanda ya san da fitar shi” zumbur ta mik’e tana tafa hannu gami da salati, tun daga nan suke ta baza neman Zaid, har police stations sunje sun bada report anma shiru.

**

A hankali ya bude idonshi ya sauke su a kan Agogon da ke mak’ale a bangon dakin Asibitin k’arfe 6:45am, tab wani irin bacci yayi haka? Ina ne nan? Daga hannu yayi yaji alamun drip, da sauri ya kalli hannun ya ga cannula, sai ya sa Kuka, Zaid ya ga tashin hankali, yayi kuka har ya gaji, sai wurin 7:50am nurse ta shigo, da Murmushi a fuskarta, tace “Good Morning” kai ya rausayar zuwa wani gefe, don kanshi na matuk’ar ciwo, nurse ta kara cewa “ya jikin naka? What do you want?” Zaid yace “I want my Mummy” nurse ta murmusa tace “kar ka damu zasu zo yanzu kaji?” Kuka Zaid ya fashe dashi, irin kuka mai hade da ihu, da sauri nurse ta fita ta kira Alhaji a waya, dama jiya da daddare ya bata mobile dinshi.

*

Bayan zuwan Mutumin ya zauna gaban Gadon yana mai kallon Zaid cike da shauk’i, ya gyara a Zaid zama yaci Abinci, sai bayan da ya gama cin Abinci suke kallon Junansu. Mutumin yayi murmushi yace “Ya Sunanka?” sai da ya maimata so biyu kafin Zaid yace “Zaid Sada Abu” da mamaki Mutumin ya kalleshi, yace “Sada Abu?” Zaid ya gyada kai, Mutumin ya tausaya ma Zaid, don ya san Labarin Sada Abu da Matarshi sun mutu a hatsarin Mota watanni biyu da suka wuce, irin be sanshi ba personally, amma Sada Abu mutum ne mai jamaa in kai baka sanshi ba, wani wanda ka sani ya sanshi, kuma dai labaran mutuwansu da ya dinga zaga k’afafan yada labarai, kama daga Jaridu, Mujallu d.s.

 

Mutumin yace “Sorry, Allah ya ji k’ansu” da sauri Zaid yace “Kasan Baba na?” Mutumin ya gyada kai yace “Mutumin kirki ne, mai kamala, Allah yayi har ya mutu bamu hadu ba”. Zaid ya fara hawaye, Mutumin yace “kayi hakuri kaji? Kowa zai mutu” chan ya nisa yace “Ni zan koma Kaduna yanzu, zan bar note idan an sallameka a kai ka gun danginka” da sauri Zaid yace “Aa, ni ba zan koma gurinsu ba” da mamaki Mutumin yace “don me?” yace “Saboda su suka kashe min Baba da Maama, nima sunce zasu kasheni” Mutumin yace “Aa Zaidu, Babanka Accident sukayi, suka k’one suka mutu, ba wanda ya kashe su” ido tsaye yace “Wallahi maman majeed ce, ai ta gaya min, kuma ta gaya ma k’awarta zata kasheni” nan Zaid ya kwashe komai ya gaya ma Mutumin iya abunda ya sani, da Mamaki ya ke kallon Zaid yana raratabo zance, ya gasgata maganar shi, yayi amanna yaro kamar Zaid ba zai iya k’irk’iro zancen nan ba, Mutumin ya hadiye miyau yae “how old aee you?” Zaid yace “Eleven” “to Mallam Zaid ya zanyi da kai?” “ka tafi dani donAllah, zan bika” da mamaki Mutumin ya ke kallon Zaid, chan yace “No, you can come with me, ba zan iya tafiya dakai haka ba ba tare da sanin kowa ba, zai yi kama da na sace ka, hakuri zakayi ka koma Gida” ido k’ek’esha yace “Ba zan koma gidan ba, in tafiya zakayi ka tafi barni, nima inyi tafiyata” chan kuma ya fashe da kuka yace “ka taimaka min Baba, ni yaro ne” a hankali Mutumin nan ya fara hawaye, ‘Baba’ Zaid ke ce mai, abunda yafi mai dadi, anya zuwan Zaid gareshi ba dalili? Tabbas akwai dalili, kallo daya da ya ma Zaid yaron ya shiga ranshi, maybe Zaid was sent to him to be the son he never had, amma kar Selfish intrest dinshi ya sa shi cikin matsala, hakan zai yi affecting reputation da status dinshi, baya son abun yayi kama da ya ya sato Yaro, amma ya zaiyi da yaron nan? In ya barshi be son hannun wa zai fada ba, ya dade ya na tunani chan yace;

“Zaid, yanzu sauri nakeyi gobe Monday, ina da report din da zanyi a Abuja, a yau nake son zuwa Kaduna har in wuce Abuja, banda time a Kano, yanzu zan tafi da kai Kaduna, Bayan na gama aiki, Zuwa Friday zan dawo Kano, zanyi Bincike na, idan naga abun da ka fadamin k’arya ne, in ka sake ka yarda na kama da k’arya zaka ga abunda da zan maka, da kaina zan kaika gun Mairon ta kasheka, Ido tsaye Zaid yace “na yarda” Mutumin yace “shikenan, barin je in karbo takardan Sallama”. Bayan Likita ya rubuta ma Zaid Magunguna, aka sallamesu, suka kamo hanyar Kaduna. Duk a tsorace Alhajin yake.

*

Bacewar Zaid ya zaga ko ina a cikin unguwarsu, ba ma kowa ya sanshi, ba inda ba a je nemanshi ba, AbdulMajid yayi kuka kamar ranshi zai fita, Daren Jiya sam Hajjo da Abba ba su runtsa ba, Mairo ko da yamma ta faki idanuwa ta fita gun Mallam danliti na Marmara don ya mata aiki, “kar Zaid ya sake dawowa,ko a batar dashi, kai ya ma tura Aljannu su kashe shi,don in ya dawo akwai Matsala” Mallam dan liti yayi daria yace “kar ki damu, gwara a kashe shi a huta, zama ki fi kwanciyar hankali” nan take ta amince, haka ta cika dhi da kudi ta koma Gida, harda ita aka bazama neman Zaid.

Ikon Allah ya hana Mallam dan liti ganin komai game da Zaid,ko menene ke hanashi ganin Zaid ba karamin garkuwa bane, to yanzu in yace da Mairo akwai matsala, zata ga gazawarshi, shi ko be so ya samu matsala da aikinshi, abun Mamaki wai Mallam da Addua Allah kar ya sa a ga Zaid, ko an ganshi to sai dai gawanshi. Hmm Muje dai zuwa…

KADUNA

 

Gida ne Unguwa guda a Mando Kaduna hanyar Airport, da wuya kaga Wakeken Gida mai Girman Gidan, Zaid be tashi cikin talauci ba, amma bai taba ganin Babban Gida kamar wannan ba, gabanshi ya fadi, ya fara nadamar biyo mutumin, kar dai ace dan yankar kai ne, Mutumin ya lura dashi, murmushi yayi yace “Gida na ne, kuma nikadai ke zaune a ciki sai masu aikina” Zaid dai kasa magana yayi.

Horn yayi da gudu maigadi yazo ya bude gate “Sannu da zuwa Oga” cewar Maigadi, Mutumin ya daga hannu Sama ya murmusa yace “Thank you Samuel”. Ya kalli Zaid da yake a tsorace yace ” Mu shiga ciki ko?” Zaid ya bi bayanshi, sai da suka yi dan tafiya kafin suka shigo main gidan, sannu da zuwa ake ta shigowa ana mishi,duk uniform ke sanye jikinsu, kuma abun mamaki duk Maza ne. Mutumin yace “Zaid, muje in nuna maka dakinka” ba tare da yace komai ba ya bi bayanshi, hawa sama sukayi kafin suka zo gaban wani daki,Alhajin ya sa hannu ya bude dakin, bakin Zaid ya fadi k’asa, ido kuri ya ke kallon dakin da akace nashi ne,ko Girman dakin zai kai girman dakin Mamanshi a kano, dakine wanda akayi adon kwalliyan da blue color a hankali ya shiga yana bin dakin da kallo.

 

Muryan Alhajin yaji inda yake cewa “make yourself at home,Zaid,ga TV game, ga TV, idan kana buk’atar wani abu,dakina na gefen dakinka, kazo ka sanar dani, in kanajin yunwa ka kira landline din chan, number 1 shine kitchen, sai ka fada abunda kake so zasu dafa ma kaji?” kai kawai Zaid ya gyad. Mutumin ya fita ya bar Zaid da tunani kalakala.

*

BAYANI;

Alhaji Sadam Abdulbasit wanda aka fi sani bda (Alhaji Sadam Audu)dan asalin k’asar Sudan ne mai shekaru 58, Alhaji Sadam mutum ne mai tarin dukiya, Attajiri ne, tun yana da Shekaru 30 yayi Hijira zuwa Nigeria saboda wasu dalilai nashi, ba ya zama da Mata, a shekarun shi na 58 yayi Aure kusan 20 amma ba wacce ke yin  sati daya a gidan ta ke neman Saki a gunshi, wacce ta dade itace wacce tayi kwana 5, Alhaji Sadam na da wani larura, Maza-Mata ne(hermophrodite) yana da hallitun Maza da Mata. Dalilin da ya sa ya baro Mahaifanshi kenan don Aurenshi biyu suna rabuwa da matan, ba dama ya wuce sai a nuna shi ana yada mai maganganu kamar shi yayi kanshi, kasancewar baida kowa  yasa ya tattaro inashi inashi yazo Nigeria. Haka ma a Nigeria ya yi aure na farko, a ranar ta nemi saki, so da yawa yana biyan mata kudi don su aureshi su haifa mai Yara, wasu saidai su amsa kudi su gudu, wasu kuma da anyi auren su kwashi rabonsu su gudu, Yana matukar son Yara, ya tara Azziki bai da wani burin da ya wuce ace yanzu yana da dan cikinsa, yanason Magaji amma ba alamun zai taba haihuwa.

 

Wasu na ikirarin Kudinshi na tsafi ne, shi yasa da yawa mutane na hana Yaransu rabarshi, duk yanda yake kyautata musu, a cewarsu yana son yara ne don yayi garkuwan kudi dasu. So da yawa in ya ga yaro a waje zai ce “zo ka amsa yaro” yaro sai yace “aa babana yace indaina zuwa gurinka, kai dan yankan kai ne shiyasa kake son Yara” Alhaji Sadam kanyi kuka yana kai ma Allah kukanshi, ya dukufa da zuwa Gidan Marayu yana kula dasu, cinsu da shansu da suturunsu, haka kuma ya hakura da Aure, ya cigaba da kyautata ma mutanen da ke tare dashi, ya kuma maida hankali ga Siyasa don ana damawa da shi a k’asar.

*

Zaid be nemi komai ya rasa ba, amma yini kuka kwana kuka, jiya Alhaji Sadam ya mai Sallam ya tafi Abuja aiki, zai dawo ranar Laraba InshaAllah. Zaid yayi bak’i ya rame, damuwa ta mai yawa, har yanzu yana kukan rashin Mahaifa, kadaici kamar ya kasheshi, ga TV, ga TV game amma ba su ta6a burgeshi ba, rayuwar shi duk ta zama wani kala, Abinci sai cookcook ya matsa mai yaci, kuma be fi yayi cokali biyu ba, wani irin Zuciya Allah ya dora mai Allah shi kyauta.

 

KANO

 

Har sun hak’ura dai da neman Zaid, don yau kwana 4 kenan da bacewarshi, damuwar Mairo daya, yanda Abdulmajid ke damuwa sosai, duk yayi bak’i ya rame.

*

Daga Abuja Kano ya wuce, Unguwar da aka mai kwatance ya nufa, yana zuwa ya ga wasu buzaye na shan shayi kasancewar bayan Maghrib ne, Sallama ya musu, kamshin turarenshi ya tabbatar musu da babban mutum ne, da wuri suka bashi wurin zama. Cikin gurbatacciyar hausarsu suke cewa “Alhaji tambaya kakeyi?” yayi murmushi “ba ku min tayin shayin ku ba” da sauri suka tura mai gabanshi, ba kyama ya kurba yace “wai ni shin me zakuce da mutuwar Mak’ocinku Sada Abu?” dayan buzu yace “ai yanzu daka ganmu haka firan Marigayin mukeyi, munji mutuwan bayin Allahn nan, al’umma gabaki daya, munyi rashi babba” Alhaji Sadam yace “haka ne” amma ya kuka ga mutuwar? Dama tafiya sukayi?” wani daga cikin buzun yace “ai ga Maigadinsu nan” Alhaji Sadam ya maida dubanshi ga Maigadin yace “Allah sarki, Allah ya gafarta musu” “Amin, kaga ranar Wata Asabar da safe, bayan Alhaji Abba da Matarshi sun zo, jim kadan naji hajiya na daga murya, abunda ba halinta ba, nayi mamaki sosai–” Alhaji Sadam ya katseshi yace “wace hajiyar kenan?” yace “Hajia Marigayiya, matar marigayi Alhaji Sada” Alhaji Sadam ya gyada kai yace ina jinka yace “saura kiris in shiga inji ko lafia, sai kuma dai na share don ba hurumina bane, bayan wasu lokkutta sai ga Alhaji da Matarshi dauke da kaya, sun fito zasu bar gidan, Fuskar Hajia yayi Ja alamun tayi kuka, hankalina be ba ni ba, na bude musu k’ofa na musu fatan dawowa lafiya, kuma abun da ya ban mamaki basu dauka Mota ba, a k’asa suka fita” Alhaji Sadam yace “toufa, to sai akayi Yaya?” sai yace “wai sai washegari Hajia Mairo tace sunyi hadari sun k’one kurmus, haka dai aka rufesu, sai kuma wannan Asabar din aka nemi Zaid ko sama ko k’asa ya bace bat, abun ban mamaki kamar almara” Alhaji Sadam ya nisa cikin tunani yace “ina sauran ‘yanuwan Zaid?” “shikadai suka haifa ba shi da k’anne” “yanzu Gadon Alhaji Sada fa?” wani Gado? Ai tun kan Alhaji ya mutu ya maida duk wata kaddarar shi kan sunan Yayanshi, komai ya mallaka ma Yayanshi, gidan nan ne kadai nashi, dashi kadai ya tsira, shima tun ran da suka bar gidan Alhaji Abba da Matarshi sukayi parking suka dawo nan, Alhaji Sada be bar ma Zaid komai ba, komai ya Mallaka ma Yayanshi, nidai nace ban yarda da hakan ba, akwai wata mak’arkashiya” “kamar me fa?” inji Alhaji Sadam, Maigadi yace “nidai bansani ba, amma waye zai sadakas da dukiyar sa gabaki daya? Nifa ko mutuwar nan tsakani ga Allah bana tunanin ta Allah da Annabi ce, nace maka a kafa suka fita, sai cewa akayi sun mutu cikin Mota kuma shi ke tuk’i?” Alhaji Sadam yayi shiru yana tunani yace “Matar Alhaji Abba fa?” maigadi yace “hmm, wannan sai a hankali, tun marigayiya na da rai take kuntata mata, Marigayiya akwai hakuri wallahi, ina sane da komai, bandai chusa kai ne cikin lamarinsu, kuma har ga Allah ina zargin harda sa hannunta a bacewar Zaid, don inaji sunayi da ita, har yana ce mata ita ta kashe Mahaifanshi shima sai ya kasheta, Wallahi duk inaji, abun ban tausayi wai kuma sai ga Alhaji Abba yazo tambaya na ko naga fitar Zaid, nikuma tsakani ga Allah banga fitar shi ba, nan har aka ci nemanshi aka gaji, in kaga Hajia Mairo ba zakace tana da wata damuwar ba, kuma dududu bacewar be kai Sati daya ba, Allah ya sa Zaid na hannun nagari, in zanga wanda ya tsince shi wallahi shawara zan bashi da ya tafi da Zaid ya nesantar dashi daga Hajia”. Nan maigadin ya ta zubo zance, yana basu labarin zargin da yakeyi. Alhaji Sadam ya jinjina kai, ya fahimci komai, ya gano bakin zaren. Nan ya musu Alheri sukayi Sallama washegari ya koma Kaduna.

 

KADUNA

 

Gabaki daya Ma’aikatan Gidan ya tara a Parlon k’asa, kama daga Mai shara, mai wankewanke, mai dafa abinci, direba, Maigadi, mai ba fulawa ruwa, d.s,hawa sama yayi dakin Zaid, yana zaune kan Window yana kallon lambun dake bayan Gidan, ya cire baki yace “Zaid, kazo muje k’asa akwai Sanarwan da zanyi” ba tare da cewa komai ba Zaid ya sauki ya bi bayanshi suk sauk’a kasa, bayan an nutsu Alhaji Sadam ya fara magana kamar haka ;

“Na san kuna da tambayoyin da kuke son yi min game da yaron nan” ya fada tare da nuna Zaid da yatsa yace “a tak’aice Wannan yaron Yaro na ne, ina nufin Da na ne, kuma Magaji na, yau na fadi na mutu dukiya na da abun da na tara duk hi ne ne, sunanshi Zaid, ina so ku mishi duk abunda yake so for he’s your Second Master, ina fatan kun gane?”  da mamaki suka gyada kai alamun “eh sun gane” Alhaji Sadam ya ja hannun Zaid suka haye Sama.

Maaikatan suka fara k’usk’us, ina ya samo yaro har yana ikirarin danshi ne? Ko a gidan Marayu ya daukoshi?, ba su da amsar ba kansu shiyasa sukayi gum da bakinsu don kar zamansu ya k’are a gidan.

*

“Zaid jiya naje Kano, naje Unguwanku, i talked to your Guardman, ya ban labarin komai, i dont know what it is exactly, but from what i heard, ina zargin Matar Uncle dinka, so na yanke hukuncin rik’e ka, ba zan maidaka inda zasu hallaka ba, ka zama dana kamar yanda kaji na fada, you are the Son i’ve never had, zan kula da kai untill my last breath” kasa magana Zaid yayi, ya dai samu kanshi da zuwa ya rungume Alhaji Sadam, Alhaji Sadam ya shafa kanshi, hawaye na fita daga idanunshi, yana jin Zaid a jinin jikinshi, a hankali yace “You are now ZAID SADAM AUDU, you are now my Son”.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

[12:02, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg��

 

Ya cigaba da cewa “You are now my Son, this is your House, all i have is yours kaji?” dan gajeren Murmushi Zaid yayi, a kwanakin nan ba kasafai yake magana ba, zai iya irga maganganun da yayi tunda yazo Gidan, Alhaji yace “Zaid, lets plan your future, zaka koma School, ba zaka cigaba da zama ba karatu ba” a dan tsorace Zaid yace “Bana son Makaranta kuma, zata bi ta kasheni” Alhaji Sadam ya murmusa “you are a very smart and wise boy Zaid, theres a great future ahead of you, zan kai ka Makarantan that noone will ever find you, i will take you far far away, and if they somehow find you, they’ll have to go through me, saboda kai yanzu nawa ne, and they cant take it away, kagane?” a hankali yace “ni sai na kashesu, sun kashe min Iyayena” Alhaji Sadam ya sauko kasa inda Zaid yake, ya kama hannunshi, cikin dabara yace “kar ka damu, idan ka girma, zamu harbesu” Zaid ya gyada kanshi, wai shi nan Alhaji wayau ya mishi beson yara da rik’o ba.

Haka Alhaji suka tafi Supermarket da Zaid, ya mishi Siyayya, kayan sawa, kayan wasa da sauransu.

B A Y A N W A T A D A Y A

Zaid da Alhaji Sadam sunyi wata irin shak’uwa ta so da k’aunar junansu, wani abu dai da zaka fahimta da Zaid shine mugun shirushirun shi, iyakacinshi da maaikata a ko aa, da Alhaji kadai Zaid ke dan fira, har iyau duk dare Zaid sai yayi Kuka kafin yayi bacci.

*

Zaid ya kan tambayi Baba ina matarshi? Sai yayi daria, yace “shi baya da mata” “yaranka nawa?” sai yace “Zaid ne yarona, sai Yarana kasansu ai (Yaran NGO dinshi, yaran Gidan Marayu)” Zaid sai yace “Ina nufin yaranka da ka haifa” sai Baba yayi murmushi sai yace “Ban tana haihuwa ba” Zaid sai yace “to kayi aure mana” sai yace “Zaid mata ba sa so na” sai Zaid yace “Saboda meyasa basa sonka?” Baba sai yace “ba zaka gane ba Zaid, you are too young, idan ka girma, i promise to explain everything to you” Zaid ya jinjina kai yace “kar ka damu ni ina sonka sosai kaji Baban Zaid, baban Yara” Baba sai yaji dadi sosai, yana ganin duk duniya baida wani arzikin da ya wuve Zaid, yana gode ma Allah da Allah ya hadashi da Zaid, don yana matuk’ar sonshi.

* *

Damuwan Alhajin Daya,inda zai kai Zaid karatu, inda wani wanda ya sanshi ba zai taba zuwa ba, ina zai kai Zaid inda ba zai samu matsi da takurar rayuwa ba? Ina zai kai Zaid inda wani mugun ba zai so shi da mugunta ba? K’asar waje zai kaishi, ko ma ya kaishi India? Ya ji kwanakin nan ana maganar makarantun India masu kyau, ya tare Zaid da maganar, maimakon Zaid yayi murna, sai ya daure fuska yace “shi baya son ya bar kasarnan,anan zaiyi karatun shi” Alhaji Sadam yace “Zaid my Son, bana so su maka wani mugun abun, shiyasa zan nesantaka dasu” Zaid yace “nidai i wont leave Nigeria” ya fada yana finalizing maganarshi tare da murtuke fuska. Sam baya son ganin Zaid ya shiga damuwa da sauri yace “Sorry. Ba zaka bar Nigeria ba amma we wont be staying here again,indai kana Kano,Kaduna,Abuja one way or the other, ko ba dade ko ba jima sai kun hadu, kuma idan wani abu ya sameka, i dont know What i’d do, Zaid you wont understand, but i love you, you are all i have now, i dont want to lose you”.

Sosai Zaid ke tausayin Babanshi Alhaji Sadam, he loves him equally amma akwai boyyayen fushin da ke dank’are a zuciyarshi, yana so ko ba komai ya dinga faranta mai rai, amma in ya tuna ya rasa uwa da uba hankalinshi na tashi, in ya tuna babu yanda zaayi ya samu k’anne zuciyar shi na baci,shifa sai ya kashe Maman Abdulmajid itace silar rabuwarshi da Iyayenshi, sai ya kashe Baban Abdulmajid, kai harta Abdulmajid din da Zaineema sai ya kashesu,but Babanshi yace sai ya Girma zasu bindigesu, to yanzu dole ya koma Makaranta, tunda Baba na son yayi karatu he’ll do it for him, a hankali yace “Rivers-Porthacourt,a current afairs shows that, its the largest, Biggest and Widest State in Nigeria” Baba ya danyi guntun tunani yace”a Porthacourt kake son yin karatun?” kai kawai Zaid ya daga, Baba yayi murmushi yace “Porthacourt it is”.

*

A kwana a tashi

 

K A N O NIGERIA

 

Zaune take gaban Dr, Doctor ya shaida mata cewa tana dauke da Juna biyu wata 1, sosai tayi murna, ta sanar da Alhaji Abba, murna dauke kan fuskarshi yace “Allah ya inganta” yace “barinje in sanar da Hajjo” fuska ta daure, in akwai abunda ta tsana be wuce yanda Abba ke rawan jiki kan Hajjo ba, yanzu Hajjo na ci mata tuwo a kwarya, kwanaki cewa yayi “zai dawo da Hajjo nan gidan, sai da Mairo tayi shige da ficenta kafin ya bar maganar dawowa da Hajjo Gidansu, tace”riga Mallam massalaci, meye abun gaya ma Hajjo? Ai ka bari cikin ya fito ko?” dariya kawai yayi yace “ai don tayi addua, ta sa mana Albarka” baki kawai Mairo ta ta6e.

 

NewDelhi

 

Tun shekaran jiya take jinta wani iri, tana jinta ba daidai ba, tashin zuciya na daga cikin abunda take fuskanta, abokiyar aikinta Simi ta lura da ita tace “Mrs Sada, are you Okay?” Yesmeen ta cije le6e tace “i think i’m sick” Miss Simi tace “you should see a Doc, there’s a Doctor for the Staffs, i will take you there”. Miss simi ta bude murya tace da abokin aikinsu ” Bhaiya ham vaapis aaenge(we’ll be back soon)” daga bangarenshi ya amsa.

Ta kamata suka k’arasa dan clinic din staffs a cikin asibitin, bayan ‘yan gwaje gwaje, Likita ya shaida mata tana dauke da juna biyu wata daya, Allahu Akbar, hawaye Yesmin ta fara na farinciki, for the first time in a very long time, shekaru 11 rabonta da haihuwa,nan tayi excusing kanta ta hau keke napep ta tafi gida, kasa hakuri tayi Sada ya dawo daga aiki, ta kirashi a waya ta shaida mai tana dauke da cikin wata 1,Shima dai sai da yayi hawaye, don da ya tsammaci haihuwar sai yanzu Allah yayi, ya godewa Allah yace “gashin nana dawowa” bayan shudewan lokutta sai gashi ya dawo, nan ya tarar da ita tana kuka, da sauri ya k’arasa gunta, “Yesmeenah, Me ya sa kike kuka? Wannan ya wuce kukan farinciki don i can see sadness in your eyes” tsagaita kukan tayi tace “Papi,na tuna Zaid,na damu naga Zaid” yace “Yesmeenah, kiyi hakuri,zamu koma ga Zaid, i promise you, for now lets take care of Zaid’s sibling” rungumeta yayi yana shafa cikin Jikinta wani dadi na sake ratsar shi.

 

Rivers PH

 

Gida ya siyan musu madaidaici 3bedroom a G.R.A Phase 3 Porthacourt, nan k’asan Unguwan akwai wata Private School

Norwegian International School, nan yayi enrolling Zaid duk a suna 2nd term, haka suka dauka Zaid JS2 don ya ci interview din da suka mishi, ba nisa daga Gidansu zuwa School din, tsaf za a tafi a k’afa amma Baba sai da ya samo ma Zaid Drivern da zai dinga kaishi Makaranta yana dauko shi, akwai mai kula da komai na Zaid, ana ce mata Iya, tun daga Kaduna Baba ya taho da ita,sun dade suna aiki tare da Baba, a gidan Marayu take itace kamar matron din Marayun,ganin Zaid ya saba da ita ne kuma tana da kyaun halaye shiyasa ya dauko ta ya kawota nan PH don ta kula mishi da tillon danshi, chan kuma wata tsohuwa tayi replacing dinta.

Duk da dakinshi na nan be kai dakinshi na Kaduna hadewa ba, Zaid be nema wani abu ya rasa ba, kome yake so ana mishi, Iya zata zauna ta ta mishi hira amma ba ya kulata, ya daura ma ranshi wani abu da shi kadai ya san ko meye.

Saboda so da kaunar da Baba ke mishi, haka ya dawo PH da zama, ya kanje Abuja ko Kaduna Aiki amma be wuce kwana 7 yake dawowa PH, yafi zaman PH yanzu, da yake babban mutum ne, haka ya fara bugabuganshi a nan garin PH duk don ya kasance tare da Zaid.

 

Bayan Wasu Watanni

 

Wani Ikon Allah a rana daya Allah ya sauke Yesmeen da Mairo lafiya, Dukkansu Mata suka Haifa, murna gun Mahaifansu ba magana.

A bangaren Mutan India, shagali Sosai mak’ota suka musu don suna shiri sosai, duk wata bidi’ar sai da sukayi duk da Yesmeen da Sada na dojewa,ba wanda ya kai Vijhay murna, don yana san Sada da Matarshi, tunda suka zo Kasar, kullum yana da abinci a gidan, shiyasa son ya shafi Babyn su, Maman wata Kaveri ‘yar wata 8 tafi kowa zak’ewa, haka sukayi Shagali suka tambayi Sada ya sunan baby, yace “su bari sai bayan kwana 7 zai sanar dasu”. Ranar Suna Sada ya yanka k’aramin dabanshi, ya rada ma diyyarshi Suna Najwanatu, NAJWA SADA ABU, anan ne sukayi wani Shagalin, abokan Aikin Yesmin da Sada sunzo da iyalansu,Yesmeen ta samu Gifts me tarin yawa, ta kuma ga mutane, ko a Nigeria ta haihu iyakan mutanen da zata gani kenan, hakan ya faru ne sabida zaman lafiyan da sukeyi da kowa,sun iya zama da mutane, shisa indiawan ke sonsu.

 

A Kano kuwa, banda goggagun mata Yan bariki, ba macen arzikkin da tazo Suna, Suna akayi na yan k’arya, don yanzu burin mairo ya cika, wanda a da be wuce ta zama a bar nuni ba, inda duniya zata san da zamanta, aiko gashi ta zama Matar Baban Mutum, matar Abba Abu guda, Suna akayi sosai kamar Biki, inda Yarinya taci suna ZIYADATU, Ziyadatu Abba Abu.

*

A halin yanzu, Hajjo ta zama abar tausayi, ba dama taje Gidan Abba, sai Mairo ta ci mata mutunci kamar ba Uwar Mijinta ba, Abba kam ba yanda zaiyi, ya kan ba Hajjo hakuri kan cewa ta hakura da zuwa gidanshi shi zai dinga zuwa,tun yana zuwa har ya daina zuwa, ya rasa gane me ke controlling dinshi.

Daga k’arshe dai Mairo ta sa suka koma Abuja da zama kwatakwata.

 

6years later

 

Ba abunda ya chanza na daga Halayen Mairo, bata son kowa rabeta, komai ta samu tafi so taci daga ita sai ‘ya’yanta, son ‘ya’ya kamar me.

 

Bayan Ziyadatu Mairo ta haifi Zinatu.

 

Zaineema na primary 6, wata irin shagwababiyar yarinya ce, duk halin uwarta ta shanye kaf,tun tana k’ank’anuwarta take rashin kunya.

Ziyada kam na da shekara 4, Allah yayi ta mai hakuri, ko Zaineema ta daketa sai dai ta 6oye tayi ta kuka don ta san da Ya Majid ya ganta tana kuka, sai ya duke Zaineema, ita kuma kwatakwata bata san hayaniya.

 

 

AbdulMajid ya zama dan saurayi, dan kimanin shekaru 17 ya gama karatun Secodary dinshi a HIG kano,AbdulMajid be da matsala ko kadan,yaro ne mai kirki,ga taimako da tausayi, Abdulmajid yayi a rayuwa, Abdulmajid is the total opposite of his Mother. Preparation din tafiya Oxford University yakeyi.

 

R I V E R S PH

ZAID

 

 

Zaid Sadam Audu,graduate of Norwegian Secondary School,the most handsome of his set, Zaid Sadam bai da damuwa da kowa da komai, abunda ya sa gaba shi yakeyi, a rana befi yayi magana kadan ba, tun Zaid na da SS1 yake shan kayan maye, irin su maganin tari don kore damuwa, Zaid bai manta burinshi ba, illa son cimma burinshi.

Kowa na gudun Kadaici, banda Zaid, Zaid na son Kadaici,shiyasa da Yamma yayi zai dauka mota yayi waje, tafiya yake na kusan Kilometer dari, ya samu wuri a bakin ruwa ya zauna kawai yayi ta kallon ruwa, yana shan maganin tari.

 

Alhaji Sadam ya shigo Gida da misalin karfe 5:49pm, ya iske Iya zaune tana kallo, da murmushi yace “Iya” tace “Sannu da zuwa Alhaji, ashe kana tafe?” yayi daria yace “ina missing jikanki ne, ko yana gida” tace “kaima ka san zancen,tun karfe 4 baya gida” waya ya ciro daga Aljihunsa, ya latso numbern ‘Son’ sai da ya kusa daina ringing kafin ya dauka, murya cikin kasan mak’oshi yace “Babana” lumshe idanuwa Alhaji Sadam yayi ya bude, yace “Son,i’m home” “Ok” kawai ya iya cewa ya latse wayar.

Iya ta gabatar mai da Abinci, yace sai yayi wanka, ya shiga cikin dakinshi yayi wanka, yana cin abinci Zaid ya shigo da Sallama, farinciki ya ziyarci zuciyan Alhaji Sadam, zuwa yayi ya rungume babanshi “Sannu da zuwa Babana” muryan Baban na rawa yace “Zaid Sadam Audu, have you been drinking?” Zaid ya danyi dan guntun tsaki yace “Babana, bacci zanyi” ya shige daki ya barshi zaune da abinci a gabanshi,duk yaji abincin ya fita kanshi, dafe kai yayi yana tunani, yana so ya ma Zaid magana, amma tunda yace “bacci zaiyi to ya na nufin kar a tadashi daga bacci, zai bari har goben.

*

“Son, ina ta planning kaika Oxford University” cewar Baba, kai tsaye yace “Babana,banaso”da damuwa Baba yace “Saboda me Son?” yace “Babana,i want to be here” duk zatonshi Zaid ya bar wammam taurin kan, yace “Son yanzu ina kakeso?” a tak’aice yace “Uniport” ba tare da ya so ba yace “whatever son wants, he gets” Zaid ya murmusa yace “Nagode Babana you’re the best”.

 

Bayan Shekara Biyu

 

Garin Porthacourt gari ne me zaman kanshi, kazo nazo, ba kalar Mutanen da babu a Garin, Mutanen kirki, Mutanen banza, ba irin sana’ar da ba a yi a Garin. Warri Garine a PH, mutanen Warri sun bambanta da sauran biladam, da kaga d’an warri zaka shaidashi, Warri people sun k’ware da Damfara, Sata, Kisa, Chuwachuwa,419, Kuma sune suka fi yawa a Uniport.

Zaid na ganin mutane kalakala,a shekaru 8 da yayi a PH yana sane da halaiyar Warri People, suna da son abun duniya balle in suka ga akwai kudi hannunka sai su nemi su shige maka, in baka da saa su kwalkwaleka tas.

 

Armstrong Warriboy ne kuma coursemate din Zaid, zai girmeshi sosai tun level100 yake son su kulla abokantaka ko don yaci kudinshi don yana ganin  kalar Motocin da yake shigowa Makarantan, halin Zaid na bashi mamaki, zai zo lectures,amma in ya zauna wuri daya to sai an tashi zaiyi motsi, ba ruwanshi da kowa, be ma kowa magana, haka kawai yake rayuwanshi shi kadai, duk yanda Armstrong yaso shige ma Zaid, Zaid ya dade wurin, tunda suka hadu a wani night club, randa Zaid ya sha giyarshi ta farko yayi tatul, Armstrong ya kaishi Gidanshi, daga ranar suka fara shiri, ya zamana duk Makarantar Armstrong kadai ne abokinshi, kuma ba wai kansu daya ba, a banzace Armstrong zai ba Zaid shekara 5, amma saboda kudin Zaid ya maida kanshi karami Zaid na takashi son ranshi.

 

 

Mata ko chaa suke ma Zaid, su zagayeshi suna mai magana amma ci kanki bece  musu, da yawa suna ce ma Zaid ya amince su bashi kansu amma sam basa burgeshi, bazai gane ba, yana kashesu sosai, akwai murmushin da yakeyi na gefen baki, in akwai abunda yafi burge mafi akasarin Matan be wuce smirking din da yakeyi ba, shi ko ba don ya burgesu yakeyi ba don Sam Mace bata gabanshi, yanda Babansh ya rayu ba Aurre, shima haka zai rayu ba aure, ba zai taba aure a rayuwanshi ba.

Zaid be dauki Mace wata abar arzikki, a ganinshi Mace Matsala ce, Mace shuuma ce, Mace munufaka ce, Mace daya ya sa shi tsanar Mata gabaki daya, shiyasa baida lokacin Mace bai ganinta da gashin Azziki.

*

 

Yayi k’okarin mancesu, ya kasa, yayi k’okarin yafe musu, ya kasa, yayi k’okarin cizgesu a rayuwarshi ya kasa, yayi k’okarin cigaba da rayuwanshi da Babanshi abun alfaharinshi amma ya kasa mance abunda suka mai da Mahaifanshi, ya kasa mance radadin rashin Uwa, ya kasa mance kwanakin da ya bata yana kuka, ya kasa mance dareranki da ya kasa bacci saboda rashin Mahaifa, k’ila sun mance dashi, k’ila sun mance sun kashe mai Mahaifa, k’ila suna rayuwarsu ba tare da damuwan komai ba, while shi nan yana da komai amma he still feels empty, ya kasa mance Alwashin da yayi, ya kasa hak’ura, dole ya binciko su, ba zai taba samun natsuwa ba har sai ya san halin da suke ciki ya tarwatsa musu Rayuwarsu duka, they surely will pay for what they did to him and his Family. Da damuwa ya mai Yawa ya dauko gwangwanin Star guda biyu a fridge dinshi ya kwankwada, a hankali a hankali ya fara samun natsuwa.

 

Sallama Baba yayi a dakin ya kutsa kai, runtse ido Baba yayi, Zaid ya ji kunyan yanayin da Baba ya ganshi, yasan Baba ya san yana shan kayan Maye kuma ranshi na baci, amma dole ce yasa yake hadawa da kayan Maye, don sosai yake da damuwa.

Baba ya zauna gefen Zaid, be damu da warin giyar da Zaid keyi ba, fuskar Baba tayi Ja don bakinciki yace “Zaid, i know i’ve trained you Well, na baka tarbiya daidai iyawata, Allah shaidane, na baka tarbiya irin yanda ya kamata, Zaid ina tsoron Allah ya tambayeni kan Halaiyarka, ina tsoron Allah ya kamani da hakkin   baka Freedom, na kan tambayi kaina, shin ban baka Gata da yawa ba? Shin gatan nan beyi yawa ba, Shin Allah ba zai kamani da Hakkin sangartan dankai da nayi ba?  Zaid ban taba kunna sigari ba, amma yau Zaid gwangwani daya na giya ya maka kadan sai biyu ko fiye da haka,Zaid kaji tsoron Allah, kar ka bari rudun Shaidan ya rinjaye ka, in kana da damuwa ka gaya min, InshaAllah zan yaye maka damuwarka” Sosai Zaid yaji tausayin Baba, amma Zuciyarshi ta gama bushewa, yace “i have one request” da sauri yace “me kake so Zaid?” yace “I want all details about Baba Abba and his Family, ina so in son ya suke? Ina son in san ya rayuwarsu take? Ina son sanin komai game dasu, and i will have my Revenge, till then i’d be anything you want me to be” Baba ya kalleshi,  da wata irin murya baba ya furta ” Zaid, na zata mun wuce wurin da dadewa, Yanda Abba da Iyalanshi suke is none of your bussiness ba ka matsala dasu, Allah kadai zai bi maka hakkinka ranar gobe Kiyama, Allah zai saka ma wanda aka cuta, ka wuce nan, ka zarce su, Dukiyarka tafi karfinsu duka, ba abunda zakayi da abun su, just let them be, basu da Mahimmanci, they dont matter at all, you are better off without them, so No, you are getting no information about them and thats final”. Cikin daga murya Zaid yace “Aa Babana, i want to cost them their Happiness, ina so in saka su a tashin hankali, fargaba, bakinciki, uk’uba, ina so su dandani abun da na dandana, i grew up with that aim in my heart”  Fuskar Baba tayi Ja, ya nuna shi da yatsa yace “I did not raise a Monster, I did not raise a heartless human, get your Humanity switch, Switch it on” Idon Zaid bushe, this may mean nothing to you, but it means everything to me, idan baka fahimceni ba, Mutanen da suka Kashe min Mahaifa, mutanen da suka tarwatsa farincikina, mutanen da sukayi silar abubuwa da dama, sune kake so na tausaya mawa? Sune kake so in ji k’ansu? Mahaifana fa? Hmm, zan dauka fansa na, ba uban da ya isa ya hanani, nobody can Stop me, not even You Baba–“. Tass Baba ya tsinke Zaid da Mari, abunda be taba faruwa ba, ko kallon banza Baba be taba ma Zaid ba, da Mamaki Zaid ya dafe kuncinshi idonshi ya rine yayi Ja, Baba da ya lura da abunda yayi yayi saurin toshe bakinshi cikin tsantsan Nadama, be taba zaton zai taba sa hannun shi kan Zaid da niyyar duka ba, murya na rawa Baba yace “Zaid i’m so Sorry, kayi hakuri, nayi saurin hannu,erhhm, I know i’m not your Father” cikin tsawa Zaid yace “then stop pretending to be” fuuuu ya wuce ya bar dakin da gudu ya fada Mota ya danna horn maigadi ya wangale gate, kafin Baba ya fito Zaid ya bar Gidan”.

 

Haba Zaid, Meye haka kakeyi? Baba ya fi karfin wulakanci a wurinka, ya wuce haka a gunka, be chanchanci haka daga gareka ba, kar a zama dan Adam butulu mana din kaga yana son ka.

*

Hello Lovers, ya kukaga Babi na Goma? Zaid be bata muku rai ba? Nidai ya ban haushi. Ya batan rai sai da na sa Omo da soso na wanke lol.

 

#1love

#ADAY

#anatare

#bibiliciousfreakingfans

#nagode.

 

Biebee Isa

#

[12:02, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg1⃣1⃣

 

Da gudu ya danna Motar ya bar Unguwar Gaba daya, Zuciyarshi na mai zafi, don me Baba zai ce ya manta da komai? Don me Baba zaice ya yafe musu, don me Baba zaice yai watsi da abun da ya k’uddurta ba zaiyuwu ba, he’s waited for this time his whole life, he cant just push it away. Amma Zaid Baba ne fa, your Only Parent, wanda yake son ka fiye da rayuwa da kanta, dan guntun tsaki yayi chan kuma ya rage gudu ya ci birki k’iiiii.

*

Zubewa Baba yayi kan kujera yana maida numfashi a hankali a hankali, idanunshi a lumshe, Zaid ya gaya mai magana, Zaid ya watsa mai kasa a ido, Zaid ya nuna mai be isa dashi ba, it hurts really bad yanda ya dauke Zaid ba haka Zaid ya dauke shi ba, da Zaid zai tsaga Zuciyarshi, da ya ga shi kadai ne abunda yake so a Duniyan nan, dafe kanshi yayi da hannu bibbiyu domin kanshi ya mai nauyi. Ji yayi digar hawaye a k’afanshi, da sauri ya bude idanunshi tare da kallon kasa, Zaid ya gani kwance kan kafafunshi yana kuka, da sauri Baba ya dago Zaid, Zaid ya k’i dagowa ya daura kanshi kan cinyan Baba, yana kuka, Baba yace “Yadai Zaid?” Zaid yace “Kayi hakuri babana, ba zan sake ba”. Ajiyar zuciya Baba yayi ya shafa kan Zaid yace “Baka laifi Zaid” Zaid ya girgiza kai, yace “Aa Babana, i’m so sorry, i mean it, ba zan k’ara ba ka yafe min, you are all i got kuma ina sonka with every breathe i take in” dadi ya lullube Baba, ya daga Zaid ya rungume yace “i forgive you Zaid, i’m not trying to take away your happiness, i know these people wronged you, amma Inallaha ma’asabirin” Zaid yace “Shikenan Babana, ya wuce” ya mik’e ya shige daki, yanda yayi maganan zaka san be kai har zucci ba, Baba ya bishi da ido yana kallon shi, ya san donshi yace maganar ta wuce, don yafi karfin shi, ba wai don yana so ba, anya baya nuna son kai cikin lamarin Zaid? Baya son ya rasa Zaid, gani yake zai iya rasa Zaid idan Mairo ta ankara dashi,amma in hakan zai ba Zaid fariniciki, zai cika mai burinshi, kuma zaiyi protecting dinshi until his last breath, Wayarshi ya ciro ya latsa yayi kira.

•*

B A Y A N  K W A N A  B I Y A R

 

Tun bayan maganarshi da Baba ya koma rayuwar daki,ba  ya bude k’ofar dakinshi,har makaranta ya yanke zuwa, haka Iya zata ta buga k’ofar don ya bude amma ba ya budewa, damuwa ce ta mai yawa,bai k’ara shan giya ba say tari sai ya bude zai sha sai ya fasa don yasan Baba ba zai ji dadi ba. Waya Iya ta ma Baba, Dama Baba bai Gari, ta gaya mishi halin da Zaid yake ciki,kullum sai sunyi waya,amma be taba nuna mai akwai wata matsala ba, hankalinshi tashe ya shaida mata yana nan zuwa Gobe da sassafe.

Hakan kuwa akayi Washeagari wurin k’arfe 4 sai ga Baban Zaid ya dawo, be tsaya amsa gaisuwan da Maaikatan gidan ke mai ba ya shige cikin dakin Zaid, ya shiga kwankwasawa, Zaid be tanka ba a zatonshi Iya ce, saida Baba ya ciri baki ya kirashi, “Zaid taso ka bude min” gaban Zaid ya fadi, yana mamakin me ya dawo da Baba yau Wednessday? A hankali ya rarrafo gun k’ofar ya bude jiki a sa6ule, da azama Baba ya kutsa kai ciki, ya nufa inda Zaid ke tsugunne,nan da nan ya ga ramar Zaid, ya fad’a yayi bak’i, hannu ya sa ya janyo Zaid tare da rungumeshi idanunshi a lumshe, jikin Zaid da Zafi, Baba yace “Zaid what did you do to yourself? You look Miserable, what are you turning yourself into?” baki na rawa Zaid yace “i’m sorry Babana,kar ka damu please” Baba yace “hmm, na san damuwarka, na san meyasa ka haka,ina zuwa” Baba ya tashi ya bar dakin, chan sai gashi ya dawo da wata k’atuwar envelop, murya a dishe ya mik’a mai envelop din yace”if its because of Abba Abu’s details here you go” farinciki ya ziyarci Zaid, amma abun mamaki kawar da kai yayi ya k’i amsa, Baba yace “ka karba, you’ve waited all your life, take it” cikin murya me kama da ta rada yace “bana buk’k’ata kuma” Baba yayi ajiyar zuciya yace “Zaid, you have Rights to this, ba zan tauye ma na, you are grown up now about 21years, i shouldnt be deciding what you should or shouldnt be doing,make your own decision, so take this envelop, everything you need is there, the whole Information” sosai yaji dadi amma sai yace da Baba,Is this Ok with you?” Baba ya daga kai yace “Go ahead Son” hannu biyu Zaid ya sa ya karba envelop din. Baba ya mik’e yace “barin shiga wanka” Allah Allah kawai yake Baba ya fita yanzu, yana fita Zaid ya bude Envelop din, da hotuna ya ci karo.

 

Hoton Farko Hoton tamfatsesen Gida ne.

 

 

An rubuta full address and description na Gidan a Maitama district,sai kuma daga k’asa a kasa Late Sada Abu’s property. Zaid ya hadiye miyau, wannan gidan ma na Babanshi ne kenan, shine suka tare da zama ko? Mu je zuwa dai.

 

 

AbdulMajid da Zaineema aka sa a jikin Hoton na biyu, Sosai Zaid ke binsu da kallo one by one,Abdulmajid, his loving brother,yayi girma be da matsalar komai, kilan tun bayan tafiar shi ya manta dashi, while shi kullum sai yayi kukan rashin shi, haushi ya cika fal zuciyar Zaid,tsanar Majid na ratsa shi kafin ya kai dubanshi ga Zaineema,look at his Zaineema, duk ta girma abunta,a yanzu ba digon sonta ko kadan a ranshi.

A k’asan hoton aka rubuta details in su, AbdulMajid, Oxford University, yana karantar Medicine yana 2nd year dinshi,ga numbern wayanshi,email address dinshi,Facebook and twitter account.

Zaineema tana Nigerian Turkish tana SS3.

Ajiye hotonsu yayi ya dauko na wacce a ka rubuta Ziyadatu,Sosai yayi mamakin bayan Zaineema Mairo ta haifa yarinya har ta girma haka?,clearly yarinyan looks young and preety, nan itama aka bada details dinta na tana primary 5 a wani Primary School.

 

 

Sai Hoton Autan Abba Abu wato Zinatu, yarinya ce da ba zata wuce shekaru hudu ba, ran Zaid sai tafasa yakeyi wato ‘yayan Baba Abba Hudu, ba wanda ya san nan gaba nawa zasu k’ara haifawa, shi an kashe mai mahaifa, su kuma suna nan suna ta hayyafa, da Maamansa na nan, kila itama da tayi 4 ko 5 nan take idonshi ya dira a kan hoton mutanen da ba zai taba mantawa ba, Hasken da suka kara, ko k’ibar da sukayi be sa su chanzawa a idon shi ba, ba zai taba Manta fuskar su ba, musamman fuskar Matar da ya tsana fiye da fir’auna, Hoton dauke yake da fuskokin Baba Abba da Mairo suna daria, basu da wata damuwa basu da matsalar komai, sun salwantar da rayuwanshi amma sun cigaba da tasu rayuwan ba tare da damuwa ko wani abu ba, a Baiyane Zaid yace “Baba Abba, dan Zaki ya girma, you and your family will pay for what you did to me and My Family. Enjoy the little time you have, farincikin ku ba me dorewa bane, zan tarwatsa ku duka, zan tarwatsa farincikinku, ku yi amfani da damar nan kuji dadin rayuwanku na tsawon Shekarun da zan tashi tsaye kanku, nan ba da jimawa ba, i’m coming for you all, i’ll come for you time din ba zato ba tsammani, da ranku amma zaku so mutuwarku, ba zan daga muku ba, ba zan rage muku ba, Ramuwar gayya tafi ta gayya zafi, ni Zaid Sadam Audu, nayi Alkawarin rusa Farincikinku gabaki daya”.

*

 

I N D I A

 

 

Najwa Sada Abu ta taso cikin So da k’aunar Mahaifanta biyu,yarinya ce me shiga rai, kawarta daya tun tasowarta, Kaveri,makarantar su daya, ta samu komai na rayuwa, Najwa ta tashi tana jin Yare uku zuwa hudu a duniya, Hausa a bakinta don Mahaifanta Hausa suke mata duk da Hausanta sirkakke, Turanci kuwa a Makaranta sukeyi, tun tana yar kankanuwa in tana Turanci sai ka rantse baturiya ce,ga kuma Yaren Hindi, Haba yarinyar da aka haifa a k’asar India ai dole take iya yarensu,gashi ko don Vijhay bhaiya da ta dauke shi kamar  na jini, har yau ya kasa iya Hausa balle Turanci. Duk sadda Najwa ta rikide tafara Hausa ko Turanci ko Indiyanci, to sai ka bude baki kana kallonta, don duk yaren da tayi sai kace bata iya ko wanne yare ba sai shi.

 

 

Alhaji Sada Abu da Hajia Yesmin sun zama yan India, don kadan ne babu su cika shekaru 10 a India, suna zaune da mutanen India Lafiya,suna kuma aikinsu suna samunsu, basu da damuwan komai, in kagansu cikin Damuwa to Zaid ne ya fado musu rai, a iya shekarun nan, so da yawa zasuyi shirin tafiya Nigeria don dauko Zaid sai su kasa, Sada kanji Kamar ana rotsa mai kai da Adda a duk lokacin da yayi tunanim Nigeri ko zuwa, Yesmin ko ji takeyi kamar ana yankar naman jikinta, akwai sadda suka ci Alwashin tafia ko ta halin k’ak’a sai sunje, ta Dubai suka bi, suna jin ance zaa maidasu Jirgin da zai kaisu Nigeria Yesmin ta fadi ta zube k’asa sumammiya, abunda yake daure musu kai kenan, duk sanda sukayi tunanin zuwa Nigeria, sai wani abu ya faru sai su kasa zuwa Nigerian.

Hoton Zaid da ke garesu suka kai akayi enlarging, ta hada mai daki irin na maza ta kafa hoton nan ciki a ranta tasa zai dawo gareta wata rana, haka zata tasa Hoton Gaba tayi ta kuka. Tun tasowar Najwa ta san matsayin wanda ke cikin Hoton, tasan Yayanta, amma kullum in ta tambayesu yana ina? Sai suce “he’s far far away” ba dai sa fahimtar me suke nufi.

 

4 Years Later

 

Zaid an gama zama Cikaken Namiji, ya gama karatun Jami’arshi, ya kammala komai,ya k’ara zama wani baudadden Mutum,baida yarda ko kadan, ba ruwanshi da kowa da komai,ko irin abubuwan social network din Zamanin nan ba yayi, da wuya kaga ya sha giya, duk da yana sha, be dai bari Baba ya gani ko ya gane.

 

Duk yanda Baba yaso ya daura shi kan harkan Ayyukanshi don Girma ya fara kamashi amma Zaid baya concentrating, burinshi daya, tanadinshi daya na yanda zai watsa Familyn Abba Abu, kullum cikin Computer yana Bincike,a cikin shekaru Ukun nan, komai da ke wakana a Gidan Alhaji Abu Zaid ya sani, duk wanda suke mu’amala dasu yana da labarinsu, Informations ta ko ina suke shigo mai, yana da Spy’s a garin Kano, Abuja da kuma Kaduna inda Zaineema tayi aure Last Month, ta auri wani dan Minister Dalhatu Bala. Duk wadannan abubuwan da Zaid keyi Baba bai da masaniya.

 

B A K A R  R A N A

 

Tun Satin da ya gabata yake dan jin ciwo ciwo cikin k’irjinshi, daurewa yakeyi don jikin tsufa ne,Girma yakeyi, sai ya share, haka ya kamo hanyar PH daga Abuja, haka kurum yaji yana son ganin Zaid, Driver ya sa ya kawoshi PH.

*

“Alhaji naga ka rame ne ko bakajin dadi ne?”cewar Iya, Baba ” yace “Bakomai Iyah,gajiyar Tafiya ne, yanzu ki kawo min farfesun Naman nan”.

Waya yakeyi da Amrstrong, inda yake bashi feedback kam yarinyar da Zaid yace ya bincika a garin Abuja wato Nana, Armstrong ya shaida mai tun bayan dawowar Majeed daga Masters take bibiyarshi tana sonshi,amma baya kulata, yarinyar bata jin magana, amma Iyayensu na son su hadasu Aure” Zaid yayi tsaki “mtss, ba wannan nake son ji ba, any news about Mairo?” Armstrong yace “Yes,but you have to see for yourself, should i come over?” Zaid ya san Baba be son abokanshi, yana so ya rabu da su, don ya san suke sashi abubuwan banza, da sauri Zaid yace “No,No, Baba just arrived, i’ll come over now” jiki na rawa Zaid ya bar dakin, in yaji Information kan Mairo har Kyarma yakeyi don duk wani motsi na ta yake son sani.

Kan Dinning ya iske Baba na sha farfesun Nama, da sauri Zaid ya k’arasa ya dauke kwanon fuska daure yace “Iyah waya bashi wannan naman?” Iyah tace “Nice wallahi, kayi hakuri, yace kadan zaici,ni banga amfanin hanashi cin Jan nama ba” Zaid ya sake daure fuska ya kwala ma Ado kira, da sauri Ado ya shigo Parlorn, cike da isa Zaid yace “Ka je kitchen ka cire duk wani Red Meat dake fridge ka rabasu da gidannan, ko zubarwa zakayi oho, banason na sake ganin Jan nama a Gidan nan, kar a k’ara siyo mana Redmeat, this the last time da zanyi warning dinka” jiki na rawa Ado ya wuce ciki don aiwatar da umurnin Oga Zaid.

Ganin ran Zaid ya baci ya sa Iyah nok’e kai, sum sum tayi hanyar dakinta, Zaid ya bude baki yace “Iyah, dagaske kar a kara bashi Jan nama” cike da borin kunya Iyah tace “ayi hakuri ba za a k’ara ba” Zaid yace “ki sa a dafa mishi Farfesun Kaza” murya kamar na rada Baba yace “ba zan ci ba,  ni wannan nake so” Zaid be kulashi ba yace “Iya, a dafa mai peppersoup din kaza, kar ki sa Maggie” Iya ta asma mai ta shige, Baba yace “DonAllah Zaid ka bani in cinye” Zaid be tanka shi ba ya zauna kusa da Babanshi ya cinye Peppersoup din, Baba ya kai mai dukan wasa a hannu yace “don me zaka cinye min nama, kuma ka sa an fitar da danyen, kuma ka hana dafa jan nama a cikin Gidan, this is cheating Zaid Sadam Audu” Zaid ya murmusa yace “Dagaske Baban Zaid ba zaka sake cin Red meat ba, wai kullum ayita magana daya, ka manta me Dr yace? Daily reminder, kar kaci redmeat, kar kaci Maggi, ka manta?let me remind you You are Hypertensive ga kuma Gout Arthritis, and–” Zaid wai don me Dr zai hanani cin abun da raina ke so? Kai kuma ka biye mishi kamar fadin Annabi,iyayenmu ba da Jan naman suka rayu ba? Wai ma a rasa abunda zaa hanani ci sai Nama? Tabdi, akwai damuwa” Zaid ya dauke kai yace “duk wanda ya sake dafa ma nama Allah a bakin aikinshi, in kuma kana so ka jamusu kace su dafa ma Nama” Daria sosai Baba yayi, yana son yanda Zaid ke nuna damuwa akan duk wani abu da ya ji6ance shi, Zaid ya kamo hannun Babanshi yace, “Babana ko baka fada mun ba, i know you are sick, i know you are really sick, donAllah kar ka sa na rasaka, daidai da rana daya ban son ganinka kwance da sunan baka lafiya, i dont want to lose you, i cant imagine life without you, You are My Life Babana” wasu hawaye suka zo ma Baban yayi saurin maidasu yace “Zaid,nama ba zai sa in rayu ba zai sa in mutu ba, in na mutu lokaci na ne” da sauri Zaid yace “Prevention is better than cure, tunda Dr ya hana, ai sai a bari, i cannot lose you Babana, i cannot” Baba ya riko hannayen Zaid yace “Zaiduna, na fara tsufa, ba mu san gawan fari ba, ina so ka koyi rungumar k’addara, ina so ka dinga fawwala ma Allah lamarinka, ka koyi hakuri dan yarona, ina sonka sosai, ina so mu tsira ranar gobe k’iyama” Zaid yace “Baba me ya kawo maganar nan kuma?”Baba ya murnusa yace “a tunaninka baka san ina sane da abubuwan da kake yi ba ko?ina sane da kana bin diddigin Abba Abu, na sani ido kawai na samaka, Zaid i wont deprive you of anything, you’re 26 now,kuma ina alfahari da kai, ko ina zan iya buga gaba ince kai dana ne, you are the son i’ve ever wanted, kai da ne tamkar da dubu, i will love you always and forever and until my last breathe, always take care of yourself, kaji Zaid Ibn Sadam?” jikin Zaid yayi sanyi, kai kawai ya gyada ya mik’e don Babanshi na kashe mai jiki yace “Kasha parpesun Kazan kaci naman sosai, sai kasha magani” Baba yace “Zaid, fita zaka yi? Please just stay with me” Zaid yayi dan jim yace “Baba i wont take long, sak’o kawai zan karbo, ina zuwa” kafin Baba yace wani abu fit Zaid ya fice, amma sai da Zaid ya jiyoshi yana cewa “Allah ya tsare min kai ya kare min kai daga sharrin me sharri” ina Zaid be tsaya amsashi ba ya fada Mota ya bar gidan Sai Gidan da ya siyan ma Armstrong.

*

Idon Zaid yayi ja sosai, idonshi kur kan Laptop din Armstrong dake playing Videon Birthday partyn Muhsin Autan Mairo, shagali sukeyi sosai, kowa ya hallara Birthday din, suna cikin jin dadi da walwala, bakin cikin Zaid Farincikin su. Be san sadda ya finciko gwangwanin barasa a firij din Armstrong ya kwankwada,cikin minti kadan ya kife kan Gado sai bacci, ganin haka Armstrong ya fita ya bar mai dakin don ya san Zaid be son damuwa in yana bacci balle yanzu da Mairo ta dasa mai wani tsanarsu don ganin Farincikim da suke ciki.

*

Ba Maghrib ba Isha’i, haka wayarshi ta shiga k’ara a karo na 11, daga cikin bacci ya ji k’aran nan, a firgice ya tashi, kafin ya lalubo wayar, wayar ta tsinke, 12missed calls ya gani, Ya illahi, yana ina aka mai missed calls da yawa har haka? Wani irin bacci yayi haka? Yana dubawa yaga 8missed calls from Iya, sai 4from Dr Patrick, da sauri ya zauna yana fadin “Babana, something is definitely wrong” Wayar Dr Patrick ya bi, ringing daya Dr ya dauka yace “Hello Zed, come to the Hospital now” dif ya kashe wayar, Zaid ya tashi da hanzari ya bar dakin, ya na hada layi ya fita daga gidan Armstrong jikinshi na rawa sosai yana tunanin meya samu babanshi?.

***

A cikin reception din Asibiti yaga Iya,felicia da Ado na kuka, Iya ta dafa kafadar Zaid tace “Zaid, saidai muyi hakuri, Uban Marayu ya rigamu gidan gaskia,Babanka ya rasu Zaid” Diff kwakwalwar kanshi da na’urar jikinshi suka daina aiki na wasu lokkuta, chan sai ya farga kamar wanda aka tsikara da allura, komai ya shiga dawo mai, Babanshi, Gatanshi, abu alfaharinshi, ya rasu? Ko gezau beyi ya k’arasa cikin asibitin, shimfde ya ganshi kan Gado an rufe da zanin Gado, gaban shi ya fadi,fuskarshi tayi Ja, tsigar jikinshi suka mimik’e,jijiyar Goshinshi kamar ta bullo,a hankali ya taka har gaban Gadon,a zuciyarshi yana me rok’on Allah yasa ba Babanshi bane shimfide kan Gadon nan, hannu na rawa ya yaye mai fuska, Baba ya gani kamar me bacci, fuskar shi ta k’ara haske,Zaid ya shafi fuskarshi, murya na rawa yace “meyasa baka tillasta min na tsaya da kai dazun ba? Meyasa baka gaya min zaka mutu nan kusa ba? Meyasa ka tafi ka barni Babana?” Ya dinga sumbatu amma ba alamun Kuka,Iya tazo ta janyeshi,ta san irin Zuciya na Zaid, ta kalleshi cikin ido tace “Zaid, Babanka ya Rasu, kayi Kuka, kayi Kuka sosai” kamar Jiran Umurnin Iya yakeyi, ya fashe da kuka “Waiyo Gatana,shikenan Allah ya dauke min Gatana!”.

 

••••••••

 

Hello Lovers, how are we all doing? Yeah, yeah i know i was mute for days, was busy with Biki, m so sorry, but its all over now, lets keep rocking it.

 

Please do Vote and Comment.

 

#1love

#ADAY

#anatare

#bibiliciousfreakingfans

#nagode

 

Biebee Isa

[12:03, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Pg1⃣2⃣

 

Kuka yakeyi kamar ranshi zai fita, ya rasa Mutumin da yafi kowa mahimmanci a gunshi, mik’ewa yayi daga jikin Baba ya share hawayenshi, ya nemi Dr, don a kai Baba Mortuary, don be so a rufe Baba a Garin PH Kaduna yake so a rufeshi, a mak’abartan da yake daukar dawainiyansu. Hakan kuwa akayi, a  Asibiti Zaid ya kwana. Washegari da Sassafe aka wanke Baba aka suturceshi, kafin su ka kama Hanayar Kaduna, da laasar suka isa.

 

Tun daren Jiya Rasuwar ta zagaye k’asar gabaki daya, daga wurare da dama Mutane suka zo Kaduna, suna jiran gawa har su ka iso. Gidan Baba cike mak’il da mutane, yaran gidan marayu sai kuka suke tayi, su aka ma rashi, basu san ya rayuwarsu zai kasance ba tunda Gatansu ya rasu, ko ina jimami ake tayi.

Kallo daya zaka ma Zaid zakaji tausayinshi matuk’a, ya zama wani abun tausayi, tun yana Kuka har Kukan ya k’i fitowa. A haraban Gidan Baba aka sallaceshi, aka dunguma aka tafi kaishi Gidanshi na gaskiya, Kuka Sosai Zaid keyi, tun balle da aka zo sa Baba a k’abarinshi, sai da Aminin Baba ya rike shi, haka har aka rufe Baba, Adduoi suka biyo baya, sai da kowa ya watse ya bar Zaid tsugunne gaban kabarin Baba.

*

Marigayi Alhaji Sadam Audu Babban mutum ne, a dole gwamnan garin Kaduna ya bada umurnin hutun kwana daya public holiday saboda Shugaban k’asa da zaizo gaisuwa garin kaduna, Tururuwa akeyi gurin yi ma Zaid gaisuwa, Manyan Mutane ne, shuwagabbani da sauransu, Zaid ji yake kamar ya sa hannu a ka ya tsandara Ihu baya son jin kalman ‘ashe Alhaji lokaci yayi’ ya gaji da magana, tun yana iya amsawa da ka, har ya koma kurman dole, haka zaai ta magana sai dai na kusa dashi su amsa gaisuwan.

 

Bayan Sati Daya

 

Har yau Zaid be bar amsan gaisuwan Mutane ba, jefi jefi wasu ke shigowa, Aminin Baba ya shigo Parlor inda Zaid ke zaune da wasu Abokan Baba, ya dan karkato daidai kunnen Zaid, yace “dan Baba, ga CEO Abba Abu’s Enterprises da Iyalanshi sun biyo su ma Gaisuwa.

Kirrr kamar k’arar k’ararrawa, CEO Abba Abu’s Enterprise? No it cant be, ba zai iya ganin su ba, he cannot face them now, atleast he’s not ready, not just now, muryan Abokin Baba yaji inda yake cewa, Zaid ku fito ku gaisa, gaisuwa kawai zasu maka, murya chan k’asa Zaid yace “Nagode” Abokin Baba yace “Aa fa Zaid ba a haka, abunda ma yan gaisuwan sun bar zuwa, kwana bakwai kana karban gaisuwa, don dai wadannan sai kace ka gode kawai? Hmm, don kana Aminin Baba zan daga ma, da ba don haka ba da sai ya mishi rashin kunya. Mik’ewa Zaid yayi ya fita daga Parlorn zai bar musu Gidan, da sauri dan dattijon ya kamashi daga kafada yace “Zaid, dont be like this, nace musu bari a kira danAlhaji su mai gaisuwa, nasan suna ta tsumayin ka, please kaje, it wont take long,atleast Babanka ba zai ji dadi ba idan kana regarding guests dinka” jin an kira Baba ne ya sa Zaid juyawa, be san me zai iske ba, amma zuciyar ba ta fasa dukan chalugude ba, tsoro da firgici ya mamayeshi, har ya isa dakin be san ya shiga ba, tafi kawai yakeyi, zaune suke su Uku, one by one ya bisu da kallo, a zuciyarshi ya dinga ambatan sunayensu a lokacin da ya dora idonsa kansu, Abba,Muhsin, kafin dubanshi ya sauka kan Hamshakiya Mandiya Mairo, miyau ya hadiye mai zafi.

 

Tsura mai ido suma sukayi, Zaid tsaye gabansu yana bunsu da ido suma suna kallonshi, jin muryan Abokin Baba sukayi inda yake cewa “DanBaba ka zauna mana” ba tare da ya jira cewar Zaid ba yace “Alhaji Abba, wannan shine da tillo gun Marigayi Gatan Marayu”.

Abba yace “Allahu Akbar, Sannu yaro, Babanka mutumin kirki ne, ban sanshi ba, amma na shaida halayenshi na kirki, kowa a k’asar nan ya san Gatan Marayu mutum ne mai taimako,muma daga Abuja muke zamuje Kano, shine nace tunda hanya ne mu biyo muku gaisuwa,Legacy din Babanka will forever live in Nigerians Mind, don he’s a Legend and a Hero.sai dai mu rok’i Allah ya ji kanshi, ya sa taimakon Marayu da gajiyayyun da yayi tayi har karshen rayuwanshi shine hanyar Jihadinshi, halayanshi nagari ya bishi” Kafe Baba Abba Zaid yayi da ido, Abokin Baba ne ya samu ya amsa Adduoin, Mairo ta murmusa tace “Allah ya ji kanshi ya kyautata namu mutuwan” a lokacin Zaid ya gaji da jin muryoyinsu, idan yayi gigin bude baki, to k’ila kasheta zaiyi da kalamai masu zafi, cikin Zafin Nama ya mik’e tsaye ya bar dakin, duk suka bishi da ido, mamaki ya kama Abokin Baba, yana tunanin me ya samu Zaid? Tuni ake zuwa musu gaisuwa amma be taba acting haka ba, meyasa sai yau? Wayancewa yayi “yace kuyi hakuri, kunsan Mutuwa, har yanzu jimami yakeyi, kumai uzuri” Abba yace “haba ai bakomai, radadin Mutuwa zafi gareshi, balle ga wannan ya tashi baida kowa sai babanshi, rana daya ya nemeshi ya rasa,dole ya shiga cikin wannan yanayin” “haka ne” Mairo tace “Daddy sai mu tafi ko?” Abba yace “to Alhaji bari mu tafi kano muka nufa Allah ya k’ara hak’uri” Abokin Baba yace “Ameen Allah ya bada lada angode” Mairo ta sa6i Muhsin dan shekara 3 a kafada, Abba ya amsheshi yana mata murmushi, murmushin k’auna sukayi wa juna,duk kan idon Zaid da yake daga waje, haka suka fita daga Parlorn, a idon Zaid, wanda komai ya gama sukurkurce mai, Wannan Murmushin da ya gani kwance kan fuskokinsu shi ya jagula mai lissafi, like wake murmushi a gidan Rasuwa in ba su ba? Basu da damuwa, basu da wata matsala, ganin da ya musu yanzu ya dasa wani tsantsan tsanarsu a Zuciya.

Its about time, lokaci yayi da zai cizge wannan farincikin a fuskokinsu.

 

B A Y A N   K W A N A   G O M A

 

Alhaji Dauda Aminin Baba ne na k’ud k’ud, shi kadai ya san Sirrikan Baba, a Parlorn Baba Zaid zaune gaban Alhaji dauda, ba kasafai yake son magana ba, shi so yake yayi nesa da kowa da komai, so yake ya lula chan uwa duniy yayi shirinsa na daukar fansa,a sama ya ji muryan Alhaji Dauda inda yake cewa “Dan Baba, yau kwanan Gatan Marayu 17 da rasuwa, a yau ne nake son sauke nauyin da ya bar mun tun shekaru da suka wuce,kasancewar kai kadai ne d’a a gun Marigayi,  bai da dangi bai da kowa, ina mai farincikin sanar da kai cewa “Duk dukiyarshi da abun da ya bari sun zama mallakinka, fadar shi Marigayin ne,sai da na daukar mai Alkawarin Mallaka maka komai, naka ne, komai naka ne”.

 

Shiru Zaid yayi,a iya girmanshi ya san cewa Babanshi Mai kudin gaske ne,ina zai iya da wannan tarin dukiya? Shi da yakeso ya yi nesa da kowa ew komai? Mallaka mai Dukiyoyin nan na nufin am daura mai Girma, Girman da beyi shirin dauka ba, wata farar takadda Alhaji dauda ya mik’o ma Zaid, hannu na rawa Zaid ya kar6a, idonshi ya ciko da hawaye da ya ci karo da rubutun Baba, a hankali ya fara karantawa;

 

“Zaid my Child, from the day i die, you became a Man, i know you are so weak,but please be Strong, be strong for me, na san kana da hidimar gabanka,komai naka ne, na dade da maida komai under your name,i was just managing everything for you, whatever you decide to do with your inheritance,i’ll be proud of you, but banda shayeshaye, take care of yourself for me. Har cikin raina nake k’aunarka, Allah ya raya min kai.

Baban Zaid

 

Zaid na kawowa daidai ga6arnam ya fashe da kuka,shi yasan Son da Baba ke mai daga Allah ne, mutuwar Baba ta dawo mai sabo fil, sai da yayi mai isarshi kafin ya tsagaita, Alhaji yace “Akwai abokan Aikin Babanka da suke so a saida musu wasu companies na garuruwa daban daban, in kana da raayin saidawa,a na kuma iya tsaida production na companyn textile and feed industry a tsaida shi, Gidan Marayu kuma ana iya sallaman kowa, komai naka ne, you can do as you wish” Zaid ya furzar da iska, ya saida Companies din Baba? Ya saida hardwork dinshi? To akan me? Kudi? Tabdi, ai kudi ba matsalarshi bane, yayi imani kudi da dukiyoyin da Baba ya bar mishi zai isa ta kula da 10 next generations to come ba tare da wani abu ya ragu ba, sannan kuma a tsaida Production din textile da feed Industry? Akan me? Meyasa zai tsaida production din da idan anyi producing Gidan marayu ake kaiwa? Son abun dunianshi be kai nan ba.

 

Kamar ba zaiyi magana ba yace “Uncle,first of all ba Companyn Sadam Audu da zaa Saida, Joint Companies dinshi kuma a raba, theres no close down of the Orphanage house,idan an kulle ina zasuje? Idan an kulle ribar me akaci? Ba zai bari handwork din Baba ya tafi a banzaba, yayi imani Baba ba zai ji dadi ba idan aka kulle gidan Marayun nan, Baba ya sha gaya mai cewa yana son Marayun nan,ko da zai tashi baida ko sisi ba zai wofintar da su ba, to shi don me zai sa ya watsar da lamarin su? Shima ai marayan ne, in ya koresu ina zasu?.

“I will continue where Babana stopped, zamu cigaba daga inda ya tsaya, GM’s da Maaikatan ko wani Company su cigaba daga inda suka tsaya, zaa cigana da Gina Masallatai, zaa inganta Mak’abartu, zaa cigaba da aurar da Marayu, zaa cigaba da kula dasu, ba abunda zai tsaya, zaa dasa daga inda ya tsaya,nothing is going to change, komai na Alheri ya isa gareshi, duk ayyukan Alherin da zaayi akan abunda ya fara, Allah ya kaimai ladar ya sa silar shiganshi Aljanna kenan, hanyar da zan nuna mishi nawa kaunar kenan.

 

Hawaye ya gangaro fuskar Alhaji Dauda, Zaid yayi tunani, Zaid yayi wayau, nan ya sa mai Albarka, suka rok’a ma Baban Zaid gafarar Allah. Zaid yace da Alhaji Dauda zai danyi tafiya ya dan huta, Alhaji Dauda yace “Bakomai, amma ya bar tafian sai bayan anyi General Meeting da ko wani Member of Sadam Audu’s Worker.

 

3 M O N T H S L A T E R

 

Gidajen talabijin, Gidajen Radio, Social networks, Magazines, Jaridu, ko ina Maganan Young Billionaire akeyi wato Z Sadam Audu,sunanshi ya zagaye Globe, Girma ya kamashi, yana aikin shi ba tare da wata damuwa ba physically but mentally, Rasuwar Baba tayi breaking dinshi, ba Faraa ko kadan.

Har gida katsina Zaid ya kai Iyah gun yaranta da jikoki,a cewarahi ta tsufa, gwara tayi retire hakan nan, ya shaida mata zai dinga zuwa gaidata don yana sonta sosai yayi Sallama da katsina bayan ya mata wani kyauta ta ban mamaki har da biya mata Makka,kafin duk ya dauke yaranta da jikokinta Aiki a Companies dinshi dabandaban, dama da yawa cikinsu sun kammala degree dinsu, aikin ne dai babu. Maakaitan Gidanshi na Kaduna, kuma ya maidasu Company maigadi kadai ya bari da mai shara.

 

Allah yayi ma Zaid kwarjini, Mata sun mai Chaaa, ba sa gabanshi ko kadan,kudi Zaid ya sake Sosai akayi Masallatai da Islamiyu da Asibitoci da Rijiyoyi a kauyuka daban daban da sunan Sadam Audu, duk inda ake neman taimako a Asibiti na tallafi, da yawa cikin mates dinshi ya sama musu Aiki based on their fields, matasan da yayi employing a Maaikatanshi da yawa suke, da magana tazo gun Zaid zaa magance ma ita,har aka ma Zaid lak’abi da ‘Dan Baba mai raba Alheri’. Bayan komai yayi daidai ne ya bar k’asar ya tafi France.

*

*

For Good 7 Months Zaid na France, in ka ganshi bazakace Yaron nan wani billionaire ne, just like his Baba, he’s living a simple life ba wata k’arya ba wani showoff, to yaron da ya gaji azziki ba wanda yayi ma Azziki haye ba.

Yayi shirin komawa Naija, yayi shirin kula da Companies dinshi, yayi shirin komawa daukar fansa, yayi shirin cimma burinshi no matter what, wadannan abubuwa biyu su kadai ne burinshi, baida wani buri da ya wuce ganin tabewar Abba Abu, da kuma Cigaba a Companies dinshi.

*

Ko kadan besan Zaman Kaduna, a inda yafi wayau yake son cigabawa da rayuwanshi a Nigeria, PH, Idi ya dauko shi a Airport, Gidanshi ya saukeshi, rayuwa da Baba ya dinga mai yawo a kai, baya bukkatan masu Aiki, rayuwanshi yake sonyi shi kadai a cikin Gidannan da ke da tarin tarihi, dominshi Baba ya siya gidan nan,dominshi Baba ya dawo PH da zama duk irin yanda Musulmai ke gudun zama a garin,dominshi Baba ya jure komai, me zaiyi ma ya saka ma Baba? Tsakanin shi da Baba sai Addua. Mata kuma na ta kawo mai hari, akwai wacce alamuranta suka fi dore mai Kai, Nadiya,a France suka hadu, Nadiya yar Abuja ce, Babanta dan kwangila ne, yarinya ce ‘yar shekara 20, amma son da take mai yasa ta dawo PH da zama don sabida shi, don ta dinga ganinshi kullum, duk da bata gabanshi amma bata zuciya ba, sai ta mallakeshi duk daren dadewa.

 

Karfinshi da hanyoyinshi ya sa yake da full Information din gidan Abba Abu, komai a tafin hannunshi yake na wanda suke hulda dasu, maaikata gareshi a ko ina wanda suke kawo mai wani moves din kowa,it appears Mutumin da Zaineema ke Aure a Kaduna shine GM din wani Company a Zaria, Babanshi kuwa Abokin Baba ne, yana sane da Kwangilar da Gwamnati ke ba AbdulMajid na Tituna da Ginene, kasacewar shi yana da degree Architecture da Msc a Quantity Survey,yana sane da Nana Nakowa na mutuwar sanshi har ana so a hadasu Aure,  yana sane da Ziyada ta gama Secondary School ta fara karatu a Baze University inda take karantar International Relation,yana sane da dan Gidan Senator Ali Aminu na Sonta, yana sane da Irin Manyan Matan da Mairo take hulda dasu, itama bata yarda ba itama matar wani ne a Nigeria, yana sane da kowanne Moves din da suke, ko ina bin diddiginsu yake, hankali kwance ya fara gudanar da daukar Fansarshi ta hanyoyinshi. Wannan Kenan..

 

C I G A B A N   L A B A R I N

 

 

 

 

 

Hello lovers, finally zamu dawo main labari, it wasnt easy to crack my brain for the tuna baya, how was the tuna baya? Sha, this is is the begining of an end.

Vote, Comment, Recommend.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

[12:04, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

 

Bibilicious freaking Fans? How you doing? kwanakin baya, a wani page nace Abdulmajeed na karantar Medicine a Oxford University, sai kuma na dawo nace yana da degree a Architecture and Msc a Quantity Survey, so Afwan, mu dauki Architecture din, zaifi hawa da labarin. Nagode.

 

Pg1⃣3⃣

 

I N D I A

 

Najwa taje Nigerian Embassy, inda aka mata interview, Wani k’arfin guiwa takeji yana zuwa mata, ba ta damu da zuwa k’asar da bata ta6a zuwa ba, bata damu da karatun ta da zata datse ba, ba ta damu da komai ba, burinta kawai taje Nigeria, burinta ta tsaida hawayen Mahaifiyarta, bayan sun dau lokaci suna tattaunawa da Vijhay bhaiya, ta tashi ta wuce gidansu Kaveri don yau yawo takeji, Kaveri na kwance ta shiga, bayan ta gaida Maa din Kaveri ta shige cikin dakinta, duka ta dada mata a baya, da sauri kaveri ta tashi ta daure fuska, “Najwa Sada Abu whats this for?” Najwa ta juya idanuwanta tace “Get up, we are going out” “jahaan ham karane ja rahe hain(Ina zamuje ne)?” Najwa ta murmusa tace “agar yah pichhalee baar jab main ek yaatra par jaana hai main ise aap ke saath rahana chaahata hoon (If this the last time i hang out in India, i want it to be with you) Kaveri da damuwa tace “is tarah baat karana band karo, tum vaapas ho jaega, mujhe pata hai (Ki daina magana haka, zaki dawo, na sani)” ta karashe hawaye na fita idanunta, itama Najwa na hawayen ta rungume Kawarta tace “tumhaaree yaad aaegee Kaveri (I’ll miss you Kaveri) Kaveri tace “mujhe bhee tumhaaree bahut yaad aaegee (Nima zanyi kewarki Sosai)”.

Kaveri ta mik’e ta taje kanta, ta dan sa lipgloss, sai da sukayi hotuna kafin suka bar gidan.

 

 

A B U J A  N I G E R I A

 

“Dad, inaso ka bashi 20 million saboda robbing dinshi da akayi, they lost alot, ina so ka tallafa musu” Dad din Nana ya murmusa yace “is that all?” Nana ta turo baki kamar yar shekara 8 tace “sai kayi maganan Aurenmu” Dad yace “Shikenan, Gobe sai ayi Processing Kudin sai a kai musu Gidan ko Baby? Da murna tace “Thanks Dad” da gudu ta fada dakinta tana tsalle tsalle.

 

Tunawa tayi da abunda wannan ya gaya mata tayi, shiru tayi tana tunanin meyasa zai tamaketa? Meyasa zai bata shawara? Kafa kafada tayi a ranta tace “indai hakan zai sani auren AbdulMajid to banda matsala, ba Syrup ba ko Giyace sai na sha” daidai tafiansu Mansion din Abba Abu, ta kur6e kwalba biyu ta syrup, ta fito tana layi, Bayan Mota ta shiga inda Mamarta take zaune da Baban, Driver ya ja su sai Maitama District.

*

Jiki na rawa Hajia Mairo ta tarbesu, ba kasafai Hajia Sayluba Nakowa ke zuwa gidansu ba, yau gashi kuwa harda Nakowan da kanshi ga kuma Nana, ina zaa saka dasu take tayi, ta zauna suka kwashi gaisuwa, ta mike tace “bari ta sanar da Alhaji Abba zuwansu” chan sai gashi sun dawo tare da shi da Yaran Gidan Baki daya, aka gaigaisa, tuni Nana ta matso kusa da Majeed kamar ta shige jikinsa, yana jin tana warin Maganin tari, Dad da Mom din Nana su ka musu Jajen abunda ya faru na Kidnapping Zeenatu, da kuma Robbing din Majeed. Sannan Dad yace da Alhaji Abba ga gudummuwarshi na Naira Miliyan 20 duk da abun da suka rasa ya wuce Miliyan 20, Daddy yace “Haba Alhaji Nakowa, wannan kudi sunyi yawa” Alhaji Nakowa yace “Haba Alhaji Abba, ka bar fadin haka, kaine fa? Zan iya maka fiye da hakan” karaf Hajia Mairo tace “mungode Allah saka da Alheri Allah ya bar zumucni” Hajia Sayluba ta amsa da “Amin”. AbdulMajid ma yayi Godia, duk sukayi Godia.

 

Alhaji Nakowa yace “To Alhaji Abba, maganar auren yaran nan, ina nufin AbdulMajid da Nana, ya kamata a zo kan Conclusion, gwara a musu auren tunda sun daidaita kansu, kan AbdulMajid ya sara, sun daidaita kansu? Inji wa? Kuri ya ma Babanshi da ido don yaji me zaice, shima Alhaji Abban, Hajia Mairo ya kalla, da sauri ko tace ” Zaa fara maganar” Hajia Sayluba tace “Yaushe? Baby Nana fa ta matsu, gaskia gwara ayi auren, ko cikin satin nan ne, tunda ba wata matsala” Idon Hajia Mairo ya raina fata, to ina ma suka tsaida magana da Majeed, amma don kar ta bata alak’ar su da Hajia Sayluba tace “Shikenan sai ayi bikin k’arshen Sati” ba tare da ta kalla AbdulMajid ba”.

 

Nana ta hau murna harda tashi tana rawa don murna, takaici ya cika Abdulmajeed, rashin kunyarta yafi 6ata mai rai, ace bata kunyar kowa? Gashi gaban mutanen da ake kirarin zasu zama sirikanta take rawa? Be san lokacin da yace “Ba zan Aureta ba, ba zan taba Aurenki ba Nana” dim Parlorn yayi, Baki Hajia Mairo ta bude cike da mamaki, bata taba tunanin Abdulmajid zai watsa ta gaban Mutane haka ba, kafin tayi magana Nana ta fashe da wani irin kuka mai kama da Ihu, Hajia Sayluba da Alhaji Nakowa hankalinsu ya tashi, Alhaji Nakowa na hargowan “Mai zan gani haka Hajji Abba?, ya Danka ke tada hankalin Diya?” Alhaji Abba yace “Decision dinshi kenan, we cant force him in baya so” ran Alhaji Nakowa ya 6aci, zaiyi magana Hajia Mairo ta tareshi da cewa “kuyi hakuri Alhaji, ku ban Miniti Goma, i’ll talk sense to Majeed, donAllah kar kuyi fushi, just 10 mins” Jiki na rawa taja AbdulMajeed zuwa dining section, Alhaji Abba da Ziyada suka rufa musu Baya.

 

Hajia Mairo ta tallabo fuskar Majeed da ya kada yayi Jazir yana huci kamar Zaki tace “Yaro, meyasa kakeson kunya tani a idon jamaa? Meyasa kake son tona min Asiri?” da mamaki yace “Mummy ki gaya min hanyar da nake son kunyataki, taya zan kunyataki?” AbdulMajeed rashin Auren Nana na nufin ka kunyanta ni, ka tozartani, ka sa nayi karamar magana, na mata Alkawarin Aurenka, ka taimakeni, bana son Alak’ar mu da su ta yanke, ka kalla yanzu, Millian 20 suka bamu, don rashin da mukayi, waye zai dauki zunzurutun kudi har miliyan 1 ta baka a wannan maran ta buhariyya? Wa zai baka miliyan 1 kyauta? Amma ji kyautan Miliyan 20, an ninka maka abunda aka karbe ma, ai ko don wannan dole ka Auri Nana” Alhaji Abba yace “Aa Maryam, ki bishi a hankali, in fa yace baya so ba zamu tilasta mai ba” Hajia Mairo ta fashe da kuka “Kaima ko Abba? Yanzu in sukace zasu kwace kudin fa? In suka datse wata Alak’a da mu fa? Ai asirin mu ya tonu, Majeed ka kasa ganewa, auren Nana Alheri ne, ba zamu ta6a karayar azziki ba, yanzu daba su tallafa mana da kudin nan ba, ba ka tunanin zamu fada kwata haba Majeed” Ziyada ta kalli Hajia Mairo sama da k’asa tace “Mummy You Sold Ya Majeed’s happiness for 20million? I’m not suprised Mommy, kin fi san kudi kan yaran cikinki” da sauri Hajia Mairo ta juyo ga Ziyada tace “Haba Ziyada, kar kice haka, Wallahi kune farincikina, i want a better future for all of you” Kukan da takeyi ne ya sa Ziyada shiru, Mairo ta cigaba “na maka abunda kakeso tun kana ciki, nayi abubuwa da dama don saboda kai da k’annenka, nima kamin just this one thing, please Majeed, in sonta ne bakayi da anyi auren za ka soma sonta” cikin daga murya yace “wai kinsan wacece Nana Nakowa kuwa? Yarinyar da bata da tarbiya, yarinyan da ake mata kirarin ‘Nancy mai maza da mata?’ yarinyar da ke shan kayan maye? Is this the kind of girl you want to call a daughter inlaw?” Hajia Mairo ta dauke wuta dif, da ido ta ma Alhaji Abba magana da ya tausasa danshi.

 

Alhaji Abba yace “AbdulMajeed, kana da shaidan tana aikata wadannan abubuwan da ka lissafo? Ka yarda ran kiyama a tsaidaka a muku hisabi? Ka taba ganinta da idonka ko gaya maka akayi?” jiki a sanyaye yace “ban taba ganinta ba, ji nayi ana fada” Alhaji yace “to kayi saurin yin Istighfari, yana iya yuwa sharri ake mata, kuma ko ba sharrin bane, kai ba ka gani ba, muma bamu gani ba mu dinga aiki da zahiri, kar ka manta zato zunubi ne ko da ya zama gaskia”. Istighfari yayi a zuciyar shi, Mairo tayi karaf tace ” Ai mutane akwai shaidar zir, don an ga Ubanta na da Azziki shisa ake mata Hassada” a dake Majeed yace “Whatever dai, Nidai ba zan aureta ba”. Kafin su ankara sai jin Ihun Hajia Sayluba sukayi, da gudu suka baiyyana a Parlorn, Nana ce rik’e da wata irin zuk’ekiyar wuk’a.

*

Kanta suka yi duka, hankalin Alhaji Nakowa a tashe, yace ” Nanana, kiyi hakuri, ki ajiye wukan nan, ba a wasa da wuka” cikin karaji tace “wasa da wuk’a? Kana tunanin wasa da wuk’a mikeyi?” wukar tasa daidai saitin hannunta ta yanka, a lokaci guda suka sa ihu, Jini ya far fita daga hannunta, ta nuna su tace duk wanda ya matso kusa dani zan chaka mai, AbdulMajid yana matsowa tace “Wallahi zan kashe kaina idan har baka amince zaka auren ba” ta karashe tare da daura wuk’ar kan wuyanta, Hajia Sayluba ta zube gaban Majeed tana kukan ya taimaketa, ba zata iya rasa Nana ba, ita kadai gareta, Alhaji Nakowa ma magiya yake mishi, Hajia Mairo a kidime, kowa hankali tashe. Nana tace “Majeed ka ban amsa, na baka nan da 15seconds, idan baka ban amsa daya ba Wallahi zan lumama cikina wuk’a”. Irge ta fara.

Yanda Majeed yaga yanayinta ya ga tana bulayi yasan ta sha wani abu, tana iya kashe kanta a banza, ga jini na zuba ta hannunta, tana kawowa 5 da sauri yace ” Na amince Zan aureki” murmushi tayi tace “ka rantse” ba watawata yace “na rantse da Allah zan aureki” tace “ranar juma’ah” guntun tunani yayi yace “gobe ne jumaar fa” wukar ta kara dadirawa a hannunta, da sauri ta fasa ihu shima yace “Na rantse gobe zan aureki Nana, donAllah kar ki k’ara illata kanki” murmushi tayi ta sake wuk’ar tare da zubewa k’asa,da sauri duk sukayi kanta.

Asibiti suka kai Nana akayi dressing hannun, tasha bacci na kusan awannin 5, tana farfadowa ta sa aka sallameta, a cewarta Amarya ce ita, bai kamata ta kwana Asibiti ba. Majeed fa??.

 

Tunda ya kulle kanshi a dakinshi bai sake budewa ba, kanshi yayi zafi, wai shi ya amince da auren Nana? Kuma gobe? Wai Nana? Kanshi ya rik’e sakamakon sarawan da yakeyi, yana ji Mummy na k’wank’wasawa yayi banza da ita, tayi tayi ya bude har ta gaji, haka zata koma jiki a sabule.

 

Sai da akayi Sallahr Maghrib AbdulMajid ya fito yaje Massalaci, ko da ya dawo daga Massalaci ya iske Mummy a dakinshi, fuska ya daure, ya samu guri ya zauna, da sauri ta dawo gunshi, ta rik’o hannunshi tana kuka “AbdulMajid, nasan yanzu katsaneni, me zanyi ka fahimci duk abunda nakeyi don kai ne? Kana tunanin zan taba cutar da kai? I want the best for you, Nana isnt bad, tana da kyanta, da gatan ta, donAllah ka kwantar da hankalinka” da ya ga zata matsa mishi yace “Mummy just walk out” kuka ta fashe mishi dashi, AbdulMajid sarkin tausayi tuni Zuciyarshi ta karaya, nan ya hau lallashinta ya tabbatar mata da zai Auri Nana..

*

Amsa kiran wayar tayi da “Hello” muryan da ta ji ne ya sata tuno da mutumin da suka hadu shekaranjiya a Silverbird, murmushi tayi kamar yana gabanta, ji tayi a tak’aice yace “fill me in” da murna ta fara koro bayani tace “ai in gaya maka, komai yayi daidai, nabi shawararka, gashi ya amince, gobe zamuyi Aure” “Good,kiyi insisting kan ayi muku dinner a goben, a beautiful girl like you deserve a Wonderful wedding” murmushi tayi wanda har ranta taji dadin kodata da yayi,a fili tace “zaka zo ko?” yayi murmushi yace “i wont miss” duk da bata sa ko waye shi ba, amma tana jin kanta da bin duk wani umurni nashi, dole kuwa a musu Dinner Party, bari ma ta kira Wedding Planner.

 

Bayan Sallahr Jumaa aka daura auren Abdulmajid Abba Abu da Amaryarsa Nana Asmau Nakowa bisa sadaki Naira Dubu 100, mutane ke cincindiron yi ma Alhaji Abba murna, AbdulMajid yak’e kawai yakeyi yana gaisawa da mutane.

Abunka da masu kudi, tuni aka hada wani Dinner a The Sheraton Abuja Hotel.

 

 

*

 

Amstrong ya kalli Zaid yace “All set sir, we can go into the mansion now”kafin ya juya ga yanmata biyu da ke zaune bayan motan sanye da Atamfa riga da skirt, yace “get ready girls”Zaid ya furzar da iska tare da danna horn a gidan,Maigadi ya bude k’ofa ya karasa gaban Mota tare da lek’awa, Zaid da ke gefe yace “Mallam Hadi ya aiki” Mallam Hadi ya yashe baki ganin an ambaci sunanshi “Aiki alhamdulilah” daya daga cikin matan dake bayan mota tace “sun wuce gurin Dinner din ko?” Mallam Hadi yace eh sun fi Awa daya da tafiya, Zaid yace “Abokan Abdulmajid   Ango ne daga Lagos, mun kirashi a waya yace yana wurin dinner ya aiko mana da key din part dinshi yace muzo mu shirya kafin mu iske su a Hotel din, ya ma ce in mun gama Falalu ya kai mu gun dinner” Zaid ya karashe tare da daga Makullan, Mallam Hadi yace “ai kuma Falalu ya tafi gun dinner shima, nikadai aka bari” dayar tace “ba Sheraton Hotep bane? Ai nasan gun, muje mu shirya kafin a tashi” Mallam Hadi ya wangale Gate suka shiga ciki zuciyarsu fari k’al.

 

Ba su sha wahalan bude k’ofofin Gidan ba, yanmatan nan su biyu tantiran 6arayi ne, ko ya k’ofa take sai sun budeta, daga Warri Amstrong ya musu waya suka taho ta jirgi.

Zaid ya bi Gidan da Ido,wani tangamemen Hoto ya gani na Familyn Abba Abu gabaki daya, ya matsa kusa da hoton ya kura ma hoton ido, idonshi yayi Jazir ganin murmushinsu. Amstrong ya katse mai tunani yace “Oga, we have to hurry” Zaid ya basu Go ahead da su hau Sama, suka hau sama, da dakin Farko suka fara, Office ne, Zaid ya musu nuni da su wuce sauran dakunan, shi kuma ya kustsa kai cikin Office din tare da mace daya. Zaid ya bi Office din da kallo, wani save ya gani, ya ce macen tayi mai unlocking, Makullai da suka fi dari ta ciro daga bujenta, ba daukan lokaci save ya bude, Zaid ya karasa ya dinga ciro files files yana budewa, murmushin gefen fuska yayi ya tattara duka a hannunshi, aka rufe Safe din suka rufe Office.

Amstrong kuwa yayi Babban Gamo, don Ghana MustGo din kudin da Baban Nana ya basu ba su kaishi ko ina ba sai dakin Mairo, Amstrong ji yake kamar yayi ihu don Murna, ga wasu Sark’a daham da Yankunne da suka samu a wurare dabandaban, har dakin Abba da AbdulMajid sai da suka shiga, suka samo abun amfani.

Zaid da murmushi a fuskarshi yace “lets get going guys, i’m done here”. Amstrong yaja ghana matan suka tattara jewelries din, bayan dayan ta sauka ta dauke ma mai Gadi hankali suka sa komai a booth suka bar Gidan,bayan ya ba Maigadi kudin da be san yawansu ba, Maigadi ya kwashi godia.

**

Bayan sunje masauki amstrong yace “Oga ya zaayi da kayan nan?” Zaid ya murmusa yace “Its all yours, share among yourselves”.suka hau shewa “Osheyyy, sai Oga”..

Su sun san Oga yafi karfin komai, su gaba ta kaisu.

*

Manage this please, i’m preety occupied these days bear with me.

 

Vote and Comment please.

 

#1love

#ADAY

#bibilicioufreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

[12:06, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad: @biebeeisa

 

Pg1⃣4⃣

 

A hankali a gabatar da Dinner party cikin yanayi na Girma, kowa sai san barka, haka taro ya tashi lafiya, da k’yar Nana ta tafi gidansu, don a cewarta a yau din zata bi Majeed. Mummy ta lallabata, kan cewar gobe da Safe zaa kaita gidansu Mijinta kafin a samo musu wurin Zama.

 

A gajiya a ka koma Mansion din Abba Abu, Zaineema da Ziyada suka shiga dakin AbdulMajid Zaineema ta kalli Yayanta don yau ya gama kasheta tace “Haba Ya Majeed, kunya ka so bamu ne dazun? Naga kana ta shan kamshi kana bata rai, haba Ya Majeed, zakayi ma Azziki k’ulli, ba kowa ake ba irin damarka ba” galala ya kalli K’anwarshi yace “kasan dai duk da aurenki ina iya miki dukkan tsiya ko? Ni ba tsaranki bane Zaineema,ki fita idona” Zaineema ta ta6e baki, tasan la shakka zai iya mata duka, ta wuce fuu ta bar dakin.

Ziyada ta bi bayanta da murmushi.

 

AbdulMajid ya kalli Ziyada yace “Yayanki ta k’i hankali har yau” murmushi Ziyada tayi tace “I miss your dramas” da kalamanta ta tausasahi, kan cewa ya saki jikinshi ya cigaba da alamarinsa, K’addararsa ce haka, Sosai yake son Ziyada,Jininshi ya ma fi haduwa da ita, inda ta bambanta da Zaineema kenan, tafita kaifin tunani da basira, idan zatayi magana tana amfani uwauba hak’uri, in kaga Ziyada na daga murya to ka kaita bango ne, ko Zinatu ta mata rashin kunya, ba kasafai take kulata ba, ba dan komai ba sai kawai bata da son hayaniya.

Gyada mata kai yayi alamun yaji duk abunda tace kuma InshaAllah Zaiyi yanda tace, murmushi ta mai ta tashi ta fita tare da kullo mai k’ofa. Sai da yayi Nafila kafin ya kwanta bacci.

 

Walima Akayi a Abba Abu’s Mansion, da daddare Amarya ta tare a dakin AbdulMajid. Anan zata fara zama kafin su tafi Kano inda AbdulMajid ke aiki.

A daren rannan burin Nana ya cika, kusan fyade ta mai, a ran Majeed mamakin Nana yake tayi, sam ba ta da kunya, ta ya zaa samu mace haka? Allah kayi mana da kyau.

Daga daren Jiya, wani irin zafaffen So ya sake rufe Nana, AbdulMajid ya kai Mijin da zaa buga gaba a nuna shi, duk da be biye mata ba, amma hakan ya wadatas.

 

I N D I A

 

Alhaji Sada ya kalli Matarshi cike da So da k’auna yace “Yesmeenah, ku shirya gobe zamu Taj Mahal” murmushi Yesmeen tayi, ta san don ta saki ranta Mijinta ya tsiro da wani tafiya, zatayi k’okari ta saki ranta, ko don kwanciyar hankalin Mijinta da tillon diyarta, tace “Allah shi kaimu Gobe Papi, zan gaya ma Najwa ta shirya”.

Da Najwa taji maganar tafian taji dadi sosai, lokaci ne da zata k’ara kusanci da Mahaifanta, in ba rabon su sake haduwa, to ba zata mance moments din da zasu samu gobe ba.

*

 

 

Washegari suka dafa abinci kalakal ita da Maama, suka shirya wurin k’arfe 9 Vijhay yazo daukarsu, Najwa ta dauko Pooh (Mage) ta sata a Mota, duk yanda Maama tayi kar aje da Magen nan Najwa ta sa Shagwaba har sai da Paapa yace abarta ta tafi da Magenta, Najwa a gaba, Maama da Paapa a baya suka dau hanya.

 

 

Tafiyar Awa Hudu sukayi suka iso TajMahal(7th wonder of the World), ba zuwan su na farko kenan ba, bayan sun zagaya ne suka samu wuri daga chan Garden suka shimfida Carpet, suka yi lunch.

Najwa ta kafe Iyayenta da ido, gani takeyi kamar ganin k’arshe take musu.

Idonta ya ciko da hawaye, Alhaji Sada ya lura da ita yace “yadai Najwa? Are you OK?” Maama ta juyo kallonta ga Najwa tace “Kya huwa beti? (Meya faru diyata?)” Najwa ta murmusa tace “Maama, Paapa, i was just thinking,Ina Ya Zaid yake? Is he alright? I just want to meet my Brother” Maama ta fashe da kuka, Najwa ta taya ta, sai da sukayi me isar su kafin Maama tace “Najwa, bansan ya Zaid yake ba, bansan ya yanayinshi yake ba, bansan da wa yake kama ba, Yana kama dani? Ko da k’anwarshi, ko da Papanshi? But I’m sure ko a Ina yake, he’s grown into a Prince Charming” ta k’arashe magana hawaye masu zafi na bin kuncinta ta cigaba “If only he’s here with us, we’d be a loving and a whole Family”.

 

Paapa ya hadesu duka ya rungume yana lallashi ” Yesmeenah, i’m a bad Husband, and a bad Father, na kasa hada Da da mahaifiyarshi, na kasa ba Matata farinciki, na kasa hada kanwa da yayanta, ku yafe min, bansan ya zanyi ba” Maama ta dago tace “haba Papi, don me zaka ce haka, why are you blaming yourself like its your fault? Kar ka manta we are in this together, kaine k’arfinmu, in ka karaya ya zamuyi?” kukan da yazo ma Najwa mai k’arfi, da sauri ta tashi ta la6e bayan Bishiya tana kallon Iyayenta na lallasan Junansu. Yaushe zata tsayar da hawayen nan? Ji take Ina ma ta matso da sati biyun da ya rage taje Nigeria kusa, ina ma zata iya ganin Yayanta, sai da ta ga sun natsu kafin ta koma gunsu tare da sake musu murmushi tace “Oya muci abinci kafin yayi sanyi”.

**

Maama ta dinga ba Najwa labarin Zaid, “Zaid baya son Kifi, ko k’arnin kifi yaji zai kama amai, Zaid na son abu mai sanyi” tayi daria tace “Zaid na son wasan banza, yana son tsalle-tsalle sosai, to yanzu da girma yazo mai, shekara 28 ko yana yin abunda yakeyi a yarintan shi?” Paapa yayi daria yace “Haba Yesmeenah, i’m sure ya bar dukka abubuwan da kika ambata” Najwa na daria ta kalli Iyayenta sa suke faraa suna maganar Zaid, tace “Paapa, a Nigeria, wani state kuke?” dogon tunani Paapa yayi yace “To God i dont remember” mamaki ya kama Najwa tace “Maama fa?” Maaman ma tunani tayi tace “ikon Allah, i cant remember, all these years ban taba tunanin sunan gari ba” abun kuma sai ya zama kamar Almara Najwa tace “Ya akayi haka? Ya ba zaku tuna ba?” “Wallahi ban tuna ba” Maama ma tace “nima Wallahi ban tuna ba” “to ya baku manta Sunan k’asar da ku kazo ba?” Shiru sukayi duka, basu san dalilin ba, Najwa da abun ya gama daure mata kai tace “Okay, ‘yanuwanku fa? Your parents” Paapa yace “Najwa nidai i cant remember, wlh i dont remember anything concerning Nigeria” yanzu kuma abun tsoro ya fara ba Najwa tace “Ina kukayi aiki? Bakuda Contacts din coworkers din ku? Ko Schools din da Yaya Zaid yayi? Anything you cant just forget Everything, think harder, Maama, Paapa” Cikin daga Murya Maama tace”Najwa, dont you get it? We cant remember a thing, Najwa,ban san me ya faru dani ba, bansan ya abu ya kasance ba, nasan abun zaiyi kama da tatsuniya, amma its real, mun munce komai, amma abunda ni ko Paapanki muka kasa mancewa shine Yayanki Zaid, mun kasa, mance shi muna da tabbacin yana Nigeria, but ba musan inda yake ba, above all ba zamu iya zuwa gunshi ba”.

 

Najwa tayi jigum tana tunani, amma takasa gane komai, yanzu ba wani hanyar da zai sadata da Yayanta kenan? Kawai shiga Nigeria zatayi, to ina ta dosa? Ita da ko hoton Yayanta bata dashi, ta ya zata fara nemanshi, anya zuwa Nigeria ba bad idea bane? Amma Hawayen Mahaifanta fa?, no she wont give up, not now da saura ‘yan kwanaki ta tafi Nigeria, Allah zai hadata da danuwanta da yardan Ubangiji, kuma zata shaidashi ta hanya mai sauk’i don Maama ta gaya mata cewa Yayanta na da irin mark dinta a hannu da wuya, so InshaAllah everything will be fine. Da haka ta ja su da wasa har suka warware suna Family Play.

 

A B U J A NG

 

Ko a gaban waye Nana ba ta da wurin zama sai jikin Majeed, abun na damunshi ainun, sam Nana bata da kunya, ga jarabar tsiya, Alhaji Abba kauda kai yakeyi don ba ikon Magana, ita kuwa Hajia Mairo in taga Nana na shishige ma Majeed sai ta yashe baki, a cewarta wayewa ce, kuma Nana ce daidai Majeed ita zata bude mai ido, don Majeed wani iri ne.

Nana bata da da’a a kan fita lokacin da taso ta dawo lokacin da taso, ko ta fita da Muhsin da Zinatu ta kaisu wuraren wasan yara, shiyasa yaran ke sonta ita kuma Mairo tana k’ara sonta. Ba ruwanta da Ziyada, a cewarta “she’s no fun to be with” gaisuwa ce kawai ke hadasu don kwatakwata halaiyarsu ya banbanta.

 

K A D U N A

 

Cika aiki ya kalli Tamfatsetsen gidan da ke gabanshi yace “Barin kira Oga, i’m sure this is the house, address din da Oga ya turo min ne” ya dauko Waya a Aljihu ya latso numbern Oga Zaid sai da wayar ta kutsa tsinkewa kafin Zaid ya daga a dakile yace “Cika Aiki” Cika aiki yace “Oga gani a Unguwan Dosan, na gane Gidan” Zaid yace good, i’ll tell you when to go in, i dont want any mistakes cika aiki” Cika aiki yayi daria yace “you can trust me on that.

 

Amstrong yace “Oga, you are after Hajia Mairo, why arent you getting to her directly? Why are you just hurting her Children” kamar bazaiyi magana ba, sai chan yace “because hurting her Children will hurt her more, she loves them alot, besides i’m just getting started, i’ll get her soon”. Amstrong ya jinjina kai, shidai ba damuwanshi bane duk me Zaid zaiyi yayi, as long as zai cigaba da cika mai Bank Account dinshi.

Bayan wasu ‘yan awanni wanda yake daidai da k’arfe 9;30 na dare, Zaid ya kira cika aiki a waya yace ” You can go in now, yana wurin Kawo, remember, bansan a sami matsala” Cika Aiki yace “Yes Sir”.

*

 

Zaineema ta shiga toilet dan yin wanka, yau da wuri zatayi bacci tunda Oga baya nan, yaje Kano gobe zai dawo, ta yi wanka ta shafa mai, kamar yadda aladanta yake ta bi ko ina na jikinta da turare mai k’amshi, yar ficiciyar riga wanda be rufe cinyarta ba ta saka,

Ta kashe wuta tare da hayewa Gado, ta so jin muryan Mijinta amma wayarshi not reachable, adduoin bacci tayi kafin ta rufe ido don yin bacci.

Khaleed ya shigo gidanshi da misalin k’arfe 10:05pm, ya ki gaya ma Matarshi Zaineema dawowan shi don yana son mata Suprise, yau amarci zasu sake, don yayi missing dinta, suka gaisa da Maigadi, ya kwashi ledojin da ya zo dasu ya shiga cikin gidan da Sallama bayan yayi amfani da makulanshi ya bude gidan, beyi mamakin jin gidan shiru ba, dama daga ita sai mai aikinta, ya tabbatar sunyi bacci, kitchen ya shiga ya ajiye ledojin kafin ya shiga dakinshi yayi wanka tare da yin nafila, kayan bacci yasa ya nufi dakin Gimbiyarshi Zaineema. Ya sa hannu ya bude k’ofar, ya lallubo makunnin wuta ya kunna, Bak’in gani Khalid Yayi, idonshi ya sauka kan Zaineema da wani katon gardi kan Gado, da k’arfi ya furta “Inalilahi wa ina ilaihir rajiun”. Cikin bacci Zaineema ta yi firgigi ta tashi da salati a bakinta. Tashi tayi da ta lura da wani kwance gefenta, da sauri tayi tsalle ta diro kan gadon, tana cewa ” Honey waye wannan?” Hannu ya daga ya kamtseta da mari yace “Ubanki ne” zuwa yayi Kan Gadon ya finciko gardin da tsakanin shi ga Allah bacci yake be san me ke faruwa ba, Khaleed ya kaima wani mugun nushi a fuska ya bude ido tare da cewa , “sweety baki gaji ba kenan” yana bude ido ya ci karo da Khaleed, ya tashi irin a tsoracen nan yace “Sweety ba kice min yau mijinki zai dawo ba da banzo ba” Zaineema da ta kasa gane me ke faruwa tace “wai waye kai? Kuma me kake cewa” Cika aiki yace “Haba Sweety, dan kinga mijinki zakiyi pretending baki sanni ba, bayan na gama biya miki bukkatunki ko?” Khaleed ya kawo mai wani Shak’a ta baya, Cika aiki ya dunk’ule hannu ya guma mai Nushi mai zafi a Ciki, da sauri Khaleed ya sakeshi yayi kasa tare da dafe ciki, Zaineema ta aa Ihu, Cika aiki ya dauki rigarshi ya zura a guje. Da gudu ya bishi amma be cimishi ba har ya fita,ba abunda Zaineema keyi in ba kuka ba, tazo taren Khaleed ya sa hannu ya tureta, yace “Zaineema, na soki tsakani na da Allah, kin haince ni, kin cuceni, ban rage ki da komai ba, kin munafince ni, tsakani na da ke Allah ya isa, na sakeki Zaineema, na sake ki,dare yayi, zan miki uzuri, amma gobe safiyar Allah ki tafi ki bar min gidana, Adultress kawai”. Wani irin kuka Zaineema ta sake tare da dafe kai, bata san hawa ba bata san sauka ba, bata san wake shirin rusa mata farinciki ba, tana kallo Khaleed ya sa kai ya bar mata Gidan, sai da taci kukanta ta shiga ciki, ta dauko waya ta kira gida duka basa shiga, da k’yar ta rarrafa dakinta amma bacci ya kaure ma idanunta, haka ta kwana zaune. Washegari da safe ta bi jirgin k’asa zuwa Abuja.

 

Yau Tuesday, Mummy tayi Sallama dakin Nana rik’e da Tray din breakfast, Nana ta mik’e tare da karban tray din Mummy tace “good Morning Mother inlaw” Wayewar Nana na burgeta, tace “morning daughter in-law, ga breakfast dinku na kawo muku” “Awwn thats so sweet” Nana ta fada tare da bude Warmers din.

Mummy tace “ina Yaro? Yazo in aikeshi Bank” Nana tuburne fuska tace “haba Mummy daga Aurenmu har zaki fara sashi ya fita, wai yaje wani bank? Tabdijam, to ai be gama hutun ba, besides jiya kwana mukayi muna abu daya so please ki barmu mu shana, in kuma naga zaki matsa mana, zansa Dad dina ya mana processing Visa mu bar k’asan” da sauri Mairo tace “No, no basai kinyi haka ba, sak’on nawa can wait, enjoy your breakfast” Byebye nana tace mata tare da binta a baya tana fita ta danna k’ofa ta sa Makulli tace “ba zai fito din ba” ta matsa wurin toilet tace”My Majeed, breakfast is ready”

*

Bari dai ta shirya ta kai kudadden nan banki, dama jira take komai ya lafa sai akai banki, to gashi Abdulmajeed bai da dama, ita zataje tunda Abba baida lokaci.

Takalma ta zira ta kira Falalu direba a waya. “Ka fito da mota zamu fita”. Ta sauko kasa tana kwas kwas, kamar daga sama ta hango Zaineema ta nufo ta a guje, ta rungumeta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya. In hankalin Hajiya Mairo yayi dubu to ya tashi, jiki har ya fara rawa, Rayuwarta, bata son kukan Yaranta, bata son tashin hankalinu, tana mamakin me ya sa Zaineen ta kuka, tana tunanin irin hukuncin da zata ma duk wanda yayi sanadiyar zuban hawayen diyarta, jikinta har rawa yakeyi, “Zaineema, kiyi shiru ki gaya min waya tabaki, me aka miki?” cikin Kuka Zaineema tace “Mummy, Khaleed ya sakeni”  ta sake fashewa da wani kukan.

Mairo ta lailayo ashar ta zuba, tace “da kika mishi uban me? Sai da ya maidaki bazawara zaice ya sakeki? To wallahi ba zaiyiwu ba share hawayenki” hayagagan da Mairo keyi ne ya fito da AbdulMajid da Nana, ganin Zaineema na kuka suka ci birki Gabansu, AbdulMajid ya juyo da ita gabanshi yace “Zaineema meya faru? Me aka miki? Ko wani abun ya samu Khaleed ?” karaf Mairo tace “ai dama wani abu ya samu shegen, wai mu zai tonawa asiri, sakin Zaineema yayi” AbdulMajid ya doka salati, me kika mai Zainee?” Mummy cikin hasala tace “mai ko zata mai? Ya gama cin moriyar ganga mana, wallahi sai naci mutuncin Khaleed, sai na watsa shi, sai na mai abunda zaiyi nadaman furta kalmar Saki ga Zaineema”. AbdulMajid yace “Mummy Calm down, ki bari ayi komai a tsanake, ba mu san me ya hada su ba, ke Zaineema, me ya hada ku daga komawanki  Kaduna Sunday?” kasa magana tayi, Mairo tace “yo me ko zata mai, ita da ta koma jiya, kuma tace ko da ta zo biki bai gari? Me zata mai? Ko don abokinka ne?” Majeed bai kulata ba ya kalli Nana yace “take her to her room” Nana ta ja k’awarta sukayi daki. Majeed ya bar Mairo sai huci take tayi, ya latso numbern abokinshi Khaleed har ya gama ringing be dauka ba, kafin ya sake wani kiran, wayan Daddy ya shigo wayarshi, a ladabce ya dauka da Sallama, daga bangaren yace;

“Waalaikum Salam, Abdulmajeed, ina Mummynku ne?” AbdulMajid ya sa wayar a handsfree yace “gata tana jinka” yace “Maryam, kudin da Alhaji Nakowa ya kawo shekaranjiya nawa ke ciki?” Mairo cikin damuwa tace “inajin Miliyan 20 ne, ya akayi?” yace “Fanaz Ventures suke so a raba shares din Abba-fanaz Shares, zasu saida ne saboda wani emergency, shine na ga why not mu siya shares din, sai mu zama mallakin joint stocks din duka?” Mairo tace “hakan ma yayi” yace “ai ba a kai ga kai kudadden nan bank ba ko?” tace “da yanzu nake shirin zuwa” yace “good, yanzu AbdulMajid ka kawo min Kudin Office”.

 

AbdulMajid yace “to Daddy” Mairo tace “Kudin ma nan cikin store din dakina” Abdulmajeed ya wuce daki, Mairo ta cigaba da cewa “Daddy Akwai Matsala” yace” Subhanallah Maryam, wata irin matsala kuma?” “Khaleed ya tona mana asiri, ya saki Zaineema” Salati Alhaji Abba yayu,yace “mai ya auku?” tace “koma meye, zan bashi mamaki” yace “Aa Maryam, ki bari ayi komai a tsanake, barin gama da Office inzo, sai muji ta bakinsu, ba zai gagara ba sai a shirya tsakaninsu” kafin tace wani abu AbdulMajid ya baiyana yace “Mummy ni ban ga wani Ghana must go ba” dam gabanta ya buga, tace “yaro yana nan a cikin store din, da hannuna na sashi a ciki” Majeed ya koma chan kuma ya sake dawowa, yace “ba fa ya nan, maybe kin kai Office din Daddy” da mamaki, jiki a sabule tace jeka chan din ka duba, ba wai don ta yarda ta kai chan din ba, da azama ta nufi store din dakinta, taga Wayam, ba ghan must go, daga kai din da zatayi taga wayam, ba Jewelry kit dinta, ta duba ta duba ba Akwatin Sark’okinta,nan da nan ta rude ta fita hayyacinta,a sama taji muryan Majeed yace “Mummy ba komai har a office din” Mairo tunani ta shiga yi, kwatakwata ta dauke dif, bata gane komai,kanta na wani irin sarawa,tabbas an shigo gidan nan an yashe su, nan ne maajiyarta, komai dinta na store din nan, zuciyarta ta amince da Barayi sun shigo gidan, “Inalillahi wa ina ilaihir rajiun ta furta a hankali” kamar wacce aka tsikara,ta zaburo a guje ta fada Office din Daddy, gun safe dinshi ta nufe, ta bude, Wayam taga Cikin safe din, Shikenan ta faru ta kare, wani irin zufa ya keto mata, fincike dankwalinta tayi, ta sa hannu cikin gashinta ta yamutsashi kamar tababbiya ko da yake dakyar ne in ba ta tabu ba, AbdulMajid da ya bkyota ciki yana kallonta yace “Mummy? Daddy ya dau documents din cikin ne, naga safe din Empty?” kamar ta6a66a tace “Yaro, sun yashe mu, sun watsa mu, wallahi sun kwashe komai, shikenan ta mu ta samemu” kamar daga sama sukaji Muryan Nana na cewa “Ashe Zaineema kwarto Khaleed ya kamata dashi a daki shiyasa ya saketa” kamar an  tsikara Mairo ta sa hannu akai ta kwallara ihu, kafin Majeed yayi wani yunkuri tuni Mairo ta arta a guje, bata ganin gabanta, ita dai gudu takeyi, daidai Staircase tayi wani tumbling, ta dinga gangarawa har sai da ta ci karo da bango, nan take ta fara b’ulbular da Jini, da k’arfi Majeed yace “Mummy”.

 

Bibilicious lovers, ga Babi na sha hudu? Kar fa kuce Mairo bata baku tausayi ba, dandan, nidai ta ban tausayi, bari maga su wa zasu tayani yi mata kuka.

Vote Vote and Vote Please.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

[12:07, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg1⃣5⃣

 

Cike da tashin hankaki, Majeed ya dinga harhada stairs bibiyu ya sauka ga Mummynsa, gabaki daya ya tallafo ta jikinshi, bai damu da jinin da ke 6ata mishi kaya ba, hawaye yakeyi, ganin Mummy bata Numfashi ya sa hankalinshi tashi, Zaineema da Nana suka karaso gun, sai ihu suke tayi,tuni Majeed ya daka musu tsawa, yace “ku mahaukatan ina ne? Mtsww, Nana je ki ki fiddo mota ki matso dashi k’ofa, Zaineema, get Dad on the phone” ba su bashi amsa ba kowa tayi yanda yace, Majeed daurewa kawai yakeyi, yana kiran “Mummy stay with me please” Chak ya dauketa ya fita da ita, daidai zuwan Nana da Mota baya ya saka Mummy, Nana ta shiga ta ja Motan, Majeed yace “Zaineema ki jira zuwan Daddy”.

*

 

Emergency aka karbi Hajia Mairo, likitoci ne tsaye kanta, da k’yar suka samu suka tsaida jinin da ke zuba a goshinta, Jini dai ya zuba sosai, Majeed ya rasa gun zama, yayi na yayi chan, sai safa da marwa yake tayi, Nana tayi k’okarin kwantar mai da hankali, amma ya k’i yarda, daidai nan Daddy da Zaineema suka k’araso, a reception suka iske su, Duk suka bi sahu, chan Dr ya fito hankali a tashe duk sukayi kanshi suna tambayan ya take? Cike da jimami yace “I’m sorry, theres nothing we could do,we lost her” Zaineema ta zabura a guje tayi dakin da taga Dr ya fito, Daddy duk yabi ya rude,ya fita hayyacinshi, jikinshi rawa yake, hawaye na bin kumatunshi, Yana Son Mairo fiye da Rayuwa da kanta, ina amfanin rayuwarshi in Mairo bata ciki?. Bakin Majeed bai fasa kiran Allah ba, “Inalillahi wa ina ilaihir rajiun yake maimaitawa, a hankali ya zame k’asa yana hawaye, Nana na kuka ta tsugguna gabanshi ta rungumeshi, a kafadunta ya ke kuka, rayuwa ta mai k’unci, shikenan Mummy ta tafi ta barsu, Shak’uwarsu da Mummy ya wuce tunanin me tunani, yasan his Mom is not all perfect, amma to him, she’s the best Mother in the whole wide world, tausayin Daddynsu ya rufeshi, tausayin k’anenshi, Ziyada, Zaineema da zafin zai zame mata biyu ga rashin Miji ga rashin Uwa, Dan autansu Muhsin, da wacce Mummy tafi kusanci da ita wato Zinatu.

 

Jijjiga Mummy Zaineema keyi tana kuka, da k’yar Daddy ya shigo Dakin ya kife kan Mairo yana kuka mai tsumma zuciya, Abdulmajid ya shigo, ya kallesu, kuka yakeyi amma ya daure yace “zaa tafi da ita gida ayi mata wanka don kaita makwancinta” kukansu ya tsanantu gaba daya, haka aka gungura Gadon Hajia Mairo har harabar Asibitin, aka sata bayan Mota aka tafi Abba Abu’s Mansion.

 

Ziyada ta shigo gidan da gudu, tana Makaranta Zaineema ta kirata a waya, a rayuwarta, bata ta6a shiga motan haya ba sai yau,a Parlorn k’asa aka shimfide Mairo, tana zuwa ta fada kanta tana jijigata, sai da Majeed ya rungumeta ya na shafa bayanta “Ya Majeed, Mummy ta tafi ta barmu” “Shhhh Ziyada” hankalin Majeed yayi k’ololuwa guj tashi da yaji Zinatu ta k’wallara Ihu ta fada kan Mummy, shigowar su kenan ita da Muhsin, Falallu direba ya daukosu, kuka Zinatu takeyi tana birgima, shima Muhsin Kuka yakeyi bawai don ya fahinci meke faruwa ba, shi dai ya ga Mummynsa kwance a k’asa. Kan Majeed ya fara Zafi, da dabara Mom din nana ta janye su tayi sama dasu don yanzu zaa yi mata wanka. Daddy da Majeed ne zasu wanketa.

*

 

Indai Idonshi ba gezau yake ba, indai lafiyar idonshi k’alau to shakka babu ya ga Hannun Mummy ya motsa, motsin ya sake gani, da sassarfa ya k’arasa gunta yana murmushi, “bata mutu ba, wallahi bata mutu ba” hankalin su gabaki daya ya dawo kan Majeed da yake k’okarin ciccibar Mummy, a tare sukace “Ba ta mutu ba?” Majeed na tafiya da Mummy a hannunshi yace “mu koma Asibiti” duk suka rufa mai baya. Ba asibitin da sukaje dazun suka zo yanzu ba, wani sabon Asibiti ne a Maitama, nan da nan aka karbeta aka hau aiki kanta.

 

An samu ta dawo hayyacinta, kafin aka basu daki a ICU, Dr ya shaida musu cewa “ta kamu da hawan Jini wanda ya zoma ta farat daya, sai doguwar Suman da tayi, gashi ta zubar da Jini da yawa, yanzu an samu Bp dinta ya dawo normal, so a barta ta huta”. Majeed ya bashi tabbacin ba zaa dameta ba, ta Windown dakin suka lek’ata, Hannunta sanye da Cannula bangare daya ana mata karin ruwa,dayan bangaren kuwa ana mata k’arin Jini, sai Hancinta manne da Oxygen mask, 3in1 kenan.(Hmm lallai su Mairo Ashe akwai sauran kwana)

 

Kwanan Mairo Uku a Asibiti ta farfado har ta fara magana, bakin ta na budewa ba salati ba ambaton Allah sai cewa tayi”Shikenan mun talauce, sun yashe mu” da gudu suka yo kanta suna kiran “Mummy”ta kallesu one by one tace “kar ku damu, ba zaku zauna ciki talauci ba, Mummy zata samo hanya, ba ku gaji talauci ba, ba kuyi sabo da talauci ba, ba–” Daddy ya katseta “haba Maryam, daga farfadowanki?” “mu bamu damu da ko zamu talauce ba, kar mu rasaki Mummy” cewar Ziyadatu, murmushi mai ciwo tayi tace “Ziyada, ba zaki gane ba,Documents din da ka sace a Office din Daddynku, Ownership Shares din Hadin guiwa ne, Ba Daddynku kadai ke dashi ba,to an daukeshi,kuma each share zai kai kimanin Miliyan Talatin, kwanaki an sace Motar Yayanku, wanda a ciki akwai Muhimman takardun Companies din Furnitures har biyu, me ya rage mana?” ta sauke naunauyar ajiyar Zuciya ta kalli Abba kafin ta kalli Majeed tace “kuyi hakuri, amma naci bashin Banki har Miliyan 15 ba tare da saninku ba, lokacin da ‘yanfashi suka tare Boy, nayi zaton bussiness din mu zaiyi k’asa, kila ma har a kai ga kulle Companies din, shiyasa naci bashin, da niyyar in an farfado mu biya banki,gashi yanzu ba da komai, bamu da komai,gashi Zaineema ba Aure, Asirinmu ya gama tonuwa” ta fashe da kuka, Zaineema da Ziyada suma kukan sukeyi,Ziyada tace “Mummy, akwai Allah, mu fawwala ma Allah komai, komai zai yi daidai, wannan ce kalar Kaddararmu, wannan kaddarar ce ta shigo RAYUWARMU,mu rungume shi hannu bibbiyu, kuma InshaAllah Allah zai bamu mafita, besides ai Yaya na aiki” Mairo Kina tunanin kwangilar Zanen Gidaje da Tituna da Yayanki ke samu jefi jefi ne zai rik’emu? Ziyada, ke yarinya ce, har yanzu baki san rayuwa ba, ina muku tsoron talauci” Majeed tausayin kansu ya rufe shi, yayi saurin kwakulo murmushi yace “Who cares if we are Rich or Poor? What matters is that we’ll be together always and forever” Ziyada tace “We’ll stand by eachother’s sides” Daddy yace “Allah ya muku Albarka” suka amsa da Amin, Mummy ta tabe baki, a ranta tace “hmm, kudi sune komai, in ba kudi ba jin dadin rayuwa”.

 

Amsa sallamar da akayi sukayi, hankalinsu gabaki daya kan k’ofar, MD Fannaz Ventures ne da wasu mutane biyu,Daddy ya k’arasa gunsu yana musu sannu da zuwa, aka gaisa a mutunce, MD yace da Mairo “Madam ya jiki?” Mairo ta kwakulo murmushi tace “da sauk’i Alhamdulilah” “Allah ya k’ara sauk’i” suka amsa musu. MD yace “Alhaji Abba, maganan Shares dinnan ne, kace zaka ban kudin,in kudin be samu ba, kabani shares din ga masu siya nan” Zufa ya keto ma Daddy, zaiyi magana Mairo tace “MD, donAllah ka bamu lokaci, wani ifti’la’i ya afko mana, amma InshaAllah zamu biyaka” MD yace “Hajia Mairo kenan, nima iftila’i ya auko min na karayar Azziki, a halin yanzu, Mahaifiyata na fama da Cancer za mu fiddata Egypt, ko da suka mana budgeting kudin, ana bukatan Miliyan 20, saboda Cancer din ya kai Stage 8, Chemoteraphy din na tsada, tsakani ga Allah banda isassun kudin da zaayi hidiman nan, shisa na yanke hukunci saida shares din a gaugauce” Dakin yayi shiru sai k’aran Ac din da sheshek’an masu Kuka. Daddy zufa ke keto mai, Mairo kanta yayi zafi, ganin ba me niyyan Magana Md ya sake cewa “DonAllah ku san yanda za kuyi dani, Mahaifiyata na cikin hali” shiru sukayi suna tunanin yanda zasu Samo Miliyan Ashirin, ba sa tunanin ko hade kudaden account dinsu duka zaa yi ba zai rufe miliyan biyar, Majeed ya ja iska ya fesar yace “Alhaji, zan kawo maka kudinka Gobe InshaAllah”.

Suka bi Majeed da Ido, MD yace “toh Allah ya yarda, Madam Allah ya k’ara sauk’i” ba ta amsa ba, sai bin shi da ido da sukayi, yana fita duk suka maido dubansu ga Majeed. Ya san bayani suke nema ya samu wuri ya zauna kana yace “Mummy, Daddy kunsan dai wannan Jarabawa ce daga Ubangijin mu,Karayar Azziki ne, so sai mun rungumeshi ko mun k’i ko mun so,MD na bukkatar kudinshi,Mummy kin ci bashi banki har miliyan 15,Mummy ta ya zamu biyasu duka?” ya kafa mata idanuwa yana son ta bashi amsa ido jawur tace “Boy, wallahi ban sani ba,ban san ya zaayi ba”a zuciyar ta kuma tana tunanin zuwa gun Bokanta don a rufe musu baki kar wanda ya sake musu maganan kudin da ake binsu bashi, zuciyarta kuma tace “tusa fa bata hura wuta”. Majeed yace “Mummy, Daddy, Muna da Azzikin da za mu biya bashi” suka ce ta ina! Yace “a sa Gidanmu a Kasuwa, a saida shi ayi settling masu bin mu bashi” Mairo ta zaburo da ga kan Gadon Asibiti, Jiri ya dibeta ya maidata kan Gado, tace “AbdulMajid, a saida Mansion? Tabb so kake asirinmu ya tonu?” Majeed cikin dacin rai yace “Asirin ki zaifi tonuwa if you go bankrupt, don terere zaayi dake, gwara bakinki  alekum a saida a biya mu koma Gida Kano, Daddy ka fada mata” Alhaji Abba, ya hadiye Miyau yace “Maryam, hakan ne mafita,hakuri kawai zamuyi, kinga MD a gaugauce yake son kudin nan, idan baa samu ba ba mu san abun da zai iya yi ba” kan Mairo ya shiga sarawa tasan basu da wani mafita da ya wuce wannan, ba abun da tafi ji kamar zama abun kwatance wurin kawayenta, ba yadda zatayi illa ta amince a saida Gidan.

 

PH Nigeria

 

Zaune kan Parlor ya daura k’afa daya kan daya yana karkadawa, hannunsa rik’e da gwangwanin lemu yana kurba, kallo daya zaka mai ka san jin dadi ya mai yawa,balle yanayin da yake ciki yanzu, farinciki da annashuwa kadai ke fuskar,yana da Labarin wainar da ake toyawa a Abuja, Musamman labarin doguwar Suman da Mairo tayi har an zata ta mutu, labarin ya sa shi farinciki matuk’a, jefijefi ya kanyi daria a ranshi yace “ai dama an rufeta tayi mutuwan da ba shiri” chan kuma yace “ai gwara ma da Allah ya sa ba lokacinta bane yayi, don Mutuwa hutu ne gareta, bata gama girbe abunda ta shuka ba” wayarshi tayi k’ara, ya sa hannu ya dauka “Idi” daga bangaren akace “Hello Oga, sun sa Gidan a Haya, shareholder dinnan Fannaz ya bukaci Share dinshi” Zaid ya murmusa sosai yace “A siya Gidan, suna buk’atta sosai, so nothing higher than 50million”. Idi yace ” Okay Sir” Zaid ya latse wayar yana jin kanshi cikin wani irin Jin dadi, a hankali a hankali komai na tafiya mai yanda yake So.

Dayan wayanshi ya ciro ya kira Managern Sadam Audu Orphanage house, Cikin muryan Nine Oganka Zaid yace “Ana Bukkatar wani abu a Gida?” Manager yace “Aa ‘yallabai komai akwai” Zaid yace “zan turo kudi ayi Ordering Swings(Liluna) da kayan wasan Yara, sannan a kwashe yaran Weekends akai su wurin shak’atawa,ayi treating dinsu sosai, a siya musu Popcorns da icecream, su ci pizza sannan ka biya da su boutique a siya musu kaya,idan na samu lokaci zan zo” a ladabce Manager yace “Zaayi yanda kace, Allah ya kara budi, ya daka da Alheri, Allah ya ji kan Gatan Marayu” Zaid yace “Ameen Nagode, yauwa, munyi magana da Goggo, tace nan sashen Manya akwai Mata 3 da suka daidaita kansu da wasu a nan cikin Gida,sai daya kuma mallamin Islamiyansu ya ke sonta, ni bansan Gori, amma goggo tace anyi bincike sosai kan Malamin, ba zai bada matsala ba tunda ya san Asilinta yace yana sonta, ina so kaje ka shaida ma Malamin cewa ‘amincewa da Aurenta yana nufin bashi ba mata kallon kaskanci don ta fito daga gidan Marayu,kar danginshi su wulakanta ta ko su yada maganar da zai bata mata rai, yin hakan barazana ce ga shi da danginshi gaba daya, zan sa a daure su, in ya amince sai a bashi ita” Manager yace “Allah Sarki Gatan Marayu, da kana da rai da ka ga Yaronka ya zama abun Alfahari, be bari marayunka sun tagaraya ba, be watsar da alamuransu ba, ya tsaya musu, ya nuna musu Suma ‘ya’yane,sun ma fi wasu da ke gaban Iyayensu Jin dadi, Allah ya saka da Alheri ya k’ara girma” a tak’aice yace “tura ma Yakubu Matan nan da zaa aurar, suje Company su zabi irin Gadaje da kujerun da suke so, a musu duk abunda suke so, su kuma mazan a hada musu lefe, sannan a basu gidaje a Compound inda zasu zauna” Manager yace “InshaAllah ‘yallabai, zaayi duk yanda kace”. Zaid ya latse wayan, ya dauko wata ‘yar waya ya kira Company dinsu na Bauchi.

*

 

I N D I A

 

Shopping suka je ita da Vijhay yi ma Maama siyayyan Groceries, kamar daga sama taji wata na Hausa a gefenta, da sauri ta kalli gefenta, Budurwa ce da ba zata wuce tsararta ba,Wankan tarwada ce, sanye take da Jallabiya Milk color,l, da sauri Najwa ta k’arasa gunta.

“Wallahi Mama India ba dadi, ji nakeyi kamar nayi shekara a ciki, abincin nasu ba dadi, spices dinsu na sani amai, banda indomie, da biscuit ba abunda nake iya ci, yanzu ma nazo Kasuwa, bari dai Mama in koma gida mayi waya, a gaida kowa” ta latse wayar, ganin wata ba indiya tayi a gabanta tana kallonta kamar zata hadiyeta, ba tayi mamaki ba, don a kwanakin da tayi a India ta lura da su Mutane ne masu gulman tsiya, da sunga fatar da ba tasu ba, sun dinga kallonsu kenan, ta sakar mata da Murmushi tare da rabata don wucewa, a fili tace “Shegu Magulmata” Najwa ta murmusa tace “Waiyo Allahnmu, me mukayi ake zagin mu?”. Chak ta tsaya don mamaki ta maido dubanta ga Yarinyar da tayi magana tace “Hausa naji kinyi?” Najwa ta murmusa tace “Hausan da kikayi ya jawo ni gareki” da mamaki tace “Naga kamar ba indiyace” Najwa tace “itace” “to ta ya ki ka iya Hausa?” Najwa ta mik’a mata hannu tace “Sunana Najwa Sada” yarinyar tace sunana “Aisha Danlami” Najwa tace “me ‘yar wace k’asa ce?” Aisha tace “Nigeria” dadi kamar ya kashe Najwa, ta rungumeta kamar ance mata ga Zaid gabanta, Aisha dai ta bita da kallo.

Muryan Vijhay Bhai taji inda yake cewa “Najwa chalo chalate hain(ki taho mu tafi)” dafe kai tayi tace “main aa raha hoon(gani nan zuwa)” Aisha ta kalleta da mamaki tace “kin fara ban tsoro, ga hausa ga India?” “I speak 4 languages” Aisha tace “Wow,ga turanci” Najwa tayi daria tace “Aisha, ina so mu zauna dake, ina da tambayoyin da nake son miki game da k’asarki, i know we just met, you dont know me, i mean no harm, ina so ki taimakeni, ki bani lokaci mu hadu please, yanzu sauri nakeyi Maama na gida tana jiran dawowa na, da munyi magana yanzu” Aisha tace “laah bakomai,sai ki zo SUNY Delhi ina Hostel, we can talk.ki ban numbernki sai in kiraki ban rik’e numbern ba” Najwa tayi dialling Numbernta a wayan Aisha, ta mata godia sukayi Sallama.

 

A B U J A

 

“50million? Majeed kana hauka ne? Ta ya zaka saida gidan nan Miliyan 50? Ko Million dari ne ai yayi kadan” Hajia Mairo ta fada rai a 6ace kamar ta bigi Majeed. AbdulMajid ya furzar da iska yace “Mummy, its urgent, i had to sell it, kinga nayi settling bank, na kuma kai ma MD kudin Shares dinshi 30million, yanzu saura 5mil” Mairo ta daka tsawa tace “Uban me miliyan 5 zai mana” Daddy yace “Zaayi settling maaikata fa, kar ku manta” Kan Mairo yayi zafi, tace “a zo a Sallameni, naji sauki” Majeed zaiyi magana tace”a sallameni ko na Sallami kaina”.

*

Nana ba zaiyiwu in dinga hidima da gidana ba inyi da Gidan Sirrikanki, kince na basu Miliyan 20 na basu, ba laifi na bane da aka sace, ba zaiyuw in kara musu ko dubu dari bane, yanda karayar Azzikin nan ya samesu, anya ba zaa raba aurenki da Majeed ba” Nana ta daka tsalle tace “Wallahi baka isa ba, to dama Kudinsu na aura? Kaine fa babana, na san da mun fi su kudi nesa ba kusa ba amma na amince na aureshi,Son shi nakeyi kamar raina, so ko da k’asa suke ci zan zauna dashi, kuma zan bishi Kano, in kaga daman taimaka musu to, nidai ba zan rabu da Mijina ba” ta tashi fuu ta fice daga gidan.

*

 

Bayan kwana Biyu Motar kwasan kaya 3 suka kwashi kaya don tafiya da shi Kano, ranar Mairo da ‘yayanta sun ci kuka, ganin zasu bar Wannan wurin da sauke kira ‘HOME’ Mairo ji takeyi kamar rayuwarta na gab da k’arewa, suma suka shirya suka kama Hanyan Kano banda Majeed da Daddy da sukayi branching a Kaduna inda zasu tsaya gun Mijin Zaineema, tunda sun ta kiranshi a waya baya dauka.

*

Khaleed na Parlor yaji Sallaman Amininshi AbdulMajid Abba da Abba, ba yanda ya iya Illa tarbansu a mutunce, bayan gaisuwa, Majeed ya k’are ma Khaleed kallo, sosai ya rame, yayi baki, tausayinshi ya kamshi, ya san yana son kanwar shi Zaineema. Majeed yace”munzo ne muji abunda ya faru tsakaninka da Zaineema,ta rantse mana da Allah, khalid wallahi sai da ta rik’e Izifi Sittin ta rantse da Allah kan cewa bata da masaniyan abunda ya faru” Khaleed yace “AbdulMajid kasan yanda nakeson Zaineema ai? Ba zan mata sharri ba,wallahi da idona na ga kwarto a dakinta kwance kan Gado” Abba ya runtse ido, yace “Mallam Khaleed, kai ka ga abunda Ka gani, ba zamu k’aryata ba, amma tambaya daya da zan ma, shin ka gansu kwance kan Gado tirmi da tabarya?” Khaleed ya girgiza kai Abba yace “Manzon Allah yace Shaidan da ake zargin  Mazinata da aikata Zina, shine a gansu kwance turmi da tabarya, Khaleed ba wai na karyata ganinka bane, amma ba ka tunanin akwai abokan gaban da suke son ganin bayan aurenku? Baka san hassadan mai hassada ba? Baka san sharrin me sharri ba?” Khaleed zuciyarshi ta kasu kashi biyu, daya ta na son gasgata Hujjojin Daddy, daya kuma yana hanashi yadda da hujjojin, inda take cewa “Babanta ne, zai iya cewa komai don ganin ka maida diyarshi dakinta” ya dai muskuta yace “Daddy, kasan ba aure in da Zargi, jin nauyinku ko duba Alakata da AbdulMajid bazai sa in kwari kaina ba, tsakani da Allah ban yarda da Zaineema ba, duk da ban taba kamata da wani hali ba kafin wannan, ba zan maida Zaineema daki na ba, sai na ga k’wakwarin hujjan cewa wannan ba ita ta kawoshi ba, kuyi hakuri donAllah, ina son Zaineema amma son ta ba zai sani makancewa ba”. Daddy zaiyi magana Majeed yayi saurin cewa “Gaskia ne Khaleed, Allah ya baiyana gaskia duk inda take” Khaleed ya amsa da Amin, ya san Majeed me saukin kai ne, Majeed yace “bari mu tafi, a hanya muke” *nan da Abuja dai?” “Aa mun bar Abuja Kano mu ka nufa” nan sukayi Sallama.

*

Gidan dai na nan yanda yake, ba abunda ya samu gidan, shara kawai akayi akwa wanke gidan don da ma su kanzo hutu, suka jera kayyayakin su, da Majeed suka iso ya samu Zaineema a daki ya mata Nasiha da ban hakuri, Mummy ta gama banbaminta tace “ko shine autan maza ya gama aurenta” Zaineema tace “Wallahi sai dai in be dawo ba” Mummy tace “mara zuciya” Zaineema ta murguda baki tace “naji din”.

 

I N D I A

 

Maama ta lura  da Dadin da Najwa keji, da ta tambaye ta me ya sata farinciki sai tace ” kawai dadi nakeji” sai tayi daria tace “Najwa ina son dariarki” ita kuwa sai tayi darian.

Gaskian lamari Waya sukayi da Aisha Danlami, inda take shaida mata zata zo makarantarsu, tace “zan shiga Aji amma 12:00pm zan gama” Jira takeyi 12 tayi ta tafi Jami’ar su Aisha, kafin lokacin ta tsaya sai hotuna take tayi. 12 na bugawa na ma Maama k’aryan zuwa Gidansu Najwa.

 

 

 

Tafian minti 45 Najwa tayi, bata sha wuya ba ta gane Hostel din mata, sukayi waya da Aisha ta gaya mata inda take, Aisha ta sauko suka hadu tare da rungume juna, suka tafi dakin Aisha, Aisha ta dafa musu Noodles sukaci tare, in ka gansu sai kayi zaton sun dade da sanin Juna.

Najwa tace “Aisha tell me About you” Aisha tace “lol, sunan Aisha Danlami, ‘yar Nigeria ce, I’m 18years, last 2weeks nazo India, Karatu ya kawoni, i miss home” Sukayi daria sosai, kafin Najwa tace “wani gari kike a Nigeria?” Aisha tace “Katsina” Najwa ta maimaita sunan gari tace “Nikam States nawa ne a Nigeria? Aisha tace “36 states” Najwa tayi shiru ta na wani tunani. Aisha tace “Baki gaya min ba Najwa, ta ya kika iya Hausa, India, English” Najwa tace “Well, Iyayena Yan Nigeria ne, but anan muke zama, as a matter of fact, a nan aka haifeni, so i was born and raised here” Aisha cike da doki tace “Ashe ku ‘yan Nigeria ne, yan wani gari ne ku?” Fuskan Najwa ya chanza tace “Wallahi I dont know” Aisha ta kalleta tace “how comes baki taba zuwa bane?” Najwa ta gyada kai tace “i’ve never been there” Aisha tace “atleast zakiji Mamanki ko Babanki na fada” Najwa da fuskan tausayi tace “they cant remember, kawai sun san su yan Nigeria ne, and ba sa iya zuwa, ko sunyi shirin zuwa, sai su kasa wani abu na faruwa da su one way or the other sai suji sun kasa zuwa, tunda aka haifeni har yanzu.” a takaice Najwa ta bata labarinsu da k’uddirinta na zuwa Nigeria, Aisha tayi shiru tana sauraron Najwa da tausayi tuni ta dago bakin zaren, Najwa tace “Shiyasa nazo ki dan yi min Bayanin yanda Nigeria yake, saboda zanje neman Yayana, kinga Kullum Maama na cikin zubar da hawaye take”.

Aisha ta ja iska ta fesar tace “Najwa, ga yanda naji labarinki, sai na san cewa Aikin Asiri ne ke cin Mahaifanki” Najwa ta maimaita kalmar ‘Asiri’ tace “menene hakan?” Aisha tace “Sihiri” Najwa ta girgiza kai tace bata san meye hakan ba.

 

Aisha tace “I really dont know how to explain this to you, But Sihiri is more like Witchcraft, like someone can cast a spell on you, and make you do things you dont want to kingane” Najwa tayi shiru tace “I know Witchcraft, i know people do Cast Evil spell on others, but i dont think such people exist” Aisha tace “Tabdijam,ai Nigeria Gidan yi ma mutane Asiri ne, Let me tell you how  most Nigerians are like; da kinji Mijinki zai sake mata sai kiyi Asiri sai maganar auren ya watse, da kin ga Mijinki ya tara abun dunia, sai kiyi asiri ya zama a tafin hannunki, sai yanda kikayi dashi, in Nigeria we call such men Mijin Hajia, da kinga Wani yafi ki kwazo da k’okari wurin aiki, sai kiyi asiri ya zama wani wawa soko, Asiri ke sa Mata ke raba Miji da Matarshi, Baba da ‘yayanshi, Asiri ke sa ana haukata mata, Asiri ke sa ka shiga duniya kar ka sake waiwayon gida, no matter how you want to go back home you cant, why saboda an maka Asiri, in Nigeria we call it ‘Kurciya’ and this is what happened to your parent, an musu kurciya ne, shiyasa duk yanda suke son komawa suka kasa” Najwa da hawaye ya gama wanke mata fuska tace”Meyasa wani zai musu haka?they are too goof to be hurt like this” Aisha ta daga kafada tace “bansani ba, kila Babanki wani mai kudi ne, Abokin aikinshi na mishi hassada ya mai kurciya, it can be anything, su nasu ma is different tunda har suna iya tuna k’asar da suke, har suna tunawa da dansu, wasu ko idan aka musu Asiri, wallahi har sunansu suke mantawa sai dai suyi sabon suna yanda kika san me Amnesia haka ake komawa” Najwa tace “it can be it kam, sabida ba so daya ba so biyu ba sun sha zuwa Airport da sunan zuwa Nigeria sai wani abu ya taso, akwai Lokacin da har sunje Dubai, Maama ta dinga suma, tana ihu da akayi transit sai dai suka juyo” Aisha tace “You see, Sihiri gaskia ne, saboda amma fiyayyen hallita Manzon Allah kuma ya kamashi, to waye a duniya da zaa ma Sihiri be kamashi ba? Sai wanda Allah ya kare” Aisha ta yi ma Najwa bayani Sosai, ta amsa duk wata tambayoyin da ta mata, kafin ta dora da cewa “Yanzu Najwa, you have to think twice, shin zaki iya zuwa k’asa kamar Nigeria? Ke da baki san inda kika Dosa ba, baki san inda zaki fara neman yayanki ba, baki san kowa ba, ya zakiyi, can you do that, can you take the risk ?” Najwa ta hadiye miyau zukut tace “in hakan zai tsaida Hawayen mahaifiyata then yes i’m ready” Aisha ta jinjina kai tana yabon determination din Najwa, tace “yaushe ne tafian?” Najwa tace “saura kwana 8” Aisha tace “kafin nan, zan sanar da ke duk abubuwan da ya kamata ki sani game da Nigeria, you have to be strong, because Naija,we no dey carry last”.

 

Ghen! Ghen! Mairo an yi escape from mutuwa, Zaid terror me zakayi next? Majeed You’re too good, Najwa, kinsan ina kike shirin kawo kanki kuwa? Tammm.

 

 

#1love

#ADAY

#Bibiliciousfreakingfans

#ana tare

#nagode

 

Biebee Isa

[12:10, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg1⃣6⃣

 

K A N O

 

“Ya Majeed! Ni ba wani Makarantan da Zan shiga, ni Funtaj Schools dina nike so, ni bana son Kano, i want to go home, bana so” Zinatu ta karashe maganarta tana kuka.

 

Majeed ya dafe kai cikin murya me sanyi yace “Zinatu,This is our Home” cikin daka tsawa tace “I dont want it here,i hate this place”. “Zinatu Abba Abu,ki san yanda zaki dinga min magana, ni ba tsaranki bane”.

 

Mairo ta shigo dakin da sauri jin Hayaniyansu, Zinatu ta fada jikinta ta rungume, ” Mummy Ya Majeed na ta min fada yana min Ihu” Mummy tace “haba Majeed, don me zaka dinga mata Ihu? Nawa Zinatun take? Yarinya ce fa”

 

Majeed ya Girgiza kai, ba tare da yace komai ya fice daga dakin, ba ya son yanda Mummy ke shagwabar da Zinatu, sam bata da kunya,bata ganin kowa da gashin azziki. Ziyada ya samu a parlor kallo daya ta mai ta san ranshi a bace yake, ba kasafai ake ganin bacin rai a fuskan AbdulMajid ba.

 

“YaMaji” hakan take ce mai wasu lokutta, ya kallota yace “Zuzu” tace “kar Zinatu ta bata ranka, haka take, all thanks to Mummy, Zeenah bata da kunya, so in ka san halin mutum, sai kaci maganin zama da shi”. Majeed yace “Ba zaiyiwu ba kuwa, mu ne Yayyinta ba ita ta girme mu ba”.

 

“But shes only a child” cewar Mummy da ke shigowa dakin, suka bita da ido har ta karaso, tace “Zeenah tace bata son Karatu a anan, infact bata son Zaman Kanon, kar ku manta Ko hutu muka zo Kano Zeena ya dinga kuka kenan kamar zata mutu, shes just allergic to Kano, so zan san yanda nayi a barta a chan Funtaj din, maybe a saida wannan gida sai mu siya Gida a Abujako ba Kamar Mansion dinmu ba, kai ko Haya ne sai mu kama, tunda yaran ba sa son nan din”.

 

Majeed ya tsura wa Mummynsa ido, kamar ba zai ce komai ba sai can yace “Wai Mummy, me kikeyi haka? Yanzu sai kice duk abunda Zinatu take so shi zaayi mata? Ita ta haifeki kenan, Mummy wannan ba so bane ba fa, Shagwabata kikeyi da lalata mata tarbiya, Mummy, we are never going Back to Abuja again, dama chan zaman me mukeyi? Ba ayyukan duk suna nan Kano ba? We are in no competition with anyone, zaman barikin ya isa haka, Ba inda zamu, Ziyada kadai zata koma ta gama session dinta, befi 2weeks ba dama, daga nan sai a karbo mata transcript sai a nemo mata ko Northwest Uni ne, We wont leave Kano, nan ne Asalinmu, da sauran 5million dinnan zamu farfado da AA&Sons furnitures,zamu biya maakaita, sannan ayi enrolling yaran a makaranta, Mummy idan kika matsa akan haka, you are going to lose me, zan tafi inda ba zaki sake ganina ba”.

 

Yana kaiwa nan ya mike ya bar Parlorn, Ziyada ta rufa mai baya, in hankalin Mairo yayi dubu to ya tashi, tana mugun son Majeed, ba ta son yayi nesa da ita, ba zata iya rabuwa dashi, a karo na farko zata sadaukar da farincikin Zinatu, don gudun rasa AbdulMajid.

 

Da daddare, Majeed ya iske Mairo a dakinta ita da Daddy, yace “Mummy, Daddy Hilal Constructing Company ke neman Architectures Worldwide, shine zaayi Test da interview on Monday, so shine nayi applying, in Allah ya sa da rabo idan naci test din kunga komai zai zo da sauk’i ko?” Daddy yace “Gaskia ne, naga advertisement din a News, nayi tunanin maka magana, Ashe ka gani, yanzu sai ka fara shirin tafiya Dubai din?” yace “Nagode Mummy bakiyi magana ba” tace “hmm, Boy sai nake ganin kamar Dubai yayi nisa, in ka samu aiki a chan hakan na nufin kayi nisa da mu kenan?” ya kamo hannunta yana murzawa yace “ba lallai ba, kinga Drawings ina cikin dakina ma sai na tura musu chan ta internet, ba abunda zai rabaki da boy dinki” murmushi tayi tace “to Allah sa a dace” ya amsa da “Amin kafin ya sanar dasu gobe zaije Abuja processing Visa.

 

*

“Habawa Hajia Mairo, kinyi kudi kin manta Abokan ki na Azziki” Mairo tayi yak’e mai kama da kuka,l tace “haba dai Hajia Aliyah, ai ban kai in mance ki ba, kece fa Aminiyar Asali” “ashe kin san da hakan shine bayan tafiyar ku Abuja ko waiwayena baki sake yi ba shekaru nawa? Sai dai mu ganku a TV ko radio” “Haba Aliya, ki bar maida hannun agogo baya, gashi dai nazo yanzu” “to ya labari?” “komai lafiya lau, mun dan dawo nan da zama ne na wani dan lokaci ” Hajia Aliya tace “toufa, karayar Azziki kukayi? Don na tuna kince ke da Kano sai hutu” Mairo ta dan daburce “habadai karayar Azziki, kawai yara ne suke son Zaman nan, na Majeed yace Zaman barikin ya ishe shi haka, kuma kinsan zan iya komai don Yara na”.

 

Hajia Aliyah ta gyada kai bawai don ta yarda da bayanin Mairo ba, da Mairo taga shirun yayi yawa sai tace “Kawata, donAllah taya zanyi in karkato zuciyan Yaron wani k’usa a k’asar nan zuwa ga Ziyada da Zaineema?” Hajia Aliyah ta katse ta da cewan “Zaineema ta fito ne?” Mairo tace “Aa, Mijinta ya rasu ne” “Ayyah, Allah ji k’anshi”. Mairo ba ta son raini, bata son abunda zaayi ta surutu dashi a kanta da kuma yaranta, Balle In Hajiya Aliya Kunnen gari tahi, to kowa ma sai yaji, haka zata zama abun zunde da nune cikin kawayensu.

 

” Ai abu mai sauk’i ne Hajia, kudi zaki sake Sosai, na kaiki gun Na kan tundu, wanu sabon shigowa ne ya na nan, aikinshi kamar yankan wuk’a”, “Allah ko Kawata? Suka chafe, Hajiya Aliya tace ” Amma fa yana da Tsadar aiki, don daga aikin Miliyan daya sama yakeyi” gaban Mairo ya fadi, ina zata samo kudadden nan? Muryan Hajiya Aliya taji tana cewa “Aff! Na manta ku manya ne, ba ku da matsalar kudi”. Yak’e dai Hajia Mairo keyi tace “idan ta shirya zatayi mata magana ta rakata”.

*

 

“Mummy, ko shekara dari zanyi a matsayin bazawara, ba zan aura kowa ba, zan jira Khaleed ya dawo min, zan jira shi ya dawo gareni, i’ll wait forever for him”. Hajia Mairo ta girgiza kai, tace “Zaineema, please” Zaineema ta katse Mummy da cewa “Wallahi idan kika matsa min da Zancen Auren wani to Wallahi zan shiga duniya, Jahilci ne ma wannan ina Iddah ki fara min zancen Aure” Mairo tayi saurin cewa yi hakuri Zaineema abun be kai nan ba”. Sum sum ta tashi ta fice ta bar Zaineema a daki.

 

Mairo ta shiga damuwa sosai,ta hade kai da guiwa tana tunanin yanda duk abunda ta Gina ke falling apart,bata ankara ba sai ganin Nana tayi ta fito daga dakinsu janye da dan trolly, ta sa mukulli ta rufe dakin tare da jefa mukullin Jaka, Sanye cikin wasu riga da skirt damammu, sai gyalen da be wuce girman Jallabiya ba, Mairo da murmushi tace “Nana,kin fito?” ba tare da gaisuwa ba tace “Eh Mummy, Jigawa zanje tare da friends dina, my Majeed baya nan, i dont want to miss him, shiyasa zanje in dan huta kafin ya dawo daga Abuja” bata jira cewar Mummy ba ta wuceta, ita ko Mairo ta bita da ido, tayi amanna AbdulMajid be san da tafiyar nan ba, ya san da ya sani da jiya kafin su wuce Abuja da Ziyada da ya sanar da ita tafiyan Nana,mamakin Shiga irin ta Nana takeyi, ita tasan ba ta damu da shigar kowa ba, amma wannan Shiga ta Nana sam bata yi kama da ta ma su aure ba, wannan shiga ta nana yafi kama da na Goggagun ‘yan bariki. meke samun su ne haka? A baiyane tace “Meke faruwa da Rayuwar mu?”.

 

PH Ng

 

“Zaid please, ya kake so inyi? Son ka zai kasheni, meyasa ka za6i ka wulak’anta ni, da kyauna da ajina da kudina? Tun France nake ta bibiyarka, saboda kai na dawo PH uni don kawai na kasance tare da kai, na watsar da rayuwar daulan da nake ciki don kai, Zaid meyasa kake min haka?”. In Bangon dake jikin dakin ya amsa maganar da Nadiya tayi to Zaid ya amsa, kamar Allah beyi hallita a wurin ba, sam ko kallonta baya yi, harkan gabanshi kawai yakeyi,yana latsa Laptop inda yake karanta reports din da aka turo mai a Kano da Abuja, inda ya ga Majeed ya dawo da Ziyada Makaranta zata zauna a hostel har su gama exams next upper week,sai kuma Ganinshi da akayi a Dubai Embassy, Sannan tafiyar da Nana tayi Jigawa, Kallo daya Zaid ya ma Nana ya buga tsaki da k’arfi yace “yarinyar nan zata rusa min shiri fa” Nadiya rai 6ace ta rufe Laptop din, tace “haba Zaid, ina nan tsaye ina maka magana, hankalin ka na wuri wata ‘yariska?” ran Zaid ya 6aci, shiyasa baya son mata, ba su iya komai ba sai distraction, ba ya son ayi distracting dinshi, rai a 6ace ya kalleta yace “bana son ana distracting dina, tunda kika zo kike distracting dina, i dont remember inviting you, banason warin jikinki, bana son kallon fuskanki” ido cike da hawaye tace “Zaid, me kake nufi?” a tak’aice yace “a sauk’ak’e– Fita” tace “What?” a dakile yace “i wont repeat myself” fizgar jakkanta tayi hanyar k’ofa tana a”You’ll regret this” murmushin gefen baki yayi ya bude laptop din yana tunanin yanda zai 6ullo ma Nana, don in bebi sannu ba, Asirin Nana zai tonu, Majeed ya saketa, ita kuma bata mai aikin da yake so tayi ba, wanda shine dalilin da ya sa yayi sandaiyar Auren Nana da Majeed, to wai me Majeed yaje yi a UAE Embassy? Ko tafiya zaiyi? Yana son sanin ina zaije.

 

Bari dai ya kira Nana nan, daga bakinta zaiji Komai, Wayarshi ya dauko ya latsa numbern Nana, sai da ya mata missed calls uku kafin ta dauka da tsawa “wai wani daniskan ne yake kirana” cikin muryan shi yace “daniskan da ya koya miki yanda zaki sa Majeed Aurenki” tsaf ta ganeshi, to me yake so kuma, tunda kwalliya ta biya kudin sabulu ai bata da sauran bussiness dashi, tace “to ya akayi ne?” ya murmusa yace “Me Majeed zai jeyi Dubai?” tace “huff, mesa zan gaya ma sirrin Mijina?” yace “saboda nace ki gaya min, kar ki manta ni nayi sanadiyar aurenku, lokaci daya zan rusashi” tsaki tayi tace “you are very stupid, ba kai ka sa ya Aureni ba, kar ka kara kirana, Stupid” ta kashe wayar tana huci, waye wannan? Me ya dauki kanshi da zai dinga kiranta yana sata abubuwa ko tambayarta abubuwa?.

 

Wayarta ya sake kira, da tsawa ta dauka da niyyar cimai mutunci, muryan nan dai ne, yace “Nana Nakowa, you’ll apologise to me,ba a min ihu, ba a daga min murya, ba a zagina,apologise for calling me stupid, and finally ki gaya min mai Majeed zaije yi Dubai, i wont ask again”. Tayi daria tace ” i like your confidence, so ka matseni ka sani in fada maka” yayi murmushi yace “ba zan matseki ba, da kanki zaki gaya min, or maybe zaki ba Nimcy ko Salim su fada min”. A firgice Nana ta kalli Nimcy da Salim din dake kan Gado suna aikata Alfasha, baki na rawa tace “ina ka sansu?” yayi daria yace “kina nufin ina na san Kwarton ki? Da dadironki Nimcy, duk Kano be isheki ba ke da Salim sai da kukazo Jigawa wurin Nimcy?, what will happen if Majeed gets to know his Wife is a hypocritical b*itch Ehh?”. Da sauri tace “No,No, donAllah kayi hakuri,don’t tell him, Zan gaya ma all you want to know”.

 

“Good, ina jinki” tace “Majeed zaije yin wani Interview ne a HILAL Construction Company on Monday, shine yazo Abuja neman Visa” Zaid ya jinjina kai yace ” in har kina son cigaba da zama da Majeed, dole ki bar akuyancin nan, ki tashi ki koma Kano yanzu, and zan dinga kiranki if i need anything concerning the Abba Abu’s,you are to keep me posted kan duk abunda ke faruwa a cikin Gidan, and duk me na tambayeki ina son Ansa, ki ka kuskura kika gaya ma wani kuna communicating da some stranger, consider that karshen zamanki da Majeed, don zan tura mai pictures dinki ke da mutanenki, so go home now”.

 

“Wait donAllah mesa kake son sanin Details din Gidan Inlaws dina, please dont harm anyone, and please kar ka tona min Asiri, na bari, in kudi kake so zan baka ko nawa kake so, dont just harm My MMajeed” Zaid yayi dariya yace”Nana Nakowa, ina da kudin da zan siya Alhaji Nakowa, da duk abun da ya tara, Money aint my problem,so get your p*nties on, and go home”. Dif ya katse wayar. Nana sai zufa, Nimcy da Salim na tambayarta me ya faru tayi shiru ta k’yalesu, da azama ta sa kaya ta gyara jikinta ta ja Akwatin ta ta bar Gidan, kwanan da batayi ba kenan.

 

B A Y A N WASU K W A N A K I

 

I N D I A

 

“Najwa Nigeria k’asa ce mai girma, nasan dai be kai birnin Delhi ba, amma akwai Dumbin mutane, kar ki sake ki yarda da kowa, people there are manipulative, zaki gansu kamar na gari, Wallahi kar ki yarda dasu, kar ki sake ki gaya ma kowa sirrinki, kar ki sake kice ke bak’uwa ce kinzo neman Yayanki wani na iya cewa ya sanshi ki bishi ya tafi dake ya sayar dake a banza, I repeat dont trust anyone with your secrets, idan kun isa Lagos, ki siya Ticket din Kano, Kano tadabo, anan zaki fara binciken ki, komai zaizo da sauk’i InshaAllah, yauwa ki siya Simcard, ki saka a waya sai ki kirani, zan gaya miki what to do next”. Najwa ta gyada kai alamun ta fahimci komai. Sosai ta mata Godia, don ta taimaka mata Sosai, ta san abubuwa da dama game da Nigeria sanadiyar Aisha.

 

Gobe tafian Najwa, jirginta zai tashi k’arfe Shidda na Asuban Yau, Tsoro ya dira Zuciyan Najwa, ta rasa sukuni, tun ana Gobe tafian, ba zama, tayi nan tayi nan, ta hahhada Akwatin ta da School bag wanda cikin Laptop dinta ne, ta faki idon Maama ta Kai Shagon Vijhay Bhaiya, har bayan Maghrib tana gidansu Kaveri, Sun yi kuka sosai don zasu missing suna, Najwa ta shaida ma Kaveri kar ta damu, zasu dinga waya kullum. Haka suka rabu.

11pm

Tana jin shigowar Maama da Paapa dakinta, daidai kunnenta suka tofa mata adduar kariya, suka manna mata kiss a kumatu kafin suka gyara mata bargon da ta duk’unk’une dashi, suka fita. Hawaye ya sauko ma Najwa, tausayin kanta, da na Mahaifanta suka diran mata, ina ma ta fasa tafiyar, ina ma ta kasance da Mahaifanta daga gobe har abada? bata da mafita dole taje Nigeria, balle aski ya zo gaban goshi, daren yau ne tafian, duk yanda ta so tayi bacci kafin Alarm dinta ya tasheta k’arfe 4 ta kasa, haka tayi ta juyejuye tana kuka, da ta ga hakan ba zai amfaneta ba sai ta tashi ta dauro Alwala tazo tana nafiloli.

 

Kirrrr Alarm dinta ya k’ila, ta kashe tare da mik’ewa ta yana gyalenta akai, Wani kwarin guiwa takeji Yanzu, wayar ta ciro ta kira Numbern Vijhay, tace “”kya aap so rahe hain(bacci kakeyi?)” yace “Nahi (Aa)” tace “kaar taiyaar ho jao,main ab baahar aa raha hoon (ka shirya Motan, gani nan fitowa)” yace “Theekhai(Okay)”.

 

Cikin sando ta shiga Dakin da su Maama ke bacci, ta tsura ma Mahaifanta idanu hawaye na bin kuncinta, ta murmusa ta karasa gadon ta zauna gefen Maama, ta lalubo hannunta ta rik’e, cikin hawaye ta fara magana ” Maama forgive me! I cant see you in more tears, Zanje Nigeria, i’ll look for my Brother, i’ll find him and i’ll bring him home, I promise”. A hankali Maama ta bude idonta, ta kalli Najwa ta murmusa kafin ta maida idanunta ta rufe, Najwa ta durk’usa ta sumbaci Maama a goshi, kafin ta matsa gun Paapa ta mai kiss a goshi tace “ka kula da Maama kafin na dawo kaji? Allah ya hada mu da Alherinsa. Ta ciro farar takkada da tayi rubutu a ciki ta ajiye musu kan bedside drawer. Tayi Bismillahi tawakaltu Alallahi wala haula wala k’uwata ila billah” ta bar Gidan. Ta shiga Motar Vijhay tana kuka, shima idonshi ya kawo hawaye be ce mata komai ba, daidai gidansu Kaveri ta mata text “Byebye meri dosti”. Suka kama hanyar Airport.

Bayan sun yi boarding da komai, suka rabu da Vijhay bhaiya, bayan sun sha kuka tare, ta shiga Jirgi ta samu wuri ta zauna, bayab

clearance Jirginsu ya tashi zuwa k’asar Dubai inda zasuyi transit, su chanza Jirgi kafin Jirginsu ya tashi zuwa Lagos Nigeria. Tunda Najwa ta shiga Jirgin nan har suka isa Dubai Kuka take tayi.

 

D U B A I INTERNATIONAL AIRPORT.

 

Suna transit wurin 8:25am. Ta je wurin da ake buga International calls, sai da ta kira Kaveri, kafi ta kira Aisha, sannan ta Kira Mamma.

10:40 am suka fara Boarding Jirgi, har yanzu kuka takeyi, fuskarta tayi Ja,duk da wayar da tayi da Maama hankalinta ya kwanta, amma tana cike da tsoro, dagasken dai ta bar Gida, Allah ya taimaketa, har ta zauna kan kujerar Jirgi kuka takeyi, da ta tuno wani Abu sai ta fashe da kuka, alamun zama da akayi a gefenta ne ya sa ta share hawayenta, tashi tayi ta mai Alama da zat wuce ya gyara ta wuce toilet ta wanke fuskar ta, ta bi Mutanen da ke zaune a Jirgin Emirates, yawanci bak’ake ne ‘yan Nigeria, ko don kasar su a ka nufa? Oho, ta dawo ta zauna.

 

Na kusa da ita ta ji yana waya cikin kwanciyar hankali “Hello, ya Exams? Ayyah Allah ya bada saa, No ta lagos zan sauka, kinsan ba ta Abuja na tashi ba, eh, InshaAllah, ki maida hankali ki gama Jarabawan, Allah bada Saa, Ameen Nagode” ya latse wayar ya sake lalubo wani numbern “Hello, yanzu zamu taho, Ameen ya Allah” yana ta waya har aka bada umurnin kashe Waya Jirgi zai tashi, hankalin Najwa ya sake tashi, ta fashe da wani irin kuka me ban tausayi wanda na zaune da ita sai da yaji karan kukanta, a hankali ya juyo dubanshi gareta, be san meya sata kuka ba, amma bari ya barta. Haka ta cigaba da kuka na tsawon lokaci.

 

Da ya ga bata da niyyan tsayawa sai ya dan tabo hannunta, ta dago tana zubura baki tana goge hawayenta da tafin hannunta, gani daya sai ta mishi kama da kanwarshi idan tana shagwaba, da ta lumshe idonta ta bude sai ya ga ta mai kama da dayar kanwanshi idan an bata mata rai, sai ya murmusa tare da zaro hanky a jikin Aljihunshi yace “Kin dade kina Kuka, kukan ya isa haka, Oya share hawayenki, biggirls dont cry Ok?”.

 

*******

Hey Fans, what just happened? I cant believe it, Waye wannan? Kar kuce mun sun hadu, su waye suka hadu yanzu, Guess muga ko daidai ne.

Next page zamuji yanda me Najwa da Maama suka tattauna akai da ta kirata waya.

 

Najwa Welcome To Naija.

 

Gaskia Akwai Ghost readers cikin masu karatun nan, donAllah ku taimaka, yanda nake faranta muku rai, donAllah nima ku faranta nawa by b and Commenting.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#gwslubnasufyan

#Nagode.

 

Biebee Isa

[12:11, 25/09/2017] ‪+234 803 414 9368‬: ��A DADE ANA YI….sai gaskia��

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg1⃣7⃣

 

Kyafta idanuwanta tayi sau uku kafin ta sauke su fes kan Mutumin da ke kusa da ita sannan ta saukar da dubanta ga handkerchief din da ke rik’e a hannunshi, mika mata ya sake yi, ta sa hannu ta karba, ta goge hawayenta, ya mata nuni da hancinta inda Majina ke zuba, ta dan ji kunya, haka ta goge kafin ta k’wak’ulo murmushi.

 

Maida dubanshi yayi ga TV din da ke gaban Seat, ya gyara zaman headphones a kunnenshi.

hankali a hankali take jan majina, ba ta damu da kallo ba, abunda ke dawainiya da ita ya fi karfin Kallo, tana sheshek’a, hawaye na bin kuncinta har bacci barawo ya saceta.

 

I N D I A

5:45am

 

“Yesmeenah, yau Najwa ko bata Sallah ne? Banga ta zo gaida mu ba” daria Maama tayi tace “Yanzu da gabanta ka fada hakan da taji kunya, wai ko bata Sallah ne, haha, tana yi fa, k’ila ta makara, ko bayan Sallah ta idar bacci ya ci k’arfinta ta koma” ya mik’e tare da cewa barin dubota.

 

Ko da ya bude dakin Najwa be ganta ba, sai Pooh da ke ta bacci kan Gado, ya dawo yace “ta tashi, tana toilet” Maama tace “Oya kazo ka kwanta kafin na tada ka Shirin Office” murmushi yayi ya haye Gado ya kwanta ya bar Maama kan Gado tana Adhkar.

 

Gari ya dan fara wayewa Maama ta shiga Kitchen, ta shiga hada musu breakfast, da sauri ta shiga dakin Najwa, ta ga bata nana, a zaton ta tana Toilet, ta bude baki tace “Najwa, kiyi sauri ki fito ki shirya, School Bus ya kusa zuwa”. Ba ta jira komai ba ta dawo dakin baccin su. Ta hau kan Gadon inda Pappa ke zaune, “rise and shine Papi, wake up” da murmushi ya bude ido tace “Good Morning Papi” “Good Morning Yesmeenah” “Oya a shiga toilet ayi wanka” ta samu ta turashi wanka.

Ta ja bargon ta ninke ta kakkabe bedsheet zata fara gyara Gadon kenan idonta ya sauka kan wata Farar takkada, tayi dan jim daga nesa kamar tana son gano wani abu game da takardan, a hankali ta taka har zuwa gaban bedside drawer, ta dauki takkadan ta bude. Gabanta ya fadi ganin rubutun Najwa kwance kan takardan, kasa karantawa tayi ta fita da gudu tayi dakin Najwa tana k’wala mata kira.

 

Shiru Najwa bata daki, bata toilet, Maama ta fita parlor tana kiran Najwa, ba Najwa ba alamunta, sai da ta zagaye Gidan tana kiran Najwa amma shiru, Dakin Najwan ta koma hannu na rawa ta ware takarda ta fara karantawa gabanta na duka chalugude.

 

“Good Morning My Beloved Parents, a Lokacin da za ku ga wannan Message din, i’m long Gone.

A kullum burina shine ganin Farinciki dauwamammiya ya wanzu a cikin Gidanmu, inda zamu yi rayuwarmu ba tare da ganin hawayen daya daga cikin mu ba, Maa, Hawayenki tamkar saukan garwashi ne haka nake ji a zuciyata, so da yawa nake danne nake shanye bakincikin da zubar hawayenki ke jamin, don kar in k’ara miki wani zafin.

Paapa, Maama, Na tafi Nigeria, na tafi neman Yayana, zan ganshi indai yana raye, zan dawo dashi Gida no matter how long it will take, i’ll find him and i’ll bring him home. Kar ku yanke Adduarku gareni, kar ku damu, i’m 18, i will be just fine.

Paapa take care of Maama before i come back.

And Maama ki adana hawayenki kuma sai ran da na dawo miki da Zaid Bhaiya, rannan kiyi kukan farincikin ki ba mai hanaki. Maa, Paaa, please be fine, Be happy. I want you to be proud of me, ina so na zama abun Alfahari a gunku. °Main aapako bahut pyaar karata hoon(i love you so very much)°”

Najwa.

 

Maama ta dafe kai hawaye na zuba daga idaniyarta, Najwa ta tafi Nigeria neman Zaid? Me Najwa ke tunani? Nigeria Sarita Vihar ne? Shikenan ta rasa Najwa itama, Shikenan ta rasa yaranta duka, Paapa ya shigo dakin yace “Yesmeenah ina Najwa? Na ji kina ta kwala mata kira” Takardan hannunta ta mik’a mai, ya karba ya karanta.

 

“Inalillahi wa ina ilaihir rajiun”cewad Paapa, ya sake karantawa, jiki na rawa ya rungume Maama da take jin duniyarta na barazanan Tarwatsewa, tun yaushe take shirye shiryen? No wonder ta cika fita kwanakin nan” ita dai Maama ba tace komai ba, sai chan tace “Vijhay yabsan wani abu, tare suke k’ulle kullensu” da sauri ta tashi ta ja mayafin da Najwa tayi sallah ta sa, Alhaji Sada ya bi bayanta, ba su tsaya ko ina ba sai gaban shagon Vijhay. Kwankwasawa sukayi yana budewa ganinsu ya sa shi sadda kai irin na marasa gaskia.

 

Murmushin takaici Maama tayi tace “Vijhay aap isake baare mein pata tha? (Vijhay dama ka sani?) kai ya gyada mata, tace “hamen sab kuchh bata(ka gaya mana komai)” nan Vijhay ya gaya musu duk abunda ya sani game da tafiar Najwa har zuwa jiya da ya kaita Airport ya dora da fadin “main bahut maaphee chaahata hoon aapako bata nahin karane ke lie, mujhe maaph kar do (I’m very sorry for not telling you, please forgive me)”. Kuka yaci k’arfin Maama da sauri ta shige cikin Gida, tana tausayin Najwa, da ta san Nigeria da ba tayi marmarin zuwa ba, Nigeria ba wani abu sai tarin Maha’inta, duk da ba a taru aka zama daya ba. Hannu ta daga sama tana rok’on Allah ya Tsare ya kare mata diyarta a duk inda take.

 

8:35am

 

Tagumi sukayi duka, sunyi jugum, Paapa beje aiki ba, Maama ko rike da letter din Najwa wanda ta karanta yafi a k’irga, kirrrr Wayar Maama yayi k’ara, bata waya take ba, amma Pappa ya mik’e ya dauki wayar ya duba, international number ce, hannu na rawa ya dauka tare da sa Speaker “Maama…” wani tsalle da Maama tayi ta amsa wayar hannu Pappa murya na rawa tace “Najwa beta, are you OK?” Najwa ta murmusa kamar suna gabanta tace “Maama i did well didnt i?” Maama kuka yaci karfinta tace “Najwa diyata, ki dawo Gida, duk yanda nake son kasancewa tare da Yayanki, ba zanyi risking life dinki ba” Najwa tace “Mamma neman Yayana gudan jini na ne risking life? Maama, nayi nisan da ba na jin kira Already ina Dubai, lokaci kawai nake jira na hau Jirgin Nigeria, Just Pray for me”.

 

Maama tace ” Najwa Wahala kawai zakiyi, ki dawo gida, bansan me zanyi ba idan kema na rasaki, bansan ya zanyi ba, Najwa please” Najwa tace “Maama, i want you to be my strength please, let me do this, donAllah Maama, ki bari na dawo miki da cikon farincikin ki, i can please Maama” Duk inda Maama ta bullo ma Najwa sai Najwa ta bulle, ba yanda ta iya, kuka kawai takeyi, Paapa ya jinjina kai yace “Najwa, I’m proud of you, ina alfahari dake, bring your brother home, your Maama and i will be waiting, Allah ya miki Albarka diyata”.

 

Najwa ta murmusa tace “Amin Paapa na, take care of Maama and my Pooh, kuma donAllah kar kuyi fushi da Vijhay bhaiya ni na saka ya min Alkawari ba zai fada muku ba” Pappa yace “Najwa donAllah ki kula da kanki, nasan you’re 18, idan kika ga theres no progress, come straight home kinji?” tace “Naji Paapa, Maama na fushi dani ko?” yace “Ya zatayi fushi da abun alfaharinta? She’s just scared” Maama kar ki ji tsoro, Allah zai kareni, zan dawo gareki and ofcourse with My brother, now bless me please” Maama ta shara hawayenta, tana murmushi tace “Allah ya Albarkaci rayuwarki Najwa, Allah ya kareki daga sharrin mutum, karfe da Aljjan, Allah ya dawo dake lafiya”. “Ameen, naji ana kiranmu zaa fara boarding, i will call you dana isa Nigeria” haka sukayi sallama, zuciyoyinsu na Alhinin rabuwa da junansu.

* *

 

Tana farkawa taji cikinta na kukan Yunwa, sai a lokacin ta tuna, rabonta da abinci tun abinci Maama da ta ci daren jiya, dazun a Jirgin India-Dubai bata ci komai ba.  Kamar Mallaman Jirgin sun san zuciyarta, don kuwa abinci aka fara rabawa seat by seat.

Ta bude abincin ta ga Taliya da miya, warin Miyan ya bugi hancinta, haka kurum taji amai yazo mata, amma da yake yunwan take ji bil hakki, ya sa ta dauke numfashinta tana tura ma cikinta taliyar. Da tayi yunkuri sai da ta fara amayo abincin da ke cikinta gabaki daya.

Mutumin da ke kusa da ita ya kalleta cike da tausayi, yanda ya ga ta galabaiita ya sa shi tausayinta, “sannu kinji, sannu” bata iya amsa mishi ba, danna alert din seat dinsu yayi alamun suna neman attention.

 

Jim kadan sai ga attendant din jirgin ta iso, Mutumin yace “She threw up, help her please” Mallamar Jirgin ta taimaka ma Najwa suka shiga toilet, wata kuma ta gyara inda Najwa tayi Aman. Kafin aka dawo da ita, yace  “miss, get her fruits and vegies with Orange Juice please” da murmushi Mallamar Jirgin tace “Right away sir” ya juyo ga Najwa da murmushi yace “Sannu, it happens haka, maybe baki san warin spices dinne shiyasa kikayi amai, but ga Fruits zaa kawo miki ki daure ki sha zai zauna InshaAllah” kai kawai ta gyada mai ta na mamakin shi, be ji kyamarta ba, ya cigaba da cin abincinshi, Jim kadan aka kawo mata Fruits, yauwa gwara hakan kan Abincin nan mai wari a cewarta , ta ci banana, apple, grapes da Lemu, ba laifi cikinta ya dauka. Mutumin ya gyara mata zaman Kujeranta, ya kunna mata Tv, haan, mamaki take, to ko shi wannan ba Dan Nigeria bane? Ta ganshi da kirki, muryan Aisha ta tuna inda take mata warning kan Yarda da mutane, har tana cewa;

 

“Wasu zaki gansu da kirki, but they are only trying to get advantage of you, wasu chance kalilan suke nema, kar ki bari Kirkin da wasun su zasu nuna miki ya sa kiyi sake ki yarda dasu, they are very manipulative, so Najwa, dont trust anyone”. Kai ta gyada a ranta tace ba zata bari kirkinshi  yaci galaba a kanta ba.

 

Da Yamma suka Iso Lagos Nigeria, bayan sun fito daga jirgin, kowa kama gabanshi yayi,Najwa ta dauka akwatinta da School Bag dinta ta fara tafiya,daga gefe taga inda ake Changing Kudi, ko wani irin kudi zuwa Naira, ta k’arasa ta gaidasu, ta ciro kudi 200usd(dollar 200)aka chanza mata. Daga dan gefe taga masu saida registered sim cards, dama Aisha tace ta siya MTN, haka ko akayi, ta siya, wuri ta samu daga gefe ta zauna, bayan ta bude simpack din sai ta ga sim din ba zai shiga wayarta ba. Waigewaige ta farayi, daga nesa ta hango wasu matasa guda biyu zaune suna zaman banza, da sauri ta k’arasa garesu. Da turanci ta gaishe su, suka amsa mata da pidgin English, tace donAllah su taimaka mata da Sim Card dinnan, dayan ya ansa sim din yana kallonta, dayan yace wani irin waya ne? Ciro wayarta tayi k’irar Iphone6 ta mika musu, wani murmushi yayi kafin yace “guy make i go cut the sim to nano, i dey come”dayan yace “Oya now i dey your backa” cikin turancin shi mara k’arko yace “mata zaije chan baya ya yanka mata sim din sai ya sa mata a wayan yanzu zai dawo” Najwa me tsarkaken zuciya tayi murmushi tace Ok, ya juya yayi baya.

 

Mintuna 15 suka shude be dawo ba, Najwa ta dan matsu da rashin dawowanshi, ta kalli abokin tace “Where is your friend?” shima ya dan daga kafada yace “I no know, ma go check on him, wait here” Najwa ta daga kai, shima abokin ya samfe. Shiru shiru dai, basu ba alamun su, tayi tunanin zuwa siyan Ticket din Kano kar ya k’are kafin su dawo mata da waya, tana tafiya tana waigen su, to ina zata siya ticket din? Wani tagani tsaye kamar Mutumin da suke tare a cikin Jirgi dazun ta karasa gunshi tace “DonAllah ina ake saida Tickets din Kano?” ya murmusa yace “wani Jirgi?” ta ta6e baki tace “ko wanne” yace “kina son Arik?” ta gyada kai tace “eh” yace “muje in rakaki to” tace “donAllah bawai aiken ka nakeyi ba ko, amma donAllah ko in baka kudin ka siyo min Ticket din, ban so inyi nisa da nan, na ba wasu Wayata su karya min sim su saka mu tun 30mins back, har yanzu ba su dawo ba, kar in bar wurin nan su dawo suyi ta nema na” daga Maganganunta ya gane k’uruciya tattare da ita, amma a zamanin nan wake yarda da wani har ya bashi Waya wai zaije ya dawo, ya dan yi murmushi yace “kawo kudin” tace “Nawa ne?” ya gaya mata ta irga mai yan dubu dubu ta bashi tare da godia, yace ta bashi wasu takardun tafiyar ta ta dauko ta bashi.

 

Har mutumin ya siyo Ticket din ya kawo mata tana nan tsaye inda ya barta, yace “gashi, Jirgin mu zai tashi 7pm” ta amsa ta k’wakulo murmushi don a yanzu ta fara tsorata da rashin dawowansu, yace “basu dawo ba?” ta gyada kai, yace “kingane?ba zasu dawo ba, halin yan Nigeria suka miki, sun gudu” ta tsura mai ido tana son gasgata abun da yake gaya mata, “No, basu gudu ba zasu dawo” zasu dawo? Ta ya kika san zasu dawo? Sun gudu fa, in ba ke ba waye zaice zai ba wani wayarshi yaje ko nan da chan ne?” Najwa tayi shiru idonta ya kawo ruwa, ta so tsaida su amma ina hawayenta ba zasu tsaidu ba, ta fara kuka mara sauti a hankali tace “i cant lose that phone, Paapa na ya siya min” daria ta dan bashi amma be dara ba, yace “kiyi hakuri Paapa zai sake siya miki wani kinji ko?, yi shiru ki bar kukan nan” duk yanda ta so yin shiru ta kasa, haka ya dinga lallashinta da ya samu tayi shiru yace “take care Jirginmu zai tashi by 7” cikin sanyin murya tace “whats the time now?” ya gaya mata tayi saitin agogonta, ya wuce Masallaci don sauke farali.

 

7;19pm suka shiga Jirgin da zai kaisu Kano, ba ta sake ganin mutumin nan ba, wurin to 9 suka iso Filin Jirgin Mallam Aminu Kano, kamar yanda taga sauran mutane sunyi, suna yin hanyar Waje, itama Wajen ta nufa, wasu ta ga sun amshi Akwatin nan matafiyan sun sa a cikin Mota sauran kuma sun shiga Motoci sun wuce, a zaton ta Taxi ne, tafiya dai take tayi, ga dare yayi, mostly ba taxi, ko don bata ga alamunsu bane oho, kuma duk tagaji, kafadanta ya sage, a gajiye take tafia.

 

“Yanmata taxi kike nema?” wani mutumi tagani da zasu yi tsara da Vijhay bhai tace “Eh, taxi nake nema” yace “bari a nemo miki to” tace “donAllah akwai dan hotel nan kusa?” mutumin ya juyo ya kalleta yana nazarinta, yarinya ce, tsaf zai mata wayau, yace “Eh akwai nan baya, kawo kayanki na taya ki rikewa naga kin gaji, ba gardama ta bashi, har School bag din, yace ki tsaya nan barin karasa chan din in kira mai taxi din, sai in rakaki har masaukin, daman aikina kenan” don tabewar basira Najwa harda murmushi tace “Ok”. (Welcome to Naija Najwa Sada Abu..

 

Gabanta ya yanke ya fadi, this cant happen again, agogon hannunta ta duba, k’arfe 10 saura, in har hasasshen ta ya zama gaskia ai ta mutu, All her life is in that luggage, hannu ta sa ta zame gyalen da ta yana kanta dashi, ta chusa hannunta cikin gashinta ta baza shi, hannunta ya fara rawa, idonta ya fara zuban ruwa, why is this happening to her? Mesa hakan ke faruwa da ita, saboda meye? Don tazo Nigeria? Zama tayi dirshen a k’asa ta rafka uban tagumi, tana kallo masu fita daga Airport din.

 

Kamar a sama taji wata Murya tace “Najwa” Allah ya sa Mutumin nan ne ya dawo mata da Akwatinta da sauri ta mik’e, murnan ta ya koma ciki da taga akasin haka, Mutumin nan ne na cikin Jirgi,tana ganinshi sai ta fashe da wani kuka kamar dama jiranshi take.

“Ya Salam, Najwa me ya sameki? What happened to you?” bata amsa shi ba sai Kukan da ta cigaba da yi, ya dan matso kusa da ita yace “Najwa fada min damuwanki, i might help you” cikin muryan Kuka ta sanar dashi Wani ya gudun mata da kayanta.

 

Dafe kai yayi cike da takacici “Ya Illahi! How can you be so careless Najwa? Ki fada min, daga wani world kika zo, because from what i’m seeing, you are no Nigerian, meyasa kike haka ne? You trust easily, Haka dazun a lagos ki ka ba wasu wayarki da hannunki, nima kika ciro kudi kika bani, nima da irin su ne da na gudu miki da kudi, yanzu kin dauka jakkunkunanki ki ba stranger, haka akeyi a k’asarku? Because you are innocent ba hakan yake nufin kowa ma is innocent ba,fisabillilah gashi ya gudun miki da komai, laifin waye, laifinki ne” ba abun da Najwa keyi in ba kuka ba. Mutumin ya ga dai fadan ba shine mafita ba yace “Najwa ya isa, kar kanki yayi ciwo,ya isa, tell me wani Unguwa kike, sai in tsaida miki taxi ya kaiki, but listen dont trust people again, ba kowa bane amintacce, yanzu gaya min wani Anguwa kike?”.

 

Kuka kawai take tayi, da kyar ta tsaida hawayenta, sai yanzu taga wautar ta, gaskian Aisha ne da ta ke ta mata gargadin “kar ta yarda da kowa” yanzu ai ta dauki darasi, baza ta sake yarda da kowa ba, baza ta sake yarda da wani ba balle sirrinta. A hankali tace mai “Wannan ne karon farko da nazo Nigeria, ban san ko ina ba”

 

Bangane ba Najwa, Karatu kikazoyi anan? Ta girgiza kai Alamun aa, yace to me kika zo yi nan? Ina Iyayenki? You can trust me, i’m not going to hurt You ”

 

A ranta tace  i trust you, but not with my  secrets, a fili tace “please dont get me wrong, dont judge me” ya gyada kai tace “Sunana Najwa erh-erhm Najwa Muhammad” tayi karya, nan da nan idonta ya fara wuriwuri, bata iya karya ba, tace “Iyayena ‘yan Ghana ne, muna zaune a chan” ta danyi shiru yace “ku da ke Ghana yana ganki a Dubai?” murya na rawa tace “a India nake karatu”  yace “So? In hutu kukayi meyasa ba zaki koma Ghana ba kika zabi zuwa Nigeria? Ko hutu zakiyi a nan din?” “erhmerhm guduwo nayi”ya zaro ido yace ” what?” tace “You See, Paapa na yake so ya aura min Abokin shi, kuma da anyi auren na haihu zai sakeni ya kwace yaron, nikuma banaso, Maama na ma bataso, shine Maama tace inzo Nigeria for 2months, kafin nan zata yi convincing Paapa ya bar maganan auren”ta karashe maganan kamar tayi kuka,  Wow  bata san ta yanda ta fara karanto mai wannan zancen ba, ba ta taba karya ba, tayi mamakin yanda ta dauko wannan idear. Ta marairaice tace gashi Yanzu an sacen komai, bansan ya zanyi ba, ta karashe tana kuka, wannan kukan gaske ne.

 

Sosai yaji tausayinta, yarinya ce, ba zata wuce tsaran kanwashi ba, tana da future, ta ya zai taimaka mata? besan rayuwanta ta baci, innocence dinta is too much, in ya barta a nan Yaudaranta zaayi, be san ina zata fada ba, be san hannayen wa zata fada ba. Tausayinta yaji ainun zai tafi da ita ta zauna dasu for sometime kafin ya san nayi da ita”come with me” yace mata, ta dago kai tace “Noo” yace “idan na barki nan kina da inda zakije? Ko da ba zaman kanki zakiyi ba? Ki zauna a hotel ke kadai? Gidanmu zan kaiki, i’m not going to hurt you, i have sisters like you” tana son yarda dashi amma wani zuciya na hanata, yayi ta maganan ta tashi ta bishi taki ta kafe wuri guda, ba wai ta bashi labarin nan bane don ya kaita gidansu, da ya gaji sai ya tashi yace “tunda kin ki yarda dani, Allah ya tsare ya kareki na tafi” ya juya ya dauki Jakanshi yayi gaba, idan ya barta nan ina ta nufa? Hannu wa zata fada? Ba zata iya ba, bari dai ta bishi. Da sauri ta mik’e ta bi bayanshi, tsayawa yayi tare da juyo wa, ya murmusa yace “Muje Gida”. Taxi ya tsaida musu yace a kaisu Hotoro.

*

 

Zaune suke gabaki daya a Parlor, suna Jiran Farincikin Gidansu ya shaida musu gashi nan zuwa, ba sai an aiko daukanshi ba zai hau Taxi. Sallama yayi a gaban Parlorn Gida tare da shigowa, da Sauri yaran suka tashi suka fada mai tare da rungumesu, Matarshi itama tazo tayi hugging dinshi tare da mai peck, kunya ta bashi sosai don a kan gidan kowa hakan ta faru, ya matsa gun Mahaifanshi ya durk’usa ya gaida su, da farinciki suka amsa suna mai ya hanya.

Mummy tace ” kaje Kayi Wanka, kazo muyi dinner muna ta jiranka” yace “wai yanzu bakuyi dinner ba har 10?” tace “dole muke jiran ka” ya murmusa yace “Well, bani kadai bane, da bak’uwa nake” Mummy tace “bakuwa kuma daga ina?” yace “Tun Dubai muke tare da ita, its a long story, to cut it short bata da inda zata zauna, let her stay here for sometime” Mummy tace “Ayyah, OK tana ina?” yace “just a min nace ta jira daga waje barin mata iso” ya fita su kuma suka tsura wa k’ofan parlon Ido.

 

Shigowa sukayi a tare. Kan Najwa a kasa ta tako, Mutumin yace “Najwa, meet My Daddy, Mummy, Wife sister and my brother” Mummy tace “welcome my daughter” Najwa ta dago da murmushi kan fuskarta ta zubesu fes kan Mummy, Mummy na ganinta ta zabura tare mik’ewa tsaye gabanta na  dukan Uku-uku, wasu tunani na dawo mata, tunanin da bata so ta taba tunawa, wannan yarinya na mata kama da wata, tsanar yarinyan lokaci guda ya darsu a ranta ba don komai ba don kama da yanayi da takeyi da Yesmeen. Cikin daga Murya tace “Ke ya sunan Uwarki?” Najwa tayi shiru, Mairo kamar zata kifeya da Mari tace “ko ba kya ji ya sunan Mamanki?” Najwa da sauri ta 6oye bayan Mutumin da tazo dashi, yace “Haba Mummy? Menene? Me ya faru” Mummy cikin hargowa tace “Ta amsa ni” Najwa ta dago da mamaki tana mamakin Sudden change din Matar, don me zata tambayeta Sunan Maama dinta?ko wani mugun abun zaa mata? To ko matar ta san Maama dinta? Baki na rawa Najwa tace “Sunan Mamata Khadija” duk sunji dogon ajiyan zuciyan da Mummy ta sake, tace “Babanki fa?” tace “Erhm sunan shi Muhammad” Mummy ta sake sauke ajiyar zuciya, kawai yarinyan bata mata bane, mtsw ta daure fuska tace “Majeed, yarinya nan ba zata zauna da mu ba, so ka fita da ita” tsulum Zinatu tace “Yes Ya Majeed, i dont like her, tell her to go out”.

 

Majeed yace ” Mummy why? Kin santa ne?” Mummy tace “Bansan ta bs, amma batayi min ba, irin su ne ke shigowa gidan mutane su rusa gida, bar ganinta karama, you dont know what shes capable of, maybe shes after you or something” nan da nan Nana taji tsanar Najwa, Majeed ya hadiye miyau yace “Mummy ba haka bane, bata san kowa a Nigeria ba, yau ta zo kasar, an sace mata Kaya, komai aka sace mata” Mummy tace lallai Majeed har yanzu yaro ne, baka san kaidin Mace ba? Tace an sace mata komai sai kai kaji tausayinta, kace bari ka kawo ta gidanku? Kila dama abunda take so kenan ka kawo ta gidanku” Majeed ya yarfa hannu kasa yace “Mummy please, wallahi akan idona komai ya faru, please let her stay” Daddy yace “Maryam, ki barta danAllah” Mummy tace “kaima ka yarda ko Daddy, besides muna fama da kanmu ya jajibo mana wata?” Daddy ya mata alama da ido, Mummy tace “Alright, just one Night” tana fadan hakan tace “Zinatu, Muhsin ku wuce muje” tayi ciki yaran suka bita a baya, Daddy ya dafa kafadun Majeed ya mai alaman ‘Sorry’ kafin ya rufawa Mairo baya, Nana sai da ta matso kusa da Najwa ta wurga mata harara kafin ta wuce dakinta itama, Majeed ya kalki Zaineema yace “Zee please, ki tafi da ita dakinki ku kwana tare” Zaineema batace komai ba tayi ciki, ya san hakan na nufin bata amince ba.

 

Ya kalli Najwa da ke ta hawaye yace “I’m sorry you had to witness this, Mummy na da trust issue, bata yarda da kowa” Najwa ta murmusa tace “dagaskianta ai, banji haushi ba, kaine dai zan ba hakuri, ka samu matsala da Family dinka saboda ni” yace “Noo its nothing, yanzu dai zo kici abinci, i’ll talk to Mum zata barki ki zauna for as long as you want” Murmushi tayi, ya karasa kan dining table, Rice and stew ne da plantain, yace “zo ki zauna kici” tana zuwa wurin table din kamshin ya cika mata ciki ta matsa baya tace “I cant eat this” yace Oh sorry, baki saba da spices din Naija ba, zakici Indomie Noodles?” tace “yeah, ina cin Indomie ko a India” yace “Alright, biyoni” ba musu ta bishi baya, wani daki ya bude mata yace ta shiga tayi wanka ta bude  drawer ta zabi kayan da zai mata, a tsorace tace “dakin waye? Kar suji haushi fa” yace “dont worry, dakin Ziyada ne, my FAV Sis, ba ta da matsala she wont mind, besides tana Makaranta”. Najwa tayi murmushi har ranta, har taji tana son Ziyada din, yace “Oya, jekiyi wanka, kafin ki fito nagama dafa miki indomie din”. Ya juya ta bi bayanshi da ido a ranta tace “Can i trust this one?”.

 

Bibilicious freaking fans, ga Najwa a Naija, gata a Gidan Wan Babanta, gata a gaban Dragon Mairo lol. Rayuwan Najwa ya chanza daga lokacin da ta shigo Nigeria. Komai ya fara faruwa a gurinta daga lokacin da ta shigo garin Kano, ya rayuwan Najwa zai kasance gaban Hajia Mairo? Ku biyoni don jin ya zaa kaya.

***

 

Thanks all, you’ve been supportive, like always Dont forget to Vote and comment please.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg1⃣7⃣

Kyafta idanuwanta tayi sau uku kafin ta

sauke su fes kan Mutumin da ke kusa da ita

sannan ta saukar da dubanta ga

handkerchief din da ke rik’e a hannunshi,

mika mata ya sake yi, ta sa hannu ta karba,

ta goge hawayenta, ya mata nuni da

hancinta inda Majina ke zuba, ta dan ji

kunya, haka ta goge kafin ta k’wak’ulo

murmushi.

Maida dubanshi yayi ga TV din da ke gaban

Seat, ya gyara zaman headphones a

kunnenshi.

hankali a hankali take jan majina, ba ta

damu da kallo ba, abunda ke dawainiya da

ita ya fi karfin Kallo, tana sheshek’a, hawaye

na bin kuncinta har bacci barawo ya saceta.

I N D I A

5:45am

“Yesmeenah, yau Najwa ko bata Sallah ne?

Banga ta zo gaida mu ba” daria Maama tayi

tace “Yanzu da gabanta ka fada hakan da

taji kunya, wai ko bata Sallah ne, haha, tana

yi fa, k’ila ta makara, ko bayan Sallah ta

idar bacci ya ci k’arfinta ta koma” ya mik’e

tare da cewa barin dubota.

Ko da ya bude dakin Najwa be ganta ba, sai

Pooh da ke ta bacci kan Gado, ya dawo yace

“ta tashi, tana toilet” Maama tace “Oya kazo

ka kwanta kafin na tada ka Shirin Office”

murmushi yayi ya haye Gado ya kwanta ya

bar Maama kan Gado tana Adhkar.

Gari ya dan fara wayewa Maama ta shiga

Kitchen, ta shiga hada musu breakfast, da

sauri ta shiga dakin Najwa, ta ga bata nana,

a zaton ta tana Toilet, ta bude baki tace

“Najwa, kiyi sauri ki fito ki shirya, School Bus

ya kusa zuwa”. Ba ta jira komai ba ta dawo

dakin baccin su. Ta hau kan Gadon inda

Pappa ke zaune, “rise and shine Papi, wake

up” da murmushi ya bude ido tace “Good

Morning Papi” “Good Morning Yesmeenah”

“Oya a shiga toilet ayi wanka” ta samu ta

turashi wanka.

Ta ja bargon ta ninke ta kakkabe bedsheet

zata fara gyara Gadon kenan idonta ya

sauka kan wata Farar takkada, tayi dan jim

daga nesa kamar tana son gano wani abu

game da takardan, a hankali ta taka har

zuwa gaban bedside drawer, ta dauki

takkadan ta bude. Gabanta ya fadi ganin

rubutun Najwa kwance kan takardan, kasa

karantawa tayi ta fita da gudu tayi dakin

Najwa tana k’wala mata kira.

Shiru Najwa bata daki, bata toilet, Maama ta

fita parlor tana kiran Najwa, ba Najwa ba

alamunta, sai da ta zagaye Gidan tana kiran

Najwa amma shiru, Dakin Najwan ta koma

hannu na rawa ta ware takarda ta fara

karantawa gabanta na duka chalugude.

“Good Morning My Beloved Parents, a

Lokacin da za ku ga wannan Message din,

i’m long Gone.

A kullum burina shine ganin Farinciki

dauwamammiya ya wanzu a cikin Gidanmu,

inda zamu yi rayuwarmu ba tare da ganin

hawayen daya daga cikin mu ba, Maa,

Hawayenki tamkar saukan garwashi ne haka

nake ji a zuciyata, so da yawa nake danne

nake shanye bakincikin da zubar hawayenki

ke jamin, don kar in k’ara miki wani zafin.

Paapa, Maama, Na tafi Nigeria, na tafi

neman Yayana, zan ganshi indai yana raye,

zan dawo dashi Gida no matter how long it

will take, i’ll find him and i’ll bring him

home. Kar ku yanke Adduarku gareni, kar ku

damu, i’m 18, i will be just fine.

Paapa take care of Maama before i come

back.

And Maama ki adana hawayenki kuma sai

ran da na dawo miki da Zaid Bhaiya, rannan

kiyi kukan farincikin ki ba mai hanaki. Maa,

Paaa, please be fine, Be happy. I want you to

be proud of me, ina so na zama abun

Alfahari a gunku. °Main aapako bahut pyaar

karata hoon(i love you so very much)°”

Najwa.

Maama ta dafe kai hawaye na zuba daga

idaniyarta, Najwa ta tafi Nigeria neman

Zaid? Me Najwa ke tunani? Nigeria Sarita

Vihar ne? Shikenan ta rasa Najwa itama,

Shikenan ta rasa yaranta duka, Paapa ya

shigo dakin yace “Yesmeenah ina Najwa? Na

ji kina ta kwala mata kira” Takardan

hannunta ta mik’a mai, ya karba ya karanta.

“Inalillahi wa ina ilaihir rajiun”cewad Paapa,

ya sake karantawa, jiki na rawa ya rungume

Maama da take jin duniyarta na barazanan

Tarwatsewa, tun yaushe take shirye shiryen?

No wonder ta cika fita kwanakin nan” ita dai

Maama ba tace komai ba, sai chan tace

“Vijhay yabsan wani abu, tare suke k’ulle

kullensu” da sauri ta tashi ta ja mayafin da

Najwa tayi sallah ta sa, Alhaji Sada ya bi

bayanta, ba su tsaya ko ina ba sai gaban

shagon Vijhay. Kwankwasawa sukayi yana

budewa ganinsu ya sa shi sadda kai irin na

marasa gaskia.

Murmushin takaici Maama tayi tace “Vijhay

aap isake baare mein pata tha? (Vijhay

dama ka sani?) kai ya gyada mata, tace

“hamen sab kuchh bata(ka gaya mana

komai)” nan Vijhay ya gaya musu duk

abunda ya sani game da tafiar Najwa har

zuwa jiya da ya kaita Airport ya dora da

fadin “main bahut maaphee chaahata hoon

aapako bata nahin karane ke lie, mujhe

maaph kar do (I’m very sorry for not telling

you, please forgive me)”. Kuka yaci k’arfin

Maama da sauri ta shige cikin Gida, tana

tausayin Najwa, da ta san Nigeria da ba tayi

marmarin zuwa ba, Nigeria ba wani abu sai

tarin Maha’inta, duk da ba a taru aka zama

daya ba. Hannu ta daga sama tana rok’on

Allah ya Tsare ya kare mata diyarta a duk

inda take.

8:35am

Tagumi sukayi duka, sunyi jugum, Paapa beje

aiki ba, Maama ko rike da letter din Najwa

wanda ta karanta yafi a k’irga, kirrrr Wayar

Maama yayi k’ara, bata waya take ba, amma

Pappa ya mik’e ya dauki wayar ya duba,

international number ce, hannu na rawa ya

dauka tare da sa Speaker “Maama…” wani

tsalle da Maama tayi ta amsa wayar hannu

Pappa murya na rawa tace “Najwa beta, are

you OK?” Najwa ta murmusa kamar suna

gabanta tace “Maama i did well didnt i?”

Maama kuka yaci karfinta tace “Najwa

diyata, ki dawo Gida, duk yanda nake son

kasancewa tare da Yayanki, ba zanyi risking

life dinki ba” Najwa tace “Mamma neman

Yayana gudan jini na ne risking life? Maama,

nayi nisan da ba na jin kira Already ina

Dubai, lokaci kawai nake jira na hau Jirgin

Nigeria, Just Pray for me”.

Maama tace ” Najwa Wahala kawai zakiyi, ki

dawo gida, bansan me zanyi ba idan kema

na rasaki, bansan ya zanyi ba, Najwa please”

Najwa tace “Maama, i want you to be my

strength please, let me do this, donAllah

Maama, ki bari na dawo miki da cikon

farincikin ki, i can please Maama” Duk inda

Maama ta bullo ma Najwa sai Najwa ta

bulle, ba yanda ta iya, kuka kawai takeyi,

Paapa ya jinjina kai yace “Najwa, I’m proud

of you, ina alfahari dake, bring your brother

home, your Maama and i will be waiting,

Allah ya miki Albarka diyata”.

Najwa ta murmusa tace “Amin Paapa na,

take care of Maama and my Pooh, kuma

donAllah kar kuyi fushi da Vijhay bhaiya ni na

saka ya min Alkawari ba zai fada muku ba”

Pappa yace “Najwa donAllah ki kula da

kanki, nasan you’re 18, idan kika ga theres

no progress, come straight home kinji?” tace

“Naji Paapa, Maama na fushi dani ko?” yace

“Ya zatayi fushi da abun alfaharinta? She’s

just scared” Maama kar ki ji tsoro, Allah zai

kareni, zan dawo gareki and ofcourse with

My brother, now bless me please” Maama ta

shara hawayenta, tana murmushi tace “Allah

ya Albarkaci rayuwarki Najwa, Allah ya

kareki daga sharrin mutum, karfe da Aljjan,

Allah ya dawo dake lafiya”. “Ameen, naji ana

kiranmu zaa fara boarding, i will call you

dana isa Nigeria” haka sukayi sallama,

zuciyoyinsu na Alhinin rabuwa da junansu.

* *

Tana farkawa taji cikinta na kukan Yunwa,

sai a lokacin ta tuna, rabonta da abinci tun

abinci Maama da ta ci daren jiya, dazun a

Jirgin India-Dubai bata ci komai ba. Kamar

Mallaman Jirgin sun san zuciyarta, don kuwa

abinci aka fara rabawa seat by seat.

Ta bude abincin ta ga Taliya da miya, warin

Miyan ya bugi hancinta, haka kurum taji

amai yazo mata, amma da yake yunwan take

ji bil hakki, ya sa ta dauke numfashinta tana

tura ma cikinta taliyar. Da tayi yunkuri sai da

ta fara amayo abincin da ke cikinta gabaki

daya.

Mutumin da ke kusa da ita ya kalleta cike da

tausayi, yanda ya ga ta galabaiita ya sa shi

tausayinta, “sannu kinji, sannu” bata iya

amsa mishi ba, danna alert din seat dinsu

yayi alamun suna neman attention.

Jim kadan sai ga attendant din jirgin ta iso,

Mutumin yace “She threw up, help her

please” Mallamar Jirgin ta taimaka ma

Najwa suka shiga toilet, wata kuma ta gyara

inda Najwa tayi Aman. Kafin aka dawo da

ita, yace “miss, get her fruits and vegies with

Orange Juice please” da murmushi Mallamar

Jirgin tace “Right away sir” ya juyo ga

Najwa da murmushi yace “Sannu, it happens

haka, maybe baki san warin spices dinne

shiyasa kikayi amai, but ga Fruits zaa kawo

miki ki daure ki sha zai zauna InshaAllah”

kai kawai ta gyada mai ta na mamakin shi,

be ji kyamarta ba, ya cigaba da cin

abincinshi, Jim kadan aka kawo mata Fruits,

yauwa gwara hakan kan Abincin nan mai

wari a cewarta , ta ci banana, apple, grapes

da Lemu, ba laifi cikinta ya dauka. Mutumin

ya gyara mata zaman Kujeranta, ya kunna

mata Tv, haan, mamaki take, to ko shi

wannan ba Dan Nigeria bane? Ta ganshi da

kirki, muryan Aisha ta tuna inda take mata

warning kan Yarda da mutane, har tana

cewa;

Add Vote

“Wasu zaki gansu da kirki, but they are only

trying to get advantage of you, wasu chance

kalilan suke nema, kar ki bari Kirkin da

wasun su zasu nuna miki ya sa kiyi sake ki

yarda dasu, they are very manipulative, so

Najwa, dont trust anyone”. Kai ta gyada a

ranta tace ba zata bari kirkinshi yaci galaba

a kanta ba.

Da Yamma suka Iso Lagos Nigeria, bayan

sun fito daga jirgin, kowa kama gabanshi

yayi,Najwa ta dauka akwatinta da School

Bag dinta ta fara tafiya,daga gefe taga inda

ake Changing Kudi, ko wani irin kudi zuwa

Naira, ta k’arasa ta gaidasu, ta ciro kudi

200usd(dollar 200)aka chanza mata. Daga

dan gefe taga masu saida registered sim

cards, dama Aisha tace ta siya MTN, haka

ko akayi, ta siya, wuri ta samu daga gefe ta

zauna, bayan ta bude simpack din sai ta ga

sim din ba zai shiga wayarta ba. Waigewaige

ta farayi, daga nesa ta hango wasu matasa

guda biyu zaune suna zaman banza, da sauri

ta k’arasa garesu. Da turanci ta gaishe su,

suka amsa mata da pidgin English, tace

donAllah su taimaka mata da Sim Card

dinnan, dayan ya ansa sim din yana kallonta,

dayan yace wani irin waya ne? Ciro wayarta

tayi k’irar Iphone6 ta mika musu, wani

murmushi yayi kafin yace “guy make i go cut

the sim to nano, i dey come”dayan yace

“Oya now i dey your backa” cikin turancin

shi mara k’arko yace “mata zaije chan baya

ya yanka mata sim din sai ya sa mata a

wayan yanzu zai dawo” Najwa me tsarkaken

zuciya tayi murmushi tace Ok, ya juya yayi

baya.

Mintuna 15 suka shude be dawo ba, Najwa

ta dan matsu da rashin dawowanshi, ta kalli

abokin tace “Where is your friend?” shima ya

dan daga kafada yace “I no know, ma go

check on him, wait here” Najwa ta daga kai,

shima abokin ya samfe. Shiru shiru dai, basu

ba alamun su, tayi tunanin zuwa siyan Ticket

din Kano kar ya k’are kafin su dawo mata da

waya, tana tafiya tana waigen su, to ina zata

siya ticket din? Wani tagani tsaye kamar

Mutumin da suke tare a cikin Jirgi dazun ta

karasa gunshi tace “DonAllah ina ake saida

Tickets din Kano?” ya murmusa yace “wani

Jirgi?” ta ta6e baki tace “ko wanne” yace

“kina son Arik?” ta gyada kai tace “eh” yace

“muje in rakaki to” tace “donAllah bawai

aiken ka nakeyi ba ko, amma donAllah ko in

baka kudin ka siyo min Ticket din, ban so

inyi nisa da nan, na ba wasu Wayata su

karya min sim su saka mu tun 30mins back,

har yanzu ba su dawo ba, kar in bar wurin

nan su dawo suyi ta nema na” daga

Maganganunta ya gane k’uruciya tattare da

ita, amma a zamanin nan wake yarda da

wani har ya bashi Waya wai zaije ya dawo,

ya dan yi murmushi yace “kawo kudin” tace

“Nawa ne?” ya gaya mata ta irga mai yan

dubu dubu ta bashi tare da godia, yace ta

bashi wasu takardun tafiyar ta ta dauko ta

bashi.

Har mutumin ya siyo Ticket din ya kawo

mata tana nan tsaye inda ya barta, yace

“gashi, Jirgin mu zai tashi 7pm” ta amsa ta

k’wakulo murmushi don a yanzu ta fara

tsorata da rashin dawowansu, yace “basu

dawo ba?” ta gyada kai, yace “kingane?ba

zasu dawo ba, halin yan Nigeria suka miki,

sun gudu” ta tsura mai ido tana son gasgata

abun da yake gaya mata, “No, basu gudu ba

zasu dawo” zasu dawo? Ta ya kika san zasu

dawo? Sun gudu fa, in ba ke ba waye zaice

zai ba wani wayarshi yaje ko nan da chan

ne?” Najwa tayi shiru idonta ya kawo ruwa,

ta so tsaida su amma ina hawayenta ba

zasu tsaidu ba, ta fara kuka mara sauti a

hankali tace “i cant lose that phone, Paapa

na ya siya min” daria ta dan bashi amma be

dara ba, yace “kiyi hakuri Paapa zai sake

siya miki wani kinji ko?, yi shiru ki bar kukan

nan” duk yanda ta so yin shiru ta kasa, haka

ya dinga lallashinta da ya samu tayi shiru

yace “take care Jirginmu zai tashi by 7” cikin

sanyin murya tace “whats the time now?” ya

gaya mata tayi saitin agogonta, ya wuce

Masallaci don sauke farali.

7;19pm suka shiga Jirgin da zai kaisu Kano,

ba ta sake ganin mutumin nan ba, wurin to 9

suka iso Filin Jirgin Mallam Aminu Kano,

kamar yanda taga sauran mutane sunyi,

suna yin hanyar Waje, itama Wajen ta nufa,

wasu ta ga sun amshi Akwatin nan

matafiyan sun sa a cikin Mota sauran kuma

sun shiga Motoci sun wuce, a zaton ta Taxi

ne, tafiya dai take tayi, ga dare yayi, mostly

ba taxi, ko don bata ga alamunsu bane oho,

kuma duk tagaji, kafadanta ya sage, a gajiye

take tafia.

“Yanmata taxi kike nema?” wani mutumi

tagani da zasu yi tsara da Vijhay bhai tace

“Eh, taxi nake nema” yace “bari a nemo miki

to” tace “donAllah akwai dan hotel nan

kusa?” mutumin ya juyo ya kalleta yana

nazarinta, yarinya ce, tsaf zai mata wayau,

yace “Eh akwai nan baya, kawo kayanki na

taya ki rikewa naga kin gaji, ba gardama ta

bashi, har School bag din, yace ki tsaya nan

barin karasa chan din in kira mai taxi din, sai

in rakaki har masaukin, daman aikina kenan”

don tabewar basira Najwa harda murmushi

tace “Ok”. (Welcome to Naija Najwa Sada

Abu..

Add Vote

Gabanta ya yanke ya fadi, this cant happen

again, agogon hannunta ta duba, k’arfe 10

saura, in har hasasshen ta ya zama gaskia

ai ta mutu, All her life is in that luggage,

hannu ta sa ta zame gyalen da ta yana

kanta dashi, ta chusa hannunta cikin

gashinta ta baza shi, hannunta ya fara rawa,

idonta ya fara zuban ruwa, why is this

happening to her? Mesa hakan ke faruwa da

ita, saboda meye? Don tazo Nigeria? Zama

tayi dirshen a k’asa ta rafka uban tagumi,

tana kallo masu fita daga Airport din.

Kamar a sama taji wata Murya tace “Najwa”

Allah ya sa Mutumin nan ne ya dawo mata

da Akwatinta da sauri ta mik’e, murnan ta

ya koma ciki da taga akasin haka, Mutumin

nan ne na cikin Jirgi,tana ganinshi sai ta

fashe da wani kuka kamar dama jiranshi

take.

“Ya Salam, Najwa me ya sameki? What

happened to you?” bata amsa shi ba sai

Kukan da ta cigaba da yi, ya dan matso kusa

da ita yace “Najwa fada min damuwanki, i

might help you” cikin muryan Kuka ta sanar

dashi Wani ya gudun mata da kayanta.

Dafe kai yayi cike da takacici “Ya Illahi! How

can you be so careless Najwa? Ki fada min,

daga wani world kika zo, because from what

i’m seeing, you are no Nigerian, meyasa kike

haka ne? You trust easily, Haka dazun a

lagos ki ka ba wasu wayarki da hannunki,

nima kika ciro kudi kika bani, nima da irin su

ne da na gudu miki da kudi, yanzu kin dauka

jakkunkunanki ki ba stranger, haka akeyi a

k’asarku? Because you are innocent ba

hakan yake nufin kowa ma is innocent

ba,fisabillilah gashi ya gudun miki da komai,

laifin waye, laifinki ne” ba abun da Najwa

keyi in ba kuka ba. Mutumin ya ga dai fadan

ba shine mafita ba yace “Najwa ya isa, kar

kanki yayi ciwo,ya isa, tell me wani Unguwa

kike, sai in tsaida miki taxi ya kaiki, but

listen dont trust people again, ba kowa bane

amintacce, yanzu gaya min wani Anguwa

kike?”.

Kuka kawai take tayi, da kyar ta tsaida

hawayenta, sai yanzu taga wautar ta,

gaskian Aisha ne da ta ke ta mata gargadin

“kar ta yarda da kowa” yanzu ai ta dauki

darasi, baza ta sake yarda da kowa ba, baza

ta sake yarda da wani ba balle sirrinta. A

hankali tace mai “Wannan ne karon farko da

nazo Nigeria, ban san ko ina ba”

Bangane ba Najwa, Karatu kikazoyi anan? Ta

girgiza kai Alamun aa, yace to me kika zo yi

nan? Ina Iyayenki? You can trust me, i’m not

going to hurt You ”

A ranta tace i trust you, but not with my

secrets, a fili tace “please dont get me

wrong, dont judge me” ya gyada kai tace

“Sunana Najwa erh-erhm Najwa Muhammad”

tayi karya, nan da nan idonta ya fara

wuriwuri, bata iya karya ba, tace “Iyayena

‘yan Ghana ne, muna zaune a chan” ta danyi

shiru yace “ku da ke Ghana yana ganki a

Dubai?” murya na rawa tace “a India nake

karatu” yace “So? In hutu kukayi meyasa ba

zaki koma Ghana ba kika zabi zuwa Nigeria?

Ko hutu zakiyi a nan din?” “erhmerhm

guduwo nayi”ya zaro ido yace ” what?” tace

“You See, Paapa na yake so ya aura min

Abokin shi, kuma da anyi auren na haihu zai

sakeni ya kwace yaron, nikuma banaso,

Maama na ma bataso, shine Maama tace

inzo Nigeria for 2months, kafin nan zata yi

convincing Paapa ya bar maganan auren”ta

karashe maganan kamar tayi kuka, Wow bata

san ta yanda ta fara karanto mai wannan

zancen ba, ba ta taba karya ba, tayi

mamakin yanda ta dauko wannan idear. Ta

marairaice tace gashi Yanzu an sacen komai,

bansan ya zanyi ba, ta karashe tana kuka,

wannan kukan gaske ne.

Sosai yaji tausayinta, yarinya ce, ba zata

wuce tsaran kanwashi ba, tana da future, ta

ya zai taimaka mata? besan rayuwanta ta

baci, innocence dinta is too much, in ya

barta a nan Yaudaranta zaayi, be san ina

zata fada ba, be san hannayen wa zata fada

ba. Tausayinta yaji ainun zai tafi da ita ta

zauna dasu for sometime kafin ya san nayi

da ita”come with me” yace mata, ta dago kai

tace “Noo” yace “idan na barki nan kina da

inda zakije? Ko da ba zaman kanki zakiyi

ba? Ki zauna a hotel ke kadai? Gidanmu zan

kaiki, i’m not going to hurt you, i have

sisters like you” tana son yarda dashi amma

wani zuciya na hanata, yayi ta maganan ta

tashi ta bishi taki ta kafe wuri guda, ba wai

ta bashi labarin nan bane don ya kaita

gidansu, da ya gaji sai ya tashi yace “tunda

kin ki yarda dani, Allah ya tsare ya kareki na

tafi” ya juya ya dauki Jakanshi yayi gaba,

idan ya barta nan ina ta nufa? Hannu wa

zata fada? Ba zata iya ba, bari dai ta bishi.

Da sauri ta mik’e ta bi bayanshi, tsayawa

yayi tare da juyo wa, ya murmusa yace

“Muje Gida”. Taxi ya tsaida musu yace a

kaisu Hotoro.

*

Zaune suke gabaki daya a Parlor, suna Jiran

Farincikin Gidansu ya shaida musu gashi nan

zuwa, ba sai an aiko daukanshi ba zai hau

Taxi. Sallama yayi a gaban Parlorn Gida tare

da shigowa, da Sauri yaran suka tashi suka

fada mai tare da rungumesu, Matarshi itama

tazo tayi hugging dinshi tare da mai peck,

kunya ta bashi sosai don a kan gidan kowa

hakan ta faru, ya matsa gun Mahaifanshi ya

durk’usa ya gaida su, da farinciki suka amsa

suna mai ya hanya.

Mummy tace ” kaje Kayi Wanka, kazo muyi

dinner muna ta jiranka” yace “wai yanzu

bakuyi dinner ba har 10?” tace “dole muke

jiran ka” ya murmusa yace “Well, bani kadai

bane, da bak’uwa nake” Mummy tace

“bakuwa kuma daga ina?” yace “Tun Dubai

muke tare da ita, its a long story, to cut it

short bata da inda zata zauna, let her stay

here for sometime” Mummy tace “Ayyah, OK

tana ina?” yace “just a min nace ta jira daga

waje barin mata iso” ya fita su kuma suka

tsura wa k’ofan parlon Ido.

Shigowa sukayi a tare. Kan Najwa a kasa ta

tako, Mutumin yace “Najwa, meet My Daddy,

Mummy, Wife sister and my brother” Mummy

tace “welcome my daughter” Najwa ta dago

da murmushi kan fuskarta ta zubesu fes kan

Mummy, Mummy na ganinta ta zabura tare

mik’ewa tsaye gabanta na dukan Uku-uku,

wasu tunani na dawo mata, tunanin da bata

so ta taba tunawa, wannan yarinya na mata

kama da wata, tsanar yarinyan lokaci guda

ya darsu a ranta ba don komai ba don kama

da yanayi da takeyi da Yesmeen. Cikin daga

Murya tace “Ke ya sunan Uwarki?” Najwa

tayi shiru, Mairo kamar zata kifeya da Mari

tace “ko ba kya ji ya sunan Mamanki?”

Najwa da sauri ta 6oye bayan Mutumin da

tazo dashi, yace “Haba Mummy? Menene?

Me ya faru” Mummy cikin hargowa tace “Ta

amsa ni” Najwa ta dago da mamaki tana

mamakin Sudden change din Matar, don me

zata tambayeta Sunan Maama dinta?ko

wani mugun abun zaa mata? To ko matar ta

san Maama dinta? Baki na rawa Najwa tace

“Sunan Mamata Khadija” duk sunji dogon

ajiyan zuciyan da Mummy ta sake, tace

“Babanki fa?” tace “Erhm sunan shi

Muhammad” Mummy ta sake sauke ajiyar

zuciya, kawai yarinyan bata mata bane,

mtsw ta daure fuska tace “Majeed, yarinya

nan ba zata zauna da mu ba, so ka fita da

ita” tsulum Zinatu tace “Yes Ya Majeed, i

dont like her, tell her to go out”.

Majeed yace ” Mummy why? Kin santa ne?”

Mummy tace “Bansan ta bs, amma batayi

min ba, irin su ne ke shigowa gidan mutane

su rusa gida, bar ganinta karama, you dont

know what shes capable of, maybe shes

after you or something” nan da nan Nana taji

tsanar Najwa, Majeed ya hadiye miyau yace

“Mummy ba haka bane, bata san kowa a

Nigeria ba, yau ta zo kasar, an sace mata

Kaya, komai aka sace mata” Mummy tace

lallai Majeed har yanzu yaro ne, baka san

kaidin Mace ba? Tace an sace mata komai

sai kai kaji tausayinta, kace bari ka kawo ta

gidanku? Kila dama abunda take so kenan

ka kawo ta gidanku” Majeed ya yarfa hannu

kasa yace “Mummy please, wallahi akan

idona komai ya faru, please let her stay”

Daddy yace “Maryam, ki barta danAllah”

Mummy tace “kaima ka yarda ko Daddy,

besides muna fama da kanmu ya jajibo

mana wata?” Daddy ya mata alama da ido,

Mummy tace “Alright, just one Night” tana

fadan hakan tace “Zinatu, Muhsin ku wuce

muje” tayi ciki yaran suka bita a baya, Daddy

ya dafa kafadun Majeed ya mai alaman

‘Sorry’ kafin ya rufawa Mairo baya, Nana sai

da ta matso kusa da Najwa ta wurga mata

harara kafin ta wuce dakinta itama, Majeed

ya kalki Zaineema yace “Zee please, ki tafi

da ita dakinki ku kwana tare” Zaineema

batace komai ba tayi ciki, ya san hakan na

nufin bata amince ba.

Ya kalli Najwa da ke ta hawaye yace “I’m

sorry you had to witness this, Mummy na da

trust issue, bata yarda da kowa” Najwa ta

murmusa tace “dagaskianta ai, banji haushi

ba, kaine dai zan ba hakuri, ka samu matsala

da Family dinka saboda ni” yace “Noo its

nothing, yanzu dai zo kici abinci, i’ll talk to

Mum zata barki ki zauna for as long as you

want” Murmushi tayi, ya karasa kan dining

table, Rice and stew ne da plantain, yace “zo

ki zauna kici” tana zuwa wurin table din

kamshin ya cika mata ciki ta matsa baya

tace “I cant eat this” yace Oh sorry, baki

saba da spices din Naija ba, zakici Indomie

Noodles?” tace “yeah, ina cin Indomie ko a

India” yace “Alright, biyoni” ba musu ta bishi

baya, wani daki ya bude mata yace ta shiga

tayi wanka ta bude drawer ta zabi kayan da

zai mata, a tsorace tace “dakin waye? Kar

suji haushi fa” yace “dont worry, dakin

Ziyada ne, my FAV Sis, ba ta da matsala she

wont mind, besides tana Makaranta”. Najwa

tayi murmushi har ranta, har taji tana son

Ziyada din, yace “Oya, jekiyi wanka, kafin ki

fito nagama dafa miki indomie din”. Ya juya

ta bi bayanshi da ido a ranta tace “Can i

trust this one?”.

Bibilicious freaking fans, ga Najwa a Naija,

gata a Gidan Wan Babanta, gata a gaban

Dragon Mairo lol. Rayuwan Najwa ya chanza

daga lokacin da ta shigo Nigeria. Komai ya

fara faruwa a gurinta daga lokacin da ta

shigo garin Kano, ya rayuwan Najwa zai

kasance gaban Hajia Mairo? Ku biyoni don

jin ya zaa kaya.

****

Nuseryber , miemiewaziri0 taatuh meeteelabo

a appreciate you for commenting line by line

#1love

Thanks all, you’ve been supportive, like

always Dont forget to Vote and comment

please.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

Ad

skia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg1⃣8⃣

Sai da ta gama k’are ma dakin Kallo kafin ta

fada toilet tayi wanshi,a toilet din ma Kuka

tayi tayi, fitowa tayi tare da tsane jikinta, sai

da ta shafa mai din da ta gani kan Madubi

kafin ta nufi Sif din Ziyada, a sama taga wat

‘yar doguwar riga mara nauyi, Najwa ta

dauka ta sa, tana mamakin yanda rigar ta

mata daidai kamar nata.

Majeed ya k’wank’wasa dakin,ta mai izinin

shigowa, da ya shigo daga nesa sai ya ga ta

na mai yanayi da Ziyada, har kasa daurewa

yayi “daga nesa kamar Ziyada wallahi”

murmushi tayi kawai, yace “food is ready” ta

daga hannu sama tace “Allah ka sa in iya ci”

daria ta bashi Sosai.

Kan dining suka nufa, daga jin k’amshin ta

san cewa zata iya ci, haka ta zauna taci

Indomie dinnan, Majeed ya dinga bin duk

wani motsinta da kallo. “Oya tashi ki koma

daki” ba bata lokaci ta tashi, suka nufa

daki,ya mata umarnin dauko Hijab cikin

wardrobe, ta dauko ta shimfida, ya ja su

Sallar Ishai, dama ita kadai ce basuyi ba,

ashe Nana na la6e tana kallonsu, yanda suke

sallahn nan kamar wasu Maaurata, bakinciki

tamfar ya kasheta ta koma daki da gudu.

Bayan sunyi adduoi ne yace da ita “Tafiya

mukayi mai nisa, ki kwanta kiyi bacci kinji?

sai da safe” Murmushi takeyi har zuci,

yanayinshi na burgeta, musamman in yace

mata ‘kinji?’ dinnan, samun kanta tayi da bin

umarnin shi.

Majeed ya shiga Dakinsu, ya iske Nana

zaune kan Gado, ta cika tayi Fam, Murmushi

ya mata yace “kizo mu fita mu ci Abinci”

harara ta jefeshi da shi, tace “kagama da

wanchan karuwar?” dimmm yaji wani k’ara a

kanshi, kalmar nan batayi ba kwatakwata,

Kalmar bata dace da Najwa ba, inda san

Wahalhalun da Najwa ta sha, da bata jefeta

da mugun alkaba’i ba kamar haka, daurewa

yayi ya kai zuciyan shi nesa yace “Nana nah,

tashi muje muyi dinner, i’m hungry” ya fada

cikin sigar shagwaba.

Waiyo Dadi gun Nana, ce mata yayi ‘Nanar

shi?’ ya yarda ita din tashi ce, wani dadi ya

lullubeta, gashi har shagwaba yake mata,

waiyo ita, wani sabon sonshi ya sake rufeta,

Majeed ya fara sonta, Cike da salo da yanga

tace “ba baka da time dina ba, sai na

wanchan yarinyar?” dunguren kanshi yayi

yace “wane ni? Haba Nana nah, i’m hungry

please” cike da kissa tace “Oya tashi muje,

kasan ban san Zamanka da Yunwa” ta ja

hannunshi.

Je ki tada Zaineema,Barin je gun su Muhsin,

tura k’ofan dakinsu yayi,kwance suke suna

kallon Cartoon, Ya k’arasa gunsu, Zinatu ta

dauke kai, Majeed ya fara fuskantan Muhsin,

yace “Superman bakayi bacci ba?” gyada kai

yayi, yace”Uhm uhmm” “Oya fita dining,

yanzu zamuyi dinner ko” yaron ba gardama

ya fita, daman yunwa yakeji. Majeed ya juya

gun Zinatu, kai ta girgiza mai “Ya Majeed if

that girl is out there, i’m not hungry” Majeed

ya furzar da iska, da wani me saurin hannun

ne da ya kai ma Zinatu Duka, amma ba haka

yake ba, responsibility dinshi ne faranta ma

Family dinshi, ya daure dai yace “Bata nan,

ta na daki, lets go” ba musu Zinatu ta tashi.

Dakinsu Mummy ya fada, iske su yayi suna

gardama da Daddy, zuwa yayi ya shiga

tsakaninsu, tare da murmushi mai sanyi yace

“Daddy, yaranka na jin yunwa, kaima kana

jin yunwa, Suna kan table suna jiran

fitowarka, Daddy ya bubbuga kafadun Majeed

ya fita parlor, Mumny ta wani dauke kai,

kamar bata san da Majeed a gun ba,

tsugunnawa yayi gabanta, ya kamo

hanayenta guda biyu ya kama ya rik’e, yana

so su hada ido amma ta k’i yarda, yasan

weekpoint din Mummy.

Cike da sanyi yace “Mummy please” tasgi

tayi ta janye hannunta tare da cewa “Majeed,

bana son yarinya, from first impression, na

gaya ma, bata yi mun ba” “Mum Najwa is

clean, i trust her” “then you are a fool, nayi

zaton kana da wayau, ashe ba haka bane,

meye mutanen yanzu ba sayi? Don kawai su

cimma burinsu, Boy, gobe ka fitar da ita, ba

zata sake kwana ba daga gobe”. Ya

shashantar da maganan ta hanyar cewa

“Mummyn Boy yunwa nakeji, lets have dinner

please” tasan bribing dinta yakeyi, don yasan

tana son shi sosai, dukan wasa ta kaimai a

hannu tace “lets Eat” “Ohh Mumny na you

are the best” ya ja hannunta suka fita

Parlorn inda kowa yake zaune.

Addua sukayi suka fara cin Abinci, duk

yunwa sukeji, ba kamar yaran, Najwa na

kallonsu, don kasa bacci tayi, sosai Majeed

ya burgeta, yanda yake son Family dinshi,

yanda ya hado kansu bayan sunyi fushi

dashi, yanason Family dinshi, hawaye masu

zafi suka zubo mata, ina ma ace Sun tashi

da Yayanta, zai so su kamar yanda Majeed

ke son Family dinshi?, Kuka ta farayi da ta

tuno Mamma, kuka ta farayi da ta tuno

rayuwansu a India, shiru tayi don ta fara jin

magana sama-sama.

“Munyi Aptitude test din, InshaAllah akwai

nasara, don komai ya tafi daidai,akwai wani

dan Nigeria a cikin Manyan, tunda ya ganni

yake ta kyautata mun, yace lafiya lau zai min

hanya, zasu neme mu sukace” Daddy yace

“Allah ya sa rabo ne” duk suka amsa da

“Amin” duk yanda zaiyi yayi dodging

maganan Najwa sai da yayi, be bari sun

sako zancenta ba balle Mummy ta burkice

masu, hakan suka gama da cin

Abincinsu,suna fira jefi jefi. Nana taji wayar

ta na ringing, da sauri ta tashi tayi daki da

gudu, da mamaki Majeed ya bita da ido,

k’arfe 11 fa wake kiranta a daren nan?.

PH Ng

Kasa sukuni yayi, fargabanshi daya, a yi

employing Majeed, in har Majeed ya samu

Aiki ai Plan dinshi zai ruguje, ba zaiyi

acheiving komai ba, all his efforts will go in

vain, ba zai bari hakan ya faru ba,Majiyanshi

ta shaida mai, Majeed ya duro Nigeria,amma

abunda be sani ba, meyi matsayin Majeed a

Hilal Investments, yana kuma so ya sani,

Mutum daya zai fayyace mai biri har

wutsiya, ya duba Agogon wayanshi, k’arfe

11:10 na dare be damu me zai je ya dawo

ba, ya latso Numbern Nana Nakowa.

Da tsaki ta dau wayan “Hello, meyasa kake

kirana da daren nan? Bashi kake bina?”

Murmushi Zaid yayi, yace “Mijinki ya

dawo,so howfar?” tsaki tayi tace “donAllah

ka daina bibiyata, you wont hear a thing

from me” Zaid ya dara yace “Is that so?”

hakan da yace Nana ta gano abubuwa cike

da “is that so?”din, sai ta tsorata da lamarin

mutumin nan, kar fa ya tona mata asiri, da

sauri ta kwashe duk abunda Majeed ya sanar

dasu Yanzu. Zaid yace “Good Girl, sai na

sake nemanki” da sauri Nana tace “kayi wa

Allah kar ka sake kirana” tuni Zaid ya kashe

wayan.

Daidai da shigowan Majeed, lokaci daya ta

shiga taitayinta, Majeed yace “Wa ke kiranki

da daren nan?” da sauri tace “Mom ce”

yanda tayi maganan ta san bai yadda ba,

amma tayi saurin isa gareshi don mantar

dashi wani tunanin.

Washegari.

Mummy da kanta ta shiga kitchen ta hada

breakfast, Tea and Bread ne da K’wai, lallai

rayuwa ya chanza musu, da breakfast dinsu

abun kallo ne, masu aiki sai suyi mus kalaci

kala kala, amma yanzu da chanjin yanayi

yazo, Tea Bread and Egg kawai zasuci, ba

kuma masu Aikin, itace zatayi dole, indai

zasu jira Nana ta musu breakfast sai dai su

yini da yunwa, bata tunanin ko ruwan Zafi

Nana ta iya dafawa, ita kuma bata yarda ta

bar yaranta da yunwa ba.

Fitowan Majeed kawai sukeyi suyi Karin

kumallo, yana fitowa yayi dining din tare da

gaishesu duka “Ina kwananku” sam Majeed

be da girman kai, har dan karami yana iya

gaidashi, har ya zauna kuma kamar an

tsikareshi ya tashi, duk suka bishi da ido,

dakin Ziyada ya nufa, ya k’wankwasa tare da

Sallama, Najwa ta amsa tare da bude mai,

Murmushi suka sakar ma Juna, kallo daya

ya mata ya san ta sha kuka Daren jiya, don

fuskarta tayi ja, idonta yayi luhuluhu, gaishe

shi tayi, ya amsa da murmushi yace “muje

muyi breakfast ko” murya a dashe tace “Your

Mummy” ya murmusa yace “Bakomi, muje”

kanta a kasa ta bi bayanshi har gaban kowa

a dining table.

A hankali tace “Ina kwananku?” Daddy kadai

ya amsa,Majeed be damu ba ya ja mata

kujera yace “sit” zama tayi, ya dauko Mug ya

hada mata Tea mai kauri, ya ajiye gabanta,

zai dauko mata egg a cooler Mairo tayi

daurin cewa “saura daya, kuma naka ne”

murmusawa yayi yace “let her have it then”

Mummy ranta bace, idon Nana kamar ya

fado saboda harara, cikin natsuwa Najwa ke

shan Shayin nan da kwai tana hadawa da

biredi har taji muryan Mummy na cewa

“Najwa, zo ki kara min Ruwan Zafin nan”

zata tashi da sauri Majeed yace “barin kara

mata” Mummy tace “Majeed”. Najwa ta mai

alamun ya bari, zata zuba mata, tashi tayi ta

dauki flask din dake kusa da ita ta k’arasa

gun da Mummy ke zaune.

Bude flask din tayi ta fara zubawa a Mug din

dake hannun Mummy a hankali don gudun

kar ta k’onata da ruwan don akwai zafi

sosai, kawai Mummy sai sakin Kofin tayi

k’asa, kofi be dire ko ina ba sai kan kafar

Najwa, wani Ihu Najwa ta saki da k’arfi tare

da zubewa k’asa sumammiya, Majeed be san

lokacin da yayi sauri ya dauketa daga wurin

ba, kuka takeyi Sosai, Kofi daya na ruwan

zafi ya zube a k’afarta, Daddy yace ” Majeed,

k’una ne sosai, ka kaita Asibiti” Daukanta

Majeed yayi tsam a jikinshi ya fita da ita, da

sauri ya dawo daukan Key, nan ne yakejin

Daddy nace ma Mummy “Don me zatayi

haka? Ya ga lokacin da ta sake ma Najwa

Cup a k’afa kuma da gangan” kallon Mummy

kawai Majeed yayi cike da 6acin rai, har

Mummy taji gabanta ya fadi, amma don bai

da lokaci ya sa kai ya fita.

Nana cikin 6acin rai tace “Mummy kina

kallon yanda yake rawan jiki kan karuwan

nan ko? Mummy har daukanta yayi fa”

Daddy ya ji takaici, ya tashi ya shige Daki,

Mummy tace “Daughter inlaw barni da shi,

har ita shegiyar yarinyar, ni na san yanda

zanyi da ita, da kanta zata rarrafa ta koma

inda ta fito don ubanta, ku dai trust me and

keep watching” Nana ta jinjina kai, Zaineema

ta ta6e baki tace “kila bata barshi haka ba,

yanda yakeyi mata akwai ayar tambaya”

Mummy tace “Aiko da bak’ar Ja6a take tsafi

sai ta bar gidan nan, mu dai je zuwa”.

INDIA

Kukan da Maama keyi har ya fara ba Paapa

tsoro, shima dai yayi kukan don hankalin shi

ya gama tashi, babu yanda zasuyo, tun jiya

suke tsumayin kiran Najwa amma shiru bata

ba alamunta, “is she Ok?”Tambaya dubu da

Maama ke tama Paapa kenan, be da amsan

da zai gaya mata, be da halin sanin ya

Najwa take? Sun kira number wayarta ya kai

so nawa dukda suna da tabbacin cewa

number ba zai shiga ba amma basu daina

dialing numbern ba.

“Najwa ta salwanta kamar yanda Zaid ya

salwanta, shikenan ni Yesmin tawa ta k’are,

ya zanyi Papi? First it was Zaid and now

Najwa? Ya Illahi, i cant take it” sai ta fashe

da kuka. Pappa sai ya rungumeta, yasan be

da bakin lallashinta, shima hankalinshi tashe

yake rashin kiran da Najwa batayi ba,

Ubangiji Allah yasa tana lafiya, Allah ya sa

tana hannu nagari, da ya samu k’arfin guiwa,

sai ya hau lallashinta da cewa “Yesmeenah,

kar ki tada hankalinki please, yana iya

yiwuwa cewa Ta isa, ko wayarta ba chaji, ko

kuma bata siya Simcard ba, maybe shes

settling, donAllah ki kwantar da hankalinki,

she is fine da izinin Allah”. Ta tsagaita kukan

tace ” amma tun Jiya ta tabbatar mana zata

kiramu,me ya hanata in komai daidai ne, da

ta na Dubai ai da wani number ta kiramu?

Meyasa sai a Nigeria ne ba zata kiramu ba?

yanzu karfe 3 fa anan, gari ai ya waye a

chan, ina jin Tsoro Papi”. Shima ya san

gaskia ta fada, addua kawai yakeyi a

zuciyanshi.

PH ng

Wani farinciki ya lullube zuciyan Zaid da ya

tuna firansu da Alhaji Haruna Mafeci na Hilal

Constrution Company Dubai. Tun safiyar yau

be sha wahalar Contacting din Alhaji Haruna

ba saboda shi din mai Connections ne, a

k’asar nan yanzu wa ka sani wa ya sanka

ne. Ga yanda firarsu ta kasance;

“Assalam Alaikum, My name is Zaid Sadam

Audu, i’d like to speak to Alhaji Haruna

Mafeci” haba ko ba komai Alhaji Haruna

yasan Young multibillionaire Zaid Sadam

Audu, tuni Alhaji Haruna ya chanza harshe

yace “Ranka ya dade” Zaid yayi Murmushi

kamar yana gabanshi yace:

“Nasan you are busy, so am i, so lets go

straight to the point, shall we?” “Yes please”

Zaid ya fara magana “Akwai AbdulMajid

Abba Abu dan Nigeria da yayi Aptitude test

din Hilal Constructions ran Monday haka

ne?”Da sauri Alhaji Haruna yace ” Tabbas,

wani dan Kano, follow up kake mai? Ai tun

rannan nayi assuring dinshi zaa bashi offer

InshaAllah, anayin wasu verification ne first

kafin nan”. Zaid yace “No, ba follow up nake

mai ba, actually bana son ya samu aikin nan,

he was my employee, so yayi betraying trust

dina ne shisa nayi firing dinshi, whatever

happens he must not get that offer kagane?”

Alhaji Haruna yayi shiru yana nazari, be ga

wani illah a tattare da Majeed ba, duk cikin

yan Nigerian da sukayi test din, Majeed yafi

burgeshi, amma saboda yana so wata rana

Zaid Sadam ya mishi Alfarma, ba zaa su

dauki Majeed aiki ba.

Zaid ya sake cewa “Alhaji Haruna ka

fahimta?” yace “Eh ranka ya dade, he wont

work with us, kar ka damu” a takaice Zaid

yace “Ban damu ba” ya kashe wayan. Ko

Minti biyu baayi ba Alhaji Haruna ya mai text

message inda yake cewa “kayi hakuri ba wai

nace kar ka damu da wani manufa bane,

Allah ya huci zuciyarka, AbdulMajid Abba

Abu’s offer is declined”. Murmushi Zaid yayi

ya mai reply da “Noted, you wont regret

this”.(Ikon Allah, wato haka abun yake wa ka

sani? Wa ya sanka? Muma Allah hada mu

da manya lol).

K A N O

Emergency aka karbi Najwa, bayan an samu

ta farfado, akayi dressing kafan da ya

suntume ya kwaye ya kuma yi Jazir, aka

rubuta mata maganin shafawa, Majeed ya

shiga bata hakuri, tayi assuring dinshi cewa

bakomai it was an accident. Haka suka

koma Gida da taimakon Majeed take tafiya.

Har daki ya kaita, ta fara baccin wahala.

Straight dakin Mummy ya wuce, Ita kadai ce

zaune Daddy ya tafi bugabuganshi.

Kallo daya ta mishi ta dauke kai “Mummy,

what were you doing? Mummy nasan da

gangan kika saki Cup dinnan, Mummy me ta

miki kika tsaneta? Idan baki yarda da ita ba

then fine, but please dont hurt her, yarinya

ce, just like Ziyada, ya zakiji in wasu sukayi

maltreating Ziyada kamar yanda kikayi? Sai

inda karfin ki ya kare ai? Zaki taka wanda ya

taka yaranki Haka kike cewa Mummy, So

Mummy Consider Najwa’s Mom, ya zataji?

Itama zataji kwatankwacin abunda kika ma

diyarta, donAllah Mummy ki bari, abunda

baka so a ma danka kar kayi ma dan wasu,

Mummy please, zata cigaba da zama da mu

for sometime, zata koma gidansu, kinji?”.

Galala take kallonshi, wato Majeed saboda

wannan tsinanniyar yarinyan ne yake mata

Waazi? Lallai kam, ba abunda taji, illa ya

shiga ta nan ya fita tanan,sai ma Wutar

kiyayar Najwa na ruruwa a zuciyarta.

Tsaki ta buga da k’arfi tace” Majeed kar

kaga Ina abubuwan da kakeso kace zaka

dinga yanda kakeso dani, daga kallo daya

naji wani irin tsanar yarinyar Mai karfi, you

cannot change that, kuma in zata zauna

wallahi sai dai boysquaters ba dai cikin Gida

ba, ganinta na k’ona min rai, ta fitar ma

Ziyada a daki” haka Mummy ta dinga surfa

Masifa. Ina Majeed bata kanta yake ba,be

tare da ita hankalinshi ya karkata ga Email

dinsa da akayi notifying din shi ta Wayarshi,

“Inalillahi wa ina ilaihir rajiun” yace tare da

dafe kai.

Da ta lura hankalinshi be gareta sai cewa

tayi “Wato ‘yar iska ka maidani ko Boy? Ina

maka magana kana latsa waya, don nace

kanwar Uwarka ba zata zauna a cikin Gida

ba ko? Anya Majeed Karuwar nan ta barka

haka kuwa? Anya bata wanke ta baka kasha

ba?”.

Da k’arfi yace “Mummy”.

Kallonshi tayi sosai, tana so ta gane yanayin

da ya shiga cikin Seconds din da ba su wuce

hamsin ba,ta karaso kusa dashi ganin

hawaye a idonshi ta dan tsorata tace “Yadai

Boy?” cikin sanyin jiki yace “Mummy i’ve not

been accepted, banci test din da nayi a Dubai

ba, Mummy, nayi depending kan Aikin nan,

Mummy i’ve failed you all” be san lokacin da

hawaye ya soma kwaranyo mai ba. Nan da

nan Mummy ta shiga hankalinta ta tattaro

Majeed jikinta, duk da tafi shi shiga tashin

hankali amma sai ta fara lallashin shi ta

hanyar cewa “Majeed, ba kayi failing dinmu

ba, You are all i’ve ever wanted, ina Alfahari

da kai, i’m really proud of you Boy, yanda ka

tsaya ma Family dinka, ka kwantar da

hankalinka, Mummy wi find a way, its Gonna

be fine” da sauri Majeed ya tashi ya share

hawayenshi, ya kamata ya zama karfinsu, ya

yi Murmushi yace “Its gonna be fine

InshaAllah, Allah ya sa Hakan yafi Alheri, kila

ba Alheri bane shiyasa Allah ya kaddara ba

zan samu ba, Allah ya musanya mana da

abunda yafi zama Alheri” ya juya ya bar

dakin, Galala ta bi bayanshi, halin Majeed na

bata Mamaki, yana abu kanar yafi uban

kowa sanin Allah ji wani addua, ta buga

tsaki, wai Allah sa hakan ne yafi zaman

Alheri, rashin samu aikin shine Alheri? Tab,

har yanzu akwai kuruciya a tare da Majeed.

Tashi tayi Zama be ganta ba ,dole ta tashi

ta nemo musu Mafita.

*****

Hello Masoyan Asali, Ga babi na sha

Takwas.

Put a smile on my face by Voting, and

commenting line by line.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

Kamata yayi ace ya kadaita kanshi a halin

yanzu da zuciyarsa ke mai zafi, Samun

kanshi yayi da shiga dakin Ziyada inda

Najwa ke Bacci, kujera ya samu ya kafa

gaban Gadon ya k’ura mata ido.

Abunda ya bashi mamaki shije irin tsantsan

kaman da Najwa keyi da Kanwarshi Ziyada,

dama ana samun irin haka? Ba ku hada jini

da mutum ba amma kaga kama har haka?

How can they look this alike? Ko da yake

ance kowa a duniya yana kama da wuni, so

it happens.

Zuciyarsa ta karkata ga rashin samun aikin

da beyi ba, sosai be ji dadi ba, amma ba

yanda zaiyi, Musulmi na kwarai shine wanda

yake rungumar k’addararsa a duk yanda tazo

mai, a fili yace “Allah ka bani ikon cin

Jarabawar nan”. Yana kallo Najwa ta bude

ido a hankali, yayi saurin tashi tare da mata

nunin ta koma bacci.

Yamutsa fuska tayi tare da yunkurin tashi,

yayi saurin cewa ” Najwa ki koma bacci

kinji?” girgiza kai tayi tare da cije baki.

Sannu ya mata yana tambayan ta in kafan

na ciwo, gyada kai tayi tare da digon

hawaye, har ranshi take bashi tausayi. A

hankali tace “Zanyi fitsari” cike da tausayawa

yace “ba zaki iya tafiya ba ko?”. Ta gyada

kai yace ” Yi hakuri ina zuwa, da sauri ya

fita Najwa ta bishi da ido.

Nana ya iske a dakin baccinsu, yace

“Nananah, donAllah zo ki kama Najwa ki

kaita toilet” Nana ta wurga mai harara tace

“dazun da ka rungumeta a kirjinka fa ka fita

da ita fa? Ai yanzuma sai kaje ka dauketa ka

kaita toilet” ya dan rausayar da kai yace

“dazun ai laluri ne, k’one kafa tayi, a sume

take fa Nana, donAllah kar ki zama mara

tausayi muje ki kamata” yanzun ma ai laruri

ne sai kaje ka dauketa ka kaita ka jirata tayi

abunda zatayi in yaso kai mata tsarki”.

Ranshi ya baci, ya juya ba tare da yace

mata komai ba, bari yaje ya rok’i Zaineema

kila ta zo ta taimaka ma Najwa.

Yana fita wata zuciyar tace ma Nana, kar

fa yaje ya dauketan, da sauri ta bi bayanshi

da ya kara ta6a Najwa gwara ta kai

zuciyarta nesa ta taimaka mata, Majeed

naganin tabishi daki yaji dadi ya tsaya a

waje, wata uwar Harara Nana ta buga ma

Najwa sai da hanjinta suka kada, tashi

Karuwa in kamaki ki shiga toilet” duk da

Najwa bata san maanar kalmar ‘karuwa’ ba,

amma tayi amanna ba kalmar arziki bace.

Kamata tayi sukayi toilet, dan gayya Nana

ke janta, Najwa tun cikin wando ta fara

fitsarin saboda Azaba, bata ga Amfanin

kamota da Nanan tayi ba, don riketa tayi

kamar tana kyamarta, Najwa ta fara hawaye,

tayi tsarki ta zuba ruwa a inda fitsarin ya

taba, Nana ta sake kamota ta jefata kan

Gado, da gayya ta kuma take kafar da ya

k’onen.

Najwa ta sa hannu ta gumtse bakinta da

sauri gudun kar ta sake Ihu, hawayenta ya

yawaita, Nana ta buga tsaki ta sursurfa

mata zagi kafin ta wuce. Majeed na ganinta

yayi saurin cewa “tayi ko?” Ba tare da jiran

amsan Nanan ba ya sa kai dakin, Nana tayi

saurin rik’oshi tace “Tace Bacci zata koma”

Majeed ya dan dakata yace “Is that So?”

tace “Yes” ta ja hannunshi suka shiga

dakinsu.

Nana na karantar damuwa a fuskar

Majeed, kar dai ace ya damu da wanchan

karuwar ne, gaskia ita ta gaji, daurewa dai

tayi tace “My Majeed, you look worried? Don

ko don yarinyar nan ne?” gabana na dukan

chalugude don gudun amsar da zai bata, iska

ya furzar kafin yace mata “Nana, ban ci

Test din da mukayi a Dubai ba Ba su ban

aiki ba”.

Nana ta rausayar da kai tace ” shine ka

damu haka? donAllah share, zan ma Dad

dina Magana, zai kula da mu duka” Majeed

yayi murmushin takaici ya daiyi shiru be ce

komai ba, nan Nana ta fara soki burutsun ta,

da ya ga zata matsa mishi sai ya mike ya

shiga Toilet.

Bayan Kwana Biyu.

Ba laifi tana taka k’afar da kanta ba tare da

an kamata ba, a cikin kwanaki biyun nan ta

gama karantar Halayyen Abdulmajeed.

Mutum ne mr kirkin gaske, yana da kawaici

da kauda kai, yana kula da ita yanda ya

kamata, ganin ana kyararta in ta fits cin

abinci yasa shi dinga kawo mata Abincinta

daki. Kafarta ya fara bushewa don maganin

hausa ya amso mata gun wani Sarkin Baka

(likitan fatar Gargajiya) Wannan Kenan.

*

“Maryam kin tuna Aina’u Habib?” Mummy

ta ta6e baki don ta ganeta tsaf, Abokiyar

Aikin Daddy ne tun shekaru 18 da suka wuce

lokacin yana Koyarwa, Sosai Matar ke bata

haushi, haka kurum bata mata ba, shirun da

tayi ne ya fahimtar dashi ta ganeta, ya

cigaba da magana, amma wannan karon

hankalinshi na kan Majeed.

“Abokiyar Aikina ce in the 90s, after a long

time mun hadu dazun a traffic, ta

tambayeka, nace mata you’ve grown alot har

kayi aure, she was suprised, tace kayo saurin

girma, ta tambayeni inda kake aiki, na gaya

mata ba aikin nan, so tace ina gaya ma ka

kai mata CV dinka, InshaAllah zata nemo ma

Lecturing a WUDIL, don yanzu she’s a Dean.

Karaf Mairo tayi tace ” Lecturing? Majeed din

ne zaiyi lecturing? Daddy Mallamin

Makaranta fa, Allah ya sauwake, kawai sai a

ga Yaro yaje wani makaranta koyar da

Dalibai, Yarona ya fi k’arfin wannan, so tell

your Old Friend bama bukata” Majeed zaiyi

magana Mummy ta dakatad da shi ta hanyat

daga mai hannu, beyi shiru ba, yace

“Mummy Lecturing fa, meye aibin zama

Lecturer? They pay Good, atleast zamu rage

ma kanmu wasu nauyin”.

“No Son, bama bukatar taimakon wannan

Bayerabiyar, ba donAllah zata neman maka

aiki ba, tun kana karami take bin Daddynka,

so bama so, bamu san me take shiri a

kanmu ba, besides i have plans for you, just

be patient”. Majeed yayi shiru, Daddy yace ”

Maryam–” Mummy tace “Allah Daddy Majeef

ba zaiyi Lecturing ba, akwai abunda nake

mai hange” Tashi Majeed yayi zai bar Dakin

Mummy ta tsaidashi a hanyar cewa “Ya

maganarmu, inace kafan nata ya warke?

Yaushe zata tafi?” Rausayar da kai yayi yace

“Mummy ki dan kara mata lokaci” kafin ta ce

wani abu ya bar dakin da sauri.

*

Tashin Hankalinta be wuce tafiyar da

Majeed yace mata zaiyi ba, taya zata rayu

da Mutanen da k’irik’iri suke nuna mata

tsana? Anya zata iya zama har yayi wasu

kwanaki baya gidan? Amma da ta tuna

kalaman Majeed inda yake ce mata “Kwantar

da hankalinki zakiyi, ba dadewa zanyibba,

k’anwata kawai zan dauko daga makaranta,

sai in dan bincika in akwai offer din Aiki but

ba dadewa zanyi ba, befi 2-3days ba, so

karki damu everything will be fine”.

Bakinta na rawa tace “Mummy fa?” yace

“tace zaa kula da ke har in dawo” jim tayi ba

wai don ta yarda dashi ba, ko safiyar nan sai

da ta zabga mata harara, ta san fa Mummy

bata santa, amma don me zata cemai zasu

kula da ita? Isit a trap?” lura yayi da ita

yace “karki damu Najwa Mummy will take

care of you for me, ita tace haka, kuma i

trust my Mom more than anything, in zatayi

zatayi, in ba zatayi ba ba me sata yi, so

since she said it, to zatayi, kedai kawai ki

dinga shafa maganin nan akan lokaci” Yak’e

kawai Najwa tayi ta gyada kai.

PORTHACOURT Ng

Ya san Hardwork din Mahaifinshi ne, ba zai

manta ba, lokacin K’asar Italy Babanshi da

Mamanshi sukaje don ganin Haduwar

Company din nan, tuna Mahaifanshi ya k’ara

tada mai hankali, sun rabashi da nashi

Mahaifan, amma suna zaune da nasu Yaran,

ba zaiyiwu ba,a hankali zai watsa su duka.

Wayarsa ya dauko yayi dialing number ya

kara a kunne yayi magana umurni ya bada

da a rushe ABBA ABU AND SON’S

FURNISHING COMPANY, ba don komai ba

sai don idan sun shiga matsi suna iya saida

Companyn su samu kudi, to kuma zasuji

dadi, shi kuma zai shiga k’uncin, don

Bak’incikinsa shine Farincikin Iyala Abba

Abu, amma inyayi haka, tunda yana da

possesion of Takardun Mallakan Gurin so

komai zaizo a sauk’ake.

**

Bayan wasu ‘yan kwanaki

K A N O

Gidan wata tsohuwar k’awarsu Hajiya

Balaraba Matar Depyty Givernor din Garin

suka nufa, bayan long process aka ma su

Hajia Mairo da Aliya wurin her Excellency.

Suna haduwa suka hau shewa, chan cikin

dakin suka k’ulle suna firan yaushe gamo,

fira tayi dadi aka sako mulki, suna fira ne

dan Hajiyar ya shigo, zaiyi tsaran Majeed,

amma tafiya yake kamar dan shekara 15,

Abun mamaki yaron nan be zame ko ina ba

sai kan cinyan Mamarshi, ya daura kanshi a

kan cinyarta ya fara zuba shagwaba. Wow

Mairo ta shagala da kallonsu, duniya bata ga

abun da ya burgeta ba kamar Hajia da danta,

shagwaba yake ta zuba mata dai biye mishi

take tayi, tace “Amjad ga wasu Mummies

dinka nan, ka gaida su” sai a lokacin ya

kallesu, da murmushi lan fuskarshi yace “My

Mummies, ina Kwananku” Mairo baki har

kunne ta amsa.

Hajiya Balaraba tace “kun ganshi nan,

shekararsa 29, amma ko budurwa be da ita”

ya wani buga kafa kamar dan yaye yace

“Mom nace miki ba zan yi aure ba, bana so

inyi nesa dake, so na hakura da Auren” Hajia

Balaraba tayi daria sosai, tace “kunji ko?

Maganar kenan, bayan na gaya mishi in yayi

aure a nan zai zauna yanda zau dinga

ganinja kullum” ya wani mak’e kafada wai

“uhm uhm”. Haushi ya cika Hajiya Aliya,

irin ya ma zaayi k’aton Gardi kamar wannan

yayi ta sakata gaban su haka kamar me

shan Nono, ita ko Mommy Mairo burgeta

sukayi, ina ma Majeed zai dinga mata

haka?.

“Amjad” Mairo ta cire baki ta kirashi, ya

kalleta, ta danyi jim kafin tace “ba zaka

zauna haka ba aure ba, shekara 29 fa? Yaro

na he’s 28 amma har yayi aure, meyasa ba

zakayi auren ba a kawo matar nan? Yanda

ga Mom dinka ga Wife dinka? Uhm?” shiru

yayi kafin yace “to, Mummy ki zaba min

matar da kike so ta zama daughter inlaw

dinki” Hajia Balaraba tace “really? Kai

amma naji dadi, Hajia Mairo nagode da kika

sa hankali a kanshi” .

Mairo tace “haba Hajiya Balaraba, ai duk yi

wa kaine, in ba damuwa ai ga ‘yar wajena

nan, Ziyada, na san zai sota” Mairo ta

lalubo wayarta cikin jakka ta nemo hoton

Ziyada ta mika ma Her Excellency”

“MashaAllah, Amjad ka gani?” ta mika mai

“Woww, ta yi Mom, ina so Wallahi” Hajia

Mairo da takama tace “ai na san zata maka,

saboda ta hadun ne” sukayi daria, yace

“Mother Inlaw ina Matata? ” dadi kamar ya

shide Mairo tace “kar ka damu, Yayanta

yaje daukota a Baze University, har nan zan

kawo maka ita” Amjad ya girgixa kai yace

“like every other princess, the prince go to

her, itama ni zan zo gunta” . ya mike yace

zamuyi magana da Mom, ku gaida gida, ya

duka yayi pecking Mom dinshi ya fita daga

dakin

Mairo taji dadi har ranta. Hassadar Hajiya

Aliya ya ki boyuwa a fuskarta, tafi shiri fa

da Hajia Balaraba, amma Hajiya Mairo ta

mata shigoshigo ba zurfi yanzu ya zatayi da

diyarta da ta mata alkawarin auren Amjad?

Mtsw, cewa tayi “Mairo tashi mu tafi Gida,

lokacin dawowan yara yayi” Mairo tace

“hakane, nasan su Zinatu ana hanya” Hajia

Balaraba ta mike a dauko rafar dubu daya

guda biyar ta basu, Mairo irin abunnan wai

ki bari, ba zamu karban nan ba, tace

donAllah ku karba, Mairo tace “Allah ya

sauwake” ba tun yau ba Hajia Balaraba ta

san Mairo da girman kan tsiya, Murmushi

kawai tayi taba Hajia Aliya, Hajiya Aliya ta

amsa tayi Godia, Hajia Balaraba tace “toh

Hajia Mairo, sai munyi waya, Amjad zaizo”

Mairo tayi Godia suka tafi.

*

Sai da Hajiya Aliya ta kawo Hajia Mairo

har Gida, Hajia Mairo tana ta jiran Hajiya

Aliya ta fiddo kasonta ta bata amma shiru,

Mairo tace a ranta *kina karyan tsiya ne”

hannu ta sa ta dauko Jakkar Hajia Aliya ta

bude jakkarar, Hajia Aliya tayi saurin riko

Jakkar tace “Yadai Hajia Mairo?” tace “kaso

ma zan dauka” hajia Aliya da mamaki tace

“kasonki kuma? Ba bakya bukata ba, ta

baki kin ki karba” Hajia Mairo tayi tsaki

tace “zancen kike so” ta dauka rafa uku, na

ukun ta irga dubu hamsi ta hade da sauran

ta maida mata sauran, ta rufe ta ajiye, ta

kalli kawarta tace “kawas, mu yini lafiya ta

bude murfin motar ta fita, hajia Aliya tace ”

Mairos, ba girman ki bane ba fa, kin fi

karfin dubu dari biyu da hamsin” Mairo ba

ta waigo ba balle ta amsata a ranta tace “ko

dubu 10 aka bani yanzu hannu zan sa in

karba”.

*

Cikinta yayi kuka a karo na ba adadi,

rabonta da abinci tun shekaran jiya da

daddare, ruwa ma sai na toilet take sha, da

ta fita sun dinga kyararta suna

tsangwamanta, har rankwashinta Mummy

tayi Jiya. Tana cikin yanayin nan sai ji tayi

an banko k’ofar dakin da k’arfi, sosai ta

firgita. Mummy ce da Nana ne shigowa

sukayi, Mummy tace ” Danubanki in ba

dakin Uwarki bane fita, yau me daki zata

dawo, ba zan yarda ku kwana runfa daya ba,

bansan mugun abun da zaki mata ba”

Najwa ta dago idanuwanta da suka soye

saboda kuka tace “kiyi hakuri, ku bari

Abdulmajeed ya dawo” Nana ta galla mata

mari tana huci tace “Abdulmajeed din

tsaranki ne da ubanki? Uban me kika ma

Mijina da yake kwakwarki? Anki a barki din”

Mummy tace ai darajarshi taci shiyasa ta

kwana har 8 a gidan nan, kuma dai don kar

in fuskanci fushinshi wallahi da na koreki

daga gidan nan, amma dole ki koma

boysquaters, shima yazo ayita ta k’are”.

“Zaki tashi ko ba zaki tashi ba?” shiru ta

musu Ta riga ta galabaita, ta mika wuya

suyi yanda zasuyi da ita, da sun san yanayin

da take ciki da ko magana ba su sata ba,

bata ankara ba sai ji tayi Mairo ta ja ta a

kasa kamar wasu kayan wanki suka fita, ba

ta bar janta ba, Azaba ma ya hanata kuka,

sai dai ta lumshe idanuwanta. A ranta take

cewa “Allah gani gareka, kila ma mutuwa

zanyi, Allah ka sa Maama da Paapa su

yafeni”.

Cikin hargowa taji ance “Mummy—” duk

suka kalli Kofa, Majeed ne da Ziyada ne

tsaye, da sauri Mummy ta saketa, Nana ta

fara sosa k’eya, ba su taba zatan zasu iso

da wuri haka ba, Majeed ya tako wurinsu

yace “Mummy amanar da kika daukar mun

kenan? Mummy ji yanda kike janta kamar

wani abun da baaso? Haba Mummy, ina

zaki kaita?” Mummy ko a jikinta tace “BQ

zan kaita, Majeed saboda kai na barta ta yi

tsawon kwanakin nan a gidan nan despite

the fact that i dont like her, but na hakura

saboda farincikinka, dont use your

happiness to take me for granted, i wont

take it anymore, Ziyada ta dawo dole ta bar

mata dakinta”.

Daddy ya shigo gidan yace ” Yadai meke

faruwa? Ziyada sannunku da zuwa” Mummy

tayi karaf tace “wanchan bakuwar nakeso ta

koma BQ tunda yaro ya nace sai ta cigaba

da zama a Gidan nan, ina laifi tunda nace ta

koma BQ?” Daddy ya danyi Jim yace

“Maryam Hakuri zakiyi, ba yanda zaayi ta

koma chan ita kadai, mace ce fa? Yanzu

zaki iya barin Ziyada ta koma BQ? Iyi

Maryam?” Mairo bata amsa shi ba, ya

cigaba da cewa “Kuma na tabbatar Ziyada

bazata damu sharing daki da Bakuwa ba do

you Mind Ziyada?” Girgiza kai tayi , Daddy

yace “kingani Maryam?” Mummy tace “to

wallahi dole yarinya ta fito ta dinga aiki don

ba za mu dinga ci da katuwar banza ba”. Ta

kalli Ziyada tace ” come with me my

daughter” fuu ta wuce Ziyada ta bi bayanta.

Daddy ya sauke numfashi yace “kuyi hakuri

Majeed, ku kara hakuri” ya wuce daki, Nana

ta wurge su da harara tayi daki. Majeed ya

kalli Najwa da ke yashe a k’asa, gashin

kanta ya rufe fuskarta, ya taka har gabanta

ya tsugunna, kamar zaiyi kuka yace “Najwa

i’m so sorry, ki yafe min, ban san haka zai

faru ba”. Da kyar ta dago kanta tace ” Ya

Majeed, ba laifinka bane, its nothing, kar ka

damu” yace “me ke miki ciwo? Me

kikeso?” a hankali tace “i am hungry” da

sauri ya tashi ya nufa kitchen, flask ya

dauko ya hada mata tea, anci saa akwai

bread ya dauko mata ya kawo yace “gashi

ki fara da wannan, kafin na dafa miki

indomie, tashi kije daki ” kai ta gyada, ta

mike a wahalce ta tafi daki, ta fara cin

bread din tana hadawa da tea din.

**

Majeed wurin Mummy ya nufa, Ziyada ta

mai nuni da yayi hakuri, ta tashi ta fita ta

barsu da Mummy, “Mummy donAllah ki dinga

hakuri, yarinyar nan abun tausayi ce, Mom

donAllah ki kara hakuri, nan da lokaci kadan

zata koma wurin Iyayenta please Mommy”

ita bata san meyasa ba ta tsani yarinyar,

zuciyarta kanyi zafi duk lokacin da ta hada

ido da ita,yanzu ma bata son maganar da

sukeyi, tayi saurin chanza maganan ta

hanyar cewa “Dan Deputy Governor Amjad

yaga Ziyada yana so kuma, zai zo” Majeed

yayi shiru chan yace “ina fatan ba tallanta

kikayi ba” Mummy tace “aa wallahi ina gida

Mom dinshi ta kirani ta ke rokana wai

yaronta yaga Ziyada yana so, kuma dama

tana son mu karfafa zumuncin mu” ga yanda

tayi magana zaka rantse da Allah iyakar

gaskiarta kenan, Majeed yace “to duka

Ziyadan kwana nawa tayi a Kanon tunda

muka dawo garin? Ina ya ganta?” Mairo ta

daburce tace “Oho fa, kila ko a makaranta, ai

inaga ba damuwa bane ba ko?” Majeed yace

“hakane, amma in Ziyada bata so, sai dai

yayi hakuri”. Mairo tayi yak’e tace ” Eh

mana” amma a ranta tace “dole ko ta

yarda”.

*

“Zaineema kidaina zama cikin daki, ki

dinga fitowa cikin ‘yanuwanki, kullum ki

dinga kulle kanki cikin daki? Sai kin kamu da

wani ciwon?” kamar jira takeyi ta fashe da

kuka tace “Wallahi Daddy sharrine, sharri aka

min, ba ruwana da kowa, ban taba sanin

wani da namiji ba in ba Khalid ba, Daddy ya

k’i yarda dani, ina son Khalid, ina son

komawa dakina, i dont want it here” Daddy

ya rungume diyarshi yana shafa bayanta,

yana matukar tausayin yaranshi, ba yaran

kadaii ba, shima yana tausayin kanshi, akwai

abubuwa da dama da be san yanda zai

fassarasu ba, akwai abubuwa da yawa da

yake sonyi, amma ya kasa, akwai abubuwa

da yawa da yake son ya tabuka, akwai

abubuwa da yawa da yake son tunawa

amma be iyawa. Kwalla a cika mai ido yace

“Zainee, hakuri zaki cigaba dayi, ki mika wa

Allah Alamuranki, inaji a jikina komai yazo

k’arshe, tashi kiyi wanka yaruwarki ta dawo,

na san duk hayaniyan da akayi ba ji kikayi ba

don hankalinki be gurin” Zainee tace “Ziyada

ta iso?” kai Daddy ya gyada mata ta mike

tace “barin shiga toilet”. Ya murmusa tare da

fita daga dakin.

*

Add

Shiga dakinta tayi, idonta ya sauka kan

Bakuwar da ke kwance kan Gadonta, jefi jefi

take sauke ajiyar zuciya, Ziyada ta kutsa kai

sosai cikin dqkin ba tare da tace ma Najwa

komai ba ta shige toilet, Najwan ma bata

san ta shigo ba, wanka Ziyada tayi ta fito ta

shafa mai ta sa kaya. Jin motsinta ya sa

Najwa dagowa a hankali, idonta fes kan

Ziyada, ta madubi Ziyada ta ga Najwa na

kallonta, kamar karta juyo, amma sai ta

samu kanta da juyowa sosai suna fuskantan

Juna.

“Me yasa muke yanayi? aa ba yanayi mukeyi

ba kama mukeyi, kama ba na wasa ba”

zuciyar Ziyada ta raya mata, tunanin da

Najwa keyi kenan itama shi din takeyi, chan

sai tayi murmushi har ranta tace “Ziyadatu,

welcome home, i’m so sorry nayi using dakin

ki, nayi using toilet dinki, nayi using kayanki,

nayi using Gadonki, kiyi hakuri, Ya Majeed ya

kawoni nan” Ziyada kallonta kawai takeyi

sosai kafin chan tace “Dont worry, i dont

Mind” ta juya ta cigaba da shafa Mai, tana

gamawa ta bude wardrobe dinta ta zaro

Doguwar riga ta saka.

Zinatu da Muhsin suka shigo dakin da gudu

suka rungume Ziyada suna fadin “Oyoyo Ya

Ziyada” murmushi tayi tace “Kun kwaso

warin rana kuke hugging dina? Ku wuce kuyi

wanka ku cire uniform” Zinatu tace “Dhurr,

bana warin rana saidai Muhsin” Muhsin yace

“liar, Ya Ziyada, ina Chocholates din da

kikace zaki kawo min?” ta mik’e ta jawo

jakkanta ta ciro ledan Chocholates ta bashi,

ya fita da gudu yana murna. Zinatu ta tabe

baki tana ma Ziyada nuni da Najwq tace

“kingan Karuwan nan? Ya Majeed yazo da

ita” Ziyada ta dago cike da tashin hankali

idonta bude tace “Zinatu, ina kikaji wannan

word din?” Ko a jikin Zinatu tace “Aunty

Nana tace Karuwa ce” Ziyada tace “Get out”

Zinatu tace “What?” cikin daga murya tace

“nace “ki fita” Zinatu ta buga tsaki tace

“mtsw dama baki dawo ba” kafin ta fita.

Ta gefen ido take kallon Najwa, da alamun

taji abinda Zinatu ta fada, haka kurum

Ziyada taji ba dadi, sharewa dai tayi ta ciro

Chocholate DiaryMilk ta ba Najwa, Najwa ta

girgiza kai Alamun Aa, Ziyada ta ajiye mata

kan cinyarta, ta juya ta bar dakin, Najwa ta

bita da ido, kafin ta dauki Chocholate din

tana sha, tayi missing chocholates sosai,

Ziyada taji tausayinta, Majeed ya bata

labarin haduwansu, ita bata da matsalan

zama tare da ita.

*WASHEGARI

Kamar yanda aka fi cewa, Ziyada tafi kowa

Miskilanci duk cikin yaran Hajia Mairo, ba

ruwanta da kowa, magana be dame ta ba,

Miskila ce, ba ta shiga harkan kannenta balle

raini ya shiga tsakani, tana jan Girmanta,

bata shiga harkan da ba nata ba, shiyasa ma

yanzu ta cigaba da cin Abincin da ke

gabanta, ba tare da ta tanka Mummy ko

Nanan dake ta muzgunawa Najwa ta hanyan

sata aiki mara amfani, tana sane dasu amma

sai tayi kamar bata san sunayi ba, har

lokacin da Nana ta daga hannu ta kamtse

Najwa da Mari wai don ta kawo mata Plate,

plate din ya fadi kasa by mistake, sai kawai

ta mareta, Najwa taji marin nan sosai,

Ziyada kamar zatayi magana amma ta fasa

don a ganinta ba ruwanta, kuma ai Najwan

na iya ramawa, sai kuma Mummy da ta

rankwasheta wanda ta ga hawaye a idon

Najwa.

Rigimar Nana yasa ta cewa Najwa ta tashi

ta mata Ginger Juice, akwai Ginger a fridge,

tayi grating tayi sieving, Najwa ta shiga

kitchen din don cika umurnin Nanan, Mairo

tace “Maiya ai naso ta kawo gardama yanzu

in nakasa shegia, wallahi s tsaneta kamar

mutuwana” Nana tace “Wallahi Mommy na

fiki tsanarta, sai kinga yanda My Majeed ke

damuwa da ita” Mummy tace “Ziyada kinyi

kokari da kika kwana da ita, Yayanki be jin

magana wallahi” ko tak Ziyada bata ce ba.

Najwa ta fito kanta a k’asa, ta kawo musu

Ginger juice din, ta ajiye, Nana tace

“danuwarki zo nan, ni zan zuba?” Najwa ta a

matso sumsum ta zuba mata a cup ta bata,

Nana ta kai baki, taji wani gartsi garsti ta

zubar, tare da mik’ewa tace “donubanki

kasheni kike sonyi? Tarugu kika saka?”

Najwa ta fara zare ido, tana girgiza kai tace

“Nahii” “Mummy sha kiji” inji Nana “Mummy

ta kai baki ta furzar da sauri, ta dauki Jug

din ta watsar ma Najwa Ginger a fuska, sai

idon Najwa, Dif Najwa tayi na tsawon

seconds kafin ta sa ihun ” YA ILLAHI,

IDONA”.

Ko a jikin Mairo illa dukkan da ta hau Najwa

dashi Nana na tayata”Kafin ki kashenu da

yaji gwara na nakasa ki, don ance kiyi mana

Ginger Juice zakije ki sa mana tarugu?”

Ziyada cikin zafin rai ta finciko Najwa daga

hannun Mummy, ta jata sukayi daki, Mummy

na kiran Ziyada, Ziyada tayi burus da ita,

Najwa kuka takeyi don wani irin radadi da

zafi takeji a idonta, kila shes going blind,

makanta ya sameta, ji tayi ana wanke mata

ido da ruwa, muryan Ziyada taji tana cewa

“ki bude idonki” girgiza kai Najwa ta hau yi

irin ba zata iya ba, Ziyada tace “ki bude, in

ba haka ba, zaki makance, gwara a wanke,

yunkurin budewa tayi amma radadin ya sa ta

runtse ido tana kuka sosai, Ziyada a tausaya

mata, da kyar ta wanke mata idon tasa kafin

fa hure ba idon ba harta fuskarta yayi Ja,

Ziyada ta jawo hannunta ta fito da ita daki,

kwantar da ita tayi kan Gado tana mata

sannu, ta fita chan sai ta dawo da Gishiri ta

sa mata a baki tace ta lasa.

STORY CO

 

Wayarta ta dauko ta latso Majeed, ringing

daya yayi ya dauka “Hello zuzu missing

me?” cikin murya “Yamaji ka dawo Gida, in

ba so kake su kasheta ba, ka rabata da

gidan nan” da sauri yace “Najwa? Me suka

mata? Mummy ce ko?” yanda taji shi a rude

ya sa ta cewa “kawai kazo Gida”.

Cikin Mintunan da basu wuce 15 ba sai ga

shi ya dawo, a kidime, yana tambayar Ziyada

meyafaru? Ziyada ta warware mai abubuwan

da suka faru tun bayan fitarshi, Sosai ya

tausaya ma Najwa, Ziyada tace ” YaMaji,

kai da ka kawo ta Gidan nan don ka kareta

daa sharrin Mutane, an gudu ba a tsira ba,

YaMaji tana da hakuri, kar ka tauye mata

hakki, ka rabata da gidan nan, don zaifi a ce

tana wani wuri da gidan, coz Mummy da

Nana are not going to stop matukar suna

ganinta a gidan nan”.

Tabbas ya san maganar Ziyada hakane, dole

ya rabata da gidan nan, yar gata ce, ba

baiwa ba, ya sake kallonta, har yanzu idonta

a lumshe suke, ya kalli Ziyada yace “Ki dan

zaban mata kaya, ki sa mata a jakka, shes

leaving this house” Ziyada ta mike ba tare

da tace komai ba ta shiga zaban mata kaya,

kala 5 ta bata, ta taimaka mai ta kaita

Motaa, duk a idonsu Mummy, be bi takansu

ba. Suka fita daga Gidan.

Tuk’i yakeyi a hankali, be da inda zai kaita

da ya wuce chan, anfi shekara 5 rabon da

yaje Gidan, duk da yana son zuwa amma

zuciyarshi na nuna mai ba kowa a gurin,

inda yake son zuwa is just an empty place,

duk da ya san akwai mutum a ciki, amma sai

yaji baya son zuwa, ba shi kadai ba, harta

Daddynshi ya kance mai yana jin wannan

yanayin, so da yawa sun sha kamo hanya su

zo gurin amma sai tsautsayi ya samesu, ko

taya ta fashe, ko wani abu ya faru a gida

wanda zai so dole su juya. A ranshi yayi

Addua, Allah ya bashi ikon zuwa yau. Binibini

yake kallon Najwa ta mudubi, chan kawai zai

kaita ta samu sukuni. Be ankara ba sai

ganinshi yayi a k’ofar Gidan, Hamdala yayi.

Ya kalli Najwa da har yanzu idanunta a

lumshe suke yace “Ina zuwa, barin shiga ciki

in ga tana nan” kai kawai ta gyada mai. Ya

bude ya shiga gidan da Sallama, Ba abunda

ya chanza na daga gidan sai dai tsufa da

gidan ya karayi saboda rashin kula, Majeed

duk sai yaji ba dadi yanda sukayi forsaking

dinta, Sallama ya k’arayi, da mamaki wata

tsohuwa ta fito daga baya tana amsa

Sallama baki na rawa tace “Abdallah” kai a

k’asa saboda Kunya yace “Naam Hajjo” tace

“yau kaine a gidan nan?” Girgiza kai yayi

yace “Hajjo ki yafe mana, donAllah”

murmushi tayi tace “Abdallah ina Abba?

Yana lafiya? Ya yanuwanka? Ina auta zinatu

nasan tayi wayau yanzu ko?” kwallah ya

cika mai ido, yanzu Hajjo bata san an haifi

Muhsin ba? Muhsin na da shekara 5, anya

Allah zai bar Daddynsu kuwa? Ya san a

yanzu suna fama da kansu ne, amma Ji

Mahaifiyar Daddynsu kamar Almajira, duk ta

tsomare ta rame tayi duhu, Me ya faru da

sauran shekarun da suka gujeta? Inallilahi

wa ina ilaihir rajiun, Allah ka yafe mana,

Allah kasa mu zama masu jin k’ai

Mahaifanmu, a karon farkon da ya tsani

Halaiyar Mummynshi, ya san duk laifinta

ne,da wayanshi so da yawa Hajjo zata zo

Gidansu Mummy ta mata Wulakanci akan

idon Daddy amma be da ikon magana. Duk

kunya ta rufeshi wa zai yarda wannan ce

Mahaifiyar Abba Abu? Su da basu san cinta

ba su san lafiyarta ba, ta ya zai kara mata

nauyi? Dole yayi setting komai daidai, dole

ya gyara kuskurensu na baya, duk da suna

fama da kansu ba zasu kara banzatar da

rayuwanta ba.

“Abdallah yadai me ya sa ka kuka?” “Hajjo ki

yafe mana, donAllah” Murmushi tayi tace “ba

kuyi man komai ba” kuka yakeyi, karar

Wayarshi ne ya katseshi, Hajjo tace ana

maka waya, matsawa cahn gefe yayi ya

dauka Daddy ne, ya dauka da Sallama jin

muryan daddy yayi cike da tashin hankali

yace “Daddy lafiya?” Abdulmajeed, Yan rusau

sun rushe mana Company, yanzu wurin fili

ne, kuma wani yazo da takardun filin wai

filinshi ne” Inalillahi wa ina ilaihir rajiun

Majeed yake furtawa, hankalinshi a tashe

yace “Daddy gani nan zuwa, calm down, ka

gaya ma Mummy? Daddy yace “Aa na kasa”

“to gani nan zuwa, Calm Down Daddy”.

Hajjo tace lafiya Abdallah? Murnushi ya

kwakulo yace ” lafiya Hajjo, Bakuwa na kawo

miki ta tayaki zama, zan dawo InshaAllah,

wani abu ya taso yanzu” Hajjo tace

“Matarka ka kawo min? Tana ina?” yayi

murmushi yace ba matata bace, kawar zama

na kawo miki, tana mota, barin shigo miki

da ita, fita yayi sai chan ya dawo da Najwa,

Najwa kamar me koyan tafiya, daga Nesa

Hajjo ta kura mata ido, da murmushi tace

“Ziyadatu haka kika girma ko? MashaAllah”

Majeed yace “ba Ziyada bace, ashe ba ni

kadai nake ganin kamarsu ba” “to wacece?”

Majeed yace “sai na dawo Hajjo, zan miki

bayani, Najwa you are staying here for

sometime, shes my Grandmother, help her

with the housechores take care sai na dawo”

sauri sauri Majeed ya fita daga gidan.

Najwa ta bude ido a hankali ta zubesu kan

Hajjo, yanzu bata jin yajin a ido suka kura

ma juna ido, a tare suka sakar ma juna

murmushi, Hajjo ta miko mata Hannu, Najwa

ta amsa tana jin matar har ranta, tace “ki

zauna a nan kinji Jikata, zan fita sanaa in

dawo, ince bakya tsoron zama ke kadai”

Najwa tace “ina tsoro, kije dani” Hajjo tayi

murmushi tace “da kin zauna, rana zaki

kwaso kawai gashi a gajiye kike kuma da

alamu idonki ba lafiya?” Najwa tace “ina

zakije?” “talla zani” Najwa tace “Meye

Talla?” Hajjo ta murmusa tace “wurin saide

saide” Najwa tace “me kike saidawa?” Hajjo

tace “Zogale” “meyene Zogale?” Hajjo tayo

dariya tace “naga alama wannan matar so

kike ki sani latti” ta kwaso robobin sannarta

ta harhada komai duk a idon Najwa, wani

abu tagani kamar leave, bata san meye ba

dai, a ranta tace “shi zata sayar?” Hajjo tace

“to na tafi, sai wurin laasar zan dawo” Najwa

tace “da ni fa zaki” Hajjo tace “da dai kin

zauna” Najwa ta karba Roban Hannun Hajjo

tayi gaba tace “ko ki zo mu tafi ko na tafi ni

kadai na bace” Hajjo tayi daria tabi bayan

Najwa, tana jin Son Najwa har ranta, ji tayi

kamar sun shekara tare.

Wani Ihun da Mummy ta sake ya sa duk

suka taru Parlor, zaune tayi dirshan a kasa

kamar yar bori, kowa na tambayan Mummy

me ya faru? Ba ta amsa su ba sai sambatun

da take tayi.

“Shikenan tawa ta sameni, ta kare mana,

bamu da sauran abun tunkaho, shikenan

waiyo Rayuwarmu, mun bonu mun lallace”.

Ziyada tace “Mummy me ya faru? Kiyi

magana mana” su Zinatu already kuka

sukeyi, Zaineema na tamabayan Mummy,

Nana ta ciro waya ta kira Majeed, sai jin

ringing din wayar tayi a Parlorn ta dago ta

kalleshi, ya karaso da sauri, Mummy na

ganinshi tace “dagaske ne Yaro?/)dagaske

sun rushe mu? Sunyi hijacking filin mu?”

Mummy Calm down” cikin tsawa tace “Dont

tell me to Calm down, ka amsa ni” a hankali

yace “Eh Mummy dagaske ne” luuu Mairo ta

yanke jiki ta fadi.

******

Bibilicious freaking fans, thanks for all your

support, Waya ta gyaru, Nagode muku da

masu kirana da message, Ga Barka da Sallah

na baku. Dont forget to Vote and Comment

line by line please.

Sai mun hadu bayan Sallah.

Ku ajiye min Naman Sallahna, sai nazo muku

yawan Sallah.

#1love

#ADAY

#anatare

#bibiliciousfreakingfans

#muyibikinsallah lafiya

#nagode

Biebee Isa.

Add Vo

 

DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣0⃣

Mummy kwance a k’asa ita ba sume ba,

ita ba a mace ba, idonta k’ek’eshe, kamar

wacce aka tsungula, ta fasa Ihun “Waiyo ni

Mairo na shiga uku, wani dan kutumar Uban

ne ya sa aka rushe mana Kamfani, kuma don

Mugunta ya saida Filin, kai Allah ya isa,

kuma wallahi shari’ah mu dasu har k’iyama,

kotu zamu maka Macutan Maha’inta”

Majeed ya dagota yace “Mummy ki kwantar

da hankalinki, ki daina ihu hakan nan”.

Cike da Masifa tace ” kai min shiru, dont tell

me to calm down” kamar an tsikareta ta

tashi tsaye kamar ba ita ta zube k’asa ba,

tace “bani key din Motarka” Majeed yace

“Mummy mana” tace “Majeed, ka bani Key

din Motarka” ya ciro ya bata ta karbe ta fita,

ya bita a baya, kafin ya bi bayanta ta shige

motan ta sa lock, horn tayi Maigadi a bude

mata, ta sa kai ta bar Gidan, Majeed sai dai

ya tsaida me Adaidaita ya bi bayanta bayan

yace da su Ziyada kar su fito.

Bata tsaya ko ina ba sai *Abba Abu and

Son’s Furnishing Company*, ta hango Daddy

tare da wasu suna maida zance, ba ta su

take ba, wasu k’arafa ta gani na electric wire

an zagaye wurin da su, ansa ‘donot touch’,

parking tayi ta fito a fusace, cikin daga

murya tace “wani daniskan ne ya msna

rusau?” hankali mutane da ‘yan jarida

sukayo kanta, Daddy yayi saurin k’arasowa

gunta yana kiran “Maryam me kikeyi a nan?”

Daddy ka barni da Marasa Mutuncin nan,

watsattsu, ka nuna min uban da ya sa aka

rushe min Kamfani” duk yanda ya so janta

ya turata mota abun yaci tura, k’arshe ma

zuwa tayi wurin electric wires dinnan wai

zata fara cirewa.

Tsautsayi ya sata kama wire din farko, da

shocking ya jata sai da ya kaita bakin Titi,

ihu ta saka kamar sabuwar mahaukaciya, ko

da yake da k’yar ne in Shocking din be ta6a

mata k’wak’walwa ba, dama ko mayafi bata

dauko ba, dankwalin da ke kanta tayi

fancikali da shi, ta kamo wuyan wani

Mutumin da bata san ko waye ba ta dinga

lafta mishi duka ko ta ina, ‘yan jaridu suka

samu rahotan dauka.

Majeed kamar ya sa ihu don takaicin

Mummy, isowarsa kenan, da ya bita nan sai

ta arta a guje, sai ya bita chan, abun haushi

ko dankwali babu kanta, da k’yar ya

kamota ya chusata cikin Mota ya ja Motar

ya wuce Gida, shikenan Mutuncin Family

dinsu ya gama zubewa, yana ganin Mummy

na bubbuge bubbugenta yayi banza da ita ya

k’yale..

*

Yau Kasuwa MashaAllah, ciniki

sukeyi sosai, ko mutum beyi niyan siyan

Zogalar Baba Hajjo ba, da ya ga Najwa sai

ya siya, wasu kan ce “Hajjo Mai zogala ina

kika samo Balarabiya?” Sai tayi murmushi

tace “Jikata ce” wasu yan zuk’i tamallen sai

suce ai ko ga kama nan” sai dai tayi daria,

din bata san ta inda suke kama da Najwa ba.

Nan da nan suka saida Zogalar nan tas, har

ana zuwa Cigiya, Hajjo taji dadi, tace to

“Tsohuwa tashi mu tafi Gida, an gama

saidawa” Najwa ta murmusa tace “wai

yanzu abin nan da dadi ne har Mutane ke

siya?” Hajjo tace “ke dai ba kin k’i ci ba,

dadi sosai ma” Najwa tace “ban sanshi bane,

ban taba ci ba” Hajjo tace “tunda yanzu kina

tare dani, zaki fara ci”.

Suka mik’e suka fara tafiya, sai da Hajjo ta

siyo k’ulli k’ullin Gobe kafin suka samu

Motan da zai kaisu Gida, Najwa cikinta ya

fara kukan Yunwa, suka zauna zuru Jin

Radio, ba abunyi, Radion ma Batiran sun

mutu, Najwa ta zuba ido taga ko Hajjo zata

mata tayin Abinci amma shiru, kai ga dukkan

alama ba a daura sanwa a gidan ba, don

bata ga alamu ba.

Hajjo ta lura da Najwa, ta rasa yanda zatayi,

batayi tsammanin ba zata iya cin Zogale ba,

habar zaninta ta ciro cinikin dazu, ta irga

Naira 100, tace ” ina zuwa” Najwa a wahalce

tace “kije dani” Hajjo ta gyara Zaninta a

kanta tace “yanzun zan dawo” bata jira

cewar Najwa ba tayi gaba, Najwa ta dafe

cikinta tana rok’on Allah ya kawo mata

Majeed, she’s very Hungry, kuma baza ta iya

ce mata tana jin Yunwa ba.

Jim Kadan sai ga Hajjo ta dawo da Indomie,

murmushi ya subuce ma Najwa, kamar taga

Annabi don dadi, Hajjo tace “Dama na san

Yunwa kikeji, gashi ya k’i boyuwa a fuskar

ki” Najwa sadda kai k’asa tayi tana

murmushi, Hajjo ta cigaba da zolayarta tana

cewa, matsalar Farar Mace kenan, ana gane

farincikinta ko akasin haka ta fuskarta.

 

Hajjo ta tattara ledojin da ke tsakar Gida ta

harhada su a murhu, da k’yar ta samu

Ashana ta k’yasta, Najwa na kallon ikon

Allah, Hajjo ta sha wahala kafin ta samu

jikkakun itatuwan kamawa, a kwano ta daura

ruwan zafin, ta zuba Indomien, cikin minti 15

Indomie ya gama, Ta juyo mata a kwano,

tace “Jikata kiyi hakuri, ga taliyar nan ko Mai

babu, bare cefane.” Najwa ta murmusa tace

“ai bansan kamshin Komai, hakan ma yayi

nagode sosai, , kizo muci” Hajjo ta girgiza

kai tace “Ita ci, wannan cimar sai ku, barni

da Zogalata”. Najwa tayi daria.

PORTHACOURT

Dariya Zaid keyi harda rik’e ciki, mantuwa ta

mance ranar da yayi dariya haka, a TV yake

kallon Network News, rahoton Kano ya dauki

hankalinshi, inda Hajia Mairo ta baiyana

gaban Filin tanata hauka har Majeed yazo ya

janyeta daga gurin, Dad kamar ya kashe

Zaid, haka yake son ganinsu, cikin uk’uba, da

rashin jin dadi, Farincikinshi kenan ganin

bakincikinsu, to in har wannan Rahoton da

aka nuno a News ya faranta ranshi, to ya

dau alwashin muzguna musu har k’arshen

rayuwarsu.

Ah dole yayi celebrating Haukan Mairo.

Dauko Shisha Pot yayi, ya hada uban flavour

ya fara zuk’a, yana busarwa, hayak’i ne, ta

hanci ta baki, wata sain harta kunne, Zaid

sai da ya zuk’i maishi kafin ya bangas.

K A N O

“Haba Mummy, wai baki san komai game da

rungumar k’addara ba?” Cikin Masifa tace

“nak’i in sani, dan ubanka wani kaddara zaa

runguma? Kasan me Asarar da muka tafka?

Da mu muka saida muka san munci kudin

mu, da ba haka ba, bansan me muka ma

Allah yake mana haka ba” da sauri Majeed

ya bar dakin ganin ta fara sakin layi, yanzu

ta tafka sa6o, Mairo dai kamar sabon kamu,

sai Ihu, da ZageZage, yaranta sai Kuka suna

tausaya ma Uwarsu.

* *

Wayarta yayi ruri, kamar ba zata dauka ba

ta dauka, kamar kullum Muryanshi a dakile

yace Matar AA Abu” dadi ya lullube Nana

cikin yauk’i tace “Yadai?” Zaid ya murmusa

kamar yana gabanta yace “kinsan FIRS?” ta

dan yak’une fuska tace “Federal Inland

Revenue Service?” Zaid yace “yauwa

‘yargari,dama ina da hanya ne, shine nace

zan samo ma Majeed aiki a chan” Nana cikin

murna tace “kai Haba dai? Dagaske kake?”

Zaid yace “Yes, yanzu ki dauko CV dinshi,

Credentials din Original Copy, don kinsan

verification dinnan sai a hankali, in ba

Original Copy ba, ba sa ba mutum offer”

Nana bata kawo komai ba tace “haka ne,

barin Majeed ya dawo na gaya mishi”.

Zaid yayi saurin cewa “ke, so kike a ba ma

wani offer din? Ke da ma zaki mai surprise?

Sai kawai ki bashi offer, ai ina ganin hakan

zaifi, kawai kar ki gaya mai, cikin halin da

yake ciki, ki ka basho offern aiki, trust me ba

zai taba manceki ba, kuma ba zai miki

kishiya ba? Kuma Mummy zata k’ara sonki,

k’imarki zai k’aru wajensu” Nana cikin jin

dadi tace “Allah ko?” Zaid yace “Dagaske”

Nana tace bari kaga, na ga inda ya aje

Folder dinshi da ya dawo daga Dubai, kamar

ka san nayi nayi Daddy na ya bashi aiki yace

wai “baya da bukatan sabin maaikata, dama

rashin aikin nan ya fara damu na, duk da

Mummy tace wai Ziyada zata auri dan

Deputy Governor, su zssu taimaka mana,

amma ai ba kamar ace Mijinka shima na aiki

ko?” .

Zaid dai na jinta, har tace “gashi na dauko, a

ina zaa kawo ma?” Zaid yace “ba sai kin ba

kanki wuya ba, already na aiko da me karba,

yana wajen gidanku, ki kai mishi Wajen, kar

ki bari kowa ya gan, kinji?”Nana tace ba

wanda zai gani, ni da zan musu surprise”

yace “Good, Yaron deputy Governor din ina

Ziyada zata aura?” Nana tace “na Kano” a

hankali Zaid yace “Amjad” tace “me kace?”

Yace “Noo, kiyi sauri ki kai mai yana waje

yana jiranki” tace “toh”.

***

Cikin kwanaki 3 dinnan, Gidan Alhaji

Abba Abu ba walwala, kowa na cikin

damuwa, yau dai Mairo da ta tashi dakin

Ziyada ta nufa, bayan Ziyada ta gaisheta

tace “Ziyadatu, dama na gaya miki Amjad zai

zo ai? To yanzu da safe Her Excellency ta

kirani, tace zaizo yau” Ziyada ta dan bata

rai, tace “Mummy na gaya miki nu banson

yaron, sakatarshi yayi yawa, he’s tottaly not

my type, gaskia yayi hakuri” Mairo ta hau

lallashi, haba Ziyada, ya zaki min haka?

Please, kinsan k’in aurenshi barazana ne a

rayuwata?” Ziyada da mamaki tace “taya

rashin aurenshi zai zama barazana a

rayuwarki Mummy?”

Add V

Start from the beginning

“Ziyada kinga dai yanda muke fama da babu

babun anan, in kika aureshi kakarmu ta

yanke sak’a, kinga rannan Mom dinsa

250000 ta bani, dashi fa nayi mana siyayyar

abinci, da ba haka ba da yanzu muna kwana

da yunwa” galala Ziyada ke kallon

Mummynta, kamar ba zata tanka ba tace

“Auren Jari zaki min kenan, da ni kike sonyi

Azziki? Mummy? Dama baki damu da

farinciki na, wato dama dogon burin da ke

ranki kenan? To Mummy, ba zaiyiwu ba,ba

Zan aureshi ba” nan Mummy ta hau

lallashinta ta, wai ta taimaketa ko gaisawa

suyi, irin magiyan da ta ga Mummy na mata

ne ya sa ta cewa “ta amince yazo a gaisa”.

*

Hajjo Mace ce da ke zaune a babban Gida

amma bata da ko k’wayar shinkafa, Bishiya

gareta na Zogale, sai ta hau bishiyan ta

katso Zogalen sannan ta gyara ta dafa, ta

tsince hakukuwan, ta diba taci, sannan ta

saida sauran a Kasuwa, a Kasuwa take siyi

k’ulli, ta daka ta hada da zogalen t sayar,

duk cinikin ba zai wuce dari Takwas zuwa

duba daya ba. Cikin kudin ne take so kuran

ruwa, don ba ko ruwan sha a gidan balle a

samu na Alwala, balle kuma ayi wanka, in

yau kuma bata da lafiya to cikin kudin ne dai

zata kai kanta Asibiti ta kuma siya magani.

Ba ta zuwa gurin kowa, ba me zuwa gunta,

A tsawon shekarun nan, da Zogale ta rayu,

shine cimmarta, da yake Magani ne, jikinta

gwanin kyau.

Zuwan Najwa saidai ta siyo Indomie ta dafa

mata, don ta sanar da ita abun da kadai take

iya ci kenan.Cikin kwanakin nan, Najwa ta

gama karantar Hajjo tsaf, ta san ita k’arin

nauyi ne ga Hajjo, ta san Tsohuwar na

takura saboda ita, kawai Gabata ne yake sa

ta na nunawa kamar ba wani damuwa, to

wanda ya kawota ya ajiye be dawo ba, be zo

balle ta san nayi, sosai take tausaya ma

Hajjo, in har dagaske ne Daddynsu Majeed

ne Danta meyasa ya barta haka? Ta san

Family dinsu Majeed akwai rudani, amma

bata san inda zata sa lamarin Hajjo ba,

kawai Addua zata tayi ma Hajjo, kuma ta

cigaba da tayata Ayukanta, ta na rage mata

nauyin wasu abubuwan, don yanzu dole ta

rage cin Indomie din nan, dan a rana

Indomien Dari uku takeci, saboda Hajjo zata

daure ta fara cin Zogale, kuma abun mamaki

inta ci Zogalen bata Amai, sai tace “yau

Hajjo ba zanci Indomie ba, yau Zogale zanci”

Hajjo sai tayi daria.

PORTHACOURT

Suna zaune dan sak’o yazo daga Kano kawo

Credentials din Majeed, Amrstrong ya karba

ya fara bubudewa, ya kalli Zaid yace “bros

you wan giveam Job?” Zaid ya murmusa

yace “No” Amstrong da mamaki yace “Ha’an,

wetin dat guy Original Credentials dey do

here?” Zaid be tanka shi ba, ya cigaba da

latselatsen waya, Amstrong ya gano me Zaid

ke niyyanyi, yana so Majeed ya shiga tashin

hankalin rashin Credentials dinshi, baya so

yayi aiki a ko ina, shiyasa ya sa aka kawo

mishi, Duk rashin Imani da taurin zuciyan

Armstrong ya tausaya ma Majeed.

Amstrong yace “Bros, Easy, E don do now,

mey you leave that Family, e tey where you

dey cause them trouble, Abeg E don do(Bros,

kabi a hankali, ya isa hakan nan, ka rabu da

Family dinnan, Ka dade kana ja musu

Matsala)”. Zaid yayi daria yace ” I never

start na(ai ban ma fara ba)”. Amstrong ya

bude baki “Haa, this one wey you dey trouble

the pikin, mo go kill the Mama na, na her

beef jam her Son(Kai, wannan da ka ke

matsa ma Yaron, Muje Mu kashe uwar mana,

dama haushinta ne da kake ji ya shafi dan).

Zaid yace ” listen Man, This woman is very

tough, killing her means ending her

sufferings, i love seeing her suffer, i cant

bring an end to her sufferings, so i will sit

and enjoy every part of it(Saurara kaji,

wannan matar Shegiyar kanta ce, kasheta

na nufin sauk’aka mata wahalhalunta, ina

farincikin ganinta a tashin hankali,so ba zaiyi

in kawo karshen wahalarta ba, zan cigaba da

muzguna mata ina jin dadi”.

Zaid ya kalli Amstrong yaga beji dadi ba,

yace “Guy, why do you even care?” Amstrong

yace “Noo, i dont, just that i dey feel for the

guy, him dey pay for him Mama mistakes(Ba

wai na damu bane, kawai yaron ke ban

tausayi, yana biyan laifikan Mamanshi). Zaid

ya jinjina kai a gyara zama kafin yace “One

thing about Hajia Mairo is that she loves her

Family and Money very much, literally these

two things are her Happiness, she’s very

tough and rough, you cant hurt her easily,

hurting what she loves most is the only

thing that can break her, that is why i keep

on bugging her Children Especially the Older

One(Hajia Mairo na san ‘Yaya da Kudi,

Farincikinta kenan, Mata ce kamar Maza, ba

kasafai zaka iya bata ranta ba, taba yaranta

ko Dukiyarta kadai ne zai girgizata sosai,

shiyasa nake takura ma Yaran, Musamman

Babban)” muryan Zaid ya k’ara kaifi wurin

fadin “i’m going to take everything she’s

ever wanted away, i will keep making her life

a living Hell, then i’ll watch her break till the

end of her Pathetic Life” Lamarin Zaid ya

fara ba amstrong tsoro, kai kawai ya gyada.

K’amshin turarenta ya cika Parlorn Gidan

Abba Abu, kanta ta ma gurin zama, tana ta

sallama ba a amsa ba, ta shigo da kanta,

kamar daga Sama sai ga Daddy ya fito,

murmushinta ya fadada, a duk lokacin da ta

ga Alhaji Abba Yanayinta na chanzawa,

Soyayyar da take mishi na nan dank’are a

ranta, saboda shi ta k’i zaman Aure, Aurenta

3 tun lokacin tana fitowa saboda shi, amma

kwatakwata bata gabanshi, ta san Sharrin

Hajia Mairo ne, amma ta san wani wuri a

zuciyarshi na sonta.

“Hajia Aina’u kece a gidan mu, sannu da

zuwa” muryar Daddy ke amo a kunnuwanta,

ta lumshe idanu tace “Alhaji Abba, nazo

muku Jaje ne, ashe abunda ya faru kenan?”

da jimami yace “Wallahi kuwa, abu da haka

yazo, kawai muka wayi gari muka ga wuri a

rushe, kuma wai an saida filin” Hajia Ainau

da tausayi tace ” Allah Sarki, Allah ya saka

muku, ya bi muku hakkinku, haka

“Rayuwarmu* take yanzu, masu k’arfi sai su

danne hakkin marasa k’arfi kuma gwamnati

na kallo, Allah ya saka muku Alhaji” Sosai

ta burgeshi ya amsa da “Ameen” cike da

kissa tace “ina mutanen Gidan?” Daddy yace

duk suna cikin Daki, ya ciro waya ya kira

Majeed yace “kai fito ga Auntynka Aynarh

tazo” Hajia Ainau ta maimaita ‘Auntynka

Aynarh’ a ranta, dadi ya ziyarce ta, akwai

Hope kenan, Jim Kadan Majeed ya fito daga

Daki, da murmushi ya k’araso Parlor.

“Aunty Ina kwana” “lafiya lao, Majeed Ashe

abun da ya faru kenan?” Majeed yace

“Wallahi kuwa Aunty” tace “Allah shi kyauta,

ya tsare gaba” ya amsa da “Ameen” tace

“Na ma Daddynka maganan Lecturing,

bansan ko kunyi maganan ba” Majeed ya

dan shafa k’eya yace “Eh munyi” tace “yanzu

ka dauko min CV dinka, in tafi dashi” Majeed

yace “Ok, barin dauko” ya tashi ya shiga ciki,

bedside drawer ya jawo don dauko Folder

dinshi, wayam, ba komai, da mamaki ya san

da hannunshi ya ajiye a nan, nan ya shiga

dubawa drawer drawer, be gani ba, ya dauko

Jakkan Laptop ya duba be gani ba, Nana ya

tada don tambayarta ko ta chanja mishi

wuri, Nana ta hau inda inda, kwana 3 da

suka wuce tana ta jiran wayan Wannan

bawanAllah be kira ba, har ya fara ganin

wautan ta na bashi ba tare da sanin ko da

number dinshi ba, tsoro ya cikata sai tayi

k’arya tace “bata gani ba” Majeed yayi shiru

ya fita, yace “Aunty, zan kawo miki har gida,

banyi photocopy ba” tace “Ok Yarona ba

matsala, sai kazo” .

Kamar daga sama suka ga Mummy gaban

Hajia Ainau tana huci, Hajia Ainau ta

murmusa tace “Hajia Mairo Ya gida ya yara?

Ashe abun da ya faru kenan?” Mairo cike da

masifa tace”tsohuwar Minahika, uban me ya

kawoki? Jaje kikazo ko munfunci” Majeed

yayi saurin shan gabanta ya ja ta

baya”Mummy Please” ta bangaje Majeed

tace “Tashi ki bar min Gida, kar ki sake zuwa

mana Gida, tsohuwar kilaki” Hajia Aina’u ta

mik’e da murmushi daidai yanda Mairo

kadai zata jita tace “Zaki ga kilakanci duk

randa na auri Abba, kashin ki zai bushe

Hajia Mairo, ba kamar ki ba, ba Boka ba

mallam zanyi taking over gidan gabaki daya,

duk wanda ya biya allonshi ya wankeshi” ta

dauki jakkarta ta bude murya tace “toh Hajia

Mairo da Alheri, Allah shi kyauta gaba”

Majeed ya bi bayanta, Daddy yace “Hajiya

Aynarh, mungode Allah bar zumunci” abun

mamaki ya kalli Mairo ya galla mata harara

ya shige ciki.

Baki bude Mummy ta bi Daddy da ido,

wannan matar tana shiga hancinta ta

k’udundune ita take ikirarin auren Abba, ji

yanda Majeed ke binta kamar wani me

neman gafata, aiko zata shayar dasu

madaran mamaki.

*

Majeed yace “Aunty donAllah kiyi hakuri,

bansan meyasa Mummy ke haka ba” H.Aynar

ta murmusa tace “haba Majeed, bakomai

Wallahi, inda sabo ma saba, so kar abun ya

dameka please” murmushi yayi yace

“Mungode Aunty” ta bude motarta ta ciro

wani Envelop tace “gashi ko” Majeed ya

mak’e hannu, tace “haba Majeed, kar ka min

haka donAllah ka karba, nasan you are in

need” Majeed ya sa hannu biyu ya amsa

yana Godia, har ga Allah tana son Jinin

Abba, sosai takeson Majeed, ta ja Motar ta

ta wuce, sai da ya ga tafiyarta kafin ya shiga

Gida.

Cikin Dakin Daddy yayi Sallama, yana jin

yanda Mummy ke balbale shi da Masifa,

Daddy yayi banza da ita ya k’yale, Majeed ya

girgiza kai, ya shiga da Sallama, Daddy ya

amsa yace “har ta tafi?” Majeed yace “eh

gashi ta bamu ma, dubu Dari ne” Daddy yace

“Allah sarki Aynarh, harda dawainiya” haushi

kamar ya kashe Mummy, wai yau Abba ke

yaban wata, lallai tayi Sanyi, tana jinsu inda

yake cema Majeed “Toh Allah ya saka da

Alheri, sai kaje ka yi siyayyan Abincin Gida”

yace “To Daddy” ya fita. Daddy be bi ta kan

Mairo ba ya fice shima.

*

Add Vote

Sahad ya fara zuwa ya kwaso Provisions

kala kala, sai da ya cika booth da abinci,

Duk yanda rayuwa ta zo musu ko ba komai

ba zasuyi rashin Abinci ba na ‘yan wattanin

nan masu zuwa, yana tuk’i Najwa ta fado

mai a rai, Salati yayi a zuciyarsa, cikin

kwanakin nan tashin hankali ya hanashi

tunano komai, reverse yayi ya dauki hanyar

Rijiyar Zaki, jim kadan ya baiyana a k’ofar

Gidan Hajjo.

Sallama yayi tare da tura k’ofan, kutsa kai

yayi, kamar ance ya daga kanshi daga gefe

ya daga kai, gabanshi ya yanke ya fadi,

idonshi kamar ya fado, tsoro ya mamaye

zuciyarsa, abu kamar almara, da sauri ya

k’arasa gindin Bishiyar Zogalen da ya ga

Hajjo a kai inda take katso Zogale tana

yaddawa a k’asa, murya na rawa yace

“Hajjo, sauko donAllah, sauko” Najwa na jin

Muryanshi ta fito da Murna, Hajjo bata so

ganin Majeed ba a yanzu, saukowa tayi a

hankali.

Da farinciki Najwa tace “Ya Majeed”

murmushi kadai yayi ya maida dubanshi ga

Hajjo yace “Haba Hajjo, ya akayi kika iya

hawa Bishiyan nan? Ba kya tsoron ki fadi? In

Zogale kikeson ci da ba siyowa ya kamata

kiyi ba? Kin kama kin hau bishiya, inta Allah

ta kasance fa, tsautsayi da be wuce rana

kika fado fa? DonAllah kar ki sake hawa

Bishiyan, in Zogale ne kuka barin je Kasuwa

in siyo miki daffafa ba sai kin sha wahalan

dafawa ba” be jira amsarta ba ya juya.

Hawaye suka gangaro ma Hajjo, Najwa tace

“oh ashe besan ita ke saidawa ba” baki ta

cire ta kira Majeed.

“Ya Majeed” ba tare da ya juyo ba yace

“Najwa ki tsaya yanzu zan dawo, barin siyo

ma Hajjo Zogale da k’ulli” tace “to ina zakaje

siya bayan ga Mai Zogalen nan ka bari a

gida?” chak ya tsaya, ba wai don ya fahimci

abunda take cewa ba, ya juyo a hankali yace

“bangane ba” Hajjo ta mata alama da ido,

Najwa ta tako har gabanshi tace “i mean,

zakaje siyi Zogalen bayan me Zogalen gata

ko dafawa batayi ba balle taje kasuwa ta

saida” ganin be fahimtar abunda take cewa

ya sa ta cewa “Hajjo mai Zogale sunan da

Yan Kasuwa suka fi saninta dashi kenan,

tunda nazo kusan 8days kenan, ban taba

ganin taci wani abu ba sai Zogale kaga har

ta koya min ci, wannan Tree din kullum sai

ta hau ta tsinko Sai ta dafa, sai inga ta daka

wani abu kamar dutse a turmi, what do they

call it? Kuli? Yes kuli, sai na rakata Kasuwa

ta saida, kullum fa sai mun fita, like every

blessed Day”.

“Inalilahi wa ina ilaihir rajiun, Allahumma

aajirni fi musibati wa akhlifni khairin minha”

zuu ya zame k’asa ya dafe kanshi da

hannunshi, Kuka yakeyi kamar ranshi zai fita,

Hajjon ma Kuka takeyi, wai Kakarshi ke

Tallan Zogale? Kullum sai tayi gangancin

hawa Bishiya? Kakanshi? Maman Alhaji Abba

Abu? “Ya Illahi” sai da ya ci kukanshi ya

gaji, kafin ya rarrafa gabanta yana rokonta

gafara kamar shi ya mata laifi, yana tausayin

Babanshi, ya san yau Daddy ya mutu wuta

zaije saboda yanda ya banzatar da rayuwar

Mahaifiyarshi, rok’onta gafara yakeyi na ta

yafe ma Babanshi, kuka takeyi sosai, Najwa

na tayasu, da k’yar Hajjo ta tsagaita kukanta

ta dago Majeed tace “Abdallah, kayi shiru,

Babanka be min komai ba, tsakanina da

Abba Addua ce kawai”.

“Wani d’an k’warai zai bar Mahaifiyarshi

cikin wannan hali? Wani dan kwarai zai

sharw Shekaru sama da biyar be ga

Mahaifiyarshi ba kuma dukansu suna raye?

Wani dan k’warai zai wofintar da

Mahaifiyarshi?” Hajjo ta katseshi tace “kul

Abdallah, ba yin Abba bane, ni na sani,

wallahi ba yinshi bane, yanda na nuna ma

Abba So fiye da danuwanshi, Wallahi ba

yinshi bane kar ma ka zarge shi, na yafe ma

Abba duniya da lahira Allah ya fiddashi daga

halin da yake ciki”.

Majeed ya so ya gane me take nufi, amma

zuciyarshi bata si ta aminta da zargin, yayi

saurin kawar da tunanin a ranshi yace “Hajjo,

kina da D’a kamar Abba Abu, kina da Jika

kamar Abdulmajid, duk da muma Rayuwarmu

na da dan targarda, amma kinfi k’arfin Tallar

Zogale, kinfi karfin hawa bishiya, wannan

Mutane suka san Asalin ki, Wallahi sai sun

dinga la’anar Daddy, kuma wallahi Bakin

mutane sai ya bishi, Hajjo ta faru ta k’are,

kin gama Zaman Gidan nan, zaki koma

gaban Danki, da Jikokin ki, Najwa Help me

get her things”.

“Aa Abdallah kar ka min haka, ni da in taka

k’afana gidan Abba, ka dai bari, barni a nan”

Majeed yace “dagaske Hajjo ba zan barki nan

ba, Wallahi Gida zamu tafi” Hajjo ta fashe da

kuka tace “Mamarka da bakinta tace kar in

sake zuwan mata gida, in dana ne, zai dinga

zuwa yana gaishe ni, gaban Abba, Abba bece

komai ba, Kar ka ja min Wulakanci donAllah”

Majeed ranshi ya baci kwatakwata Mummy

bata kyautawa yace “da da Yanzun ba daya

bane, ba wanda ya isa ya wulakantaki, ko

Mummy ce, ba zan bari ba, ki yarda dani” sai

da sukayi mahawara kafin Hajjo ta amince

zata bi Majeed da sharadin idan taga zaa

mata Wulakanci zata dawo ya amince.

Jikin Najwa yayi sanyi ganin zata koma

Gidan Jiya, Majeed ya lura da ita yace “Dont

worry, i got you both” Murmushi suka ma

juna, Hajjo ta dauki kaya kala biyu ta sa a

Jakka, don a cewarta ba zata kwashi kaya

da yawa ba, in zama beyi dadi ba dawowa

zatayi.

*

Har shi ma gabanshi faduwa yake don

be son yanda Mummy zata karbesu ba, yayi

parking, A tsorace suka shiga gidan a Parlor

suka iske Muhsin na Kallo, Oyoyo ya tashi ya

mai, ya bi su Hajjo da ido, Majeed yace

“Muhsin ba ka gaida Hajjo ba” cikin

hausanshi yace “Ina kwana” Hajjo hawaye ya

ciko mata, wannan Jinin Abba ne, amma ko

haihuwarshi bata sani ba ta shafa kanshi

tace “Ina wuni dai ko?” ya gyada kai, Majeed

yace “je ka kira min Zuzu da Zainee” da

gudu yayi dakin Ziyada yana kwada masu

kira “Ya Ziyada, Ya Zaineema, Yaa Majeed

na kiranku”. Nana na jin Muryan Majeed ta

fito, tana yauk’i idonta ya sauka kan Najwa,

Najwa gabanta ya fadi, Nana ta daure fuska,

“My Majeed me wannan yarinyan ta dawo

yi?” a tsaye ya kalleta yace “Zauna” jin

muryanshi cike da seriousness ya sa ta

zama, ba ta damu da Tsohuwar da ta gani

ba.

Ziyada ta shigo parlorn da Sallama,

Murmushi kawai ta ma Najwa ba tare da

tace komai ba, ba wai don ta san Hajjo ba ta

gaisheta, Hajjo tace “Ziyada ce?” Majeed

yace “eh itace” ya kalli Ziyada yace “Zuzu

kinsan wannan?” ta girgiza kai alamun “Aa”

ya jinjina kai yace “ta shiga ta kira

Zaineema, Kafin tazo sai ga Zainee ta fito rai

bace, bata san abun da zai dameta, ta fito ta

kalli Hajjo shekeke, ta so ta ganeta, don ta

san ta, da wayonta ta je gidan Hajjo, don dai

kawai sun dade basu hadun nan bane, ko

nuna alamun ta santa batayi ba tace ”

YaMajeed gani” a dakile yace ” baki iya

gaisuwa ba? Ko ba ki ganeta bane?” baki ta

turo tace “Ina wuni?” Hajjo ta amsa ta na

Murmushi, Majeed yace “Barin kira Mummy”.

Duk da Gabansu duka faduwa yakeyi, amma

sun dake, Majeed ya shiga Dakin yana

Sallama, fushi takeyi dashi da Daddynshi

sabida zuwan Hajia Aynau, yace “Mummy,

munyi bak’uwa” hararshi tayi tace “waye”

yace ke dai taso “Mummyna” jan hannunta

yayi suka fita Parlo, Najwa ta hango, bata

gane ta kusa da ita ba, Ranta a bace tace

“dawowa da ita kayi?” har suka zo gaban

Tsohuwar, Mairo tsakani ga Allah bata gane

ko wacece ba, sai da Hajjo ta bude baki

tace “Mairo mun wuni Lafiya?” kamar ta arta

a guje don dago me muryan baki na rawa

tace “Hajjo?” ta juya ta kalli Majeed cikin

rashin fahimta. “Me kikeyi a nan Hajjo?”

Majeed yayi saurin cewa “don Uwa ta zo

Gidan danta sai ace me tazo yi?”.

Majeed ya kalli kannenshi yace “Ziyada,

Zinatu Muhsin, Meet your Grandmother, itace

Mummyn Daddy” Mummy tace “Majeed What

are you Doing?meyasa ka kawota nan, ya

ma akayi ka san inda take?” Majeed yace

“Mummy, Hajjo ta dawo nan da zama,

mutuwa ta raba, gidan Danta ne” wani

Shewa Mummy ta sake tace “Kutumar Bala’i,

ka fara shayeshaye ko Majeed? Kowa ka

gani ka kwaso kace nan ko? To Wallahi baka

isa ba, tun kuruciyata ban zauna da Hajjo

ba, yanzu ba zan zauna da ita ba Wallahi,

dole ta koma inda ta fito” be bi ta kanta ba

yace “Ziyada, ina so ki koma dakin Zaineema

da zama, ki bar ma Hajjo da Najwa dakinki

kinji?” Ziyada tace “Okay Yaya” da dan

Dokinta, ba wai tana da saurin sabo bane,

amma sai taji son Kakarta, ta matsa kusa da

ita tace “Najwa taimaka ki tayani kwaso

kayan Tsohuwar nan, barin nuna mata

dakinta” Hajjo tayi dariya tace “kece dai

Tsohuwa, kina gani na sabon Jini” Najwa

tayi daria, Ziyada ta kama hannun Hajjo ta

mik’ar da ita.

Mummy ta finciko Ziyada, tace “kar ki

tabata” Majeed shima ya janye Mummy tare

da daga murya “Enough is Enough Mummy,

uwar Mijinki ce kike ma haka as if she’s a

piece of trash?” Mummy tace “She is a Piece

of trash” Ran Majeed ya baci yace “Mummy,

Wa billahilazi Laillahaillahuwa, ba me bina

bashin rantsuwa, idan kika takura, ko kika

muzguna wa Hajjo while her stay here, Z.an

tafi, zan barki Mummy, and i will never Come

back, kindai ji rantsuwar dan Musulmi” baki

na rawa tace “Majeed are you threatening

me?” yace “i am not, na dai gaya miki,idan

na tafi, i will make sure you never see me

again” to ya tabo kahon zuciyarta lakwas

tayi, huci takeyi, bata son abun da zai rabata

da Majeed, fuu ta wuce daki kamar zata

tashi Sama, ya kalli Nana yace “And Najwa,

shes my Guest ba ruwanki da ita, ko kallon

banza kikayi mata, dagaske zan rabu dake

Nana” Nana ta k’ulu iya kuluwa, ta tashi a

fusace ta wuce daki, Ziyada tace “karki

damu Tsohuwa, muje Daki” Hajjo tayi dariya

tace “zaki san tsohuwa in saurayinki ya

ganni yace ni yake so” sukayi daria duka,

Majeed yaji dadin yanda Hajjo ta sake lokaci

guda, ya zaro wayanshi ya kira Daddy yace

ya dawo gida akwai bakuwa na jiranshi,

Daddy yace dama yana kusa da Gida gashi

nan dawowa.

*

Daddy na dawowa Majeed be ce mai komai

ba ya ja hannunshi ya turashi dakin Ziyada.

*

Mairo kuwa kamar tayi hauka cikin daki,

meke faruwa da ita ne? Asirin da tayi ya

fara karyewa ne? Ya akayi Majeed yaje Gidan

Hajjo? Ya akayi Hajjo ta yarda tazo Inda

suke, bayan Boka ya tabbatar mata da cewa

sun rabu kenan da Abba? Ya akayi Abba ke

mata gardama har ya na wurganta da

mugun kallo Tab duniyar na juya mata baya,

a fili tace “na shiga uku ni Mairo”..

°°

Bibilicious freaking fans, da fatan munyi

Sallah lafiya, nagode da yanda kuke hakuri

da rashin post din da ke zuwa muku da wuri,

ku min uzuri, ina da patient din da ba lafiya,

ku sata a adduoinku don Allah, Allah ya bata

lafiya ya sa Zakkan jikine Amin.

So ya Wannan Babin? Me kuke tunanin zai

faru nan gaba? Any hunches? guesses? No?

Drop your Votes and Comment Line by line

Please.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣1⃣

Ramewa, tsamurewa da Duhun da tayi ba zai

sa ya mance Fuskar nan ba, Fuskar da tayi

sanadiyar kawo shi Duniya, Fuskar

Mahaifiyarshi ya gani a jikin Madubin dakin

Ziyada, hawaye suka soma suntiri a

kuncinshi, bai tantance ba, shin dagaske ne

itace ko ba ita bace ba, Matsowa yake tayi

har sai da ya zo daf da daf da ita kafin ta

zube kan guiwowishi gabanta.

Ba su ji shigowanshi ba, sai dai ganinshi

sukayi durk’ushe gaban Hajjo yana Kuka,

baki na rawa tace “Abbaaa” cikin muryan

Kuka yace “Ummma”, Ziyada ta ja Hannun

Najwa suka fita suka bar musu dakin. Kasa

daurewa Hajjo tayi ta fara Hawaye, Daddy

kasa magana yayi dai hawaye, sai ya bude

baki zaiyi magana sai ya kasa, Itace tace ”

Kar ka damu Abba, Kayi Magana”.

Kuka mai sauti ya sake kamar karamin yaro,

“Umma, ni mai laifi ne na sani, ni watsatse

ne na sani, ni butulu ne na sani, duk son da

kika nuna min, Umma ni na sa k’afa na

shure, ni na wofintar dake, fiye da shekaru 5,

bansan cin ki ba, ban san shan ki ba, Umma

Allah ba zai barni ba, kema ba zaki yafe min

ba, amma Umma ki sani, bansan meke

dawainiya dani ba, amma Wallahi ba yin

kaina bane, Wallahi bansan ya abubuwa ke

faruwa ba”.

Murmushi mai ciwo tayi, ta dago hannu ta

shafa fuskarshi, tace ” Abba, na sani, na san

ba yin ka bane, kar ka damu, Akwai Allah,

Allah ba Azzalumin kowa bane, Allah na yafe

komai banda hak’k’in Mutum, in dai ina da

Hak’k’i, Allah ka bi min Hakki na akan duk

wanda ya shigo tsakani na da Yaro na, Allah

ka bi min Hakkina, Wahalan da nasha Allah

ka sani, Allah ka isar min, kayi shiru

Abba,kar ka sake zubar da hawayenka, na

yafe maka”.

Gyada kai yayi amma ya kasa tsaida kukan,

Kamo kanshi tayi hannu biyu, ta karanta mai

Ayatul Kursiyu da AmanarRasulu, sai wasu

daga cikin ayoyin Shi’fa, ta tofa mai akai ta

shafa kanshi, shiko ya saura kanshi a kan

cinyarta yana sauke Ajiyar Zuciya.

*

Ziyada ta ja Najwa Kitchen don daura Abinci,

Ziyada jin kanta take cikin Farinciki, Zahiri

bata da san mutane amma sai taji ta sake

da Najwa, kawai yau Nishadi takeji, Tuwon

Semovita Miyar Egusi tace da Najwa zasuyi,

Najwa dai kallonta take tayi da ta kasa

daurewa sai tambayanta tayi meye tuwo?”

Ziyada ta kalleta da mamaki, Ya zaayi Najwa

tace bata san Tuwo ba, ai har Ghanan sun

san Tuwo, yanda da ta ga Najwan nayi ne ya

sa ta zargin ko Najwa ‘yar Ghana ce kuwa?,

amma rana bata karya, “ban labarin k’asarku

Ghana” inji Ziyada.

Hinkim Gabanta ya buga, bata san komai da

k’asar Ghana ba, kuma har yanzu bata

farfado daga Yaudaran ‘yan Nigeria ba,

Generosity din Majeed da Ziyada ba zai sa ta

yarda da su ba har ta bude mata sirrinta,

inda inda ta kamayi, a tak’aice tace “Zan

baki labari wata rana, yanzu dai muyi

focusing kan Tuwo”. Yanayin da tayi

maganan yasa Ziyada zarginta, amma don

dai bata da hujja ya sa ta kauda tunanin

wani abu. Haka suka cigaba da Girki har sai

da suka gama Tuwo da Miyan Egusi, kafin

Najwa ta fita don bata son warin Kifin da

Ziyada keyin Farfesun *Catfish *.

***

Wani Fara’a taga Daddy nayi, baki har

kunne, bakinta na rawa tace ” Daddy, me ke

saka farinciki?” galala ya kalleta, yace “Ji

Maryam da wata magana, Umma nagani

mana, har kya tambayeni me ke sani

Farinciki? Ga abu a Zahiri?”

kinsan yaushe rabon da na ganta? Yau da

tace min ta yafe min, sai naji kamar an

sauke min dutsen Uhudu a kai, Allah ya ma

AbdulMajeed Albarka, yanda ya sadani da

Mahaifiyata, ba zai taba tabewa ba da sunan

Rabbi” Mamaki ya hana Mairo Magana sai

dai uhm da tace.

Haduwa sukayi gabaki daya a Dining Table,

da k’yar Majeed ya samu Mummy ta fito,

Daddy jiki sai rawa yakeyi, ya dauko Coolern

Parpesun Kifi ya tura ma Hajjo Gabanta yace

“Umma, kici” Murmushi ta mishi, mantuwa

ya mance rabon da taci Abinci haka, abu

kadan Daddy zaice “Umna kaza, Umma

kaza” haushi kamar ya kashe Mummy, kowa

na ta cin Abinci, banda Najwa da take ta

juya cokali, ta zurfafa a nata tunanin,

Maama, Paapa, tare suke cin Abinci, kewansu

ta ke ji, ko wani hali suke ciki? Majeed na

lura da ita yace “yadai Najwa? Ko in dafa

miki Indomie?” Duk suka kalleshi da

mamako, barin ma Nana da take ji kamar ta

makureshi.

Najwa ta Murmursa tace “Aa, ina iya ci” yace

“Oya Eat, in ba za ki iya ci ba a dafa maki

Indomie” ta soma dauke numfashi tana

hadiye tuwon nan, don bata son Warin Kifin.

Najwa ta fara tashi, tace ta k’oshi, Hajjo

tace “ki kara mana ‘yarJikata” Najwa tace

“Nakoshi” Mairo ta tabe baki, Najwa ta mike

ta koma daki, hannu ta daura a kai, hawaye

suka fara sunturi, magana ta fara ma kanta

da k’arfi, “Najwa Sada Abu, zama ya kawo ki

Nigeria? Shin kina yin Abunda ya kawoki?

Kin san halin da kika bar Maama a cikin

kwanakin nan? Ke baki nemi Yayanki ba, ke

ba ki nemi Maama kin sanar da ita hakin da

kike ciki ba, duk da zata shiga damuwa

atleast call her and tell her sje shouldnt

worry about you, tell her you are Ok, Najwa

how can you be so Stupid?”

Sai ta fashe da Kuka tace “Maama i’m so

sorry, ya zanyi? I dont know who to trust,

bansan ta ya zance ma Majeed ya kira min

ku ba, bayan i told him a different story, me

zai faru in Asiri na ya tonu? Me zai faru in ya

gane k’arya nake mai tun farko, k’ila zai

koreni daga gidansu, ni kuma i wont take

that risk, ba zan bashi chance din sanin

wacece ni ba, dole in tashi da k’afafuwana,

in yi abun da ya kawoni k’asar nan”. Haka

ta dinga surutai ita kadai dole fa ta fara fita

neman Yayanta, amma ta ina??

Da Asuba bayan sun dawo daga Masallaci,

dakin Hajjo suka nufa, tana zaune kan

darduma Daddy da Majeed suka shigo da

Sallama, sai da ta shafa Adduar da takeyi ta

amsa Sallamarsu, daga gefe suka tsugunna,

Majeed ya gaishe da ita yana tambayarta

“ya kwanan bak’unta?” tace “Alhamdulilah”

Najwa da ke kan gado ta gaishe su, Majeed

ya mik’e yace “bari ya koma daki” sukayi

Sallama ya wuce, ya bar Daddy nan, Najwa

ta koma bacci, Daddy da Hajjo ko suka sha

firarsu har gari ya waye.

******

Da sauri Mummy ta shigo dakin su

Zaineema, tana kiran “Ziyada,Ziyada” Ziyada

tafi to daga toilet da sauri tace “yadai

Mummy?” da fara’arta tace “Yau Dan Deputy

Governor zai zo wurinki, yanzu mukayi waya

da Her Excellency” Ziyada ta daure fuska

tace “Mummy ni wallahi ban son haka,

donAllah kice kar yazo” Hajia Mairo ta hau

lallashinta kan cewa ta rufa mata Asiri, ta

shirya yanzu zai zo fa” tashi kawai tayi ta

shige toilet, Mummy ta kalli Zaineema da

take kwance tace “Zainee please talk her

out” daga Gira tayi alamun “OK”.

*

“Ziyada meyasa kikeyin haka?” ba gwara

miki Auren ba? Ni yanzu da nake zaune a

nan kin san yanda nakeji? Ji nake kamar in

koma Kaduna, ko Khalid zai wulakantani ba

zanyi fushi ba saboda ina son Mijina, kuma

Aure shine rufin Asirin Mace, ki saurareshi in

yazo please, dan Deputy Governor ne fa,

yanda muke shiga one problem or the other,

ki ka aureshi ai mun warke, Mummy ta bar

shan wahala, ke ma zaki cigaba da School

dinki a Base ba sai an saki wani BUK Ko NW

ba, think about it”. Ziyada ta kalli yayarta ta

watsar, kamar ba zatayi magana ba chan

tace “Auren Jari kuke so inyi kenan,hmm,

zan saurareshi ne kawai don mu fahinci juna

amma in be mun ba, Allah ya sa dan

Shugaban K’asa ne, ba zan aureshi ba, one

thing is for sure, ba zan taba auren wanda

bana so ba” ta tashi ta wuce dakinsu Hajjo”.

***

3:00pm

Jikin Mairo 6ari yakeyi ganin sha tara ta

arzikin da ake ta shigowa da su, da kanta ta

shigo da Amjad har Parlor, k’amshin shi ya

kaure Parlon gabaki daya,Mairo kamar ta mai

sujadda takeji, tace “barin turo maka Ziyadan

ko?” yace “Okay, Mummy” Mairo ta shiga

ciki, Zeenat ya yafito da hannunshi, tana

karairaya ta matso, sai yaji ta burgeshi, yace

“whats your name?” tace “Zinatu Abba Abu”

ya dinga mata tambayoyi tana bashi amsa,

ya ciro bundle din 500 yace ta siya

chocholates, ta karba tace “thanks” har ta

juya zata shiga ciki ta juyo ta kalleshi, tace

“i hope you marry my Sister Ziyada” ya

murmusa yace “I surely will” ta sa kai ta

wuce ciki.

Fama take tayi da Ziyada kan ta fita su

gaisa, ta k’i, Mummy bata da wani choice da

ya wuce ta rok’i Hajjo ta roketa ta fita, tace

“Hajjo, kice mata taje bakonta na jiranta, ba

dadi a barshi, gashi dan babban gida, be

saba jira ba” Hajjo tace “yau ga tsiyan

banza, ina aka ta6a gudun masoyi? Maza ki

tashi ki tafi ko in sa6a miki, haka akeyi?”

Chan kuma sai ta hau lallashinta tace “So

kike naje na miki sinacin(snatching)? Ina

laifin wanda yace yana sonka? Gaisuwa ne,

ba zai rage miki komai ba” ta turo baki tace

“Mummy kin gaya ma YaMaji?” Mairo tayi

karya tace “ai abokinshi ne, shi ma ya mai

kwatancen gidan” Ziyada ta mike ta ja

hannun Najwa wai ta rakata, Mairo ta galla

ma Najwa harara, nan da nan Najwa ta zame

hannu, tace “kije kawai” Ziyada ko tace “in

ba da Najwa ba itama ba zata ba” Hajjo tace

“tashi ki rakata Najwa, ba don son ran Mairo

ba ta bar Najwa ta rakata, suna fita ta bi

bayansu, tace ” ke Najwa zo ki kawo mishi

abun motsa baki, Najwa tace “Ok Mummy,

jeki Ziyada, yanzu zan zo” Ziyada tayi gaba,

Mummy ta tasa k’eyar Najwa suka wuce

kitchen.

****

Tayi Sallama kanta a k’asa, ya mik’e tsaye

“Sweetheart sannu da zuwa” Ziyada ta dago

kai ta kalleshi, mayataccen kallon da yake

binta dashine bataso, wuri ta samu ta

zauna, cikiciki tace “ina wuni” cikin doki yace

“lafiya lau beautiful” ya sauko k’asa kamar

me neman gafara, yayi yayi ta dago kai ta

k’i, yace “ina Mummy, Mummy kinga ta ki

dagowa in ganta da kyau, Alright, Fine,

Sunana Amjad” Ziyada da dai ko ci kanka ba

ta ce mai ba, yayi yayi tayi magana ta yi

shiru, haka yayi tagumi ya tsura mata ido.

****

Nana ta fito tana karairaya, “Brother Inlaw,

sannu da zuwa” da faraa suka gaisa, ta

gabatar da kanta a matsayin matar Majeed

Yayan Ziyada, suka gaisa tace “to brother

inlaw, na barka lafiya, ni na fita, sai mun

sake haduwa a Sha Soyayya lafiya” yayi

dariya, tare da daga mata hannu. Takaici

kamar ya kashe Ziyada, Nana batayi ba ko

kadan, haka Mummy da Zaineema suka

shigo suka Gaisa, Mummy tace “kaci

Dambun naman please, feel at home”

murmushi kawai yayi, Mummy ta ma Ziyada

ido alamun ta kula shi, Ziyada ta dauke ido,

haka Amjad ya cigaba da surutanshi amma a

banza.

Add

Najwa ta shigo da Sallama dauke da tray

cike da kayan mak’ulashe, ta durk’usa ta

gaida Amjad, ya amsa da faraa, yace “ya

sunanki?” tace “Najwa” “Nice name, are you

her sister?” Najwa tayi saurin kallon Ziyada

tace “uhm, erhm, eh” yace “Najwa Ziyadatu

bata magana ne? Ta k’i min magana, ki

gaya mata tana wahalar dani, please” Najwa

ta murmusa kawai ta kama gabanta don

Mummy ta gargade ta, da da ta kaimai ta

juyo”. Haka ya cigaba da yi mata fira ba tare

da ya damu da ta tanka ba ko ba ta tanka

ba, yana ta bata labarin France inda yayi

karatu, sai kuma Maganar Mommy dinsa.

Amjad fari ne k’yak’yawa sai dai siriri ne

sosai, duk kyanshi Ziyada bataji ya burgeta

ba ko dis, ita bata son Namiji haka, he’s

nosy, kuma ta lura dashi dan Mommy ne,

abu kadan zaice Mommynshi kaza, haba!

Surutunshi ya cika mata kunne, Gode ma

Allah tayi don taji wayar shi yayi k’ara

Alamun kira ya shigo, tana jinshi yace

“1minute Sweetheart let me answer this call”

Shiru tayi bata amsa mai ba.

PORTHACOURT NG

Gyara tsayuwarshi yayi tare da kara Waya ya

a kunnenshi yana murmushin Mugunta

“Hello, Amjad Sahabi” yana jin muryanshi a

k’agauce yace “Yes who is this?” Zaid ya

sake murmusawa yace “This is Zaid Sadam

Audu” da murna yace “OMG!! ZSA kaine?” a

tak’aice yace “yeah!” Amjad yace “Wow, its

been long, tun France, how have you been”

Zaid da ya soma k’ulluwa da surutan Amjad,

ya sanshi talkative ne, to shi ba wannan ya

kira shi ya ji ba, ya dai daure yace “Amjad,

kaje Zance Gidan Abba Abu gurin Ziyada

Right?” Amjad ya kalli Ziyadan da ke wasa

da yatsunta, yace “yeah, ya akayi kasani?”

Zaid yace “lol, ya ba zan santa ba, Aurenta

kake sonyi? Amjad are you out of your

senses? Kasan bansan shiga harkan mutane,

amma da naji kaine kake nemanta shiyasa

nace zan gaya ma, duk da we werent on

good terms back then, but ba zan ga abunda

zai cutar da kai in dauke ido ba” Amjad ya

dan fara tsorata yace “Zaid, ban gane ba”

Zaid yace “ka binciki Khalid Maikudi a garin

Kaduna, he was Zaineema’s Ex Husband, na

san ka ga Zaineema s a gidan, Khalid ya

saketa ne saboda ya kamata da Kwarto a

dakin aurensu, and Matar Majeed Nana, God

that girl is terrible, wannan karya ce,

muguwar ‘yar slow ce, shes a wh*re,

muguwar ‘yariska ce, in ba ka yarda ba, na

maka sending pictures dinta ta Whatsapp,

and then Ziyada, da tana karatu a Base

University, da aka gano tayi ciki shine suka

neman mata transcript suka cireta a

Makarantar, Suka barar da cikin a Ikhwaan

Clinic, if you are in doubt kaje ka bincika

Clinic din, da kake ganin Ziyada kamar

Saliha, ai ta fisu iskanci, don ta dame su ta

shanye, Hajia Mairo kuma, ka bincika kaji

halayarta ko gurin Mom dinka, ka tambayeta

halaiyarta da suna School, Amjad listen and

listen good, Alhaji Abba Abu ya samu

karayen Arziki, ba su da komai sai gidan da

suke ciki, bar ganin Gidan Tamfatsetse, shi

kadai suka mallaka, duk buga buga sukeyi,

so suke su hadaka da ita ka zaman musu

source of income, is that the kind of girl you

want to marry? Babanka is a Respected

Man, Auren diyar Abba Abu will tarnish your

Family’s Image” Amjad yayi shiru yana

nazarin Zaid, yace “Are you sure?” Zaid yayi

dan tsaki yace “trust me i have nothing to

gain idan na musu sharri, you have sources,

ka bincika ka gani, i thought you should

know ne, don ni na san halaiyarsu kaf, we

were once neighbors a Abuja, Use your brain,

Number dina ne, if you need anything” Dif

Zaid ya kashe wayar, ya Murmushin jin dadi

ya san yaci nasara.

K A N O Ng

Zufa ya shiga keto ma Amjad, tunani

barkatai, shin ya yarda da abin da yaji? To

Zaid Sadam ne ya gaya mishi, Zaid Sadam

kuwa ya sanshi a France, ba ruwanshi da

harkan kowa, duk yanda Amjad ya so shige

ma Zaid a wannan, Zaid be bashi chance ba,

har Zaid ya k’are zaman France Amjad ba

zaice ga Abokin Zaid ba, Zaid be damu da

kowa ba, to don me zai musu k’arya, yana

da kudi sosai don me zai bata lokaci wurin

musu sharri? lokaci daya zuciyarshi ta

aminta da abunda Zaid ya fada mai, Allah ne

ya soshi, ya tsamoshi daga sharrinsu, ya

wurga ma Ziyada wani kallon tsana ya tashi

ya kwashi keys dinshi, ya sa kai ya fita, da

mamaki ta bishi da ido, to me ya faru, duk

da bata damu ba, taji ba dadi, amma da

alama wayar da ya amsa ne aka bashi bad

news. Ta kwashe kayan ta kai kitchen, Su

Mummy suka mata chaa, “ya tafi? Ya kuka

kare?” Ziyada bata son surutu sai kawai tace

“yace zamuyi Waya” ta shige dakin Hajjo.

****

WASHEGARI

Sadaf Sadaf ta k’araso Parlorn daidai Wayar

da ke ajiye ta ci burki, ta dauka wayan, bata

san wayar waye ba, addua take Allah ya sa

wayar ba Password, tana swipping ko taci

saa wayar ba Password, ta tura wayar cikin

rigarta ta fita waje da sauri tayi baya wurin

boysquaters. A sarsarfa ta sa numbern

Paapa, sai da ta kira so uku be dauka ba,

kamar tayi kuka, tayi dialing numbern

Maama, itama kira take tayi amma no

response, Waiyo Allah Najwa ji take kamar ta

sa ihu, tana so tayi waya da Maaman ta, jin

Alamun ana takowa ta inda take ya sata

deleting numbers din da sauri ta maida

wayan a riga ta koma parlor, inda ta ga

wayan ta maida ta ajiye, ta koma Daki.

I N D I A

Kwanaki 18 daidai kenan da tafiyar Najwa, in

ka Alhaji Sada Abu da Matarshi sai sun baka

tausayi, Rayuwa suke kamar Matattu, ba su

da wani jin dadi da walwala, duk sun rame

sun fita hayacinsu, barin ma dai Maaman

Najwa, hardai shirin biyo ta Nigeria sukayi,

kamar Kullum suka kasa, wannan karon

Paapa ne ya sul6e ya fadi k’asa, ya karye

k’ashi, yanzu haka suna Asibitin Apollo inda

Maama ke aiki, Zafi dubu da goma wurin

Maama, ga rashin sanin halin da diyarta ke

ciki, ga Miji kwance a Asibiti ba lafiya. Da ta

samu Bacci ya dauki Paapa, sai tace bari ta

tashi taje Gida tayi wanka, sai su dawo tare

da Vijhay.

*

Wayar Paapa yayi ta ringing har So uku kafin

nata ya hau ruri, tana cikin gida, Wayoyin

kuma suna cikin Mota inda ta barsu, sai da

tayi wanka ta dan dafa musu Abinci, kafin ta

kira Vijhay suka koma Asibiti, ba tare da ta

duba Wayarta ba ko na Paapa, ko da suka

isa Asibitin, Paapa ya farka, Maama tace

“Papi kya huwa?” a hankali yace ” Najw a-” ta

karado gunshi da sauri ta riko hannunshi,

yace “Yesmeenah, nayi Mafarkin Najwa na ta

kwala min kira” da sauri ta tashi ta wawuro

Jakkarta ta ciro wayoyinsu, Ikon Allah taga

missed calls 3 ana Paapa, Biyar ana ta,

kuma international call, callcode din Nigeria

+234, kuka ta fashe dashi tace “Wallahi Papi

Najwa ce, Najwa ce ta kira mu” yunk’urin

tashi yakeyi Vijhay ya tareshi.

Maama tabi bayan Missed call din ana dauka

“Meri Beta(Diyata), Najwanatu Ke ce?” shiru

ba amsa, Hello kinaji? Kiyi magana mana,

bakiyi missing Maama dinki bane? Haba

diyata ki min magana” nan ma Shiru, sai

nishin da takeji sama sama, Maama ta fara

shesheka tace ” ba zakiyi magana ba, to ga

Paapan ki ? Da sauri ta ba Paapa wayan

“Papi tak’i ta min magana” Paapa ya amsa

wayan “Hello, Hello, ba kya jine, kiyi magana

mana” dif sukaji wayar ta katse, hannu na

rawa suka sake dialing, sai akayi rejecting,

da su ka kara sai ji sukayi wayar a kashe,

Maama tace “Papi meke faruwa? Najwa ta

kira mu taki magana” Paapa yace “kwantar

da hankalinki, it shows that Najwa is fine,

tunda har ta iya kiranmu, kila service ne,

network ne, shiyasa baa ji, ko kuma chargy

it can be anything, thing positively

Yesmeenah, Najwa zata sake kiranmu kinji?”

Da haka ya lallabata har ta dan kwantar da

hankalinta.

K A N O Ng

Ta shigo Parlo dauke da plate din fruits, ta

zauna tana cin Apple cike da tak’ama da isa,

Hajia Mairo kenan, Uwar Gidan Abba Abu,

tana chanza Channel taji wayarta na ringing,

Janyo wayar tayi ta ga International Number

ce, +91, da mamaki tace “toufa, wannan

numbern wace k’asa ce?” tana dauka ta sa a

kunne tare da fadin “Hello” Muryar da taji ne

ya sa kirjinta Dukan Chalugude, gabanta

kamar ya fashe don duka da sauri, tayi

k’asak’e tana sauraron Muryan da ke Amo a

kunnenta, ba zatace ga abunda matar ke

cewa ba, amma hankalinta in yayi k’ololuwa

to ya tashi, bata gama tsurewa ba, sai da

taji Matar tace “Papi” hankalinta be kai ga

tashi ba kamar yanda taji Muryan Namijin da

ta fara So a rayuwarta, ba zata iya mance

Muryarshi ba, tsoro da fargaba ya sata latse

wayar, a guje ta fada dakinta, ta shige toilet

da gudu, shower ta sakar ma Kanta, bata

damu da kayan da ke jikinta ba, ya akayi

haka? Shine tambayar da ke kai kawo a

kanta, ta ya akayi suka kirata? Ya akayi

suka samu numbern ta? Sada? Yesmin? Ya

akayi suka ita kiranta wai? Ita da aka bata

tabbacin zasu guje duk abunda zai sadasu

da Nigeria, ta ya zasu iya kiran Nunbern

Nigeria? Tsigar jikinta duk suka mimike, ina

ma zata iya kuka, ta kasa, Kar fa su dawo,

ta ya akayi, Mamaki da tsoro sun hanata

yarda da cewa su dinne suka kirata, da

gangan ta k’aryata kanta, ba su bane, it

cant be them, ba Sada bane, ba Yesmin

bane, ba su bane, kar ku min haka, kar ku

dawo, kar ku dawo donAllah, ba kunya ba

tsoron Allah Mairo ta daga hannu sama tana

rokon Allah, Allah ya k’ara nesanta Sada da

Matarshi da Nigeria, amma fa kamar taji sun

fadi Sunan Najwa, what if sune Parents din

Najwa? What if-?” da sauri ta kawar da

tunanin nan, a fili tace “No, it cant be” ita fa

duk yanda zata kawar da tunanin nan sai ta

kawar dashi, ta gama da babin Sada da

Yesmin, abunda ya faru sama da shekara 18

shine zaace sai yanzu zasu baiyana? Be

yiwuwa, kawai banzan tunani take tayi, ba su

bane, Mairo da taurin Zuciya, ta kan kitsa ma

kanta abunda take so ta yarda dashi, haka

tasa Zuciyarta yarda da ba su din bane, ta

fito daga toilet ta chanza kaya, kai tsaye ta

dauko wayarta ta kunna, tayi blocking

numbers din da aka kirata dasu ta fito

Parlor.

*

Tana fitowa ta ci karo da Najwa, gaban su a

tare ya yanke ya fadi, ita Najwa tana tsoron

ganin Mummy, ita kuma Mummy ganin

Fuskar Najwa tayi ya rikide mata ya koma

mata na Yesmin. Kiris ya rage ta fadi k’asa

amma da yake Mairo Mace ce mai kama da

Maza sai ta cije tace “ke zonan” jiki na rawa

Najwa ta k’arasa gaban Mummy ta durk’usa,

Mummy tace “tambayan ki zanyi, in kika

sake kika min k’arya sai na miki mugun

duka kinaji na” Jikin Najwa ya hau karkarwa,

ta gyada kai, Mummy ta dauko wayarta ta

nuna mata last call tace “ke ki ka kira

numbern nan?” da sauri Najwa harda rintse

ido tace “aa” Mummy ta jinjina kai tace

“danubanki ke ‘yar wace k’asa ce?” muryan

Aisha ta tuna inda take ce mata “Najwa you

must not trust anyone” baki na rawa tace

“Ghana” cikin tsawa tace “ina Iyayenki suke

zaune?” tuni Najwa ta gama tsurewa, wani

tsawa da Mairo ta daka mata sai da ya sata

ciwon kai lokaci guda, “suma ‘yan chan ne,

‘yan Ghana ne” “k’arya kikeyi” “dagaske”

Mummy tace “karbi wayan nan, sa numbern

Iyayenki, ki kirasu in tabbatar” Najwa ta

tsure tace “ban rik’e number dinsu ba” Mairo

ta jawo ta ta hau kilarta, k’arya kikeyi,

Najwa ta hau kuka a hankali yanda ba kowa

zai ji ta ba.

*

Kamar daga sama sai ga Majeed, da sauri ya

k’arasa gunsu, cikin Zafin nama yace

“Mummy me nace miki game da Najwa?”

cikin Hargowa tace “wannan yarinyar

Makaryaciya ce, shes not what she says she

is, wayana ta dauka ta kira Iyayenta, na

tambayeta ita yar wace k’asa ce tace wai

Ghana, kuma numbern da aka kira ni da shi

irin Asian countries din nan ne, nace ita ta

kira numbern ta k’aryata, dan uwarta nace

ta ban numbern Uwarta, wai ba ta rik’e ba,

dan uwarta wani da zaice be rike numbern

uwarshi ba?”.

Majeed yace “muga Numbers din” “kika sake

kika nuna mai numbers din ya bi bayan

wayan kinsan Majeed da bin didik’i ya gano

gaskian lamarin k’aryarki ta k’are” Zuciyar

Mairo ke mata gargadi, da sauri tace

“Nagoge numbers din” Majeed yace “Mummy

ki bar Najwa please, idan bata so ta baki

numbern Iyayenta ba dole bane, ta fada bata

so Baban ta ya san inda take saboda zai

mata auren Dole, da sanin Mamarta ta zo

Kasar nan, ba ruwanki” Mummy tace “kai

wani irin sakarai ne? Cutarka takeyi wallahi,

yaudararka takeyi” Majeed ya kalli Najwa ya

kalli Mummy yace “Allah ya san da Zuciya

daya nake zaune da ita, inta cuceni ita da

Allah, zata cigaba da zama damu har sai

randa tayi niyyar tafiya Gida, So Mummy

please, this should be the last time, Enough

is Enough” Mummy ta bude baki cike da

mamaki, Najwa kuwa taji ba dadi, anya

Majeed ya chanchanci haka? Kallonta yayi

yace Zo Najwa, yayi gaba, da sauri ta bi

bayanshi.

*

Mota ya shiga ta bi bayanshi, horn yayi aka

bude musu gate ya fita daga gidan, ba me ce

ma danuwanshi k’ala, sun danyi tafiya kafin

ya shiga wani katafaren guri, daga sama ta

karanta *Farm Center* ya dan kalleta yace

“i’ll be right back” duk da hawayen da takeyi

sai da ta murmusa, ya fita, ba a fi minti 20

ba sai gashi ya dawo da leda a hannu, ya

mik’a mata ta kalleshi, yace “karba mana” ta

sa hannu ta amsa, ta bude, kwallin waya ta

gani *Gionee P2* ta dago kai ta kalleshi, ya

murmusa yace “You can call Maama

whenever you feel like, simcard din sai after

24 hours zai zama active, kiyi managing, na

san its not like your Iphone6, amma–”

katseshi tayi tace “Allah ya saka da Alheri,

Allah ya biya, Nagode, i cant thank you

enough” Murmushi yayi, ya kunna mota suka

dau hanyar Gida, sai da ya tsaya Eatery ya

siya ma su Ziyada Snacks, a hanya yake ce

mata “Najwa, ki k’ara hak’uri Kinji?

Everything will be Alright” farinciki takeyi, ta

ma mance da abunda ya faru, wannan wayar

ya share duk wank bakinciki Mummy, ba

zata iya gode ma Majeed ba, anya ta mai

adalci kuwa? Bari dai ta gani, if he’s worth

her trust.

WASHEGARI

Kallonta yayi da takaici, baya tunanin ko

Asuba tayi, gari ya gama Wayewa, 8 saura,

tun dazun ya ke ta neman Credentials dinshi

amma ba alamun su, ba inda be bincika ba,

da ya ga ya kusa zautuwa da nema, ya sa

shi buga Nana”Nana nah, tashi donAllah”

bacci be isheta ba, syrup din da ta

kwankwada jiya ba su saketa ba, cikin

magagin bacci tace “My Majeed, ka barni

donAllah, kaina na ciwo” sausautar da murya

yayi ace “Ki daure ki tashi kiyi Sallah” ko

motsi bata k’ara ba, zuwa yayi ya dagata

Sama ya sada ta da toilet, yana jin tana

mishi mita yayi mata shiru.

Sai da ta idar ya ke ce mata “Nikam Nana

baki ga inda na ajiye folder din Credentials di

na ba?” gabanta ya yanke ya fadi, in-ina ta

soma yi “aa, aa wallahi, bani na dauka ba”

jin yanda tayi maganan ya sa shi dakatawa

ya kallota sosai, jijinta ya fara rawa, mamaki

ya rufe Majeed, me ke sa Jikinta na rawa?

Sai kace mara gaskiya? Majeed ya danyi

nazari, ji yanda take wuk’i wuk’i da ido, anya

kuwa?.

*

Dabara ta fado mai yace “Kin kaima

Daddynki ne ya nemo min Aiki?” baki na

rawa tace “Aa” Majeed yace “to wa kika kai

mawa?” bakinta na karkarwa “Wani ne yace

in bashi Credentials dinka zai sama maka

aiki a Inland Revenue” Majeed yayi k’uri yana

kallonta, ji yake kamar ya fadi don wani jirij

da ke dibarshi, a hankali yace “Nana sai ki

bashi Original Copies? Ina kika taba ganin

anyi haka? Haba Nana, ba wannan ba,

kirashi yanzu kice mai zanzo in karba

Original Credentials din, in yaso sai in bashi

photocopy, Nagode”.

Tayi shiru, ko motsi ta kasa, ya sake cewa ”

kirashi Nana” baki na rawa tace “banda

Numbernshi, da Private Number yake kirana”

ruf ruf idon Majeed ke kullewa yana budewa,

baya son yarda da abunda kunnuwansa suke

jiye mai, yayi kamar beji me tace ba, ya sake

tambayarta, “Nana, ki kirashi yanzu inje in

karbo Folder na” da tsoro ta sake maimaita

mai “Banda numbernshi, ban san da me zan

sameshi ba, shi ke kirana ba nike kiranshi

ba, yace in aikin ya samu zai gaya min,

suprise nake son yi maka, shiyasa ban gaya

ma ba” jin shiru be amsa ta ba ya sata

kallonshi, ganinshi tayi a k’asa, a kidime ta

karasa gunshi, ba ta san yanda akayi ya

yanke jiki ya fadi ba. Ihu ta sake da k’arfi

tare da fashewa da Kuka, kukan da takeyi ne

ya hada kan ‘yan Gidan Gabaki daya a dakin.

Mummy kamar tayi hauka, ta tataro Majeed

jikinta tana kiran Sunanshi, Hajjo kadai tayi

tunanin dauko ruwa ta yayyafa mai, ina be

ko mosta yatsa ba, Ziyada da sauran Yaran

sai kuka suke tayi, Najwa ma fuskarta yayi

Ja, duk cikin tashin hankali suke, Daddy yace

“Ziyada kira Fallalu akai shi Asibiti” da gudu

Ziyada ta fita.

Chan sai ga Fallalu nan yazo, aka Cicibeshi

akayi Asibiti dashi. Daddy yace “su tsaya a

gida” shi da Mummy da Nana suka tafi

Asibitin.

******

Masoya ga Wani Babin, ya kuka gani?

Spoiler Alert; Zaman Nana ya kusa k’arewa

a gidan Abba Abu, kuma akwai sabon

Member a gidan, Guess who?.

Har yau ba zan fasa gode muku da kuke

kasancewa tare dani ba, na san bana muku

update akai akai, Wallahi i’ve been busy ne,

in nace zan dinga yi a kai akai zanyi shine

fiii sha a wuce gurin, kuma ba zai yi dadi ba,

kuma ba zaku so hakan ba, Nafiso na natsu

na muku a tsanake, da haihuwar yuyuyu

gwara daya kwakwara. Ku cigaba da

kasancewa tare dani.

Ehen Wattpadians! You know i love you ko?

Show me love Vote and Comment line by line

please.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣2⃣

Ka sa sukuni tayi, duk yanda ta so ta

daure ta kasa, toilet ta ta kunna pampo

shige tare da fashewa da kuka, kuka take

sosai kamar an aiko mata da sak’on

Mutuwa, bata san ta shak’u da Majeed ba,

bata san zata shiga damuwa haka ba, me ya

sameshi? inalillahibwa ina ilaihir rajiun, Allah

ya baka lafiya, ban san ne zanyi ba if

anything should happen to you Ya Majeed”.

Sheshekar da takeyi ya fara k’ara, Hajjo da

Ziyada da ke cikin damuwa suka k’ura ma

K’ofar Toilet din ido, Hajjo tace “Ziyada,

kamar kuka nakeji” Ziyada ta dan kasa

kunne tace “Najwa ce” ta mik’e don dubota.

K’wan k’wan ta kwankwasa mata, “Najwa

bude K’ofar” Najwa na jin muryan Ziyada tayi

saurin wanke fuskanta, ta fito, bata san sunji

Kukan da take tayi ba, ta murmusa cikin

rashin gaskiya, Hajjo tace “zo nan Najwa,

menene abun kuka? Addua ya kamata ki

mishi, zaiji sauk’i da yardan Allah” kamar jira

take yi ta sake fashewa da Kuka.

Ziyada ta ga Najwan ma tafita shiga

damuwa, ba zata yi mamaki ba, don Yayanta

akwai shiga rai, balle ita da ya taimaka, ya

fiddo ta daga rana ya sata inuwa, kamo

hannunta tayi, tace “Najwa, kar ki karya min

Zuciya donAllah, ba abunda zai sameshi,

he’ll be fine, kar ki damu” Najwa ta rik’e

hannun Ziyada gam, tace “Mu bisu” Ziyada

ta zaro ido tace “what?” Najwa tace “Mu

bisu Asibitin, muje muga halin da ya ke ciki,

hankalina ba zai kwanta ba, please Ziyada”

Ziyada tace “Daddy yace mu zauna a gida

har su dawo” Hajjo da take sauraronsu ta

hadiye yawun da ya k’afe a bakinta, ta

karanci soyayya da shak’uwa tattare da

Najwa, chan sai tace “tashi kuje Ziyadatu,

nasan kema kina son zuwa, tashi kuje in kin

san Asibitin”.

Ziyada tace ” Na sani” tuni Najwa ta saka

Hijab, Ziyada kuma ta yafa mayafi, suka fita

daga dakin, Ziyada na karantar Najwa, duk ta

fita hayyacinta, ta rasa sukuni, sai da Ziyada

ta rik’e mata hannu don ta k’arfafa mata

guiwa, A daidaita sahu suka samu, suka fada

mishi Asibitin da zasu, suka shiga, ba me

magana, kowa da abunda zuciyarsa ke sak’a

masa. Asibitin fa?.

*

Suna Isa Asibitin akayi da Majeed

Emergency, nan da nan Maaikatan Asibitin

suka karbe shi a ka dukufa aiki, Mummy,

Daddy da Nana sai safa da marwa suke,

Mummy ta kalli Nana rai bace tace “meya

same shi, me kika mishi?” Nana jiki ya hau

rawa, bata taba ganij Mummy ta mata

magana a irin yanayin nan ba, cike da bacin

rai da fada, to me zata ce mata ya faru?

Tsoro duk ya kamata, tace “nima ban sani

ba” Mummy ta dan kura mata ido tana san

karantar abu daga ciki, tace “in wani abu ya

same Yarona, I will kill you Nana, na san duk

kece, bari ya tashi, dama ba sonki yake ba,

wallahi in ya gaji da zama dake sai ya sake

ki, ni ban kashe Yarona ba, kema ba zaki

kashe minshi ba ” Nana ta tsorata matuk’a

ta rasa abun yi, ta tsura a guje kamar

Mahaukaciya.

Daddy ya dafa kafadun Mummy yace “Easy

Maryam, ba abunda zai sameshi, bari muga

fitowar Likitocin”. Haka suka dinga sunturi,

daga reception zuwa gaban dakin

Emwrgency, kusan Minti 15, sai ga Ziyada da

Najwa kamar an jefosu, Fallalu Direba suka

gani waje ya nuna musu inda su Nana suke.

Mummy na ganin su bata yi magana ba, don

bata da energy din magana, ita hankalinta

kachokam yana gurin Yaronta, bata san halin

da yake ciki ba, ya zatayi?. Daddy ne yace

“Yadai Ziyadatu? Ba nace ku tsaya gida ba?”

Ziyada tace “Sorry Daddy, hankalin mu ya

kasa kwanciya ne”. Daddy yace “ba abunda

zai sameshi da yardan Allah, ina su Zinatu?”

a hankali Ziyada tace “suna gida” Daddy ya

jinjina kai, idonshi ya sauka kan Najwa da ko

magana ba ta iya yi, kallo daya yayi mata

ya san cewa taci kuka sosai, fuskarta yayi

Ja Sosai, idanunta sunyi luhuluhu, haka

kurum yaji tausayin Najwa, Daddy yace “Its

Okay Najwa, he will be fine” kai kawai ta iya

daga mai, Mairo bata da lokacin kallonsu

balle ta tanka musu.

Suna hakan ne Dr’s din suka fito, gabaki

daya sukayi kansu, Dr Hisham yace “ku muje

Office” da sauri suka yi hanyar Office din,

saida Mairo ta rigasu duka, sai da Dr Hisham

ya zauna ya kalli Daddy yace “Alhaji Abba,

Meke sa AbdulMajeed Damuwa? Ya Salam,

how Old is he?” charaf Mairo tace “He’ll be

29 nextweek” Dr ya jinjina kai, yace “29

years amma yana fama da * High Blood

Pressure?* tun yanzu ya fara fama da BP?

Ko 40 fa be kai ba, meye damuwanshi?” duk

sukayi shiru, Dr ya shiga fada yace “He’s too

young da zai fara shan Wahalan Hawan Jini,

sam Hawam Jini ba ciwon Samari ba,

Imagine BP dinshi ya haura 200, wannan in

ya cigaba da yanke Jiki yana fadi yana

suma, Zuciyarshi bugawa zatayi ba tare da

bata lokaci ba, and you’ll lost him for good” .

STORY CO

Mairo tace “God Forbid, Dr, bari, gaya min

how’s my baby now? Ina fatan ya dawo

daidai?” Dr ya kalleta yace “hmm, mun samu

jinin ya sauka, but he’s stressed out, na

bashi bedrest for one week, kar ku dameshi

da abunda zai saka shi cikin damuwa, and

abar bashi Abinci mai gishiri, in ya farfado

nurse zata bashi magani, he’s very weak, ku

barshi ya huta please, in ya tashi komai zai

zama normal, amma zan rikeshi anan for a

week”.

Mummy taja numfashi, sai yanzu ta dan

samu natsuwa tace ” ai Dr, gwara ka barshi

a Asibitin, wallahi shike stressing kanshi,

Yaro baya nan baya chan, InshaAllah zamu

kiyaye” Dr ya kalli Najwa ya murmusa yace

“You must be his Wife, Alhaji ya gaya mun

AbdulMajeed yayi aure” Najwa baki ya

mak’ale takasa cewa komai, Mummy ta balla

mata harara, tace “Noo, ba ita bace,

she’s–” ba ta karashe ba, Ziyada ta k’arasa

da fadin “Family, Shes Family” Mummy ta

bude baki, Daddy ya murmusa, Dr ma ya

Murmusa yace “Mallama Ziyada ina su

Zinatu?” ta amsa mai, Dr ya mike yace “bari

ya tafi rounds, suka mai godia ya fita daga

Office din.

PH Ng

“Whoa! Wait is he Alright?” tambayar da

Zaid yayi ma Amstrong kenan da ya sanar

dashi an kwantar AbdulMajeed a Asibiti,

Amstrong ya tsura mai ido, yana son ya san

wani yanayi Zaid yake ciki, idan beyi k’arya

ba, zaice ya ga damuwa a idon Zaid, amma

bari ya tabbatar da hakan, gyaran Murya

yayi yace “Why are you worried?” Zaid ya

dan yi Jim, chan kuma da sauri yace

“Ofcourse Not, i careless what happens to

the Abba Abu’s, serves them right” yayi sauri

ya tashi ya shige daki don gudun ma

tambayoyin Amstrong, sai dai me? Yana

shiga daki ya rasa sukuni, ya rasa meke

damun shi, baya son zuciyar shi ta tabbatar

mai da damuwa ya shiga, Shisa ya kunna

amma sam ya k’asa zuk’a, hankalinshi ya

gaza sukuni, ba wannan yake sonyi ba, chan

k’asar Zuciyar shi, akwai abunda zuciyar ke

son sani, tsaki ya buga da k’arfi ya ciro

Wayan yayi dialing wani Number, chan

k’asan Mak’oshi ya fara magana; “Mallam

Musa, je Softie Hospital din Dr Hisham, ka

binciko min, meya samu AbdulMajeed, make

it Quick” dif ya latse wayan, ya dafe kanshi

da hannu biyu, ya buga tsaki karo na ba

adadi, a fili yace “bawai na damu da halin da

kake ciki bane, ya ma zaayi na damu? I pray

Condition dinka yayi tsanani” sai dai a cikin

zuciyanshi be fatan hakan.

KANO

Cike da Maye ta wuce Tourist lounge, kallo

daya zaka mata kasan cewa ta k’wallu, sai

da ta biya Gida ta kwashi Kwayoyinta masu

gusar mata da Hankali, k’wayoyin da ta bar

sha duk saboda Majeed, yau hadin da tayi

yafi k’arfin ta, yau Mummy ita ke ma

barazanar rabuwa da Majeed? Mummy ta

bar sonta.

So take ta huce takaici, duk da yanzu jin

kanta take a sama, ba wani shege kamarta,

a gaban Entrance din ta kira Saleem Waya

muryarta cike da maye tace “Kana ina ne

wai? Kasan bansan Jira, in bata min lokaci

zakayi ka turo min Nimcy, kace mata ina

jiranta” tsaki tayi ta kashe wayan.

Wuri ta samu tana mari ta na mayenta

hade da sambatu, ta gaji, har ta fara daukan

hankalin mutanen wurin da Sambatun ta.

*

Sallama taji ana mata, da rinannun

idaniyarta ta dago ta kalleshi da k’yar,

“Nana matar Abdulmajeed Abba ko?” kallon

alamun rashin sani ta mai tace “yeah?” yace

“Ina Majeed?” cikin layi take magana tace

“yana Asibiti” Subhanallah meya sameshi?”

“kawai don na bada Credentials dinshi a

neman mai aiki ya Suma, daga taimako fa”

daga yanda take magana ya gane cewa

akwai matsala, kamar a buge take, yace “to

me kikeyi a nan?” a tak’aice tace “ina jiran

Saurayina da Girlfriend dina” Gabanshi ya

fadi, kar dai abunda yake zargi ne, da sauri

ya ciro wayarshi ya lallatsa, a buge take, zai

iya getting information daga kanta ba tare da

tayi k’arya ba, da sauri yace “What?” ta dake

maimaita mai kafin tayi dariyan ‘yan bariki

tace “kaima dan k’auyen ne ko? Lol, Majeed

ba zai iya dani ba, Salim da Nimcy kadai

suka san yanda suke wadatas dani” baki na

rawa yace “Erhm Nimcy din Mace ce?”

Ehmana sun fi dadin harka, kaima in kana so

akwai guys din da zan hadaka dasu” baki na

rawa yace “no karki damu, ina da su”

“hahaha kace kai dan hannu ne, sha, samun

numbernka zan kiraka” karban wayanta yayi

ya sa mata number, yace “gashi na miki

saving” tace “yauwa, ga Salim nan zuwa,

wuce donAllah kar ya ganmu tare yayi

Zuciya, Kishi gareshi, da My Majeed kadai ne

be Kishi saboda ya san son da nake mishi,

yi sauri sai na kiraka” jikin shi duk yayi Sanyi

ya wuce yana mamaki.

Duk sun hadu a dakin Asibitin, sai dai ba me

magana, zaune suke Jugum kamar anyi

Mutuwa, shi Majeed be son ganinsu cikin

damuwa, ya kalli wannan ya kalli wanchan,

chan sai yace “Zeenah meyasa bakuje

School yau ba?” cikin Muryan Shagwaba

tace “ba kai bane baka da lafiya?” ya

Murmusa yace “lafiyata lau, Fallalu yazo ya

maida ku gida, 2 nayi ku wuce Islamiya,

nima yau zaa sallameni, kafin ku dawo ina

Gida ko?” kafada ta mak’e yace “Pleaseee,

kije Islamiya, naji sauk’i” da k’yar ta Amince,

Muhsin yace “YaMajeed inci Apple dinka?”

Majeed yace “Eh Muhsin kaci” da tsallenshi

ya dauka yana ci, Majeed ya kalli Ziyada

yace “Oya Zuzu, je ki duba Fallalu na waje?

Duk ya zo ya kwashe ku ku koma Gida,

yanda kuka tsura min ido kamar ance muku

na mutu” Ziyada ta ja hannun Najwa don ta

rakata amma Najwa ta tirje, hakan ya sa

Ziyada tafiya ita kadai, Majeed ya ga abunda

tayi, sai dai kawai ya Murmusa, a bakin

K’ofa ta ci Karo da Nana da ta shigo hannun

nik’i nik’ da kayan Abinci, raba Juna sukayi

suka wuce.

Ba tare da ta gaida mutanen da ke zaune

wurin ba, Iyayen Majeed da Kakarshi, Nana

ta wuce kai tsaye Gadon Majeed ta fada

kanshi tare da rungumeshi, ido ya runtse

kafin ya bude a hankali, “My Majeed are you

Alright?” da k’yar ya iya daga mata kai, ta

taba nan jikinshi ta taba nan, wai ita tana

duba in akwai inda ke mai Ciwo a jiki, haka

zata dauko Pear ko Apple, ko grapes tace

yaci, Murmushi ya ke k’wakulowa ya girgiza

kai, a hankali yace “Nanah, ina Credentials

din an kawo?” dimmm tayi, Mummy tayi

karaf tace “wani Credentials?” baki na rawa,

Nana tace “Aiki na bada a samo mishi”

Mummy ta kalleta tace “a ina?” a takaice

tace “Inland Revenue” Mummy tace “Allah ya

sa a dace” Majeed yace”Nana please, kice a

yo sauri in a kawo, if there are busy ni ki

gaya min inda suke inje duk nisan su, i need

that Folder, My Whole life is in it”. Mummy

tace “Tsaya, Original Copies din ta dauka?”

Nana ta sunkui da kai, Mummy ta dan bude

Murya tace “ke Original Copies kika dauka?”

a hankali ta gyada kai, Mummy ta rafka

Salati tace “Danubanki ke jahilar inace? Ina

kika taba ganin an nemi aiki Da Original

Results? Yi Maza Maza yanzu ki kira, a

kawo, ko ni inje in karba” kwalla ta fara tace

“yace Zai fa kawo min” Mummy tace “ayi

Maza a kawo, don Wallahi in wani abu ya

samu Credentials din nan, Wallahi ko Alhaji

Nakowa ba zai iya kwatarki daga hannuna

ba, Sakara Mara Amfani kawai”. Daddy ya

tare ta yace “Maryam Easy mana, ance kar

ayi Hayaniya har yanzu fa kwance Majeed

din yake, kiyi hakuri ayi komai a hankali, tace

zaa kawo, ki bari a kawo din” huci take

kamar Zakanya, ta samu wuri ta zauna tana

karkada k’afa, Majeed ya sausauta murya

yace “Kiyi hakuri Nana, donAllah a kawo min

Credentials dina kinji?” tausayi ya bata, ta

daga kai tace “Kar ka damu za a kawo” ya

gyada kai ya koma ya kwanta.

Shiru dakin yayi kowa da tunanin da yakeyi a

Zuciyar shi, Ziyada suka shigo da Fallalu, ya

ma Majeed ya jiki, Majeed ya amsa da

Murmushi, yace “Fallalu ka kwasar min

tsohuwan nan da Jikokinta kai min su Gida”

Hajjo ta wurga mai harara tace “kai Abdallah

ba ka rabo da ba’a” yayi daria tace “to yan

jikoki mu tafi ko?” Muhsin ya rik’o hannun

Hajjo, Daddy yace “Umma ayi mana Addua

daga nan zan dawo Gida” hajjo ta murmusa

tace “Allah ya hadaka da Alherin Mai Alherin,

ya kuma nisantar da kai daga Sharrin Mai

Sharri”duk suka amsa da Amin,”Amin Umma

nagode” banda Mummyn da ta wurge su da

harara tana sak’a ma ranta wani abun da ita

kadai ta sani.

*

Daddy ya tasa k’eyar Muhsin da Zinatu a

gaba, zai raka Hajjo bakin Mota, Zaineema

ta matso kusa da Gadon Majeed, ta mai kiss

a goshi tace “Kaji Sauk’i” kai ya gyada mata

tare da mata murmushi, ta juya ta bi

bayansu Daddy.

A haraban Asibiti suka ci karo da Motar

Hajia Aynarh, ta fito cikin shiga ta Alfarma,

mai aikinta ta fito rike da katon Basket, suka

karaso gurin da Motar su Fallalu ke parke

suna niyan fita Asibitin “Alhaji Abba baka

kyauta min ba, ya ba zaka gaya min Abunda

ya samu yarona ba tun jiya sai dazun?

Haba” Daddy yayi Murmushi yace kiyi hakuri

ko? Ai dai na gata miki yau din, tayi dariya

cike da Kissa tace “to na hakura” ta kalli

gaban Mota inda taga Dattijuwa, ta dan

rusuna tace “ina wuni? hajjo ta amsa da

faraarta, sai da Daddy ya kalli su Zaineema

kafin suka gaidata, dama duk gidan daga

Zaineema sai Zinatu ne ba sa yi da Hajia

Ainau, Daddy ya mata alama da ido yace ”

thats My Mom” ta bude ido tace “are you

serious?” Ya daga mata kai, ai da sauri ta

zagaya gaban motan ta rungume Hajjo

kamar ta santa, ta zube k’asa a guiwowinta,

tana kwasar Gaisuwa, Mama Ina wuni? Ya

gida ya Jiki? Mama ya kike? Ya kowa da

kowa” Hajjo ta amsa baki har kunne tana jin

dadin yanda Hajiyar ke gaidata, kunsan

Yarbawa da Biyayya, da kissa nan da nan

Hajiya Ainau ta shiga Zuciyar Hajjo. Daddy

yace “To Fallalu ku tafi ko?” Hajiya Aynarh

ta dinga daga ma Hajjo hannu har suka bar

Asibitin, hakan ya ma Daddy dadi.

Idonshi ya sauka kanta, Ko ba a fadi ba ya

san tana cikin damuwa, tunda suka gaisa

dazun da safe da suka shigo ta mai ya jiki,

be k’ara jin Muryarta ba, tana da damuwa,

ina ma zai iya jin damuwarta, da ya yaye

mata shi da iyawarshi, ya lura da yanda take

tirjewa na bata son tafiya, har yanzu din ma

tirje ma Hannun Ziyada takeyi “lets wait a

little longer” yaji ta fada a hankali, Ziyada ta

mata Ido da Mummy, Najwa ta marairaice

tace “Please” Ziyada tace “OK”.

Mummy ta lura da su basu tafi ba tace

“Ehen?” Ziyada tace “Erhm zan tsaya sai

anjima ina zaki tafi” Mummy ta galla ma

Najwa harara tace “kefa? Come on wuce”

kafin Ziyada ta kare Najwa, Majeed yayi

Charaf yace “Mummy, let her be if bata son

tafiya,Najwa zaki bi su Hajjo?” Da sauri ta

Girgiza kai Alamun Aa, yace “Oya zauna

abunki” da sauri ta zauna, Mummy ta buga

tsaki ta shige toilet, Majeed ya maida

dubanshi ga Ziyada yace “Zuzu, Monday zaki

fara Zuwa Northwest University, i’m sure

zakiga a lot of changes, na san baki saba

Schooling a irin Makarantun ba, not like your

Base University” Murmushi tayi tace “I dont

Mind at all YaMaji, Allah ya saka da Alheri

Amin”. Sosai yaji daidi yace “i’m proud of

you”.

Ya maida dubanshi ga Najwa dake wasa da

yatsun hanayentayace “Ina wayanki?” tace

“Uhmm?” Yace “Uhm”tace “yana Gida” “ba ki

mayi amfani dashi ba ko?” “Eh nasa Charge”

Ziyada tace “ina zata iya amfani dashi bayan

she spent the Whole day Crying, in ka ganta

jiyan nan sai ka tausaya mata, ta shiva

damuwa sosai, ta k’i barin k’ifar dakin nan,

binibini sai ta lek’a ta Window taga ko ka

farfado, da akace ka farfado kuwa murna

kamar tayi mene, da Mummy ta koramu Gida

tayi kuka taso ta kwana fa, tsakar dare ina

ganinta tana Sallah tana cewa Allah ya sa

karka mutu, hahaha Adduar da ta yi tayi

kenan a baiyane, Allah ka sa Ya Majeed kar

ya mutu” kunya ya lullube Najwa, ashe

kowa ya san kalar damuwan da ta shiga?

Nana sai binta take tayi da kallon tsana,

Majeed ya dinga jin wani irin abu na ratsar

shi, ya tsura mata ido, ganin bece komai ba

ya sa Najwa dagowa ta kalleshi, karaf suka

hada idanu, ta so dauke kai sabida wani

kwarjinin da ya mata, amma ya datsen

kallon yanda ba zata iya dauke ido daga

nashi ba, da ido ya mata alamun ta zo

wurinshi, a hankali ta tashi, taji kafarta ya

mata nauyi, da kyar ta k’arasa har gabanshi,

kanta a k’asa, Murmushi yayi mata, cikin

k’asan mak’ogaro yace “have you been

Eating?” da sauri ta daga kai ta kalleshi yace

“kin rame, ki dinga cin Abinci, ina so idan na

maida ma Maama ke tace kinyi k’iba” bata

san lokacin da ta fashe da dariya ba, Ziyada

ta kallesu tayi Murmushi tana raya wani abu

a ranta, Nana ta buga tsaki tace “sai ki

samu wuri ki zauna kin ma mutane tsaye a

ka” da sauri Najwa ta koma wurin zamanta

ta zauna, Majeed bece da Nana komai ba, ya

dai so ta kalleshi ya tabattar mata “da cewa

komai zai zama daidai” amma ta k’i dagowa

balle ta kalleshi.

Mummy ta fito daga toilet, tace “Yaro kaci

Abinci mana, da kaina na dafa maka, Taliya

kake so ko Shinkafa?” kai ya girgiza alamun

“aa” yace “bana jin cin komai Mummy” tace

“OK, ka gaya min in kaji Yunwa kaji?” kai ya

gyada mata” ya maida kai ya kwanta, kusa

da Ziyada Mummy ta zauna, ta na jan

diyarta da firan Amjad, don daga Nanan har

Najwan haushi suke bata.

Sallamar Daddy da Hajia Ainau ya

ratso kunuwansu, duk suka zuba ma k’ofar

shigowa Ido, Daddy ke gaba, sai Hajia Ainau,

sai wata yarinya rik’e da kwandon basket,

Gaban Mummy ya yanke ya fadi kamar taga

fatalwa, yanayin da ta gansu sun shigo suna

fara’a kamar wasu maaurata, Najwa da

Ziyada suka amsa sallamar, Mummy ta fara

huci kamar Jirgin da zai tashi sama, Aunty

Aynarh ina wuni? Cewar Ziyada da

Murmushi, duk miskilancinta bata ma Hajia

Aynarh, Matar da ke zuwa Abuja don kawai

taga ‘yayan Daddy? Hajiya Aynarh tace “dont

stand there, come and give me a big hug” da

sauri Ziyada ta k’arasa gun Hajia Aynarh ta

rungume, Daddy sai faraa baki kamar gonan

Auduga, duk da bata san Najwa ba amma

taga tana kama da Alhaji Sada, itama bude

mata hannu tayi alamun itama tazo, tasowa

tayi cike da kunya ta rungume Aunty Ainau,

tace “wacece Wannan?” Daddy yace “Najwa

kenan, Bak’uwad Majeed ce” Hajiya Ainau

tace “Allah Sarki, kamar Jinin Marigayi” be

gane Marigayin da take nufi ba sai kawai

yace “Eh haka fa” cike da Kissa tace “Hajia

Mairo ashe Yarona beji dadi ba?” Mairo ta

fara kumfan baki, Hajia Aynarh ta murmusa

a hankali daidai yanda Mairon kadai za tajita

tace ” sai haushi kikeyi kamar karya” a fili

tace “Haba, ba kya ganin Yarona na bacci,

be fa da lafiya, ke kullum muka hadu sai

kinyi ihu, to Allah ya baki hakuri”. Hajiya

Aynarh ta k’arasa inda Majeed ke kwance,

Nana ta kalleta tace “Sannu” bakin harara

Hajiya Aynarh ta wulla mata, bata amsa ba

ta kai hannu goshin Majeed, a hankali

Majeed ya bude Ido ya zubeshi kan Aunty

Aynarh, Murmushi yayi yace “Aunty” tace

“yarona ya jikin?” cike da shagwaba yace

“naji sauki Aunty kice su Sallameni” Nooo

boy, ka kara hutawa, har sai BP dinka ya

gama sauka ko?, hakuri zakayi, kaci Abinci?”

a hankali ya gyada kai alamun “aa” tace “har

past to1? Aa ba zan yarda ka zauna da

yunwa ba” ta juya da sauri, ganin Najwa ta fi

kusa da Basket din da Gloria ta ajiye ya sa

ta cewa “Baby na, dauko min Basket din nan,

kizo ki zuba mishi Amala” ta kalleshi tace

“da kaina na Tuk’a maka, na san kanaso,

zakaci ai?”. Kai ya daga alamun “eh”.

Start from the beginning

Shikenan, abun ya gama kashe Mairo, tun

zuwan Hajia Aynau ta tsaya sandare kamar

an dasata, anya matar nan ba da Jinin

Oduduwa take tsafi ba? Ji yanda kowa ke

sonta, ji bakin Daddy, ji Ziyada, ji Majeed din

da yanzu yace mata ba ya jin Yunwa, amma

daga zuwanta ace zaici Abincin Yarbawa,

wai Amala, muryan Hajia Aliya ta tuna inda

take mata gargadi *”Wallahi Mairo kashinki

ya bushe in Ainau ta shigo Gidan nan,

Yarbawa? Ki raba kanki da kishi da

Bayarabiya, Wallahi sai kin raina kanki, don

su wuce tunaninki, Mugun yaniska ne,

matsafa, kaf zata siye Mijinki da Yaranki kaf,

duk su dawo karkashin ikonta”* da k’arfi

Mairo tace ” Inaaaa Sam, ba zan yarda ba,

na fi k’arfinki Ainau, nafi karfin ki bakar

Matsafiya, kurwa na da na Iyali na kur, ba ki

isa ba wallahi, kinje kinyi barbade zaki kawo

ma Yarona Abinci ki shanyeshi ko? Wallahi

karyanki ya sha karya” Hajiya Ainau ta san

ta gama kashe Mairo da kissanta, ta kara

mariaraicewa tace “Abba, lafiya? Me take

cewa is she Alright? Mairo abun ya fara

tsumata, da sauri ta yo kan Hajia Ainau,

Daddy yayi saurin shan gabanta, ya jata

suka bar dakin, daidai yanda Mairo kadai

zata ganta, Hajia Ainau ta ciro halshe tana

mata gwalo, Mairo ta k’ara tsurewa, Daddy

ya ci nasaran fiddata waje, Ziyada ta bi

bayanta.

Da k’yar Daddy da Ziyada suka sa Mummy a

Mota, ita sai dai a barta ta je ta ma Hajia

Aynau dukan tsiya, wai ta shigo rayuwarsu

ne don ta hallaka su, ta ma Daddy Asiri yana

binta kamar rakumi da akala, ita ba zata

yarda ba, Hauka Mummy tuburan keyi wanda

Daddy ya lakanci hakan da Kishi, da abun

yayi yawa sai da Ziyada ta fashe da kuka

kafin Mummy tayo shiru, a haka suka isa

Gida.

Majeed ya girgiza kai yace ” Ki Kara hakuri

Aunty kinsan halin Mummy” tace “kar ka

damu, abunda takeyi be taba damuna ba,

Baby dauko abincin, mana, kin tsaya kina

kallo like a cartoon” ta karasa maganan tana

zolayan Najwa, Najwa ta murmusa ta dauko

basket din tana tafiya sumi sumi, “Oya zuba

mishi, serve him” Najwa ta bude coolers din,

taga abu bak’i” yanayinta ya sa Hajia Ainau

gane bata san meye wannan ba, tace “baby,

baki san meye wannan ba ko?” tace “Nasani,

bak’in tuwo ne” hahah suka fashe da daria,

Amala sunan shi,Majeed ina ka samo ‘yar

kauyen nan?” yayi Murmushi yace “chan

kauyen Dubai” sukayi daria, Hajiya Aina, tace

“ahh yar gayu ne, noway zata san Amala,

Oya zuba mishi Miya din, Iwedu ne, kisa mai

Gbomo din da yawa” kamshin ya bugi hancin

Najwa, sai taji tana son ci, mik’a mishi plate

din tayi” Hajia Ayna tace “Aa, dont be a lazy

girl na, feed him joor” Najwa ta daburce,

wani irin shauk’i ya shigeta, da sauri Nana

ta yi yunkurin karbe Plate din, Hajia Aynarh

ta galla mata harara da baki tace “Dont

touch my plate” Nana tace “haba meye

haka? Nice fa matar shi? Ya zakice ma

wannan karamar yar iskar tayi feeding dinshi

bayan his wife is here, this is not right”

Kallon Zakici Ubanki Hajia Aynau ta ma

Nana, nan da nan Nana ta shiga taitayinta.

Majeed ya murmusa yace “Najwa bani plate

din, i can eat by myself” da sauri Najwa ta

ba shi plate din, ya karba, tsaki Nana ta

buga ta suri jakkarta ta fita daga dakin ranta

bakirkirin.

Da spoon ya fara ci, duk da bakinshi ba taste

amma yana jin dadin Amalan, yaci Gandan

da yake da laushi kamar tsoka, Najwa ta

k’ura mai ido, tana kallon yanda yake jin

dadin Amala din, tana hadiye miyau. Majeed

na lura da yanda take hade miyau ya

murmusa yace “Najwa, ki zuba kici” da sauri

tace “No na koshi” Hajiya Aynarh tace dont

be silly girl, ki zuba kici” a kunyace ta zuba,

tana zaton ba zata iya ci ba, amma tana

sawa a baki taji wani irin dadi, mara

misaltuwa, tunda tazo Nigeria bata taba

k’oshi kamar na yau ba.

Hajiya Ainau ta na nan har dare, da zata tafi

ta ba Majeed 50k. Har bakin Mota Najwa ta

rakata, kafin ta koma Daki daga ita sai

Majeed ghen ghen.

*

“Oya come and sit here” ya mata nuni da

kusa dashi, cike da kunya ta k’arasa gun, ta

zauna, sun dade suna kallon Juna, suna saka

abubuwa da dama a zuciyoyinsu kafin

Majeed yayi magana “ashe kin damu dani

haka? Kina ta kuka? Eh Najwa”tace “uhm?”

yace “Uhm” tayo shiru ta sadda kanta k’asa,

cikin murya kasa kasa yace “bana son

kukanki, alot of times in Mummy ta saki

kuka inaji kamar nayi hauka, bana son kina

kuka, bana so in maida ma Maama ke tace

hawayenki ya k’are” tayi daria yace “Always

Smile, Be happy kinji Pure Heart?” ta dago

kai da sauri ta kalleshi ya kashe mata ido

daya, da sauri ta kawar da kai tana blushing

yace “yes, kinji ni da kyau, i just called you

Pure Heart, i named you pure Heart because

you have a Pure and beautiful Heart Najwa, i

like it keep it up”. Wani irin abu taji daga kan

kanta har zuwa yatsun kafanta, bata san ko

meye ba, ba ta san ya zata sa abun ba,

kawai ita dai taji wani iri, ta kuma kasa

barin Murmushi.

Haka Majeed ya dinga janta da fira, tun tana

kunya har ta sake ta biye mai suka sha firan

da tun da tazo Nigeria bata taba irinshi da

kowa ba.

STORY CONTINUES BELOW

Har akayi Sallahn Isha’i kafin Mummy da

Fallalu suka dawo, Mummy ta galla mata

harara dama all this while tana tare da

Majeed? Ita ta kan manta da itama, Fallalu

ya kwashi Baskets din Abinci, zai tafi

Majeed yace “Fallalu tsaya ka tafi da Najwa”

Najwa tayi saurin tashi ta bi bayanshi tare

da cema Mummy “Good Night” Iskar da ya

debo Najwa Mummy ba ta kalla ba balle ta

sa ran Amsata.

BAYAN KWANA BIYU

Gaba ki dayan su zaune kan Carpet,

Majeed na zaune Kan Gado, shi Wallahi ya

gaji da Asibitin nan, ya fa ji sauki, kwana 4?

Ba fa abunda ke damunshi, dole yau Dr

Hisham ya Sallameshi, kullum kawai yan

gidansu sai dai su zo su tare a Asibiti kamar

Parlo? Ya gaji dole yau a Sallameshi, da

k’yar ya samu Mummy ta bashi wayanshi,

yana kunnawa sai ga waya an kirashi, “Hello

Aliyu Gadanga ah haba? Ya akayi ka san ban

lafiya, Ina Softie Hospital na Dr Hisham,

room 9, Okay Sai kazo”.

Mummy tace “wani Aliyu?” yace “Aliyu

Tijjani” “Allah sarki ashe kuna zumunci” yace

“Gaskia muna waya sosai, mu kan hadu

sometime” tace “ai tun biki da yazo Abuja

rabon da mu hadu” yace “yau zaki ganshi”

haka Mummy take, duk ta san Kawaye da

Abokan Yaranta, sai ta yarda da su suke

Abokantaka, Lokacin da Majeed na Turai

karatu, har chan take binshi don ganin

mutanen da yake hurda dasu, haka kurum

Mommy bata hada yaranta da kowa ba.

*

Sai ga Aliyu ya shigo bayan wasu yan

dak’ikai, a ka hau gagaisawa, ya dinga bin

Ziyada da kallo, yarinyan ga girma ta kara

kyau, haka ya karasa Gadon Majeed, suka

chafe hannu da Majeed, inji Majeed”Abokina

ya akayi ne, duk naga kayi cool abunka?”

Aliyu yace “hmm, Abokin sai a hankali, wai

me ke damunka na ganka gadon Asibiti, but

you look totally fine” Majeed ya bude Murya

yanda yan kasa zasuji shi yace “Kinji ko

Mummy, kice Dr Hisham ya Sallameni”

Mummy tayi daria.

Majeed yace “kasan abubuwan sai a hankali

stress ne ya min yawa”.

Aliyu ya jinjina kai ya na tausayin Abokin shi,

Majeed yace ” Wai ya kake min Kallon Abun

tausayi ne?” Aliyu yace “ai abun tausayin ne

kai Majeed” Majeed yayi daria yace “kaifa

dan iska ne, menene?” Aliyu yace “hmm, so

kake in kara tara ma gajiya? Kana fama da

stress? Bari dai sai kaji sauki” duk da

gabanshi na faduwa, be san da me Aliyu

yazo ba, amma ya samu karfin guiwan sonjin

me ke tafe da Aliyun, don ya lura bakin shi

akwai magana Majeed yace “haba abokina,

gaya min ya akayi ne?”.

Aliyu ya ja numfashi yace ” kasan ina aiki da

Trust fund? So sai akayi hosting meeting a

tourist lounge Conference hall” Majeed yace

“Ehen nagane” “so bayan Meeting din ne, na

bi ta reception na kama ma wasu Clients

Daki, naga Matarka daga nesa, sai da na

duba Hoton dinner dinku a wayana kafin nayi

confirming itace, so i thought kuna tare ne,

sai na k’arasa gunta, na mata sallama nace

kamar matar AbdulMajeed Abu, hali da

yanayin da take ciki ne ya bani tsoro

matuk’a”. AbdulMajeed ya sauke Ajiyar

Numfashi yace “Hmm, cikin halin Maye ka

ganta ko Aliyu?” Aliyu yace “dama kasan

tana k’walewa?” Majeed yace “i thought ta

daina, ashe tanayi, she do drugs and all,

abun Nana sai ita, Allah ya shirya” Aliyu

yace “thats not all” Majeed ya zaro ido yace

“Aliyu, me takeyi a Tourist lounge?” Aliyu ya

zaro waya daga Aljihunshi yayi playing

recording din ya ba Majeed ya ji. Majeed

Murmushin takaici yayi ya lumshe

idanuwanshi ya bude a hankali, bakinshi na

maimaita “Inallilahi wa ina ilaihir rajiun” sai

da ya samu natsuwa ya cire baki yace

“Mummy” Hajia Mairo ta dago kai tace “yes

son” da hannu ya mata Alama da tazo, da

sauri ta tashi tana tambayanshi me yake so?

Wayar Aliyu ya mika mata bayan yayi playing

mata recording din, lokaci guda ta shiga

mummunan tashin Hankali, Allah yasa bata

goga maka wani mugun ciwo ba, ma shiga

uku ni Mairo, Daddy ya taso da sauri tare da

su Ziyada, Mairo ta mik’a musu wayar sukaji

sakin layin da Nana take tayi, duk suka dauki

Salati.

Ziyada tace “Mummy tun farko sai da Yamaji

ya gaya miki halinta kika ki yarda, you see

what you caused?” Majeed yace “I told you

so Mummy, i told you so” cikin tashin

hankali tace “this is not the time to blame

me, Daddy ka nemo Dr Hisham ya zo ya mai

awon HIV, dole ake ma Majeed test”. Da

sauri Daddy ya fita duk tsuka tsure suna

tararrabin me zai faru.

*

Bayan 2 hours sai ga Nana ta shigo dakin

Asibitin tana yauk’i, a dage take kallonsu,

saboda abunda Hajia Aynarh ta mata

shekaran jiya bata zo Asibitin jiya ba sai yau,

ko kallonsu batayi ba ta wuce ” straight

Gadon Majeed” Mummy zata tashi Ziyada ta

rike mata hannu, Daddy ya mata alaman da

abarta da Majeed.

“My Majeed ya jikinka?” Murmushi yayi yace

“Nana, na taba musguna miki? Ko na miki

hainci? Ko na cutar dake ta ko wani fanni,

daga Aurenmu zuwa yau?” ta kalleshi da

mamaki tace “me ya faru my Majeed?” yace

“ki amsani” tace “No, baka taba” yace “to

Alhamdulilahi, Nana kije na sauwake miki, na

sakeki saki daya, Nana na yafe miki da

abunda kika min Allah ya yafe miki, ki nemi

tuban Allah” ai bata gane me yake cewa ba,

cikin tashin hankali tace “Me kake cewa My

Majeed?” Yace “na sakeki saki daya” tace

“Kutumar, wallahi baka isa ka sakeni ba,

uban me na maka da zaka sakeni, auren

zobe mukayi mutu ka raba takalmin kaza”

Mari Mummy ta dauke ta dashi, tace “Mutu

ka raba dawa? Shegia yar iska, yar codein,

yar madigo, mazinaciya, kinji kunya, karuwan

Babanta, Hajia Sayluba anyi asarar haihuwa”

Mummy ni kika mara? Uban wa ya kala min

sharri?” Mummy ta wawuro wayarta, Aliyu ya

tura mata recording din, ta ma ta playing,

muryarta tace, amma bata san ta saki layi

haka ba, ranan she was super dozed off, sai

ta fashe da kuka, tana kururuwa wai sharrin

shaidam ne, a yafe mata ba zata sake ba,

amma kar Majeed ya rabu da ita.

Igiyar Charger din dake chargy Mummy ta

ciro, kafin kowa ya ankara sai jin ihun Nana

sukayi, Mummy ta daddage ta shandara

mata, Majeed yace “Mummy stop” ina

Mummy bata ji ba, Mummy ta cigana da

shandara ma Nana, duk yanda Daddy da su

Ziyada suka so hana Mummy amma abun ya

faskara, har sai da Nana ta arta waje da

gudu, Mummy ta bi bayanta, har kasa tana

zaneta, Mutane sai taruwa suke ganin ikon

Allah, kafin kace kwabo yan jarida sun zo,

kafin zuwa Polisawa, da k’yar aka kwace

Nana daga hannun Mummy, bayan Mummy

ta fallasa Asirin Nana gaban duniya don

playing recording din tayi kowa yaji, wasu

suka mata adduar shiriya, wasu kuwa suka

tsine mata, abu dai beyi dadi ba.

PH Nigeria.

Tsaki ya buga karo na ba adadi, ya san

zaman Nana zai k’are a Gidan Alhaji Abba,

amma beyi zaton abun zaizo da wuri haka

ba, yaso ta mishi task daya, wadda shine

final task dinshi,Mallakan Gidan da ta mishi

haka shi da kanshi zaiyi sanadiyar barinta

gidan, amma ta kwafsa mai, ta bata mai

Budget, komai na tafiya as planned, Nana ta

bata mai lissafi, ya sake sakin tsaki,

Amstrong na kallonshi, yanda ya ga Zaid ya

lumshe ido, a daura kanshi kan kujera ya san

cewa tunani Zaid yakeyi, tunanin mugunta

kuma, tunanin da Zaid yake ba Alheri bane,

what is he planning this time around, yana

kallon bakin Zaid na murmushi, yana ganin

yayi smirking yasan cewa ya sama ma

kanshi mafita, Zaid ya bude lumsasun

idanuwanshi, a hankali yace “its Time(lokaci

yayi)” Amstrong yace “time to what boss?

(lokacin men)” “its time i meet them face to

face(lokaci yayi da zamu hadu gaba da

gaba)” Kano here i come, cant wait to see

my Uncle, my cousins and above all my Evil

Uncle’s Wife, i’m coming for you all”.

Amstrong yace “what are you planning? Me

kake shirin yi?” How will u meet them face to

face?ta ya zaka hadasu da su gaba da

gaba?” Zaid ya murmusa ta gefen kumatun

shi yace “i’m going to live with them(zan

zauna tare da su), in their House(a cikin

gidan su), My House(Gidana)”.

°°°°°°°°°°°°°°°

Bibilicious freaking fans, We have a newest

Member in the Family, Who’s Excited? Whats

Zaid planning? How? Ku biyo ni dai.

Shikenan Zaman Nana ya kare? donAllah a

mata hakuri a dawo da ita, don nasan akwai

™Majeedholics fans, suna so suyi ma

Nanarshi snatching, sha ba hope, Mairo ta

kasa ta tsare, sai tayi screening Next

Matarshi, nasan lot of you are shouting

Najwa’s name, Najwa-Majeed?? not

happening, kuyi zeroing mind dinku, nothing

of such will happen lol.

Zaid a Kano? Me kuke tunanin zai faru a

gidan nan?

Theres a fire on the Mountain run run run.

Mutane na na Niger, na ji sak’on ku,

InshaAllah idan na saka turanci me wuya zan

fassara da hausa a bracket, da na iya french

da na saka lol.

Wattpadians, show me love please. Vote and

comment line by line.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreaking

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣3⃣

* KANO*

Kanshi Yayi zafi, ranshi na k’una, ina ma

mafarki yakeyi, ya san Nana ba natsatsiya

bace, yasan halaiyar Nana tun kafin Aurensu,

amma beyi zaton har yanzu tana yi ba, yayi

zaton Aurenshi zai sa ta bari, ashe na haka

bane, abun nata har ya cigaba, tabi maza

tabi mata, kai Inalillahi wa ina ilaihir rajiun,

ya na jin hayaniya a waje, be ma da k’arfin

tashi balle ya lek’a wainar da suke toyawa a

waje.

*

Ita Asalinta bata son tashin hankali, tuni ta

soma hawaye, bata taba ganin irin tashin

hankalin nan ba, garin irin tashin hankalin da

Mummy keyi a waje, har ‘yan Media sun

hallara wuri ya cika, Daddy na hana Mummy

wasu abubuwa, su Ziyada hankali tashe, taji

ita ba zata iya cigaba da kallo ba, zame

jikinta tayi ta koma dakin da Majeed ke

kwance, zaune yake, amma kallo daya ta

mishi ta san cewa hankalin shi be tare da

shi, a hankali ta taka har gaban Gadon da

yake zaune, a hankali ta furta “Ya Majeed”

kai ya dago firgigit, “pureHeart” ya furta a

hankali, ba wai taji abunda yace bane, aa

bakinshi kadai ta lura da abunda yace.

Girgiza mai kai tayi tace “Dont hold it, cry,

kayi Kuka Ya Majeed” kamar ko Umurnin ta

yake Jira ya fashe da Kuka, har jikinshi na

rawa, tausayinshi ya kamata, tayashi kuka,

kusan mintun su 9, kafin Majeed ya tsaida

hawayenshi ta hanyar gogewa da bayan

hannunshi, ya kalleta yace ” PureHeart, kukan

ya isa haka” yana k’wak’ulo murmushi, da

sauri ta tsaida nata hawayen ta janyo kujera

ta kafa kusa da shi gaban Gadon.

Ba tare da ta bari sun hada ido ba, cikin

sanyi murya ta fara “so da yawa Allah na

jarabtar mu da abubuwa kalakala, ba don

komai ba, sai don ya gwada imanin mu, ya

ga shin zamu rugumi kaddarar da ta zo

mana? Zamu yi questioning Allah’s

Judgement? Or zamu Fawalla ma Allah

komai, muyi moving on? I know there are

times da zaka ji you want to give up on this

life, sometimes zakaji kai komai ya fita a

ranka, amma dont give up, Allah yace ‘Ku

rok’eni, zan amsa muku’ so ina so ka dage

da Addua, Allah ya baka ikon cin taka

Jarabawar, kuma don hakan ta kasance da

kai, kace ba zaka k’ara yarda da Mace ba,

ko kace ba zaka k’ara aure ba, ba duka aka

taru aka zama daya ba, kawai kayi Adduan

Allah ya changing ma a better wife”.

Kur ya kafa mata idanuwanshi, kunnuwanshi

na sauraran duk abunda take cewa, zai iya

rantsewa kan be taba jin murya me dadin ta

Najwa ba, duk da Hausarta be fita duka, sai

yaji Hausarta ta mai dadi, kamar ta Yaro me

koyon magana, wani abu yakeji game da ita

da ba zai iya fassarawa ba, ji tayi yana

kallonta, ta gefen ido ta dan kalloshi, karaf

suka hada idanuwa, da sauri ta dauke nata

idon, cikin wani siga yace ” PureHeart,abun

is somehow, but i’m fine now tunda daman

mun san hakan na iya faruwa, kawai dai

mun sama ran mu Positivity ne, amma

nagode ma Allah, Allah shine abun godia da

ya fiddo halayen Nana a fili, ba kisan kalar

Drama din da akasha ba kafin na aureta, sha

its in the past, but yanzu ai gwara da Allah

ya baiyana mana true colors dinta ko?” shiru

tayi saboda irin yanda ya kafeta da idanuwa

yana jiran ta bashi amsa.

Bata ce komai ba, yace “Ehen, gaya min,

kince in rok’i Allah Allah ya chanza min Mata

kamar PureHeart kikace ko?” da sauri ta zaro

ido tace “ni bance kamar ni ba” ya dan dara

yace “kin yarda kece PureHeart dina?” kunya

ya rufeta, abunka da fara mace nan da nan

kumatun ta suka danyi Ja saboda dadi

wanda ya hade mata da kunya. Murmushi

yayi yace “Someone is Blushing” da sauri ta

sa hannu ta rufe fuskarta tana Murmushi me

sauti.

Banko dakin Mummy tayi Kamar wata

zararra, gadan gadan ta yo kan Gadon

Majeed, Najwa na ganin haka tayi saurin

tashi, Fadawa kan Majeed Mummy tayi ta

rungumeshi, tana shafan kanshi, Najwa tayi

hanyan fita k’ofar ta ba ma Mummy Baya,

don Majeed ke kallonta, Mummy na kallon

dayan barayin, yana rungume Jikin Mummy,

ya furta “*PureHeart* ” a hankali ta juyo, da

baki yace mata “I love you” daburcewa tayi

lokaci daya, bata taba zaton hakan daga

gareshi ba, kamar dazun fuskarta ya fara

blushing, har kumatun ta sunfi dazun ja, cike

da kunya ta fita waje, inda ta ci karo da su

Ziyada da sukayi tsuru, shikuwa sake

Rungume Mummy yayi tare da kwantar da

kanshi kan kafadunta.

Jin yace “i love you” Mummy ta fara

magana, a zaton ta da ita yakeyi, kamar

zatayi kuka “Boy, I’m sorry, ka yafe min, na

maka zabin tumin dare, kayi hak’uri, we are

getting yout Credentials back, na kira Dr,

yanzu zaizo ya maka test din HIV, boy my

son are you Alright?”.

Murmushi yayi, ya rik’o duka hannayenta,

yace ” I’m Fine Mummy, I’m totally fine” still

dai sai anyi Test dinnan, saboda tsaro,

yasan ba amfanin gardama da ita, sai ya

chanza magana yace “da anyi Test din zaa

sallameni, nagaji wallahi” tace “No, sai ka

k’ara kwana, bakayi 1week din da Dr yace

ba ai” yace “Noo Mummy, so kike dan

kudadden da suka rage mana su k’are a

gadon Asibiti? Duk kwana 25,000 fa, haba

Mummy, kar ki manta, Monday Zuzu zata

soma zuwa School, akwai abubuwan da nake

son siya mata, in ina kwance a nan me kike

tunanin zai faru? Zamu kwana mu tashi sisin

Kobo ba mu dashi, so please kice ma Dr naji

sauk’i ya sallameni” ta kalleshi cike da So

da k’auna, me tayi Allah ya bata d’a kamar

Majeed? Majeed Yaro ne da ko wacce Uwa

zata so Danta ya kasance kamar shi, ka sa

hakuri tayi sai da ta sake rungumeshi tace “I

love you too” dariya yayi a ranshi yace “that

one wasnt actually for you tho” a fili yace

“and i love you More, Mummyn Majeed”.

*****

‘PureHeart I love you’ sune kalmomi hudu da

kanta ke nanata mata, tayi murmushi a karo

na ba adadi, tayi lamo jikin bayan Motan da

Fallalu ke maidasu Gida, itama tana jin wani

abu game dashi, “but is this love?” sai

Murmushi take tayi har suka isa Gida, sai da

Hajjo ta tanka tace “Najwa, ko dai bushara

aka miki da Gidan Aljanna, wannan faraa

haka?” sai ta sa hannu ta rufe fuska saboda

kunya.

Cikin ikon Allah da aka gwada Majeed ba a

samu komai ba, he’s HIV-, hankalin Mairo ya

kwanta, aka sallameshi Washegari, suka

dawo Gida, hankalin kowa a kwance ganin

Majeed ya samu sauk’i, yanzu burinta ta

maka Nana Kotu, don ba zataci bulus ba

akan cutar mata da Da da tayi, ba ubam da

ya isa ya taba danta ya kwana lafiya, kuma

duk inda Takardun Majeed suke sai an fiddo

su ko da komai da ta tara zai k’are, ba ta

sanar da kowa k’uddirinta ba ta fara

gudanar da burinta, ragowan Kudadden da

ya rage musu harda wanda Hajia Aynarh ta

hada ta samo Lawyer, ta dangana da Kotu

Washegari aka kai Sammaci Gidan Alhaji

Nakowa Abuja.

A B U J A

Kwance take kan Cinyar Mom dinta tana

kuka mai taba zuciya, Dad dinta safa da

marwa yake, ranshi in yayi dubu ya baci, ya

rasa me ke mai dadi, cikin hargowa yace “Ni

Hajia Mairo zata ma haka? Ni? Ni zata

tozarta, wulakanta diyata da tayi be isheta

ba, har sai da ta makani kotu? Lallai Hajiya

Mairo da Iyalanta zasu gane shayi ruwa ne,

zan tona musu asiri, zan wulakantasu, zan

tozartasu” Hajiya Sayluba rai 6ace tace

“bayan duk hallacin da Nana ta musu, ta so

dansu tsakani da Allah, ta zabi zama dashi

duk da tasan basuda komai, ta rabu damu ta

bar daula ta bisu ta zauna da su cikin

talauci, amma itace abun k’ulla ma sharri da

mata k’azafi, bayan a yad’ata a social

media, yanzu kuma an kawo mana

Sammacin Kotu, kai cin fuskan yayi yawa,

Daddyn Nana kar ka barsu duka”. Nana na

shasheka tace “Mom, Dad, ba ruwan My

Majeed, Mummyn sa ne, please kar ku mai

komai, ku bashi hakuri ya dawo dani, i cant

live without him” ta fashe da kuka,

lallashinta suka hau yi, suna bata hakurin

cewa ta hakura da Majeed, ba za su iya

dawo mata dashi ba, kawai suyi focusing kan

Case dinsu na court kuma by all means sai

sunci, don daga Lagos Alhaji Nakowa zai

dauko Attorney.

PH Nigeria

Dadi yaji da labarin ya iso gareshi, a fili

yace”The Nakowa’s and The Abba’s are

against eachother? Intresting(da Iyalan

Nakowa da na Abba suna ganin Hanjin

Juna? Abu yayi dadi)” Amstrong yace “what

are you planning Oga(Shirin me kakeyi?)?”

Zaid ya Murmusa kawai, ba kasafai yake

furta abunda yake shirin yi ba, ya fiso a ga

Action kawai, a ranshi yace;

‘zan bari su fafata a tsakaninsu, me kudi

shike Nasara a k’asar nan, idan Alhaji

Nakowa ya gama dasu Hajiya Mairo, nikuma

zan cigaba daga inda na tsaya, yanda

breaking dinsu ba zai min wuya ba’

Amstrong ya bishi da ido, yanda Zaid ke

lumshe idanuwa ya san cewa wani muguntan

yake kullawa, Zaid ya san lungu da sak’on

Mugunta, ya sake tambayarshi kan shirin me

yakeyo, sai Zaid ya shashantar da maganar

ta hanyan cewa “Get me an Appointment

with Rita Phillips” da mamaki Amstrong yace

“Rita Phillips why?” murmushin Mugunta

Zaid yayi yace “I need me a Makeup Artiste”

da mamaki Amstrong yace “Why?” Zaid ya

fashe da Daria yace “Watch the Master and

learn” ya zaro wayarshi ya latso wata

numbern a wayarshi, ba zai iya tuna ranan

da ya kirata da hannunshi ba, amma yanzu

da yake bukatar hakan ya taso, dole ya

kirata.

*

Tana kwance tana dogon tunani, anya akwai

asararriya a duniyan nan kamarta? Ta

banzatar da rayuwarta ta kan Namiji daya,

ba don Azzikinshi ta ke sonshi ba, sonshi

take tsakanin ta da Allah, tana Aji Biyu a

France, da zai dawo Nigeria saboda sonshi

ta bar karatun ta na chan ta dawo UNIPORT

don kawai ta kasance tare dashi, gashi shi

be son iskar ya debota ba, kwatakwata be bi

takan ta, tana cikin wannan tunanin ne

wayarta yayi ruri, kamar ba zata daga ba ta

duba, ganin me kiranta ya sa ta daka wani

tsalle tare da kafan wayan a kunne

“Hhhello?” muryar da tafi ko wanne dadi a

gurinta taji yace “Na’eelah” cike da shauk’i

tace “Zaid” yace “Errhm, kin tuna lokacin da

kikace idan ina son wani abu a wurinki in

gaya miki?” da sauri tace “Eh, ka gaya min

ko meyene, nikuma zan makashi with all my

Might” ya murmusa kamar tana gabanshi

yace “This is somehow complicated” tace

“kar ka damu i’ll do it, anything for you” ya

gaya mata abunda yake so ta mishi, ta danyi

jim tace “idan na maka haka zaka aureni?”

kai tsaye yace mata “Aa, amma zanji dadi

idan kika min hakan” taji ba dadi, ta so tace

ba zata iya abun da yake so tayi ba, amma

ta na son Zaid, his happiness comes first, a

hankali tace “Okay, I’ll do it” murmushi yayi

yace “Good, comeover now” ya kashe wayar,

Naeelah ta jima zaune, tana mamakin Izza

da nuna isan Zaid, ita zata mishi abu amma

not even a thanks, tashi tayi ta gyara jikinta

ta fita don zuwa gidan Zaid.

KANO

Tun Sallamar Majeed daga Asibiti, suna

zaune lafiya da junansu, saboda Majeed

Mummy na kawar da kai bata kyara da

tsangwaman Najwa, bayan idonshi tana

harararta da hantararta. Tun a Asibiti Najwa

bata sake bari sun kebe da Majeed ba, sai in

sun hadu a Parlor, shima gaisheshi takeyi ba

tare da ta kalleshi ba, saboda wani irin

kunya da yanayin da takejin kanta a duk

lokacin da suka ke6e da Majeed.

Da daddare Zasu hadu gabaki daya su ci

Abinci, Mummy ke dafawa, bak’in cikinta ta

dafa Abinci Najwa taci, da ta lura Najwa bata

son Kifi, sai ta dinga yin Abinci da Kifi, Najwa

ko da taga Abinci da Kifi sai tak’i ci, sai tace

ta k’oshi, sai Majeed yace “me kikaci? barin

dafa miki Indomie” sai Mummy tayi saurin

cewa “haba, barta ta dafa da kanta zata fi

jin dadinshi ko Najwa?” sai ta gyada kai ta

shiga Kitchen ta dafa Indomie dinta, Muhsin

yace “Ya Najwa, me zai sameki in kika ci

Fish?” tayi murmushi tace “I will fall sick”

Muhsin ya kalli Mummy yace “Mummy, ki

daina abinci da Fish, Ya Najwa will fall sick

idan taci fish kinji Mummy?” duk suka kafe

Mummy da ido suna jiran me zata ce, Yak’en

dole tayi tace “na bari” har ran Majeed yaji

dadi.

A ranta ko ta aiyana sai ta sa kifi yanda

Najwa ba zata gane ba taci ta ga me zai faru

da ita, yarinya sai shegen Iyayi, wai bata iya

cin Kifi, Washegari da rana tayi abinci da

Man Kifi, ba zaka gane ba in har ba gaya ma

akayi ba, sun hadu gabaki daya zasuyi lunch,

two spoons kadai tayi numfashinta ya fara

daukewa, Majeed ya fara lura da ita, “Najwa

are you Ok?” duk hankalinsu ya dawo kanta,

cikin shesheka take cewa “abin abinci, ki-fi”

Majeed ya tashi da sauri ya tsiyayo juice ya

bata tasha, Muhsin rai a bace yace “Mummy

kinyi Abinci da kifi?” baki na rawa Mummy

tayi karya tace “aa, banyi ba, da kun gani ai”

“YaMaji mu tafi Asibiti” cewar Ziyada, Daddy

yace “she needs a first Aid treatment” kamar

zata shide ta fara magana a hankali,

“FresssshTomato” Majeed yace “me kika ce?”

da kyar ta maimaita, da gudu Ziyada ta

shiga kitchen ta dauko Tumatir guda biyu,

Majeed ya Amsa hannun Ziyada, da bakinshi

ya fasa tumatirin ya kafa mata a baki, ya

juye mata ruwan tumatir din a baki, ta dinga

tsotsa, haka ya fasa dayan ya juye mata, a

hankali a hankali numfashin ta ya fara

dawowa daidai, Daddy yace “Muje Asibiti”

tayi murmushi ta girgiza kai tace “i’m fine

Daddy” “are you sure?” “Eh, ba wani abu,

dama idan haka ya faru dani, Tomato

Maama take bani, dana sha sai in dawo

normal” Hajjo ta jinjina kai tace “haka fa

mutum zaiji beson wannan abincin, kamar

Sada, shima beson Kifi” Damm gaban Mairo

ya fadi, ya akayi Hajjo ta iya furta sunan

Sada?hakan na nufin ta iya tunashi? Shin

Abba ma ya tuna? Kafin kowa ya fahimci

abunda Hajjo tace tuni Mummy tace “bari a

dafa maki Indomie Najwa” duk da sunyi

mamakin sudden change din Mummy amma

ba su ce komai ba” Najwa tace “No Mummy,

sai anjima, yanzu i lost taste” ta tashi ta

wuce daki duk suka bita da ido, Majeed ji

yake kamar ya bita, duk yabi ya damu,

wannan shi ake kira da reshi ya juya da

majuyi, tayi don kuntata ma Najwa, gashi ta

k’are da k’untata ma yaranta don har fuskar

Zainee ta karanci Damuwa.

*

Hajjo tayi ja ta k’ara kyau abunta, tana

samun kula yanda ya kamata, duk da

Mummy bata gama sakewa da ita ba, amma

jikokinta na sonta, don har Zaineema na

zuwa dakin ta zauna ta dinga jin firarsu da

Ziyada in kadaici ya isheta, Zinatu ce dai ba

ruwanta da Hajjo da Najwa, Jiya ma Aunty

Ainarh ta kawo ma Hajjo Garan Abinci,

tuwon shinkafa miyan Kubewa danye sai

Farfesun Ganda, Hajjo tayi ta shi ma Aynarh

Albarka, abunda ya kashe Mairo ganin duka

yaran Gidan sunci Abincin Hajia Aynau,

bakinciki kamar ya kasheta.

Wasan buyan da suke da Najwa ya fara

damun Majeed, aika Muhsin yayi dakin Hajjo

yace “ka karbo min Wayan Ya Najwa” da ya

isar mata da sakon ta tashi ta dauko wayar

ta bashi, Wayar da tunda aka siyota bayan

tayi charging ta saka a drawer, ba kwanciyar

hankali lokacin Majeed na Asibiti balle ta kira

Maama, ta so kiransu yau amma tasan ba

kudi, kuma ba zata iya rokon kowa ya sa

mata Kudi a waya ba.

Majeed ya duba wayan ya ga batayi komai

dashi ba, waje ya fita ya mata activating Sim

din ya mata recharging da katin 1500, ya

mata saving Numbers din yan gidan, harta

Whatsapp sai da ya mata logging.

*MONDAY*

Yara sun tafi Makaranta, Daddy ya fita ‘yan

bugabuganshi, Mummy ma ta fita wurin

Lawyer dinta, har yau bata sanar dasu

Majeed kan cewa ta kai su Nana kotu ba, ta

bari sai ana gobe zaa shiga Kotu sai ta gaya

musu don kar yanda zasu sa ta janye k’arar.

Zaineema kamar kullum tana daki tana

kwance, Hajjo itama na daki tana jan chasbi,

Ziyada ko Majeed ya tafi kaita School

kasancewar yau zata fara karatu a

NorthWest University.

Najwa ta dauki wayarta, ta zagaya

boysquaters, ta ja dogon numfashi kafin ta

furzar, dialing numbern Paapa tayi, ringing

uku ya dauka.

I N D I A

K’afar shi da sauk’i, suna dai Asibiti ba a

sallamesu ba, duk abubuwan duniya ya

damesu ya ishesu, ko wannensu karfin hali

kawai yakeyi don karfaffa ma danuwanshi

guiwa, suna zaune a dakin Gadon Asibitin

jugum Wayar Paapa tayi k’ara, jone yake a

Chaji, Maama ta tashi ta cire wayar daga

charge, tana ganin numbern +234 location ya

nuna Nigeria ne tayi saurin dauka ba tare da

mik’a ma Paapa wayanshi ba.

“Hello, Najwa beta” zumbur Paapa ya tashi,

shima yana kiran “Najwa” Maama na jin

hucin numfashinta a kunnenta, tayi amanna

Murmushi Najwa keyi, cikin sanyin murya

tace “Maama” a tare suka fashe da kuka,

nan aka shiga labarin yaushe gamo.

K A N O

Maama ta dauki wayar, “Hello Najwa Beta”

hawaye suka fara suntiri a idon Najwa, yanda

Maama tayi maganan kamar dama tuntuni

wayarta kadai suke jira, ba su san ko waye

ba amma tana dauka ta kira sunanta, cike da

doki tace “Maama, i’m so sorry, na san na

saku cikin damuwa, ku yi hakuri, wallahi

abubuwa da dama ne suka faru, shiyasa

kuka jini shiru, please Maama kuyi hakuri”

Kuka Mama ta fashe dashi, tana jin kukan

har ranta, Maama tace “Najwa, are you

Alright? Ina fatan lafiyar ki lau, ki gaya min

diyata” “I’m fine Maama, ina Paapa?” He’s

fine saidai- ji tayi an karbe Wayan, “Hello

Najwa” a hankali tace “Paapa, are you OK?

Are you taking care of my Maama? Kuyi

hakuri na barku without a word, i know you

are sick worried about me, a Airport ne nayi

loosing Everything” nan ta labarta musu

abunda ya faru, suka jajanta mata, abu beyi

dadi ba, Maama tace “Najwa, kina ina

yanzu?” Najwa tace “Ina Kano” ba wai don

sun tuna ina ne Kanon ba tace “Kano a ina,

gidan Wa?” “Erhhmm Gidansu Majeed da

Ziyada, shi Majeed din ne ya taimakeni”

Paapa tace “you need to be very careful,

zamuyi processing yanda za mu turo miki

kudin jirgi ki dawo India, you’ve been away

for long, we cant handle it”.

Baki na rawa Najwa tace “Paapa Ya Zaid din

fa? Ban ma fara fita nemanshi ba fa, Paapa

ku dan karamin lokaci, i need to find my

brother, haba nasha wahalan da ba zan bari

wahalan ya tafi a banza ba ba tare da na

hadu da Brother dina ba” Maama tayi karaf

tace “wahala Najwa? Wace iri? Me ya faru

dake? Are you Alright?” ta katseta da sauri

“Maama stop overreacting, bansha wahala

ba fa, kawai i mean i cant stop now after all

that has happened, ina ji a raina na kusa

ganin Yayana, in nace zan dawo yanzu ai

komai ya tashi for Nothing, afterall thats why

i’m in Nigeria, to find my brother, i cant stop,

atleast not now, Maama kuyi hak’uri ku

k’ara hakuri,ku tayani da addua ba zan dawo

India ba sai da Yayana, i dont know how,

but a raina ina ji i’ll see him soon, this my

Number, zamu dinga magana time to time,

and yes I need that money, ku tura mun

kunji, I love you so very much, Maama

Paapa, i miss you” ba ta bari sunyi magana

ba ta katse wayar. Dadi ya rufeta, sai taji

kamar an sauke mata nauyin shekara da

shekaru, tayi magana da Mahaifanta,

farincikinta suna lafiya, ba abunda ya

samesu, yanzu zata jira su tura mata kudi,

ta fara binciko Yayanta, ta koma k’asarsu,

su zauna as one big happy Family, ta share

hawayenta, tana juyawa wa zata gani?

Majeed ne tsaye da hanayenshi biyu

rungume a k’irjinshi, da alamu duk maganar

da ta gamayi a waya da da mahaifanta akan

kunnuwanshi, a ranshi yace “ta min k’arya,

tazo Nigeria neman Yayanta ne, meyasa

zata min k’arya? Bata yarda dani bane?”

Iyakar rudu Najwa ta shiga tuni jikinta ya

fara rawa, bude baki tayi zata mai magana

ya daga mata hannu alamun ta dakata, jiki

ba walwala yace;..

°°°°°

Bibilicious freaking fans, ya kuke, ya jirana?

Lol, i’ve missed you sosai, hakurin zan

cigaba dai da baku, wannan page din bezo

muku kamar yanda kuke tsamanni ba, amma

kar ku manta sannusannu bata hana zuwa,

next page abunda kuke tsammani zai

faru,kun sani ai? ko sai na fada? Ok

Haduwan Zaid da Abba Abu’s family.

Ya zaa kare a Kotu tsakanin Mairo the

Dragon (lol) and Family din Nakowa? Wa

zaici nasara a tsakaninsu? Guess

Wai shin Me Zaid ke Planning? Makeup

artiste? Seriously? Me zaiyi da makeup

artiste? Any guesses? Ehen meyace Na’eelah

ta mai?

And Majeed? Ya fara son Najwa, amma ya

gano Makaryaciya ce, shin zai sake yarda da

ita kuwa? Zata kare kanta? Ko kuma wani

karyan zata shirga mai?

Heheheh Nextpage will come soonest, i

promise, just bear with me please

Vote, Comment and Share.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣4⃣

Daga hannunshi yayi alamun ta dakata, bude

baki ta sake yi da niyyan yin magana ya

katseta ta hanyar cewa ” shhh PureHeart, kar

kice komai” idanun ta ta kyafta so biyu a

kasalance tace “Yes i lied to you, na maka

k’arya, kayi hak’uri, zan gaya maka” girgiza

kai yayi yace “Kowa na son Privacy, i respect

Privacy alot,musanman Family Issue, so kar

ki damu, ba sai kin gaya min ba I

understand” ya juya bayan ya sakar mata

murmushi me sanyi.

Har ya fara tafiya, ta girgiza kai ta bi

bayanshi tare da cewa “Nazo neman Yayana

ne, tunda nake ban taba ganinshi ba” chak

Majeed ya tsaya kafin ya juyo, cikin yanayin

da ya fi kama da rashin yarda yace “What?”

a hankali ta tako har gaban shi ta cigaba;

“Asalin Parents dina ‘yan Nigeria ne,

Unknown reason ya sa su komawa India,

kafin tafiyarsu, sun bar Yayana da yake

Makaranta, kuma they couldnt come back for

him, so an haifeni a India, na girma a India”

Majeed cikin rashin fahimtar abunda take

cewa yace “Bangane ba PureHeart, me kike

cewa?”.

“Iya Sani na, Mahaifana na son zuwa Nigeria

neman Yayana Zaid, sun rabu dashi yana da

shekara 11, a duk lokacin da sukayi shirin

zuwa Nigeria, wani Badluck zai faru dasu,

har su kasa zuwa, A kullum Maama na cikin

Kuka, muna da komai amma rashin

Danuwana na sata cikin damuwa, farincikinta

ragagge ne saboda rashin shi” Majeed yayi

shiru yana nazarin maganganunta kafin yace

“Me kike nufi da ba zasu iya zuwa Nigeria

ba?” dogon numfashi Najwa taja kafin ta

sake tace “its kinda complicated, but you see

tun bayan barin su Nigeria, they cant

remember anything about Nigeria, they dont

even remember the State they are from, all

they could ever remember is that they are

Nigerians, and they left their Son in some

Boarding house(abun na da dan mamaki, tun

barin su Nigeria, suka mance komai, ba sa

iya tuna komai, ko garin da suke sun manta,

su dai sun san yan Nigeria ne su, kuma sun

bar Dansu a Makarantar Kwana).

Kan Majeed yayi nauyi da Zafi a hankali ya

furta “Sihiri” da sauri Najwa tace “Exactly,

haka Aisha ta fada min, maybe someone is

jealous of them or something” Majeed yace

“it can be anything” Najwa ta gyada kai da

ta lura ya fahimceta “An haifeni na tashi a

India” “how comes kika iya Hausa?” tayi

murmushi tace “Well na tashi naga su

Maama na hausa, a gida is hardly muyi

Indianci ko Turanci” Majeed ya Murmusa

yace “basu manta aladarsu ba”. Murmushi

tayi sannan ta dan chanza fuska tace “tunda

na fara Wayau nake ganin Hawayen Maama

na ta dalilin Rashin Danuwana, Alwashi na

dauka, sai nazo Nigeria, sai na share mata

hawaye, sai na nemo Yayana, ba don na san

ta inda zan fara nemanshi ba, bansan inda

zan dosa ba wurin nemanshi, k’udiri daya ne

a raina, zan nemoshi, zan ganshi, sai dai in

baya raye,no matter what da izinin Allah” ta

share hawayen da ta fara kafin ta cigaba sa

magana “i’m sorry na maka k’arya, i just

dont know who to trust, my first Day in

Nigeria was a Terrible Experience, kai shaida

ne, ina tsoron kar wani yayi amfani da

bansan kowa ba ya min mugun abu, maybe

saboda ni bak’uwa ce or something, but ka

yarda dani, nayi niyyan gaya ma gaskia,

yanzu ina iya cewa, bayan Paapa da Maama,

you are the one i trust the Most”.

Yayi murmushi mai nuna jin dadi sosai ga

maganar ta ta k’arshe yace “na fahimce ki

fully PureHeart, farkon haduwan mu naga

wautarki, har yanzu ina ganin wautarki, you

are so Innocent and Naive, some may call it

Stupidity, da hausa muna ce mai ‘sokonci’,

literally zan iya ce miki ke Sokuwa ce, i

mean wanene cikin hankalinshi zai dauki

Waya ya ba wanda be taba gani ba? Wa zai

yarda ya ba wani Akwatinshi da ke da

muhimman abubuwa ya tafi dashi da sunan

zai kai Mota? Eye?” sukayi daria gabaki

daya, ya cigaba “so until you find your

Brother, ni zan zama Yayanki, kuma zan kula

dake, kuma zan kareki da Iyawata, and zan

taimakeki da iyawata, kuma da yardan Allah

zan sada ki da Iyayenki, kuma zan tayaki

neman Yayanki, kuma zan kalleshi cikin

idanu, in tayashi murnan kasancewarki

kanwanshi, kuma zan bashi hakurin rashin

kasancewarku tare don ba zaku kasance tare

yanda ya kamata ba, saboda ni zan daukeki

in kai ki Gidana”..

Hannu ta sa ta rufe fuskarta, yace

“PureHeart dago ki kalleni” a hankali ta dago

yace “ina ce yanzu ba ‘yar Ghana bace

wanda za a ma auren dole?” tayi dariya ta

girgiza kai, yace “Ok now lets Find your

Brother, da sauri sauri, don shi zai ban

Aurenki, whats his name again?” dariya tayi

tace” ZAID, ZAID SADA” a ranshi ya Maimaita

sunan, a fili kuwa yayi Murmushi yace “OK,

lets find Zaid Sada” tayi dariya tace “How?”

ya kashe mata ido daya yace “dagaske ban

sani ba, amma mu je zuwa” yayi gaba ta

bishi a baya, tana jin Majeed har ranta.

LAGOS

Sun kawo decision, wannan ne karonsu na

k’arshe, well maybe, ya gama karance ma

Na’eelah Plan dinshi, ta amince zata bishi

kano har tsawon kwanakin da yake so ta

zauna. Sai da suka fara zuwa Lagos, inda

Zaid zai hadu da Rita Phillips, rannan

Appointment dinshi ya shiga Office dinta,

Rita ta ji dadi Matuka, irin the whole Mighty

Zaid Sadam Audu in her Office? Thats an

honor, Zaid ya karanta mata irin makeup din

da yakeso, ta jinjina kai ta shaida mai

makeup din 8hours ne, sai an dauka awa

takwas ana yi, ya dan bata fuska, be son

zama, amma in zaman zai sa shi cimma

burinshi to zaiyi hakan, so tace yaushe zaa

fara makeup din? Yace “zai kirata, but in

zaayi makeup din, sai tazo Kano kuma

maybe a rana daya zaayi makeup din so

biyu, it depends dai, kuma yana da bukatan

duk lokacin da yake son makeup din s

kasance tana garin Kano, be damu ba in

zata kashe Appointments dinta, kawai ta hau

Jirgi tazo Kano, or maybe zai dauketa ne

hire har sai ta gama mishi aiki, so ya bata

umurnin yin Calculations gabaki daya, har da

su kudin Accomodation, kusan mint 10 tana

Calculating, a dan tsorace ta kalleshi tace

“4.3 million”. Zaid ya mik’e tsaye yace “Rita

Phillips, I’ll see you in Kano” ya juya ba tare

da ya sake cewa komai ba. Ta bishi da ido,

to me hakan ke nufi? Ya amince zai biya ko

be amince ba? To yace he’ll see her in Kano,

yana nufin sai tazo mai makeup din kenan?

God he’s too bossy”.

K A N O

“Aliyu A A yan fashi suka kama shi a hanyar

shi na zuwa Wudil” cewar Majeed da ke

sanar da su Mummy, Mummy tayi zumbur

tace “Kai Subhanallah, ince dai ba su mai

mugun abu ba ko?” Majeed ya dan daga

kafadu yace “abun mamaki ko sata basu

mishi ba, kawai dai wai sun karbi wayanshi

ne sun mai formatting komai” Daddy yace

“da sauki tunda ba su mishi komai ba, kaje

ka ganshi ko?” Majeed yace “eh naje, daga

chan nake yanzu” Mummy ta lula duniyar

tunani kawai tace “Alhaji Nakowa ne ya turo

mishi barayin nan” duk suka bita da ido tace

“haba, ga abu a baiyane, Alhaji Nakowa ne,

ya zaayi ace Armed Robbers su tare ka, su

karbi wayanka suyi wiping komai? Su maida

maka wayanka ba tare da ko dunguran ma

kai sunyi ba? Wallahi they were after that

recording” Daddy yace “Maryam, ki tsarkake

tunaninki, kila ba haka bane, maybe they

were after something else” Hmm Mairo tace,

ita dai tana da tabbacin Alhaji Nakowa ne

yayi aiken nan, saboda recording dinnan, su

Daddy ba zasu gane ba, don ba su san

wainar da ake toyawa ba, saboda an kai mai

sammaci shiyasa yake neman hanyar

salwantar da evidence dinsu ko? Dole tayi

taka tsantsan, kawai dai su hadu Kotu, sunci

nasarar kwace na hannun Aliyu, amma ita ba

zata bari ba, bari ta kira Lawyer dinta ta

tura mai, komai ta fanjama fanjam kawai.

B A Y A N K W A N A B I Y U

Kullum sai sunyi waya da su Maama, ta sa

Kaveri ta nemo mata numbern Aisha, suna

chatting sosai, ta bata labarin abubuwam da

suka faru da ita bayan rabuwarsu, Aisha tace

“i told you so ai, yanzu you need to be very

careful, ki kula da kanki” nan ta sake bata

shawarwari. kwana biyu ta na cikin walwala,

ba ita kadai ba, duk Ilahirin Familyn Abba

Abu, ba su da wata damuwa, kwana biyu,

suna zaman su lafiya, ina ma wannan

farinciikin dawamame ne? Ina ma su

kasance haka har karshen rayuwansu, ba su

da damuwa, ba su da wata matsala.

Kullum Majeed ke kai Ziyada Makaranta ya

daukota, da Muhsin ya dawo Makaranta, zai

rugo da gudu wurin Najwa wai ta koya mai

Homework, zata karba tayi guiding dinshi, in

bata gane ba sai ta tura shi wurin Ziyada, ita

kuwa Zinatu tafi k’arfin Najwa ta koya mata

Homework, haka take damun Daddy ko Ya

Majeed su koya mata, don ta san ko kallonta

Ziyada baza tayi ba.

**

Kamar mara gaskia, Mummy na fita da Mota

yayi Sallama dakin Hajjo, Hajjo tace

“Abdallah, har ka dawo daga kai Ziyadatun

Makaranta? Yace ” Eh Hajjo, jikarki zaki ara

min, zamu dan fita” Hajjo na lura da Najwa,

tunda Majeed ya shigo dakin bata da sauran

sukuni, Hajjo ta murmusa irin yanda manya

keyi, tace “a dawo lafiya” Najwa tayi kamar

bata ji me suke cewa ba, sai da Majeed yace

“Muje ko Pure Heart?” kanta a kasa ta tashi,

dama akwai Hijab a jikinta, tace “naje” Hajjo

tayi dariya tace “bahausa, kin tafi zakice ba

naje ba” sukayi dariya.

Kasancewar Daddy ya fita da dayan Motar

ya sa Majeed tsaida musu keke Napep, ya

dan kallota yace “kin ta6a hawa?” kai ta

gyada mai, yace “Oh hakane ko? Tuptup

kuke ce mai a India” murmushi kawai tayi,

yace “PureHeart, ki dinga bude baki kina min

magana kinji?” ta dan turo baki, yace “you

look cute” ta sa Hannu a fuska ta rufe, yayi

daria, yace da me adaidaita sahu, “Rijiyar

Zaki zaka kaimu, ta wurin Islamiyan Mallam

Sanda?” suka shiga suka fara tafiya, shiru

shiru ba wanda yayi magana sai Majeed yace

“baki ce ina zamu ba?” tayi shiru yace “Ehen

Ina jinki” a hankali tace “i trust you”

murmushin jin dadi yayi.

Daidai Islamiyan suka tsaya, naira 500 ya

ciro ya ba mai adaidaitan, yace “jirani ina

zuwa” gyada mai kai tayi, yayi gaba ta bishi

da ido.

“Assalam Alaikum” Majeed yayi Sallama a

gaban shago, Wani dan Dattijo mai sanye da

Alkyabba fara da Charbi zungurere ya amsa

mai da “Waalaikum Salam, Bismillah” Majeed

ya dan sunkuyar da kanshi don K’ofar bata

da tsayi ya shiga, bayan ‘yan gaisuwa,

Mallam Sanda yace “saidai ban ganeka ba”

Majeed ya dan Murmusa yace “AbdulMajeed

ne, na wurin Alhaji Abba Abu” Mallam Sanda

ya fadada fararsa, “to to, AbdulMajid ne?

Haka ka koma? Ka zama magidanci, rabona

da kai tun randa kazo min bankwana zaka

tafi Makaranta Turai” Majeed ya Murmusa

yace “gaskiya ne, an kwan biyu” nan suka

sake kwasar wani gaisuwan.

“Allah gafarta Mallam, tare nake da wata a

waje, Mahaifanta na tare da wani Matsala,

haifaffun Nigeria ne, amma rana tsaka suka

hada kayansu suka bar K’asar, yanzu ba su

iya tuna komai game da Nigeria, ko Garin da

suke ba zasu iya tunawa ba, kuma duk randa

suka shirya zuwa Nigeria, InshaAllahu sai

wani abu yayi sanadiyar rashin zuwan su,

shine nake so in akwai taimakon da zaa iya

yi?” Mallam Sanda ya danyi shiru, chan yace

“Shigo min da yarinyan” Majeed ya tashi ya

fita, tana nan rak’ube, yace “PureHeart, ki

shigo, munzo wurin Mallam ne, zai miki

tambayoyi, ki bashi amsa kinji? Trust me,

everything will be fine”.

Ta bi bayanshi, suka shiga Shagon, kusa da

AbdulMajeed ta zauna, ta gaishe shi, Mallam

Sanda ya dinga mata tambayoyi tana bashi

Amsa iya saninta, Mallam Sanda ya kalli

Majeed yace “Kurciya ce aka musu” Majeed

yace “Kurciya?” Mallam ya gyada kai alamun

eh yace “Kurciya ce, ana yin shine a lokacin

da ake so a nesanta mutum da wani wuri, ko

a musu farakku, maana a musu katanga, an

shiga tsakaninsu da Mahaifarsu, Yanuwa da

Abokan Azziki, yana iya yiwuwa wani ke

hassadarsu, ko k’yashinsu” kan Majeed yayi

zafi, yana mamakin mutanenmu, how can

someone be so heartless? Sai yaji ya

k’yamaci hassada a zuciyarshi, ya kyamaci

me hali irin na Hassada. Majeed yace

“Mallam, yanzu me abun yi?”.

Mallam Sanda ya dan Muskuta yace “Addua,

Addua zamu tayi, da Ikon Allah da yardan

Allah Sihirin zai karye, kila ayi k’aik’ayi koma

kan Mashekiya, maana abun ya koma kan

wanda ya musu, ni da Dalibai na zamu sauke

Alkurani Maigirma har lokacin da zasu

baiyana, ba zamu bari ba, har sai randa suka

iya tuna ko da sunan garinsu ne, Yayanta

kuma, da Yardan Allah, indai yana cikin

K’asa Nigeria, in har da ransa, da Izzar Allah

zai baiyana kanshi a duk inda yake, kar ku

sama zuciyoyinku komai, Ikon Allah ya wuce

tunaninku, da Ikon Allah zai baiyana Yayanta,

a Mace ko a Raye”. Ya k’ara da fadin suma

su dage da Addua, k’arfin Addua zai

bayanasu duka, Majeed ya hau Godia, ya ciro

5000 ya ba Mallam, Mallam ya girgiza kai

yace “aa Abdul, dauki kudinka, taimako ne,

aka ma wasu bare kai?” Majeed ya girgiza

kai yace “Aa kar muyi haka da kai Mallam,

Sadaka ne, a sai ma masu Sauka ruwan

Sanyi” Mallam yayi Murmushi yace “Allah ya

saka da Alheri Allah ya sa a dace, Najwanatu

Allah ya Baiyana miki Yayanki, Allah ya sa

Mahaifinki suci galaba kan masu son ganin

bayansu” duk a tare suka amsa da “Ameen”.

A lokutta da dama, Allah na daura ma

bayinsa Soyayyahn junansu, balle ma in suka

maka abunda ba zaka taba mancewa ba,

zakaji duniya ba wanda kake so sosai

matuk’a kamarsu, hakan takasance da

Najwa, tana jin AbdulMajeed Abba har cikin

ranta, tun kafin ya furta mata So, bayan ya

furta mata kuma sai soyayyarsa ta ninku a

Zuciyarta, a yanzu kuwa da ya bada himma

wurin taimakawa don haduwanta da Yayanta

da kuma Mahaifanta, sai taji a ranta kamar

dama don ta hadu da Majeed ne tazo

Nigeria, ya mata abunda ba zata taba

mancewa ba, duk da bata ga an samu

Nasara ba, amma ina laifin wanda ya so

taimaka maka da k’uddirinka?, wanda ya

dauka matsalarka ya maida nashi? Wanda

ya maka hallaci tun daga farkon haduwarku?

Zuciya bata da k’ashi, kuma Zuciya na son

mai kyautata mata, ta ya ba zata so

AbdulMajeed Abba ba? Taya ba zata so ta

rayu dashi ba?. Duk cikin Keke Napep take

ta wannan zanttutukan a zuciyarta,

muryanshi taji yana waya.

Hello Zuzu, erhm, kiyi hakuri kiyi taking A

daidaita Sahu, Mummy ta fita da Motana,

but idan ta dawo zanzo in dauke ki” bataji

me Ziyadan tace ba, sai jin Majeed tayi yace

“are you sure you’ll be OK alone?” OK be

safe, i’ll see you when you get home, I love

you Kinji?” da Murmushi ya kashe wayan.

Soyayyan da ke tsakanin Yanuwan na

burgeta, ina ma zata ga Yayanta, zai kula da

ita kamar yanda Majeed ke kula da

k’annenshi, Allah ya baiyana mata Yayanta

Zaid.

“PureHeart” taji yace, ta dago kai ta kalleshi

ido cikin ido, yace “Ina so in k’arashe

k’arshen rayuwana da ke, Ina matuk’ar

k’aunarki, Kina sona?” kanta ta chusa cikin

cinyoyinta tana Murmushi mai sauti, yace

“PureHeart, meyasa kike min daria a duk

lokacin da na gaya miki abunda ke Heart

dina? Am i some laughing Stock?” da sauri

ta girgiza kai, yace “then ki gaya min, kina

sona? Zan fahimceki in kikace Aa, but right

now i need an answer” shiru tayi, har ya cire

ran zata tanka, ya maida kallonshi kan Titi,

har sun iso kwanar Gida ya ji tace;

“tum meree khushee ho, aap hamesha ke lie

mere hain,

Mein tumseh bahut pyar kharta hoon (Kaine

Farincikina, You are my Forever, Ina

matuk’ar Sonka)”.

” Ehen, Ina jinki, Fassara min” shiru tayi, ta

juyar da kanta tana kallon hanya, ya dan

daga kafada yace “Kawai dan anga banjin

Indianci sai a dinga zagina ko?” ta rausayar

da kai tace”bafa zaginka nayi ba” yace “to

fassara min, sai in Yarda” da ta lura

tsokananta yake, sai ta kulle ido tana girgiza

kai, Kallon k’auna ya bita dashi, duk da be

san ma’anar abunda ta fada ba, ya tsinci

kanshi da jin dadi, da Murmushi baki kamar

Gonar Auduga, har Mai Adaidaita ya iso

Gidan, da sauri ta sauka ta shige ciki da

saurisauri, gudu gudu”.

********

Fitowarta lecture kenan, kasancewar

sabuwa ce a Makarantar kuma dai bata da

saurin sabo, take tafiyarta ita kadai cikin

yanayinta na sanyi, straightahead Gate ta

nufa, don YaMaji ya sanar da ita ba zai

samu zuwa yau ba, har ta fita bakin gate

taga Mutane na ta kai kawo, hayaniya, ko ta

tsaya nan ba zata samu Keke Napep ba,

kawai sai ta fara tafiya, tafiya takeyi kanta a

k’asa, wata bak’ar Mota k’irar 508 ta tsaya

daidai gabanta, haka kurum taji gabanta ya

fadi, shiyasa take son Ya Maji ya dinga zuwa

daukota, ita bata son Samarin nan marasa

kunya, masu tare yanmata a waje, tsaki

kawai ta ja, ta gilashin Motan ta hango

Drivern na waya, suna hada ido ya sakar

mata da wani irin murmushin da ya sa

jikinta rawa, da sauri ta dauke idanunta daga

gareshi, amma ta kasa gaba ta kasa baya,

ka kwarjini ya mata, har yanzu bai bar

murmushin nan ba, ya bude k’ofa, tuni ta

fara jin k’amshin shi, sanye yake da ‘yar

black top, idonshi da glass amma k’ilan bana

gayu bane don farine it might be medicated,

ba dai ta sani ba ya fito ya fara taku zuwa

gabanta, tuni jikin Ziyada ya fara rawa,

tasan Yayanta Majeed me kyau ne, amma

meyasa tafi ganin kyan wannan halittar? Ko

dai Aljani ne? Tambayar da take ta ma kanta

kenan, har sai da ya bude baki yace “Hello

My Happiness, its nice to finally/physically

meet you” ya fada yana kara mata wannan

murmushin.

Wani Yanayin da zata rantse bata taba

shiga irinshi ba ta shiga lokaci daya, kamar

robot ta tsaya kallonshi, ya gama kasheta,

ya santa ne da yake dangantashi da

Farincikinshi?” kasa motsa baki tayi, ya dan

daga hannunshi yayi waving daidai fuskarta

yace “Hello? Yadai?” firgigit kamar wacce

aka tada daga bacci, yace “Okay, lets get

you home” sai da k’wakwalwar kanta yayi

mata nazarin abunda ya fada don ita

kwatakwata turancin ya dauke mata “ya

kaini gida yake nufi?” da sauri ta girgiza kai

alamun aa, kar suje Gida Ya Majeed ya

ganta, ba zai ji dadi ba.

Ya dan marairaice fuska yace “Ok, mu bar

School premises first” bata samu chance din

bashi amsa ba sai ji sukayi ance “Bahbah, ba

wannan bane Zaid Sadam Abdu, the

youngest Multibillionaire?” abokai biyu ne ke

maganan kuma zasu girme ma shi Wannan

din, sai taji dayan yace “Kai Muje mu

tambayeshi, Allah ya sa shine, ai mu mun

warke” bata ankara ba sai ji tayi ya finciko

hannunta ya jata da gudu, ya bude murfin

k’ofan gaba, ya tura ta ciki, shima ya zagaya

da gudu ya tada Motar, suna jinsu sukace

“Wallahi shine mu bishi” suma suka koma

suka tada Motarsu, da gudu ya Ja Motarshi

yayi Gaba, su ka bishi a baya, gudu yake

sosai, ganin jikin Ziyada na rawa ya dan

kallota yace “Calm down, i’m not gonna

kidnap My Happiness, I got you, trust me” ta

dago kai ta kalleshi, ya kashe mata ido daya,

ko me wannan bawan Allahn keyi, to ya na

tasiri a kanta, duk abunda yayi kashe mata

jiki yakeyi, k’asan Gada yayi parking, ya

kallota yace “I want you to be my Forever”

bakinta yayi nauyi, yace “Ok, Sunana *ZAID

SADAM ABDU* hotonki nagani a Wayar

Friend dina, he’s your friend in some Social

network cant remember which actually,

Mss_Ziyada isit?yeah i think, tunda naga pic

dinki naji ina sonki, na sa a nemo min ke,

shine aka ce min kina Kano a NWU, ina da

numbernki, amma ban kiraki ba, nafison mu

hadu one on one, kawai naji ina son haduwa

dake, you know daga wani Gari na taso

nazo Garin Kano saboda ke? Tun daga garin

Porthacourt, yanzun nace barin zo in nemeki

a NWU, ina zuwa kuma bansha wahala ba,

da ke na fara cin karo, ina ganinki i recalled

your face so well, nayi taking risk din zuwa

gareki, ko zaki min wulakanci i wont mind,

Saboda i love you so much”.

“My Forever, ki Amince dani, Aurenki nake

son yi, ki gabatar dani wurin Mahaifanki, if

you need me to give you time, you have

Forever to think about it, i have Forever to

wait for you, coz you are my Forever”.

Zuciyar Mace Rauni gareta, balle a ka samu

wanda ya kallamlamceta, nan da nan Ziyada

ta fada ma wannan Guy din, Zuciyarta ta

Aminta dashi, Zuciyarta tayi naam dashi, a

yau ta fara ganinshi, amma sai ji tayi kamar

don shi akayi ta, in bashi ba sai rijiya. Da ya

lura maganganunshi sunyi tasiri a Zuciyarta,

sai ya bude Mota ya fita, ta bishi da Ido,

Keke Napep ya tsaida yayi magana, ya ciro

1k ya bada akan idonta, ya dawo wurin

Motar ya bude mata ta fito, jiki ba kwari, ya

rakata har gaban Mai Napep yace “Ka

tuk’ata a hankali, kar ka dauki kowa” Mai

Keke Napep yace “Angama Oga” ya juya

gareta, ya sakar mata murmushin da ya san

yana tasiri a Zuciyar ‘yanmata yace “Stay

Safe My Forever, sai na kiraki, I love you so

much”.

Tunani dubu dari a Zuciyar Ziyada ta rasa

tunanin me zatayi, ita dai kawai ta san tana

son ZSA, haka har suka iso har kofan Gida,

tayi mamakin yanda mai Napep din ya

kawota har Gida, sai kuma batayi mamaki

ba, don Zaid din ya mai bayani, shi da ya

bar PH yazo dominta, dadi kamar ya

kasheta, ta shiga gida baki kamar gonan

Auduga.

Da daddare ya kirata, chan daki ta kulle

Kanta, suka sha Soyayya, tana mamakin

kanta, tana da wuyan sabo, bata san

mutane, amma itace nan ta zage take waya

da wani wai Saurayi, ashe haka abun yake?

Cikin Wayan Awa Biyun da sukayi, Ziyada taji

a ranta cewa bata da Miji sai Zaid, tana jin

shi cikin Jinin Jikinta, cikin Bargo da duk

wani tsoka na jikinta.

Washegari da Majeed ya sauketa a School,

har ya juya zai tafi ta tsaidashi, tace mishi ”

YaMaji, kar ka damu, yau ma zan hau Keke

Napep, i know you are committed, tend to

other things” Majeed ya dan nazareta, ya

lura tun jiya take ta walwala, yace “Zuzu, is

there anything you are not telling me?” da

sauri tace “No, ofcourse not YaMaji” yanda

tayi magana ya san cewa k’arya take mai,

ya gyara zama jikin Mota yace “tun yaushe

kika fara min k’arya? Zuzu are you inlove?”

Fuskarta ta bashi amsa, saboda nan da nan

yayi ja, da sauri tace “Bye YaMaji, kar nayi

lattin lectures” ta juya ya dakatar da ita ta

hanyar cewa “Zuzu” ta juyo yace “I’d like to

see him” kasa boye murmushinta tayi, tace

“Bye Ya Maji” da sauri ta wuce yayi

Murmushi yace “Yara Sun Girma”.

K O T U

A tunaninta k’aramin case ne tunda sunada

all evidences, za kawai a ba Nakowa Rashin

gaskia, a hukuntasu, Nana ta mayar musu

da Credentials din Majeed a wuce wurin,

shiyasa taga gwara taje tayi representing

Family dinta, taje Kotun ba tare da ta sanar

da kowa ba a gida.

Kotu ta cika Mak’il, Nakowa da Iyalanshi sun

hallarta, a ka karanto Sunan Shari’ar, Alk’ali

ya buk’aci da a kira Mijin Nana ya fito gaban

Kotu, Lawyern Mummy ya sanar dashi cewa

Hajiya Mairo kadai ta Hallara a Kotun, Alk’ali

ya tambayi ina Mijin Nanan? Mairo tayi

karya tace baya k’asar, nan da nan Alk’ali

yayi watsi da lamarin yace, an daga

Sauraron Kotun har sai Mijin Nana ya dawo,

tace Sati me zuwa zai dawo, Kotu ta daga

Sauraron case din sai bayan Sati Biyu, aka

Sallamesu, Hajiya Mairo ta gama wurgansu

Hajia Sayluba da Nana da bak’aken

maganganu kan Nana, wai Karuwar Babanta,

ta ja Motarta ta wuce, Alhaji Nakowa ya

Murmusa yace ” kina da sauran baki har na

sati biyu, Bayan Sati Biyu bakinki zai mutu

Murus”.

* * * *

Yau Laraba yayi dropping Ziyada a

Makaranta, ya bi ta Rijiyar Zaki gun Mallam

Sanda, Mallam Sanda ya nuna mai ba wata

Matsala, ana ta Addua da saukar Kurani,

InshaAllah akwai Nasara, Iyayen zasu dawo

Hayyacinsu, Yayan kuma zai bayyana gaban

k’anwarshi in dai yana da rai, Godia Sosai

Majeed ya sakeyi, ya ja Motarshi ya tafi, be

san ya akayi ba be ankara ba sai gani yayi

wata ta zube a gaban shi, k’ii ya ci burki

don kar ya takata, da saurinshi ya fito waje,

titin Rijiyar Zakin be da kyau, ya tsugunna

gabanta yace “Baiwar Allah? Tashi a hanya?

Baki da lafiya ne?” dago Fuskarta tayi,

budurwa ce da ba za ta wuce du Ziyada ba,

yana hango boyyayen kyaunta da wahalar

rayuwa ya boye a fuskarta, kayan jikinta

kwandala biyar ba zaka siyesu ba, bakinta

ma rawa tace “Kayi wa Darajan Manzon

Allah tsira da Amincin Allah ka taimakeni”

Majeed Sarkin tausayi ya sa hannu cikin

Aljihu, dubun biyun da ya rage mishi ya ciro

ya bata” yarinyan tayi murmushi me ciwo

tace “ina ma kudi zasu magance min

damuwata?” ya tsura mata ido, yana

tausayinta har ranshi, yace “taso mu shiga

mota” ba gardama ta bi bayanshi suka shiga

Mota.

“Baiwar Allah Meye damuwanki?” Sunana

Na’ila Shehu, ni Marainiya ce, Ina da Yaya

daya Nura, Kurma ne, be jin magana be iya

maidawa, sai dai ya mayar da nuni da

hannu, Rayuwanmu ya chanza tun randa

Mahaifanmu suka rasu, Yayana be da wani

mamora, gidan da muke haya yau da Asuba

aka mana koran karnunka, bamu san inda

zamu dosa ba, ka taimakeni, kamar yanda

Allah ke taimakonka, ka rufa min Asiri, yanda

Allah ke rufa ma Asiri, na san baka sanni ba,

ka bami masauki, zan nemi Aikatau,

InshaAllah ko zuwa nan da Sati daya zuwa

Biyu, zan samu yanda zanyi don Girman

Allah”. Jikin Majeed ya gama sanyi, shi

yasan shima yana da bukatan Taimakon,

Babban Gida da Motan da aka ga ya na

hawa, ana mishi zaton Shi wani Hamshakin

maikudi ne, to hamshakin ne, amma a da

ko? Tausayi Na’ila ta bashi, duk da shima

yana da bukatan taimakon, zai taimaka mata

ita da Yayanta, ko a boysquaters su zauna,

kafin su samu yanda zasuyi, Allah ya bashi

ladan, ya kalleta da tausayi yace “Ina

Yayanki?”

M

ajina ta ja, tace ” yana Ja’en” Majeed yace

“ki nuna min hanya” tace “toh”. Ya ja Mota,

sun danyi tafiya me nisa kafin suka iso

Ja’en, da kwatance suka iso wani Unguwa,

Unguwan dai sai a hankali, da hannu ta nuna

wani wuri tace “ga Yayana chan”. Majeed ya

kai dubanshi ga inda take nune, wani ya

gani a tsugunne, yara sun zagayeshi suna

waka, “Kurma ne, Bebe ne, bai da amfani”

Na’ela ta fashe da kuka tace “hantarar mu

sukeyi kullum, haka muke fama” da sauri

Majeed ya fita daga Motan yayi inda yaran

suke, takalmanshi ya cire yayi kamar zai

buge yaran, da gudu suka ware suna mai

gwalo.

Majeed ya matsa kusa dashi, ya hade kai

da guiwa, Majeed ya sa hannu, bai kyamace

shi ba, ya dago shi tsaye, karaf idanuwansu

ya gwaraya, sunyi kusan Sakwan Goma suna

kallon Juna ido cikin ido, wani kallo ne da ba

su san na meye ba, kafin shi Nuran ya juya

kallonshi ya koma mai Kallon Rashin sani,

Na’ela ta karaso gun, da hannu Nura ya

mata alama da waye wannan? Ta mayar

mishi da hannu kan ya kwantar da

hankalinshi, Majeed yace “kuzo mu tafi

Gida”. Naeela ta ja hannun Yayanta Nura ta

tura shi a bayan Mota, ita kuma ta shiga

gaba, Majeed yayi starting Mota yayi Hanyar

Gidansu Gabanshi na dukan Ukuuku, be san

yanda zasu kwashe da Mummy ba. Yana

Mamaki, mutane da yawa in zasuyi abu sai

dai su nemi Izinin Mahaifinsu, amma su

gidansu ya sha Banbam, Mummy ce ke da

gida, harta Daddyn in zaiyi abu, sai ya

tambayi Izininta, wannan wani irin rayuwa

ne?.

Ta Madubi yake kallon Nura, shi kuwa

Nuran yasan shi yake kallo, so ya k’i bari su

hada ido, kallon da ya mishi dazun ya so

kwance mishi abubuwa da dama, a cikin

idanunshi ya ga Tausayi fal, da ya cigaba da

kallonshi, zai kasa aiwatar da abunda yayi

niya, its better suyi avoiding Eye Contact,

duk da shi Namijin Duniya ne, ya dade yana

Jiran ranan da zasuyi gani gaka da ‘yan

Gidan, sai yau yake jin shi daban, jikinshi

yayi Sanyi, amma in ya tuna Shekari nawa

ya kwasa yana gina Fansarshi sai yaji

Sanyin Jiki ba nashi bane, he went through

alot to stop now, ba zai yiwu bane, lokacin

da suka sha kwanan Gidan, Rayuwanshi ya

soma dawo mai, ya tuna lokacin da ya bude

Wallet din Baba Abba ya kwashe kudin Cikin

ya gudu ko takalma be da a k’afa, duwatsu

na chakar mai k’afa, ya gudu don tseratar da

Rayuwanshi, Hawaye ya gangaro mai, ya sa

hannu ya share, a idon Majeed, nan ya kara

jin tausayinsu duka, horn yayi Fallalu Direba

ya bude Gidan, ya shiga Yayi Parking.

Nura ko ince Zaid ya daga kai ya bi Gidan da

Kallo, komai na nan yanda yake, ba abunda

ya chanza, Da ba dan Hajiya Mairo ba, da

yanzu shi da Mamanshi, da Babanshi, da

K’annen da Allah kadai ya san yawansu ne a

Gidan nan, Kai, Wallahi dole ya Wulakanta

Hajia Mairo da Zuriarta, ba zai taba yafe

mata ba, duk sauran Farincikinsu sai ya

rusar dasu, ya fara da Ziyada, sai ya bari

lokacin da ya zamana ba zata iya rayuwa

babu shi ba, lokacin zai Wulakantata, ya

tozartar da ita, he’ll break her heart

up,shatter her dreams and she wont be able

to love ever again.

Hannun Naeela ya ji a na shi, ashe ana ta

mai magana ya zo su shiga yana chan

duniyar tunani, oh oops, hakan ma yayi, don

abun yayi kama da Kurman gaske.

9:45am ne, Kan Dinning Table, Mummy,

Daddy, Zaineema, da Hajjo keyin Breakfast,

Majeed ya shigo da Sallama, Mummy ta

amsa mai da faraa, “Boy, Har kadawo daga

kai Ziyadan Makaranta?” ya gyada kai tace

“zo zauna kayi breakfast” yanayinshi ya

chanza, tace “Yadai Boy?” yace “Mummy

bani kadai bane, tace ” kai da su waye?”

yace “Mummy, ni da wasu bayin Allah ne” a

takaice ya basu labarinsu Naeelah, Mummy

tuni ta fara hura hanci tace “AbdulMajeed,

kafita ido na tun wuri, wato kaine Redcross

ko? Kai kafi kowa Imani, to sannu Mai

taimakon Agajin gaggawa, kayi na farko kaci

Nasara, shine kace bari ka karo wasu har

biyu ko? Mace har da Namiji, saura maka

Mutanen dutsen Dala, ban ma san ganinsu

tun wuri ka fitar da Mutanen kar in saba

maka” kafin Majeed yayi Magana, tuni Zaid

ya Banko Labulen Dinning din ya shigo,

Hajjo, Daddy, Mummy da Zaineema suka

Mik’e tsaye lokaci daya…

°°°°°

Ghen Ghen, So Majeed yaci Alwashin

taimakon Najwa ko ta halin k’ak’a, hmm

this Majeed always Acting the Good Guy.

Is Zaid really Playing Ziyada? Poor Ziyada,

girl is into the guy like Sosai, anya Zaid zai

taba Sonta? is there hope for these two?

Zaid in Abba Abu’s? Omg, What is Zaid

doing? What will happen next? Dont ask me

I really dont know.

Zaid a Roof daya da Najwa? Seriously?.

Hello Bibiliciousfreakingfans, ga Babi na

Ashirin da hudu, kamar yanda nayi maku

Alkawarin zaizo soonest gashi na cika.

Nasan Zaku k’ara min Uzuri, saboda na

koma Makaranta, abubuwan za su sake

Yawa, amma nasan kuna tare dani kamar

yanda nake tare daku. Bear with me please.

Tsakani da Allah ‘yan Labe (Ghost

Readers)kuna k’ona min rai, ganin gari ne

zai sa kayi karatu a Wattpad amma voting

ya gaggareka? Haba mana? Ba kusan yanda

nake son ganin Notifications din Voting din

da kukeyi ba, ba fa zai rageku da komai ba,

donAllah yan labe ku bari, haba mana, ba

girmanku bane, yanda kuke karantawa

kunajin dadi kuyi wa Allah kuyi Voting nima

inji dadi.

Ehen to the real

wattpadiansbibiliciousfreakingfans, sorry

didnt get to reply your comments, was super

busy, lets keep rolling Aye?

we good now, Vote and Comment Line by

Line.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

Biebee Isa

Add Vot

DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣5⃣

Daya bayan daya ya ke binsu da kallo,

su ma duk shi suka zuba ma ido, idon Zaid

ya tsaya chak kan Hajjo, yana tunanin inda

ya san fuskar, tabbas yasan Fuskar nan,

amma a ina, ‘Umma Hajia ce’ cewar

zuciyarsa, zubewa yayi a k’asa, Majeed yayi

saurin tarban shi, Mairo ta fara surfa bala’i,

“danubanka waye sa’anka a nan da zaka

shigo kana bin mu da wani mugun kallo?fita

danubanka” da sauri Zaid ya daga Ido ya

watsa ma Mummy wani mugun kallo wanda

zata rantse da Allah taji tsoro.

Naeela ta shigo da sauri ta zube inda Zaid

yake, tace “kuyi mai afuwa, be san abunda

yakeyi ba, ya ga ‘yallabai ya shigo ne,

shiyasa ya biyoshi, kuyi mai aikin gafara” ta

tallabo Zaid ta mikar da shi, tace “Ya Nura

mu fita, mesa ka biyo shi?” sosai Hajjo taji

tausayinsu, tace “ka sa musu Abinci

Abdallah” Mairo tayi karaf tace “Burauba ne!”

Daddy yace “Maryaaam” alamun gargadi, ta

kalli Daddy kafin ta wuce fuuu kamar zata

tashi sama. Zaineema ma ta tsame

hannunta ta shige ciki. Daddy ya kallesu

yana me tausauya musu “AbdulMajeed, ka

basu abinci suci” yace “to Daddy” ya matso

inda warmers din suke aje, ya zuzzuba musu

a plate, Hajjo tace kuzo ku zauba ku ci”

Naeela tayi murmushi ta karaso, Zaid na

tsaye yayi kamar beji ba, sai da Hajjo ta

mik’e ta kamo hannunshi tana fadin “Zo nan

Jikana, Zo kaci abinci” kallonta yakeyi sosai,

wani abu na ratsa zuciyarshi, ‘Jikanta’ ko ta

ganeshi ne? Binta kawai yayi ya zauna kan

dining table din.

Matso mai da Plate Hajjo tayi da sauri ya

kawar da fuska a ranshi yace ‘i cant eat this

shit’, Taliya ne da Miya, ya ma zaayi yayi

breakfast da Taliya da Miya?, kuma yana

kallon kalar taliyar ya tsaneshi, shiyasa ba

zai iya ci ba, shi da duk kayan Abincin

Gidanshi na waje ne, Hajjo ta tabo shi, ta

mai alamu da ya ci, kai kawai ya girgiza

mata, Naaela da ke cin abincin tace “Hajia

ya k’oshi, da Safen nan na sai mashi k’osan

talatin ina jin ya k’oshi, idan yana jin yunwa

zai min alama” Hajjo tace “to shikenan”

Majeed yace “Daddy, wai da Boysquaters zan

sauke su?” Daddy yace “anya, Majeed? Ina

ganin BQ dinnan duk karikitai ke ciki” Majeed

ya danyi shiru sai chan yace “da Mummy

zata yarda, ita Na’ilar sai ta zauna tare da

‘yanmatan, shikuma Nuran sai mu zauna

tare a dakinmu”.

Hajjo tace “ita Yarbudurwar sai tazo nan

dakin mu hadu da Najwa” Daddy ya nisa

yace “hakan ma yayi” Majeed yace “Mummy

fa?” “kar ka damu da ita” cewar Daddy,

Naeelah ta zube k’asa tana godia harda

kukan farinciki, ta k’ara da cewa, zata dinga

fita neman aiki, in Allah ya sa aka dace, zan

tara sannan mu san nayi, Mungode”.

Hakan kuwa akayi, tana gama Kalaci

Hajjo ta tafi da ita daki, shi kuma Majeed ya

kama hannun Zaid suka wuce chan dakinshi,

Majeed ya tura Zaid cikin toilet, ya mai

alama da yayi wanka. Fita yayi yana me

neman numbern Najwa ringing daya ta

dauka: “PureHeart ina BQ ina jiranki, i want

us to talk” cikin sanyin Muryarta tace “Sorry,

bana gida”da mamaki yace”what?” tace

“Sorry, ban gaya ma ba, Mamma ne ta kira

tace sun tura min kudi a moneygram na

GTBank” shiru Majeed yayi yace “Stay where

you are, gani nan zuwa”. Ya kashe wayar ya

fita.

*

Tsaki yayi a karo na ba adadi, yana

lek’awa ya ga Majeed ya fita, shima ya fito

daga toilet din, ya dan zaro wayanshi daga

cikin wandonshi, ya dan latsa wasu

numbers ya kira, “Hello Arm” Amstrong daga

dayan bangaren ya amsa “Hello Oga” Cike da

matsuwa Zaid yace “i’m tired, i cant survive

here” Arnstrong yayi daria yace “too early for

you to say” Zaid yace “I cant eat the sh*t

they are eating here(ban iya cin abinci da

suke ci a nan)” sosai Amstrong yayi daria

Zaid ya fara k’ulluwa yace “f*ck you! Get me

lunch later, text me what to tell that girl (ka

kawo min abincin rana anjima, ka min text

din abunda zance ma yarinyar nan, yana

nufin Ziyada)”. Amstrong ya tsaida dariyan

shi, yace “OK”.

Katse wayar yayi yana kallon dakin

AbdulMajeed, a Lokacin dakin Mahaifiyarshi

ce, ya tuna lokacin da Maman shi ke mai

wanka shi da AbdulMajeed, lokacin da zasu

tube zir su shiga wanka tare, a dakin nan

suke wasan banza mama ta bisu da gudu

suyi ta wanata suna zagaye dakin a guje,

dakin nan na da tarihi, yana cikin tunaninshi

ne wayarshi tayi vibrating alamun text ya

shigo, yana budewa ya karanta yayi tsaki,

shifa ya fara gajiya da shirin nan, yanzu

mace zai fada ma wannan abunda

Armstrong ya rubuta? Raini ne be so, to

raini ma na yaushe tunda har zai kalla

wannan yar karamar yarinyar ya kirata da

“*my Forever *” dole ta rainashi ko nan gaba,

balle yanzu wannan kalamen da Armstrong

ya typo mai, wai ya ma Ziyada forwarding,

guntun tsaki yayi ya mata forwarding,

kalamai ne masu ratsa zuciya, be san ta

inda zai fara maganganu da mace ba, be san

me ake ce ma mace ba, tun daga randa ya

hadu da Ziyada, a fili ko a waya, duk abunda

ya fada mata, shirin Amstrong ne, sai

abunda aka karanto mishi yake karanta ma

Ziyada shi, sai ka rantse da k’wak’walwarshi

yake karanto mata, tsaki yake tayi, wannan

shine hardest pretense, yana jin wani iri a

duk lokacin da ya ma Ziyada wani maganan

k’auna, ko na So, tsaki yayi ya kwanta kan

Gado.

Ta fito first lecture dinta tayi receiving

message dinshi, kalaman Soyayya ne, sai a

karshe ya sanar da ita ba zata samu

ganinshi ba sai nextweek saboda yaje wani

aiki a Abuja, zatayi missing dinshi sosai,

saboda a ‘yan kwanakin nan, tayi sabo dashi

ba na wasa ba, reply ta mishi da “take care

of yourself for me, i’ll miss you Handsome”.

Text din na shiga ta latso Majeed tace mishi

“na gama lectures” ya shaida mata gashi

nan zuwa shi da Najwa.

*

Ta Moneygram zata karbi kudin da Paapa ya

turo mata, Najwa ta bada Details din da

Paapa ya mata sending, tayi claiming

ownership Kudin da ya turo 300usd kusan

duba dari da goma a kudinmu na Nigeria.

(MoneyGram: Account ne da banks ke

budewa k’ark’ashin kasashen Waje, Normally

In zaa turo maka kudi daga India Misali kana

Nigeria, ta Moneygram zaa tura ma, bata

account numbernka ba sunanka zaka bada,

abunda akeyi, shine shi me turo Kudin, zai

ba shi wanda zaa tura ma Kudin wasu Secret

Questions and Answers don da Question and

answers din za ka karbi kudinka in kaje

Bank, in kaje Banki, zaa a baka form, sai kayi

filling stating the senders details and amount

da aka turo ma, you withdraw on the

counter, with the Provided details, thats how

you claim ownership, Ina Fatan mungane?).

Tsayawa tayi a cikin Bankin gudun kar a

samu matsala ko wani ya fizge mata kudi

don ta har yanzu tana tsoron yan Nigeria,

tana nan zaune cikin bankin har Majeed

yazo, ya shigo “Pure Heart meyasa kika fito

baki gaya min ba?” sadda kai k’asa tayi, ya

girgiza kai tare da Murmushi yace “Oya muje

mu dauko Zuzu a School, tace ta gama

Lectures” gyada mai kai tayi, su ka fita daga

Bankin, tana so ta bashi kudin amma ta rasa

yanda zata bashi, rikewa dai tayi suka shiga

mota, a cikin Motan ne yake bata labarin su

Na’eela, har ranta ta tausaya ma Nura

Kurma.

**

Tana shiga Parlornsu taji k’amshin shi,

tayi amanna shi ke da k’amshin nan, me zai

kawo shi Gidansu? Amma dai turaren ne, da

sauri tace “YaMaji munyi bak’i ne?” Majeed

ya kalli gabas da yamma ko zai ga Na’eela

ko Nura be gansu ba, yace “No, Me kika gani

ne?” tace “kawai na tambaya ne” Majeed ya

Murmusa yace “Mun k’aru ne, Naeela da

Yayanta zasu dan zauna da mu for

sometime” bata da damuwa, bata tsaya

tambayan ko su waye ba, tace “barin je na

watsa ruwa ta shige dakin Zaineema, Majeed

ya maida Hankalinshi kan Najwa cikin

muryan rada yace “Pure Heart kinyi breakfast

kuwa?” Kai ta gyada mai, yace “PureHeart”

ta daga kai ta kalleshi suna hada ido yace

“Wallahi ina sonki” da sauri sauri ta shige

dakin Hajjo tana dariya, Ya bita da kallon

k’auna.

*

Da rana Zaid ya leka Parlo ya ga ba

kowa, cikin sanda ya fita, har ya fita faga

gidan ba wanda ya ganshi, Cikin Motan

Amstrong ya shige, da yake Motan na da

Tint, yana shiga ya sauke Ajiyar zuciya “i

hardly breathe in there (da k’yar nike

numfashi a cikin gidan)” dariya Armsyrong

yayi ta yi, sai da Zaid ya wurga mai harara,

da sauri ya juya baya ya dauko Basket, ya

bubude ya zuba mai a plate, bayan ya ja mai

kujera baya, kamar mayunwaci Zaid ya fara

cin Abinci, sai da ya ci ya k’oshi, kafin ya

dora da gwangwanin kalan lemun da yake

sha, Amstrong ya bashi powder din da ya

kawo mai, ya mai bayani cewa a abinci za a

zuba, ya karba, Amstrong ya tambayeshi in

ya ga “Ziyada” harararshi yayi ya bude K’ofa

ya wuce, Amstrong ya bishi da daria, sai da

ya shige gida Amstrong ya ja Mota ya wuce.

Kamar baki, yana shiga Parlor sai ga

Ziyada ta fito daga dakin Hajjo, kallon kallo

suke yi, Ziyada ta fara jin k’amshin nan,

mutane basu dameta ba, amma sai ta samu

kanta da ce mai “Ina wuni” shiru yayi kamar

be ji ta ba, a ranta tace “ko dai be ji ba?” ta

bude murya ta sake cewa “ina wuni” sai ma

ya kawar da kai kamar be ga kowa ba,

Ziyada ta samu kanta da jin ba dadin rashin

ansa gaisuwarta, ta bude baki tace “Ina

wuni?” kamar dole, “wannan kurman Banzan

ki ke gaidawa? Mummy ce me fadan hakan,

Ziyada tace “Mummy ban gane ba” Mummy

tace “baki ga wata kazama dakin Hajjo ba,

Yayanku ya kawosu, wai basu da gida waye

waye, shi me Orphanage house, ko ince shi

me Safety House, duk wanda be da gida ko

yake neman taimako sai ya kwaso ya kawo

gidan nan, nan gaba Mata da Miji da Yaranta

zai kwaso, wannan Kurma ne, nan gaba sai

gurgu, kuturu ko makaho, ko wa yace ma

Boy ana taimakon mutane yanzu, wasu zaka

musu dare su maka rana, hausawa na cewa

tsintaciyar mage bata mage” ina sam

hankalin Ziayda baya kan Mummy, a hankali

take takawa gaban Nura, tausayinshi ya

mamaye ranta, Allah ta tuba ya zaa ce

wannan kurma ne be ji be magana, bak’i ne,

amma ta ga kyaunshi, Mummy tayi saurin

shan gabanta ta ja ta suka wuce dakinta.

Da daddare Majeed ya ja hannun Zaid sukaje

Masallaci Sallah, Majeed sai nan nan yake

da Zaid har suka dawo gida. Zaid ya ma

Naeela text cewa ya ajiye mata powder din

da zata zuba musu abinci gobe, yana nan

karkashin dogon kujera, wurin sha daya da

kowa yanna daki ta fita ta dauko, ta boye a

zaninta, Washegari bayan Yara sun tafi

School, Mummy na Abinci, Naeela ta faki

idonta ta zuba maganin a Abincin nan, bayan

sunci Abincim ko mintuna goma ba a rufa

ba, suka buge da bacci, daga Mummy,

Majeed, Hajjo, Zaineema da Daddy banda

Najwa da ko fitowa batayi ba, saboda tana

Azumi, Bedroom dinsu Mummy Zaid ga nufa

ya fara bincikenshi hankali kwance, ya kusa

mintuna sha biyar be ga wani abu me amfani

ba, tsaki ya buga da k’arfi, duk girman gidan

ba komai ciki, efforts dinshi zai zama a

banza, so yake ya mallaki gidan nan ko ta

halin k’ak’a, ba wani takardun Gida ko wani

abu, aikin banza yakeyi kenan? Bata

lokacinshi yake yi a gidan nan? To zamanshi

a gidan be da wani amfani, rai a bace ya fita

ya koma dakinsu, yanzu ya zaiyi, meye

abunyi? Wani tunani yazo mishi, why not ba

zai tsaya ya ga ya shariar Mairo da Nakowa

zai kasance? Sai yayi using shariar akansu,

in Nakowa bai ci Shariar ba to duk wani plan

dinshi zai rushe, Nakowa ne last hope dinshi

kan Gidan nan, Allah yasa yaci Shariar kawai,

zaijira tunda Jibi ne zaa sake zaman Kotun.

**** Bayan kwana Daya****

Ga yanda Najwa ta fuskanci Na’eela, ta

gane Yarinya ce mai Ilimi, duk yanda Naeela

ta so maida kanta Jahila wacce bata san

komai ba, Najwa ta gane akwai Ilimi tattare

da ita, ba dai tace mata komai ba, shiyasa

duk yanda Naeelah ta so jin k’wakwaf kan

dangantakarta da yan Gidan ta k’i gaya

mata, kawai ce mata takeyi ita bakuwa ce,

har yau Najwa bata hadu da Nura ba. Naeela

ta kan ba su labarin Kurumtan Yayanta,

harda kuka saboda tausayi Najwa da Hajjo

keyi.

**

Idan zatayi waya dasu Maama ta fiso taje

BQ don nan zatayi waya hankali kwance, in

daria zatayi to tayi da kyau, in kuka zatayi

sai tayi da kyau, da sauri sauri tayi hanyar

BQ, daga nesa ta hango bayan mutum

mamaki take waye wanan? Saboda daga

ganin bayan ta san ba Majeed bane, Majeed

yafi wannan tsawo, waya yakeyi, kawai sai

ta samu kanta da labewa bayan wani bishiya

ta kasa kunne tana sauraron abunda yake

cewa, “Arm, am sick and tired of this house,

no aircondition, well there is but its outta

gas, it is useless(Ni nagaji da gidan nan, ba

Ac, ko da yake akwai amma ba gas, be da

amfani)” “ya buga tsaki saboda abunda

Armstrong yace ” Yeah One more Day, until

they are done with the Court, they’ll see me

for who i truly am, maybe not(Eh saura

kwana daya, da sun gama da Kotu, za su ga

ko ni waye, kila kuma ba a lokacin ba)”.

Gabaki dayansu sukaji muryan Majeed, a

hankali Zaid yace “will call u back Arm” ya

tura wayar cikin Aljihhu, yak’i juyowa, Duk

abunda yakeyi a idon Najwa, duk da taji me

yake cewa amma sama sama, ba zata ce ga

abunda yake nufi ba, tana ganin Majeed ya

k’araso, Nura ashe kana nan, ya kamo

hannunshi, yace “mu koma ciki” sokoko Nura

ya bishi a baya.

Abu daya Najwa ta fahimta, wannan shine

Yayan Naeela, Wannan shine aka ce Kurma,

amma ita shaida ce tayi magana, karewarta

waya taga yakeyi, haka kurum taji bata yarda

dasu ba, da kunnenshi taji yana magana

maana ba kurma bane, and one thing is

clear, they are after ‘yan Gidansu Majeed, ba

zata bari su cuce su ba, ba zata bari su

zalunce su ba, zata saka musu ido har sai ta

gano me suke so da su Majeed, da ta gano

su zata yi exposing dinsu, a baiyane tace

“Nura, i wont let you hurt My Jaan”.

Afuwan Habibties, nasan cewa an kwan biyu,

ku min uzuri, Makaranta ya boyeni, nasan

page dinnan yayi kadan kuma sai a hankali,

da kunsan yanda nayi typing dinnan ehm, ku

fara dashi next page zaizo cikin weekends

dinnan Asabar ko Lahadi InshaAllah.

Ga Najwa ta gano Nura, ya zata kasance?,

A babi na gaba zamu ga Mairo da Nakowa a

Kotu.

Sorry Sorry.

Vote and Comment Please.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

Biebee Isa.

DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣6⃣

Ya san Hajiya Mairo, shes sharp, tana

iya yin abubuwanta ta ci Case dinta da

Alhaji Nakowa, in kuwa Alhaji Nakowa yayi

loosing case dinnan, Zaid is doomed, kawai

bari ya sa a zo ayi mai Operation once and

for all, ya faki idon Majeed ya fita ya koma

BQ.

*

Waya takeyi da Maama tana jin footsteps

tayi saurin ce ma “Mamma i’ll call you back”

ganin so called Nura ne ya sata 6oyewa a

bayan Bishiya, da sauri ya ciro wayarshi ya

latso Armstrong, “Hello Arm, get your guys

ready, come to the Mansion for Operation”

sun dade suna magana ya gaya mishi

abubuwan da yake so suyi da daddare, a

k’arshe sai taji yana cewa “Yeah use your

masterkey, i’ll unlock the innerlock for easy

passage, and arm i dont want you to fuck

up, OK bye”. Ya juya da sauri ya koma cikin

Gida.

Da mamaki Najwa ta bishi da kallo, “This

Nura got some nerves” bari taje ta gaya ma

Majeed, da sauri ta bi bayanshi, har tana

harde kafafunta, to what Evidence gareki?

Inji Zuciyarta, Najwa mind your own

bussiness, Zuciyarta ta gargadeta, da sauri

ta tsaya chak, tana tunanin abunyi.

Da Daddare wurin k’arfe 11:30 na dare,

Majeed ya latso Najwa a waya, Firan k’auna

suke tayi, Majeed harda k’yalk’yalewa da

daria yakeyi, Najwa tace “Jaan, ka daina

daria da k’arfi, ni ka ga nan Hajjo da Na’ila

sunyi bacci kar in tadasu” dariya yayi sosai,

yace “ni kuwa zance ni kadai ke dakin, ba

kowa bane kusa dani, saboda kurma ke

kwance kusa dani, kin ga ko ko loudspeaker

zan sa inyi ihu abun ba damunshi zaiyi ba

don ba ji yakeyi ba” Nura yayi lamo ya rufe

ido kamar me bacci,sai ya samu kanshi da

jin haushin furucin da Majeed yayi, wato

shine Kurma ko? Sai yaji ma beda wani

amfani, wai shin da wa Majeed ke waya?

Dama yana da yanmata, a ransa yace “i’ll

find whoever she is, i’ll destroy her, i pledge

to destroy your happiness, sai muga ta

yanda zakuyi waya har kace ni ba kowa

bane”.

Najwa a ranta tace “ba kurma bane, yana

jin duk me kake cewa” a fili tace “still dai ka

ga ni ba ni kadai bace, kar in dauki Alhakin

su Hajjo” Majeed ya sauke numfashi yace

“Shikenan PureHeart, banji bacci amma dole

zanyi, Sleep Well Kinji?” ta murmusa kamar

yana kallonta tace “You to My Jaan” a tare

suka ce “I love you” sukayi daria, yace “sai

baki a waya ko? Gobe sai kin fada miin a

fili” dariya tayi ta kashe wayan. A bangaren

Majeed murmushi yayi a baiyane yace “I love

You PureHeart” Zaid ya maimaita kalman

“PureHeart” a zuciyarshi, ba a dade ba

Majeed ya bangas, Nura ya haska fuskar

Majeed yaga bacci yake, a hankali ya bude

k’ofar, yaje ya zare Sakatan Jikin k’ofar

Parlorn,yanda dasu Armstrong sunzo Key

kawai zasu sa.

Kasa bacci tayi, kowa yayi bacci, ta janyo

wayarta taga k’arfe 12 da wani abu, ta ji

tabbas an bude k’ofa, abunda ya faru da

rana ya fado mata, a hankali ta tako ta dan

budo k’ofar dakinsu, ta ga shigewar Nura

dakin Majeed, bayan ta tabbatar ya shige

ciki, ta fita cikin Sanda, ta saka duka

sakatan kofar, harda na sama wanda ba a

sakawa, ta koma kasa komawa bacci tayi,

har ga Allah ta ji wurin karfe 1, ana ta murda

k’ofan Parlor, alamun ana so a bude, amma

da yake ta sakata, ko motsi kofar beyi,

handle din kawai ke motsi, Armstrong ya ma

Nura text, why are we having hardtime

opening the Door? Are you sure you unlocked

the locks?( Meyasa muke shan wahalan bude

k’ofan, ka tabbatar ka cire Sakatan? )” cikin

hasala Zaid ya mai reply, “what are you

saying? I’ve unlocked them, just open the

goddam door( me kake cewa? Na cire mana,

dallah ku bude kofan)” Armstrong ya sake

k’okartawa, ya mai reply “Still not opening”

Zaid yayi tsaki ya mik’e da niyar zuwa ya

zare musu sakatan da ya san ya zare su,

Ringing din wayar Majeed ya katse mishi

hanzari, da sauri ya koma kan Gado ya

kwanta, Majeed cikin bacci ya dauka “Hello

PureHeart baki bacci ba?” a ran Zaid tsaki

yayi, sai da ya lallasheta kafin ta barshi ya

koma bacci, ta kira Majeed ne don ko Nuran

zai yi planning yin wani abu in idonshi biyu,

gwara Nuran ya ga ba bacci yake ba”.

Zaid na jin alamhn shigowan Messages din

Armstrong, Toilet ya shiga don mishi reply,

Cant we just shoot and scare the hell outta

them? They’ll open up( muyi harbi mana, da

munyi harbi zasu ji tsoro su bude mana

k’ofa )” cikin dacin rai

Zaid ya mai Reply “No dont shoot, abort

Mission, go home( aa banda harbi, ku watsar

da aikin kawai, ku tafi gida )” Armstrong ya

ba yaranshi Umurnin su tafi, Sosai ran Zaid

ya baci, waye ya saka Sakata? Ko wani ya

ganshi da ya je cirewa? Amma he made sure

sai da kowa yayi bacci yaje ya cire sakatan,

to ko wani ya san Plan dinshi ne? No

impossible, ba zai yiwu ba, tsaki yayi karo na

biyu, yana me jin haushin budurwar Majeed,

da bata kirashi ba da ya je ya bude musu

Kofar, da sun shigo sun ba Mairo tsoro a

basu duk wasu Necessary documents din da

suke so, kuma ya dau alwashin ko ina take

sai ya nemo ta ya wulakanta ta, he’ll make

sure they dont get eachother.

WASHEGARI

Ta dade tana tunanin yanda zata sanar

musu da batun, ganin zama ba zai mata ba,

ya sa ta yin ta maza zuwa inda Daddy da

Boy suke, shigarta Parlorn ya janyo

hankalinsu gareta, Majeed ya gaida ta fuska

sake tare da mik’ewa don basu guri da

Daddy.

Dakatar dashi tayi ta hanyar cewa “akwai

important maganan da nake so muyi Boy” a

nutse ya juyo ya samu guri ya zauna tare da

bata hankalinsa.

Sai da ta kalli Daddy kafin ta fara magana

“Dama akan Wannan yar iskar yarinyar nan

ne Nana bayan ha’intar mu da tayi, ta

salwantar ma Boy Credentials,a zahirin

gaskiya ni ban yafe abun da tai mana

ba,kuma shirun nu na nufin taci bulus, hakan

yasa na maka su Court, k’ilan Kotun zasu sa

ta fiddo maka da Takardunka, anyi zaman

farko last 2weeks, gobe ne zama na biyun

kuma ana buk’atar ku da ku halarci zaman

dan bada taku shaidar”.

Daga Daddy har Majeed sauraronta kawai

suke, ganin damuwa a fuskokinsu yasa ta

Murmushi tace “kar ku damu, nayi amfani da

kudaden nan na dauko babban Lawyer, so

zamu ci case din”. Kai a k’asa Majeed yace

” ki janye k’arar” da sauri tace “what?” yace

“Mummy ki janye k’aran”. Ganin ba wasa

fuskan Majeed yasa Mairo matsowa kusa

dashi ta hau lallami tana k’okarin nuna masa

fa’idar kai k’arar Kotun.

Cikin dan fada yace “Haba mummy sai

kace wasu Wanda basu san Allah ba, muna

musulmai ace mun kasa daukar kaddarar da

Allah ya nufo mana? Ni wallahi na hak’ura

da Takardun nan, na san su salwanta, da

Credentials din na nan da tun kafin ki san da

batarsu da Nana ta maido min dashi, abunda

kika kasa ganewa, ita karan kanta Nanan ba

ta sa wata ba ba, wani ne ya ya yaudareta,

wai tsaya ma, wani evidence kike dashi yau

in Nana tace ita bata san da zancen

credentials dina ba? We are talking about

Court here, where everything works only with

Evidence (Maganan Kotu muke, komai da Sai

da Shaida)”.

Mairo tace ” No Boy, we have Evidence, balle

ba zata k’aryata ba, Kotu kadai zata saka ta

nemo maka Takaddunka, da kuma cin

amanarka da tayi da aurenka a kanta, haba

ko da wannan ai an kamata redhanded,

saboda ina da Audio din kuma na tura ma

Lawyer na Saboda tsaro, ka taimakeni

Majeed, kasan ba wanda ya isa Kotu ta

kirashi ya k’i zuwa ko? Kotu tace kaje in

baka je ba, bansan me zai faru ba, Daddy

Please ka sa baki”.

Daddy kam kai ya jinjina, be san mesa

Maryam ke yanke hukunci ba tare da ta nemi

shawaran kowa ba, yanzu ta san da wa

takeson Ja? Alhaji Nakowa fa? Duk da ya

san Cin Case din nan ba k’aramin abu bane,

don dai kar ya kadar ma Majeed da hankali

ya hau lallashin shi, amma tabbas ran Daddy

ya baci yace “AbdulMajid, aikin gama ya

gama, Mummynku tayi shirme, babu yadda

zamuyi, wuri ya kure mana dole goben mu

halarta a zaman, kayi haquri kaji ko? Allah

ya ma Albarka”.

Majeed kai kawai ya iya kad’awa ga

mahaifinsa ya mik’e cike da bacin rai ya fita.

Tashi tayi zata fita, har ta isa daidai wurin

kofar dakinsu kenan ta jiyo daddy cikin

kakkausar murya yana cewa “MARYAM

DAWO NAN KI ZAUNA” da bata san

Muryanshi ba, da ba tace shine ba,cike da

mamaki ta juyo tana kalllnshi Galala, ganin

Fuskar shi cike da Umurni da rashin wasa ta

k’arasa cikin Parlorn ta samu wuri ta zauna,

tana me cike da mamaki wai yau ita Abba

Abu ke ba umarni har wani tafarfasa yake

kamar d’anyar ganda.

Daddy yace “nikam Maryam yaushe zakiyi

hankali ki gane jiya ba yau bane? Maryam ki

ma kanki fada? Kinsan wani irin danyen aiki

kika baro mana kuwa? Wa ke takara da

Nakowa? Wani me hankalin ne? Wato ke duk

abunda ranki ya aiyana miki shi kikeyi ko?

Ni da gidan nan bani da ikon sanin meke

wakana a ciki? Sai da ta baci nakeji, Wallahi

Maryam ki kiyayeni, ki fita idona”.

Ta inda daddy yake shiga ba tanan yake fita

ba yana kai aya ya mike a fusace ya nufi

bedroom dinsu.

Tsoro ya darsu a Zuciyar Mairo, ko a

shekarun baya da yake mata fada be mata

irin wannan ba, sosai ta tsorata, k’aryarta ta

k’are, things are falling apart, tunani kala

kala a kwanyar kanta, saboda tsabar

mamaki ko yatsunta kasa dagawa tayi balle

ta iya cewa wani abun.

Yanda taga Rana haka ta ga dare,

kwatakwata bacci kauracewa Idanunta yayi,

Abubuwa kala a ranta, ta kasa gane dalilin

da ya chanza Daddy dare guda, Lallai reshe

ya juya da Majuyi, wai yau ita Daddy ke

daga ma Murya, har ya kirata da

Sakarya,Tabbas dole ta tashi tsaye ta san

abun yi tun kan dare ya mata, a dayan

Bangaren karon farko da tsoron Haduwarta

da Nakowa ya darsu a Zuciyarta, Daddy duk

ya ruguza mata lissafi, bata san ya zata

kaya ba, a kan Idonta aka kira Assalatu.

*******

Sosai ta firgita da taji abinda ake so ta

fada a Kotu, ta kalli Dad da Mom kafin ta kai

dubanta ga Attorney dinsu, tace “Amma ba

haka bane ba fa, ni da kaina na dauki

Credentials din nan, na kai ma wani a waje,

ya za kuce ince bansan da zancen ba?” Mom

ta hau lallashinta tace “ita sam ba zata

karyata Majeed ba” Dad yace “Nana, do you

want to rot in Jail? In ba haka kikayi ba, za

a saka ki a Prison kuma i cant save you, ina

so ki ba Attorney Hadin Kai, zan sa a nemo

mishi Credentials dinshi, zan bashi aiki, kuma

zan rokeshi ya maidaki dakin ki, that is in

munyi winning case din, others ba zaki koma

dakinshi ba, kuma zaa kulle ki maybe life

imprisonment” Sosai ta tsorata, bata son

haka ya faru, bata son zama part of any of

this, kawai tana so ta koma wurin Majeed

dinta, a wuce gurin, a haka Dad dinta ya

dinga dorata, da kyar da sudin goshi ta

amince zatayi abunda suke so, haka aka

dinga karanto mata Irin Shaidar da zata

bada a Court Gobe.

(Anzo gurin,daidai gurin, who is excited?

Ghen ghen)

KOTU

Kotu ta cika ta batse da jama’a, kowa da

zaman da yazo saurara, mafi akasari

manyan Mutane ne abokan Huldan Hajia

Mairo Da Alhaji Nakowa, kowa ya hallara,

Nana ta k’i yarda ta kalli inda su Majeed ke

kallo, a ka gabatar da Shari’ah,

Ba tare da bata lokaci ba Alkali ya umurci

Lauyan masu kara da ya gabatar da Majeed

a gaban Kotu.

Majeed ya fito jiki ba kwari, yau ko Breakfast

beyi ba, tsayawa yayi inda aka tanada domin

bada Shaida. Lauyan Alhaji Nakowa ya nemi

da abasa izini ya yiwa Majeed tambayoyi,

nan take Kotu ta bashi dama.

Lauya Usman Baraji Me kare wadda ake

k’ara ya fara jefa masa tambayoyi kamar

haka:

“Ko zaka iya fadawa kotu Sunanka, inda

kake zaune da kuma Sana’ar ka?

Jim Majeed yayi kafin yace, “Sunana

AbdulMajeed Abba Abu, ni mazaunin garin

Kano ne, a halin yanzu bana aiki Amma ni

Architect ne”.

“Mallam AbdulMajeed shin menene Alakar ka

da Wacce ake kara?”.

Majeed ya hadiye miyau din takaici kafin ya

amsa da;

“Matata ce a da amma yanzu babu aure a

tsakanin mu, ba ma tare”.

Lawyer ya sake jefo mai tambaya”Wacce

take k’arar fa ko menene Alakar ka da ita?”

A takaice yace”Mahaifiya ta ce”.

Barrister Usman Baraji ya karanto ma Majeed

k’arar da Mahaifiyarshi tayi ya tambayeshi

“Mallam AbdulMajeed muna so ka gaya ma

Kotu, shin wannan bayani da na maka haka

yake?”.

“Eh ya mai sharia haka abun yake, babu

tangarda a bayanan da mahaifiyata ta ba ma

Kotu”.

Barrister Usman Baraji yace “tsakani ga Allah

kaga Lokacin da Nana Nakowa ta daukan

maka Credentials ta ba ma wani?” Majeed

yace “Aa bangani da ido na ba, amma da

bakinta tace ita ta dauka”.

Barrister yace “tambayar itace Kaga Lokacin

da ta dauka da Idonka?” Majeed ya hadiye

miyau yace “Aa bangani ba” Barrister yace

“Kaji Audion da ake ikirarin tayi a cikin

Maye?” Majeed yace “Eh da kunne na naji”.

“Mallam AbdulMajeed Kotu tagode da

wannan shaidar da ka bayar zaka ka iya

zuwa ka zauna har sai an sake buk’atar ka.”

Yayi Godia ya juya ga Mazauninshi.

Barr ya maida dubanshi ga Alk’ali yace ” Ya

Mai girma Mai sharia, a report din da muka

samu, sun nuna mana tambayarta yayi wata

ba ma Takardunshi, k’ilan ta tsorata da wani

abu ne ta amsa abunda ba tayi ba, sannan

kuma maganar Audio dinnan, muna so a

sanya ma Kotu taji, Nagode Ya Mai girma

Mai sharia “.

Alkali ya juya kan Lauyan Mairo ya umarce

sa da ya gabatar da shaidunsa.

Lauyan Mairo ya mike cike da isa ya ce

“Ya Mai Sharia, Shaidar mu Kenan

AbdulMajeed, kuma ya bamu tashi Shaidar,

shikenan shaidan da mu ke da”.

Cikin zafin rai Mairo tace “wani irin shikenan

Barrister Khalim? Ina audion? Ka musu

Playing”.

“Wani Audio kenan Hajiya”?

“Kutumar Babba burauba! yau akeyin ta, Bar

khalim bansan wasan banza dana wofi,

Audion da na tura maka lokacin da nazo

Office dinka, nace maka Alhaji Nakowa ya sa

anyi Attacking Aliyu Abokin Majeed an goge

Audion, don kar a samu matsala na zo har

Ofishinka na tura maka?”

Barrister Khalim yace “Aa Hajia Mairo, i dont

know what you are talking About, ni baki

turo min ko wani Audio ba”.

Wani tsallen da Hajia Mairo tayi sai da ta

chakumo wuyan Barrister Khalim, tace ” Ni

zaka mayar ‘yar iska? Kaika Nakowan ya

sayeka ko? To wallahi baka isa ka mayar

dani mak’aryaciya ba” Alkali ya tsawatar ma

Mairo, yace “ta yi taka tsantsan da yanda

take gabatar da kanta a gaban Kotu, Kotu ba

zata dauki wulakanci da shashancin banza,

Kotu ta ma Mairo gargadi da Babban Murya.

Mummy tace ” Ayi Hakuri Ya Mai Sharia,

raina ne ya baci, amma ba matsala in shi

ya sayar da Audion, ni ban sayar da nawa

ba, yana nan cikin Wayata” Alkali yace “ta

gabatar da Audion gaban Kotu” da Murmushi

tace “Minti daya” ta koma gun zamanta ta

bude Jakarta ta ciro Wayarta ta hau

latselatse, kusan mintina 5 shiru, take zufa

ya hau ketowa Mairo audio dinnan ko sama

ko kasa ta rasa shi a wayarta.

Da sauri ta kalli direction din da Alhaji

Nakowa yake, watsowa mata mairo

murmushin mugunta yayi, zufa ya shiga keto

mata, ta san k’aryarta ta k’are, a hankali

tace “Yau ake yinta” wurin Barrister Khalim

ta nufa, tace “Bar Khalim kai wa girman

Allah ka bada audio dinnan, kayi hakuri, i’ll

pay twice what they paid you”.

Barrister Khalim yace ” Ki daina bata min

lokaci, ki daina bata ma Kotu Lokaci, hakan

na nufin, there was never an Audio, you

made everything up” Zuciya taci Mairo, ta

hau surfa ma Barrister Khalim Zagi ta uwa

ta uba, Alkali ya sake tsawatar ma Mairo a

karo na biyu yace “Malama Mairo idan kina

da wata shaida da zaki gabatar to bismillah

kotu na sauraronki inko babu to kotu zata

zartar da hukunci a kammala wannan shariar

ba ku kadai bane”

Ai kamar jira take nan ta hau surfo balai da

masifa ba kan Lawyern kadai ba Kotun duka,

ta inda take shiga ba ta nan take fita ba,

zage zage take kamar sabon hauka,sai sakin

layi take tayi “ni zaka yaudara Khalimu?

wato Alhaji Nakowa yayi bribing dinka? Ya

saye Kotun gabaki daya, har Alkali tsohon

Najadu, to wallahi ba zata sabu ba, sai na

shayar daku madaran Mamaki dukan ku”

Alkali ya umurci YanSanda su kama Mairo,

“da sauri Majeed ya nemi Afuwa a madadin

Mahaifiyarshi, ya ba Alkali hak’uri, janta yayi

ya koma wurin Zama don jiran Hukuncin

Judge.

“Lawyern wanda ake k’ara ko kana da abun

cewa?” cewar Alkali, Barrister Usman Baraji

yace “Ya Ma girma mai Sharia, ina so Kotu

ta gayyaci Nana Nakowa gaban Kotu” “Kotu

na Bukatar Nana Nakowa a gabanta”

Alhaji Nakowa ya sadda kansa daidai yanda

Nanan zataji shi yace “go Nana, you know

what you must do” kai ta gyada ta tashi ta

je gaban Kotu ta tsaya, Bayan ta amsa

tambayoyin Gabatarwa Barrister Usman

Baraji ya fara mata tambayoyi kamar haka;

Add Vote

Nana Nakowa, shin kin dauki Credentials din

AbdulMajeed?” tace “Aa ban dauka ba” “ya

akayi kika tsinci kanki a halin da kike ciki

yanzu?” Nana ta juya ta kalli Mummy tace

“Wata rana Mummy ta kirani dakinta tace

ince ma Dad dina ya bani 5mil” sai nace

mata tayi hakuri, shima Daddyn beda kudi

yanzu, shikenan ta fara threatening dina, wai

in ban nemo mata kudi ba, zamana da

Yaronta ya k’are, zata k’ala min sharrin da

ba zan iya firda kaina ba, da nuna mata ni

ban san inda zan samo mata kudi ba ramfa

ya baci, the next day sai naji tace wai na

sace ma Majeed Credentials kuma wai ina

bin Maza”

Mairo mamaki ya hanata motsi, ta san ita

Makira ce, amma bata taba zaton Nana ta

fita iya Makirci ba, kirikiri Nana ta shirga

mata k’arya, kotu ya hau surutu, kowa da

abunda yake tofawa, sai da Alkali yace

‘Order’ kafin aka sausauta. Barr Usman yace

“Mungode Nana Nakowa, Ina son Kotu ta

kira mana Alhaji Ado Nakowa” Alhaji Nakowa

ya gabata gaban Kotu, Barr yace “Me ke

tsakaninka da Hajiya Mairo?”

Alhaji Nakowa yace “Matata k’awarta ce,

kuma mun taba wata kwangila da Alhaji

Abba Abu” Barrister yace “kace kana da

Maganan da kake so kayi a gaban Kotu kafin

a yanke Sharia?”

“Ya Mai sharia

“A lokacin da AbdulMajeed yake auren

Nanata, Hajiya Mairo tana amfani da son da

diyata ke ma danta tana amfani da hakan

matsayin jarinta kamar yadda ta gaya muku

da kanta, bata sati bata buk’aci kudi daga

gun diyata ba, in Nana ta nuna babu saibta

mata barazana cewa zata sa Majeed ya

saketa, haka diyata ta kare rayuwarta gidan

Abba Abu cikin Barazana, baya ga haka, ina

bin Hajia Mairo Naira Miliyan 30, ta karba

Miliyan 20 kamin auren danta da yarwurina,

Miliyan 10 kuma daga baya ta karba bayan

sunyi karayar Arziki, nima ba su ke gareni

ba a lokacin, amma saboda naga akwai

Alakar auratayyar yaranmu, nayi chukuchuku

na hada mata akan zata biyani in ta sayar

da wasu kadarorinta da tayi ikirarin tana

dasu, shine nake son Kotu me Adalci ta da

tace mata ta biyani, ina da bukatar amfani

da su”.

Kamar Robot haka take zaune, komai ya

dauke mata dif,ba ta gane komai, sai da

Majeed ya zungureta “Mummy yaushe kika ci

bashin Miliyan Talatin? Firgigit ta tashi

kamar wacce aka tsikara, kamar ta rufe

Alhaji Nakowa da duka tace “Babban Balaeen

chan, Kaci uwar rainin wayau Alhaji Nakowa,

dan kutumar babbar buraubaka wani yace ka

bamu Miliyan 20 dinnan? Ba lokacin da kuke

son Majeed ya Auri Nana bane kuka kawo

mana Miliyan Ashirin din har gida ba?

Saboda kai baka tsoron Allah, kuma da yake

karya cike yake a tunbinka zaka ce Miliyan

30 ne, kuma wai bashi, to Mortgage bank ma

yaci Ubanshi, shege Makaryacin banza, sai

ka danneni ka karba, karfi yaci daru ya

danne, Mutumin banza”.

Da k’yar Alkali ya sa Mairo yin shiru, ya juya

ya tambayi Alhaji Nakowa Shaidansa na

Maiaro ta karbi Bashi a gunsa, yace ” kwarai

kuwa ina dasu ya mai shari’ah, ganin da

nayi Miliyan 20 da ta karba da farko bata

fara biya ba, hakan yasa naji shakkun sake

bata wasu kudaden don nima lokacin ina

fama da kaina, Don haka nace sai ta sa ka

hannu a wadannan takardu guda biyu, sai da

tayi signing gaban Matata Aminiyarta, da

wasu k’awayensu su 3,” Alk’ali yace a

gabatar da takardu gaban Kotu, Sakatare ya

amshi takardun daga hannun Alhaji Nakowa

ya ba mai shariah”.

Sosai Alkali ya karance takardar sannan ya

sa aka mik’awa Mairo ta duba ko tana da

Ja,

Cikin tashin hankalin da tun da tazo duniya

bata taba ganin irinshi ba tace”WALLAHI

WALLAHI ALKALI BAN SAN WANNAN BAYANI

BA, TABBAS WANNAN SA HANNU NA NE

AMMA NI BA NI NAYI BA, wani ne yayi

fabricating Evidence dinnan, dis is a Forged

Signature”.

Alk’ali yace “Alhaji Nakowa kana da Shaida,

baya ga takardun nan?”

Alhaji Nakowa yace “Shaidun da ke jikin

Takardun, Hajia Sugrah, Hajiya Zarah Bukar,

da Hajiya Suwaiba wanda suke ce ma Mom

fateey, kuma duk suna cikin Kotun nan mai

Albarka”

Alk’ali ya bukata da su fito gaban Kotu, ya

musu tamboyi suka amsa, suka shirshirga

tasu karyan, suka ce a gabansu akayi a

garin Abuja, tayi Signing din kudin a kan

Idanunsu, kuma Alhaji Nakowa ya bata kudin

kan idanunsu.

Mairo ta hasala ta chakumo Hajia Suwaiba

don sun fi shiri tana jijjigata “Wallahi k’arya

suke man, kuji tsoron Allah Hajia Suwaiba,

ku tuna Zaman mutunci da Amana da mukayi

da juna, kar Alhaji Nakowa ya siyeku kuyi

min kazafi” Mom Fateey ta bangajeta tace

ba wani “kazafi, abunda muka gani ne muka

fada, mu muna bayan gaskia”.

Bakin Hajiya Mairo be mutu ba, nan ta hau

surfa ruwan zage zage da tsine tsine, harta

Kotun da Alkalin sai da ta zage tas, Majeed

ya ji kanshi na barazanar fashewa, a hankali

ya zame jikinshi ya bar Kotun.

Kotu ta dau Hayaniya, kowa da abunda yake

tofawa, Alk’ali yayi ‘yan rubuce rubucen shi,

Alkali ya umurce kowa da yin shiru, da k’yar

aka samu kowa yayi shiru, Alkali ya zartar

da hukuncin shi kamar haka;

Bayan Kotu ta saurari bangarori biyu, na me

k’ara, da wadda ake k’aran, Kotu tayi watsi

da k’arar Hajia Mairo a matsayin Kara Mara

kan Gado, saboda rashin kwararun hujoji da

Shaida, sannan kuma Kotu ta ci tarar Hajia

Mairo Naira Dubu Dari Biyar don ta ci Zarafin

Kotu ta Wulak’anta Kotu, Sannan kuma Kotu

ta Umarci Hajiya Mairo da ta biya Alhaji

Nakowa kudin sa Miliyan 30 a tsakanin

Watanni Uku, in ba haka ba, Kotu zata

kwatar mai hakkinshi da karfi, kuma zata

fuskanci fushin Hukuma, duk wanda

Hukuncin nan beyi mai ba, to yana iya

daukaka k’ara zuwa Kotun K’asa” A nan

Alkali ya kawo k’arshen Shariar Hajia Mairo,

da Alhaji Nakowa Kotu, Alkali ya mik’e kowa

ya mik’e.

Kasa Motsi tayi ta kasa yarda, komai sai

kware mata baya yake, tana ganin Alhaji

Abba ya fita a fusace, ina ma zata iya

hawaye, tana kallon Alhaji Nakowa da

Iyalanshi suka tako har gabanta da

Murmushin Farincikin yace

“Da wa ta 6are Hajiya Mairos? Na gaya miki

sai kinyi nadama, tsautsayi ya sa ki ka

makani kotu bayan baki da ko sisi, while kin

san komai yanzu in baki da kudi ba a

damawa dake, bansha wahalan komai ba,

har kawayenki, da Miliyan daya kachal na

sayesu, hahah kin ban tausayi fa, anyway

duk inda zaki nema min kudi ki nemo min,

kafin kotu ta Wulakanta min ke, hahah ku

mu tafi”. Nan suka barta zaune da ta rasa

abun yi, da k’arfi ta sake Ihu sai da Kotun

gaba ki daya ya Amsa.

*****

Ghen Ghen Ghen……

Najwa kina rusa ma Zaid Plans ko? Allah ya

sa ya gane kece, he’ll roast your skinny ass

back to NewDelhi India Lol.

Haha, ya kuka ga Shari’ar Nakowa da

Mairo?

Anya Mairo tayi deserving haka? Wannan

sharri kala kala? Who wants justice for

Mummy? Mummy kar kiji komai, akwai

Allah.

A bar Mairo haka?

Yayyy Loverz, i made it, dama nace zaku

jini yau, so please ku cigaba da mun Uzuri

kunji? Makaranta, ba kullum zaku dinga

samun post ba, maybe once a week, but i

know you love me zaku min uzuri, so please

bear with me.

And Yay Wattpadians, You know you are the

best right? ADAY yayi hitting 6k votes

Wallahi naji dadi sosai, lets keep rocking it,

ILYSVM nagode Sosai, Allah ya samu

Aljanna duka, da masu voting da Ghost

readers din, amma dai ghostreaders, hmmm

nayi shiru.

Please Vote and Comment line by line.

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

DADE ANA YI….sai gaskia💭

NA

BIEBEE ISA

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

Pg2⃣7⃣

Yana shiga Gida ya ci karo da Najwa,

yanayin da ta ganshi a ciki ya bata tsoro, ko

da aka gano Asirin Nana ba ta karanci

abunda take karanta a fuskarshi ba yanzu,

tsoro ya bata, a hankali ta matso kusa dashi

huci yakeyi a hankali, yak’i kallonta, yak’i

bari su hada ido, cikin sanyi tace “Meri Jaan

(Rayuwana)” runtse idanunshi yayi, be ma

san su hada ido, saboda yanayin da yake

ciki, hannu ta sa ta kamo hannunshi, janshi

tayi har gaban 2sitter, zaunar dashi tayi, ta

wuce kitchen da sauri, roban Ruwa me sanyi

ta dauko da Cup, tsiyaya mai tayi ta mik’a

mishi, beyi gardama ba ya karba cup din ya

kafa kai, kurba uku ya shanye ruwan tas,

ganin haka ya sa ta karbi Cup din, kara

tsiyaya mai tayi ya sake karba ya shanye

tas, zama tayi dan kusa dashi ta fara nanata

” Inalillahi wa ina ilaihir rajiun” tayi ta

maimaitawa har sai da Majeed ya fara bi,

haka sukai tayi har tsawon Minti Uku, kafin

ya samu dan natsuwa.

Daddy ya shigo Gidan shima a sukwane,

hankalinshi shika tashe, Najwa ta tabbatar

abunda ya samu Majeed shi ya samu Daddy,

shima ruwan Sanyin ta dauko mishi, ta

tsiyayya mai, ta bashi ya sha, a hankali yace

“Nagode” wucewa tayi daki ta sanar ma

Hajjo, halin da ta ga Daddy da Majeed,

mikewa tayi tana sallalami, fita tayi Parlo,

“Abba me ya faru?” a raunane ya dago kai

ya kalleta, a hankali ya kwashe komai ya

gaya mata, a fili take maimaita “Inalillahi wa

ina ilaihir rajiun, ita ko Hajia Mairo me ya

aiketa? Inace an bar maganar da dadewa?to

yanzu meye abunyi?” Daddy ya sauke

numfashi yace “Biyan Kotu kawai zaayi,

amma ban san inda zamu samo Kudi ba”

Majeed ya nisa kafin yace “A sayar da Gidan

nan” Daddy yace “AbdulMajeed” Majeed ya

katse shi ta hanyar cewa “Daddy, ina zamu

samu 30.5 Million? Daddy, mun rasa komai

fa, ina ganin mu sa Gidan nan a Kasuwa din

gudun cin Mutuncin Alhaji Nakowa da Kotu”

Daddy ya jinjina kai yace “Haka ne” Hajjo

tace “Sai mu koma chan Rijiyar Zaki ko?

Tunda tsaf gidan zai kwashe mu duka” haka

suka cigaba da maganan sa Gida a Kasuwa

har Mairo ta shigo ko Sallama babu.

Kallo daya zaka mata kasan cewa damuwa

ta cika zuciyarta fal, tayi kalar tausayi, duk

ta fita hayacinta, kujera ta samu dan nesa

da Hajjo ta zauna tana mayar da numfashi,

Majeed ya so mata magana amma ganin zai

kara cikin damuwarta ne kawai ya sashi yin

shiru, Mairo ta ja tsaki karo na ba a dadi, ta

dan muskuta tace “Sai na shayar da Alhaji

Nakowa Madaran Mamaki wallahi, sai na

nuna mishi ruwa ba tsaran kwando bane, in

banda iskanci, ni zai yi wa Sharri? Shi kudi

ko? Duk ya siye su Suwaiba, To wallahi sai

na daukaka k’ara, sai munje Babban Kotu da

su” dukkansu tsura mata idanuwa sukayi,

chan Daddy yace “Enough Maryam, please,

mun yanke Hukuncin zamu Saida Gidan nan,

a biyasu kudin su, wata Shari’ar Sai A

lahira” wani ashar Mairo ta laliyo, tace “in

sun isa hadari ya daukeni, ba su isa mu

saida gidanmu ba, ba su isa bane”.

Muskutawa Majeed yana rufe idanuwanshi a

hankali, saboda zafin ds suke yaji muryan

Daddy na cewa “Na bar sakar maki komai na

Gidan nan Maryam, na bari, ni zan ja

ragamar Gidana, daga yau, ba zaki sake yin

wani abu ba tare da sani na ba, ba zaki sake

yanke hukunci ba tare da shawarata ba, in

kuma kikayi, Maryam, zan baki mamaki

Wallahi” yana kaiwa nan, ya tashi ya kalli

Maman shi, ya mata alama da zai shiga

daki, kai ta gyada mai, ya wuce ciki, Hajjo ta

kai dubanta ga Mairo tace “Hajia Mairo,

hakuri zakiyi ku koma Gidana, dakunan zasu

ishemu duka” wani irin harara Mairo ta buga

ma Hajjo, kafin ta ta figi gyalenta tare da

Mukulli ta fita.

Duk suka bi bayanta da Ido, Hajjo tace da

Majeed “Abdallah, Allah ya maka Albarka, kar

ka sa damuwa a ranka, tashi ka shiga daki,

ka huta ma ranka, komai yayi zafi

maganinshi Allah, tashi ka tafi” Majeed ya

tashi ba tare da yace mata komai ba ya

shige dakinshi, tashin hankali bai sa ya tuna

wani Nura ba, be ma lura be dakin ba, Zama

yayi kan Gado tare da fashewa da kuka,

wannan wani irin bala’i ne, ya Allah ka kawo

mana k’arshen wannan Musiba, Allah ba mu

ds wani wayau sai wanda ka bamu, Allah ka

sa muci Jarabawarmu” sai da yayi kuka san

ranshi, kafin ya zube kan Gado.

****

“M y Forever, kinsan ya nayi kwanakin nan

ba tare da na ganki ba? Eyi? A daddafe nayi

su, i couldnt even focus on the work, kawai

naji ba zan iya k’ara kwana daya ba tare da

na ganki ba, na bar aikin nazo Kano”

Wani Murmushin jin dadi Ziyada keyi, Allah

ya san son da take ma BawanAllahn nan, duk

wani magana da yayi yana ratsa kwanyarta

da duk wani sasan jikinta, bakon yanayin da

bata saba ji ba takeji, tana jin in bata auri

Zaid ba, ba zata iya rayuwa ba.

Kallon da take binshi da shi ta kasa cewa

komai.

Zaid a zuciyanshi ranshi s baci, sai ya kai

zuciyarsa nesa yake iya furta mata kalaman

da yake gaya mata, balle yau part din da

Armstrong ya bashi ya mai nauyi, shifa be

sonta, be taba jin sonta ba, yana amfani da

ita ne don ya idasa ruguje Mairo, in komai ya

kare be ma san me zaiyi da ita ba, yasar da

ita zaiyi kamar abu wanda bayaso, ko kuma

a mata fyade, Yes Zuciyarshi ta raya mai,

Fyade kawai zai kashe Mairo da ranta, duk

wani dan Gidan zai mutu da bakincikin

Fyaden da aka ma Ziyada, shi yafi karfinta,

be iya hada jiki da ita, duk dai ta k’are,

Armstrong zai ba ita ya mata lagalaga,

wannan shu’umin murmushin yayi yana

cigaba da tunaninka ya kusa mancewa da

ita.

” Ka aureni” abunda kunnuwanshi suka jiye

mai kenan, ranshi yayi tsananin baci, ya

zaayi, wannan banzar yarinya ta ta6a

tunanin zai aureta, shes dumber than he

thinks, har ta kusa gane chanzawar

yanayinshi, tace “ranka ya 6aci ne don nace

ka aureni?” da sauri ya k’ak’alo murmushin

da iyakarsa la66a yace “Farinciki ne ya

lullubeni, Aurenki zai fiye min komai dadi,

Nagode”. Ziyada Dadi kamar ya shideta jin

kalaman Zaid, tace “yaushe zaka turo?” sai

da gaban Zaid ya fadi, amma ya dake yace

“yaushe kike so na turo?” Dadi ya kusa

sakata daka tsalle, tace “zan gaya ma

Yayana, sai suyi maganar, sai ka turo ko?”

kafada ya dan daga, yace “Your wish

Milady”.

*

**

“Zaku ban hanya na wuce ko sai na faffala

muku mari?” Cewar Mairo a fusace, daya

daga cikin Securityn yace “ke kinsan inda

kike maganar nan kuwa? Ki kula fa kar

bakinki ya ja miki. A fusace tace “Ya ja min?

Ka san ya nake da Oganniyar taku?

Aminiyarta ce tun kafin tayi tunanin zata auri

His Excellency, tun wuri ku ban hanya in

wuce” dayan yace “da da yanzu ba daya

bane, masu appointments kadai ke shiga, ba

zaki shiga ba sai an bamu izini, so in kina da

Number dinta, ki kirata, mu kawai masu bin

dokana” nan Hajia Mairo ta fara rattafo

Masifa “Dokar Banza, dokar Wofi, aiko

karshen aikinku yazo”.

Horn sukaji daga cikin Gidan, da sauri suka

bude, Amjad ne cikin wata Bak’ar Mota Mai

Tint, duk da bata san waye cikin Motar ba

saboda bak’in Gilashin sai ta hau sa mai

Hannu, har ya sa kai zai fita daga Gidan, ya

ga ana Daga mai hannu, ya kallo Matar dake

kusa da wata Corolla yagane Hajia Mairo ce

Kawar Mom dinsa, jiki ba kwari ya fito, da

doki tace ” Yauwa Son In-law, wadannan

yan iskan Masu Gadin ne suka hanani shiga,

nafi 20mins tsaye, ka koresu, ka sallamesu”.

Amjad ya dan Murmusa yace”Aikin su kawai

sukeyi, inda sun barki kin shiga suna iya rasa

aikin nasu”.

Ba haka taso ba, sai dai ta chanza Zancen

da tambayar Her Excellency, a tak’aice

yace”tana ciki, ku barta ta shiga” juyawa

yayi da niyyar komawa cikin Motarshi ta

tsaidashi da “Fita Zakayi?” a takaice yace

“Eh” ta dan kwantar da Murya tace “ko zaka

dan hakura mu shiga ciki, maganan da nazo

da ita ta shafeka” shigewa Motar yayi tare

da kunna mata wuta, daidai ita ya tsaya yayi

wining glass yace “Ki shiga Mom na nan, duk

me ta yanke daidai ne” daga nan ya ja

Motarshi ya wuce, Mairo bata da lokacin

tunanin Changing Amjad ta galla ma

Securities din harara tace “Sai ku barni na

wuce ko?” ta fada Motar ta, suka bude mata

gate din ta shige ciki.

Sai da tayi kusan Minti 35 tana jiran Her

Excellency kafin ta shigo Parlorn da aka

sauke Mairo, Ba kamar zuwansu na farko ba,

da sune har Bedroom dinta, yau wani parlo

aka sauketa kuma Hwr Excellency ta shigo

tana yaushi tana yamutse fuska, Mairo ta

hau kwasar Gaisuwa, kamar ba zata amsata

ba ta amsata, karo na farko da Mairo taji

Shakku, ta fuskanci wulakanci kawai Maman

Amjad ke mata, amma da yake itace

mabuk’aciya, bata ji haushi ba tace “Your

Excellency, dama Maganar Yaran nan ne,

Amjad da Ziyada, naga sun fahimci Juna,

kuma suna son Juna, me zai hana azo ayi

auren nan tun wuri?” wani kallo ta mata da

ya sa hanjin cikin Mairo kadawa, hanjin

cikinta sun fara sabawa da tashin hankali, ba

wuya sun kada, kamar ba zatayi magana ba

tace “ta ina suka fahimci Juna? Tunda yaje

so daya ya kuma zuwa?” Mairo na in ima

tace “suna waya” tace “Haka Makaryaciyar

diyar taki tace miki?” Mairo baki ya hau

rawa, tace “tsaya kiji Hajia Mairo, Amjad ba

zai auri Karuwar diyarki ba, duk abubuwan

da takeyi a Baze University a tafin hannun

mu suke, ni da kaina na sa aka min bincike

balle ace sharri aka mata, balle ba abun

mamaki bane don diyarki ce, meye baki ba

Mairo? Menene bakiyi ba lokacin yarintar ki,

ban manta ba fa, i was even stupid to think

zan hada zuria dake, so please tun da

sauran Mutuncinki a idanu na, ki bar

maganar nan kawai”.

Add

Wani irin tashin hankali Mairo taji, Ziyadarta

aka ma sharri? Like duk cikin yaranta mata,

itace daban, tafi su natsuwa, Zaineema

rashin hakuri, Zinatu rashin kunya, amma

Ziyada magana ma bata dameta ba, ba kuma

ta da saurin sabo, amma itace ake ma

sharri? Wani Zuciya na tunzurata ta watse

ma Her Excellency karama, wani zuciyar

kuma na tausarta, “kari kiyi saurin daukan

hukunci, Her Excellency kadai ne best choice

dinta na samun kudi, so ba zata wargaza

lamarin ba, hakuri ta ba Zuciyarta kafin ta

fara magana cike da ladabi da biyyaya.

” Your Excellency, kinsan shaanin yara ba a

shiga tsakanin su, i’m sure dan karamin

problem ne, kuma na san zasuyi sorting out

da kansu” Her Excellency ta murtuke fuska

tace “Wai ke dak’ik’iya ce? Ko fahimta na ne

baki ba? Amjad ba zai auri ragowar Garada

ba, akai kasuwa, ko mata sun k’are, Amjad

ba zai auri diyarki ba” Hankalin Mairo ya

sake tashi, ta dai sake nutsuwa tace “Ok

naji, abar maganar Aure, but donAllah your

Excellency, ki dan ban wani abu, like Million

2, ina so na daukaka k’ara ne zuwa babban

kotun duniya” Her Excellency tayi daria tace

“Iska na wahalar da mai kayan kara, wato

baki daddara bane kenan? Kina nan kin

zama abun daria a gari, ai sjariar ku Live aka

nuno shi, shiyasa ma na sake tsorata dake,

bayan abubuwan Alheri da Alhaji Nakowa ya

muku, ki rasa abinda zaki saka mishi sai

Sharri? Kika lak’a ma diyar shi Sharri? Ko an

gaya miki kowa kamar diyarki ce? Haka kuke

saka Alheri da Sharri? Wato haka misali in

anyi aure da Amjad din haka zaku laka mai

sharri? To ba zai yiwu ba, mu ba tsaran yinki

bane, kikace zakiyi mana abunda kika ma

Nakowa, sai kin karashe miserable life dinki

kina nadama, sai na karar da Family line

dinku, so tun muna shaida juna get lost”.

Ran Mairo ya baci amma ganin fushi ba nata

bane yasa ta zube kan guiwowinta biyu, tana

rok’on ta da ta bata ko da bashi ne, amma

haka Her Excellency ta shafewa idonta toka

ta karta mata rashin mutunci karshe tace ”

ko ta tashi ta fitar mata daga Gida, ko ta sa

Security suyi mata wulakanci, su tozarta ta”

ganin ba kirki ne dasu ba, kuma in ta tsaya

mata rashin mutunci, to abun zai sake kwaye

mata, saboda wa ya isa ya ma matar SSG

wulakanci? Jakkarta ta fizga da karfi kana ta

juyo ta wurga ma Her Excellency kallon

zamu sake haduwa, kafin ta fita fuuuuu.

Kwantar mai da hankali take tayi tunda ta

kirashi a waya, be san meyasa ba, a duk

lokacin da yake magana da Hajia Aynarh,

yana samun kanshi cikin nishadi, a yanzu da

yake cikin tashin hankali, sai ya tsinci kanshi

cikin saukin zuciya, yanda take jawo mai

hadisan daukan k’addara ya k’ara burgeshi,

abunda yafi burgeshi shine, da yaji tace zata

taimaka mishi da ko da Miliyan biyu ne, ta

burgeshi matuk’a, amma sai yace da ita

“Hajia Aynarh, nagode kwarai da irin

guddumuwan da kike bani da Iyalina a duk

lokacin da bukatar hakan ya taso, amma

gaskia ba zan amince da wannan ba,

mungode Allah ya saka da Alheri, Allah ya

baki ladan niyya”. Shagwabewa tayi kamar

tana gabanshi, tace “Haba Alhaji Abba, kar

ka min haka, wallahi nayi niyya, nasan ba

zan iya biya muku bashin nan ba, amma a

dan rage, DonAllah kar ka juya hannun

kyauta baya”. Murmushi ne ciro yayi yace ”

dagaske ba zamu amsa ba, mun sa Gidan

nan a Kasuwa, za a siyeshi fiye da Miliyan

20, InshaAllah zai kai 30 din, karki damu

mungode”. Ba yanda batayi ba, amma Fir

Alhaji Abba ya k’i, chan tace “to shikenan,

zan dai zo in tafi da Muhsin da Zinatu

Gidana, sai su cigaba da zuwa Makaranta

daga Gidana, don kar tashinku yayi affecting

dinsu, ka tuna barinku Abuja, da k’yar aka

samu Zinatu ta sake”. Alhaji Abba ya jinjina

kai yace ” to kinga wannan ba zan hana ba,

dama basu san da zancen ba, Yaronki kadai

ya sani, ya hana a gaya musu” Hajiya

Aynarh tace “Allah Sarki AbdulMajeed, sosai

yake bani tausayi, Allah ya kara mai hakuri

da dangana, InshaAllah zan zo Bayan Laasar

na dauke su” haka sukayi Sallama.

B e san tsawon lokacin da ya dauka a haka

ba, yaci kuka har ya gode ma Allah, rashin

aikinyi ya fi daga mai hankali, yanzu in suka

bar Gidan nan, ya rayuwansu zai kasance?

Abinci zai musu wuya? Ya zaiyi ya kula da

Mahaifanshi da k’anen shi? Hannu biyu ya

daga sama yana rok’on Allah sauki a

lamarinsu, kafin ya tashi ya dauro Alwala

don zuwa Sallahr laasar.

A gajiye ta shigo Gidan, ranta a bace, kafin

ta dawo gida sai da ta biya Gidan Hajiya

Aliya kawarta, tarban da ta saba mata ba irin

shi tayi mata ba, ta gaya mata yanda sukayi

da Matar SSG Hajiya Aliya bata yi mamaki

ba, Mairo ta bukaci dubu dari biyar gun Hajia

Aliya don ta koma gun Bokansu don ya mata

maganin damuwarta duka, Hajia Aliya ta

juya mata baya, nan suka hau sama sukayi

zage zage tare da tona ma junan su Asiri,

karshe dai yaran Hajia Aliya suka ma Hajiya

Mairo rashin kunya da wulakanci suka

wurgota waje, Daki ta wuce straight tana

zuwa ta zube kan Gado, komai ya juye mata,

bata da kowa, bata da Mafita, bakin cikinta a

saida tangamemen Gidan nan, anya ba zata

kira Alhaji Nakowa ta nemi sauki gunsa ba?

Kar dai ya ga gajiyawarta ya rainata, Tsaki

tayi ta fada toilet da tunani dubu dari da

chasa’in a kwanyar kanta.

Na’eelah ta zagaya baya don kiran Zaid a

waya, tun jiya ba su hadu ba, Ringing daya

ya dauka, a lokacin ya koma makeup wurin

Rita Phillips, kamar bazai dauka ba yayi

excusing kanshi ya dauka, cikin yanayinshi

yace “Eelah” tace “akwai Matsala, Dad dina

ya gano ina Kano, ranshi ya baci, yace in

dawo Gida, kar ma in sake inje PH, already

ya min Booking ticket,yana expecting dina a

Abuja by 8, i’m scared, he sound soo serious,

kana ina Z?” cikin rashin damuwa yace “then

ki koma, just write them a note, tell them

zaki je Kauye dubo Danginki, in kin ganesu,

zaki dawo ki tafi da Nura, su taimaka su

kular miki dashi kafin lokacin dawowarki”

tace “nagane, so yanzu yaushe zaka dawo

Gidan, ina ganin Sun rasa case dinsu na

Court, Majeed ya dawo hankali a tashe,

yanzu ma Mom din ta dawo, daga gani Plans

dinka are in place, I want to see you kafin na

tafi please” ya danyi guntun tsaki, yace

“makeup ake min, kinsan ana daukan atleast

5hours anayi, i’ll come see you a Abuja As

soon as Possible” cike da kwantar da murya

tace “Please, let me see you before i go” dan

shiru yayi, ya ga ta taimaka mishi sosai,

kuma tana sonshi, bawai don tausayinta ba,

sai don ya rama mata halacin da ta mai, don

shi beson zama indebted to others, yafi so in

ka mishi abi ya rama maka, yace “Ki rubuta

wasikar, ki aje inda zasu gani, i will send

Arm to pick you up” be jira cewarta ba ya

kashe waya.

Wayar ta bi da ido, tana ba kanta tausayi, a

fili tace “Ina sonka Z, sonla ya makantar

dani, ina abubuwa marasa kyau don kai, har

cutar da bayin Allahn nan mukayi wanda

zuciyoyinsu ba komai sai tausayi, Allah ka

yaye min son Z, Allah ka yafe min, da sauri

ta chusa wayar tsakanin ta, ta waiga baya

taga ba kowa ta wuce ciki don rubuta

wasikar.

Najwa ta fito daga maboyanta, tunda taga

Naeela ta zo baya ta biyota, zarginta ya

tabbata gaskia, Naeela da Nura ba abunda

sukace sune ba, Iphone 6 ke hannun Naeela,

aiko ba karamar mutum bace, kalamanta na

waya tayi amanna da Nura take, saboda tayi

amanna be gidan, kuma ta dan fahimci wani

abu, Nura shine ke son wani abu da Familyn

su Majeed, ita Naeelah kawai tana taimaka

mai ne saboda tana sonshi, ta jinjina kai,

InshaAllah ba zasu ci nasara kan Majeed

dinta ba, zatayi protecting dinsu InshaAllah,

da taimakon Allah zatayi exposing Nura

Kirikiri, a fili tace “Allah ka taimakeni”.

I N D I A

Tunda ya dawo aiki, kanshi ke sarawa, zama

yayi kan sofa ya dafe kanshi da duka

hanayenshi, yana so tunano wani

abu,tunanika kala kala suka shiga dawo mai

a hankali, amma ba zaice ga abu daya

k’wak’wara ba, ya dan gano wani abu, shi

dai ya san yana da Danuwa daya da kuma

Mahaifiya amma sam kamaninsu sun bace

mai, haka kurum yaji yana son zuwa Nigeria

gun Matarshi da Yayanshi, bayan nan ba zai

iya baiyana me yake ji ba, haka Maama ta

iske shi, itama duk wani sukuku take, “Sannu

da Zuwa Papi” cikin yanayi yace

“Yesmeenah, ina so naje Nigeria” ta numfasa

tace “wallahi ,tun da na tashi nake jina wani

iri, sai tunanin Gida nake, Ko Umma na da

Abbana suna da rai? Ko sun bar Adamawa?”

ita atleast ta tuno nata Mahaifan, ta kuma

gano inda suke, bayan nan ba abunda zasu

iya tunawa game da Dangin Sada ko Garin

da Sada ya fito, kwantar mai da hankali ta

hau yo tace “Papi, mu cigaba da Addua,

yanda muke iya tunasu, a hankali komai zai

dawo mana, InshaAllah, mu k’ara hakuri,

Muje kayi wanka na kira maka Diyarka ku

gaisa ko?” kamar dan yaro ya gyada kai, ta

kamo hannunshi suka shige daki.

tart from the beginning

K A N O

Kan Idanunta Naeela ta shiga wata Mota

bak’a, nan zarginta ya tabbata, they are not

what they say they are, sunada wani

mummunan k’udiri, to wa zata fara sanar

mawa? Majeed? Ko ta gayama Hajjo? Amma

ai bata da wani Hujja, jiki sa6ule ta shiga

cikin Gidan, akwai Mutane amma kamar ba

kowa, chan dakinsu ta shige.

**

Hajiya Aynarh tayi Sallama a k’ofar Parlor,

kowa duk na dakinshi, ganin sunyi nisan

kiwo ne yasa ta daukar Waya ta kira Alhaji

Abba, a lokacin yana toilet, Mairo jiki ba

kwari ta dau wayan, ganin Hajia Aynarh ne

ya sata dauka rai a 6ace “Hello Alhajina”

Mairo ta fusata tace “Alhajin Ubanki,

munafuka tsohuwar kilaki, zaki kira min Miji

kice mishi wani Alhajinki?” Hajiya Aynar ta

murmusa tace “Fito Parlor ki gaya mun duk

abunda kike son fada min a fuska na, amma

ki kula, kwanan nan, saurin hannu ne dani,

abu kadan sai in mari Mutum” dip ta datse

Wayan, ta bar Mummy da takaici, oh tana

ma Gidanta? A Parlornta? Aiko yau za ta

sauke ma Hajiya Aina duk wani abu da ke

kanta, yau sai taci Ubanta, da sauri ta dira

kan Gado ta fita Parlo a fusace.

Daidai da fitowar Majeed, kallo daya

Zaka gane yana cikin damuwa, ganin Hajia

Aynar sai ya fadada murmushinsa, ya

k’araso, daidai da isowan Mairo, ta ja ta

tsaya, bata son abunda zai k’ara ta6a

Majeed, Yaron ya ga rayuwa, abunda tayi

niyyan yi ta fasa, juyawa tayi, yana Hangota

ya kirata “Mummy” cikin sanyin Jiki ta

k’araso, ta zauna, duk aka gaisa da Hajia

Aynarh har Daddy ya fito, Hajiya Aynarh tace

“Ina Yaran nawa? Suzo mu tafi ko?” Hajia

Mairo ta wurga mata wani kallon ina zaki

dasu? Cike da Kissa Hajia Aynarh tace “Hajia

Mairo, dama gani nayi tunda yaran nan basu

san meke faruwa ba, why not in dauke su

mu tafi Gidana, yanda Tashin ku ba zaiyi

affecting dinsu sosai ba?” Mairo ta galla

mata harara tace “Sai kuma nace miki ina

bukatan taimakonki, yarana yarana ne ni

kadai, ni zan kula dasu, ni zan san yanda zan

kwantar musu da hankali, kuma zanyi kai

dominsu, ba zamu ta6a loosing Gidan nan

ba” Majeed ya daure fuska yace “Mummy,

Please Not now” Daddy yace “jeka hado

musu kaya, har Uniform, tace daga Gidanta

zasu dinga Zuwa Makaranta” ba gaddama

Majeed ya tashi ya shige dakin Yara.

Ya gansu zaune suna kallon Cartoon, yace

musu “Kallo akeyi? Wa zaijr Gidan Aunty

Aynarh? Muhsin yace “Niiii” Zinatu tace “bani

ba” Majeed ya samu wuri ya zauna kusa da

Zinatu yace “Tab yarinya zakiyi Missing,

kinga Gidan Aunty Aynarh kuwa? Babba,

harda Swimming Pool, kuma ana cin Dadi,

gashi kullum sai taje Shoprite, zata siya

muku teddies da sauran kayan wasa Woww,

nima da zata je dani da naje, amma tace da

ku zata tafi” wani sashe na Zinatu na son

zuwa ko don abubuwan da Mom dinta ta

saba musu dasu lokacin suna Abuja, tum

bayan dawowan su Kano komai ya chanza

musu, tana son sake experiencing irin

wannan jin dadin, a hankali tace “Ok, zanje”

Majeed ya sa tafi kamar dan k’aramin yaro

yace “Ok lets get your things ready, kowa ya

fito da kayan dayake son tafiya dasu” duk

suka tashi suka harhada, a wani katon

akwati suka fita. Har Zinatu suka fada kan

Hajia Aynarh suna rungumarta, daria take

tana musu magana, Sai da Gaban Mairo ya

fadi ganin wannan katon Akwatin, gani takeyi

kamar Hajia Aynarh rabata zatayi da

‘Ya’yanta, kafin tayi Magana karaf Hajiya

Aynarh tace “Ina Mama(Hajjo)?” Majeed yace

“bata dan kinzo ba, barin sanar mata” da

sauri ta sauke Muhsin daga Jikinta tace

“Nooo, barin shiga na gaisheta” hakan ya ma

Daddy dadi, yana son yanda take girmama

Uwarshi, Jagora Majeed ya mata har

Dakinsu, ya tsaya daga waje.

Ziyada na ganinta ta mik’e ta rungumeta,

bude ma Najwa hannu tayi itama, ta

rungumeta, kafin ta durkusa har k’asa ta

gaida Hajjo, Hajjo baki har kunne, ta kalli

Ziyada tace “Oya taso ki shirya, nazo tafiya

da ku ne” Ziyada ta murmusa tace “Ok” ta

fita don zuwa dakin da Zaineema take,

Aynarh tace “Mama kema ki shirya mu tafi”

Hajjo tace “ayi haka, ni ki barni nan” Aynar

harda bubbuga kafa kamar karamar yarinya

tace “nidai gaskia Mama ki taho mu tafi,

kinsan yaran nan basu san me ya faru ba,

damuwa zai damesu, shisa zan tafi da su

duka don su rage wasu damuwan” ta kalli

Najwa tace “Baby ina kayanku? Duk mu tafi”

Najwa ta murmusa, duk runtsi ba zata bar

Gidan nan ba, har sai ta tona ma Nura Asiri,

tafiyarta na nufin Nura zaici galaba akan duk

wani abu da yayi niyar musu, tace “Aunty ga

kayan Hajjo nan, ni i cant leave due to some

reasons, but InshaAllah when everything is

settled Ya AbdulMajeed zai kawo ni” bata

san uzurinta ba amma tace “OK Baby, hada

min Kayan Mama, Ki kawo mana Parlor, ta

waiga ta ga Hijab din Hajjo, ta dauka ta

saka mata, ta tayar da ita, rike da

hannuwanta suka isa Parlo, Bakinciki uwa ya

kashe Mairo, Daddy ko Dadi kamar ya

shideshi, har na dan lokaci kadan ya manta

da damuwar da suke ciki, ya ji dadin yanda

Aynarh kema Mamarshi.

Ziyada ta fito hannunta dauke da dan

karamin trolly a kunne Majeed tace ” Ya Maji

i want us to talk” Majeed yace “now?” ta

girgiza kai tace “lokacin da kake da lokaci”

ya ja hancinta “Zuzu ina da Lokacinki

Always, gaya min damuwarki” baki na dan

rawa tace “dama wannan ne yace yana so

yazo Gida” Majeed ya ja numfashi, suna da

babbar matsala yace “Zuzu, akwai abunda

ya faru, ki bari in komai ya zama settled sai

yazo ko? Daga fuskarta ya karanci ranta ba

haka yaso ba, ta kirkiro murmushin da ko

labban bakinta be kai ba tace “OK” ajiyar

zuciya yayi yace “Fine, bayan kin dawo

School gobe, zanzo Gidan Aunty Aynarh, then

we talk OK?” kai ta daga mai tare da

Murmushi.

“Anya Hajia Aynarh ba mu daura miki nauyi

ba? Hardasu Mama?” cewar Daddy,

Murmushi tayi tace “Meye daurin nauyi? Ka

manta duk Girman Gidan nan nikadai ke ciki

sai masu Aiki, ai ni bazan damu ba in ku

duka zaku koma Gidana” Mairo ta wurga

mata harara ita ko ta kashe mata idanu,

Majeed yace “Zuzu ina Zaineema?” Ziyada

tace “Uhm tace ita zata zauna nan, ba zata

ba” Majeed yace “Barinje in ganta” Dakim ya

nufa, da k’yar ya shawo kanta ta samu ta

hada kayanta, a tare suka fito, Majeed yace

“to Pure Heart kefa?” duk suka waiga gun da

Majeed ke kallo, duk ta daburce dauke da

kayan Hajjo, tace “Erhm, umm ni ina nan,

zan taya Mummy da aiki” Mairo ta galla

mata harara, Majeed ko yaji dadi, yana son

ya dinga ganinta ko hankalinshi zai kwanta.

Daddy yace kuzo kuyi ta tafiya kar Magariba

ya muku a hanya, Majeed ya ja Akwatin duk

suka fita Waje banda Mairo da ta koma daki

don kanta da ke barazanar fashewa, aka

sanya kaya a booth, suka shiga Mota, Hajia

Aynarh harda makala ma Hajjo seatbelt

kamar zasu bar garin, Daddy dadi dai, suka

daga musu hannu byebye suka tafi.

Wayarta yayi k’ara, tafi so in sun kirata taje

chan Bq suyi wayarsu, don nan zata sake

tayi magana, da sauri tayi baya don amsawa,

kamar yanda take hoping su Maama ne, sun

dade suna waya kafin ta yo hanyar cikin

Gida, lokacin Gidan ya fara duhu, alamun

Sanda taji, tana waigawa taga Nura ya shigo

ta gate yana magana da Maigadi, nan

Maigadi ya karantar dashi komai, na ganin

da yayi an fita da Yaran Gidan da Hajjo, Zaid

ya jinjina kai ya ciro abu ya mika ma mai

gadi, kafin ya sake sanda yana takawa cikin

Gidan, Shikenan, ta kama Nura na magana

da Maigadi, wato Maigadin ma minahiki ne,

yaci saa ba wanda ya ganshi, yana shiga

Daki AbdulMajeed ya fito daga toilet

Majeed yace “Allah Sarki Bawan Allah, shaf

na manta daku, abubuwan sunyi yawa kuyi

hakuri kaji?” Nura dai kafeshi da ido yayi,

ciro wata takkada yayi a cikin dukunnanen

Aljihunshi ya mika ma Majeed, Majeed ya

Murmusa ya karba ya fara karantawa;

_ Assalam Alaikum, ina me baku hakuri ga

Dawainiyar da kuke da mu, nasan kuma

kuna fama da kanku, hakan yasa ni tafia

neman danginmu a k’auyen Bichi,

InshaAllah zan dawo nan ba da dadewa ba

don tafiya da Yaya Nura, ku cigaba da kula

min dashi, Ubangiji Allah ya saka muku da

Alheri.

Nagode nice Naeelah_.

Allah Sarki cewar Majeed, Ya kamo hannun

Nura kamar ya san me yake cewa yace

“Kayu hakuri, zaka daina ganin k’anwarka na

dan lokaci, zata je ta dawo kaji” ya shafa

kanshi kamar dan yaro, yace bari naje

Masallaci nayi Sallah, Majeed ya fita daga

Dakin, a Parlo suka hadu da Daddy shima

Masallaci zaije, Zaid na kallonsu ta hannun

kofa, ya ciro waya ya kira Ziyada, nan take

shaida mai sunzo Gidan Wata Auntynsu,

chan zasu kwana, a hankali yayi ta bugun

cikinta har sai da ta gaya mai abunda yake

son sani, ya mata Sallama yace “zaije

Masallaci”

A fili yace “so ba kowa a Gidan yanzu? Daga

ni sai Mairo, sai Zaineema? Perfect, ya fito

daga Parlo ya nufa gun Maigadi, yace ” bani

abun nan da Arm ta kawo jiya” jiki na rawa

Maigadi ya dauko ya bashi, Zaid yace

“yaushe zasu dawo?” Maigadi yace “Chan

suke Maghrib da Ishai, so sai bayan Ishai,

sai ma sun gama karatun Masallaci da

sukeyi bayan Ishai, so zasu kai 8;30” Zaid ya

Murmusa yace “yanzu 6;22, ina da lokaci,

Maigadi ya Murmusa Zaid ya shige ciki,

daidai k’ofar Dakin Mairo ya zubar da wani

abu, kamar ruwa, in ba ka kalli wurin ba, ba

zaka san akwai abu a zube ba, Murmushi

yayi na mugunta, da tafito ta taka zata

sul6e ta fadi, k’ila ta samu karaya, ko

tsagewar kafa, ko gocewar k’ashi, Allah ya

sa duk abubuwa Ukun su sameta”

A ranshi yace “da kin fito Hajia Mairo, zakiyi

muguwar faduwa, wani mummunan abu zai

samu k’ashin jikinki, ko na hannunki, ko na

bayanki, ko na kafafunki ko kuma duka, Allah

sa haka” ya wuce dakin Majeed cike da

Annushuwa.

Add

Duk abubuwan da yake kan Idon Najwa,

tunda taji an bude kofan dakin Majeed ta

leko, tasan ba lafiya ba, ganin Nura ya shigo

da wani abu yayi hanyar dakin Mummy, ta

san cewa he’s upto Something,

Sai da tayi kusan Minti 11 tana neman

abunyi, kafin ta yanke hukuncin dauko

Mopper, a hankali ta bude kofan, ta karasa

gaban Dakin, tsugunnawa tayi ta lakuto

abun kasan, kamar mai, kamar sabulun ruwa,

yauki da santsi gareshi, mopper ta sa ta

goge, ta shiga toilet ta wanke Mopper din, ta

dawo da ruwa ta zuba ruwa a kasa ta sake

gogewa, santsin da yawa, sai da ta dau

tsawon lokaci tana gogewa kafin ya gogu,

har ta taka taga lafiya lau, ko Mummy ta

taka ba abunda zai sameta. Da sauri ta

koma ciki.

Kasa kunne yayi don jin Ihun Hajia Mairo,

shiru ba wani labari, har kusan awa daya ya

shude, ya na jin karad bude k’ofa ya mike da

sauri yana lekenta, dadi ya ziyarceshi, tana

fitowa ta wuce kitchen, baki bude Zaid ya bi

inda ta bi da ido, ya akayi haka? Ta wurin

tabi ya sani, ranshi a bace ya latso wayar

Armstrong, yana mai fada, abunda ya bashi

beyi ba, ko tangarda batayi ba balle ta fadi,

Arm da mamaki yace “Ka tabbata ta wurin

ta bi?” a fusace Zaid yace “what nonesense?

Ba ni na saka da kaina ba? Ta wurin ta bi”

Amstrong yace “it cant be, abun nan yana da

karfi, ko lightly ta taka sai tayi mummunan

faduwa balle tiles ne santsin yayi yawa, its

impossible ace ya bushe, maybe wani ya

gani ya goge” Zaid yace “kar ka gaya min

maganan banza, wa zai goge, ba kowa a

gidan fa” haushi ya sa Zaid kashe waya, ba

haka yaso ba, yaso Hajia Mairo ta nakashe,

wuri ya k’ure amma zai san abunyi kafin

gobe. Haka ya dauro Alwala yayi Maghrib.

WasheGari

Da sassafe Aunty Ainah ta tashi ta hada

masu breakfast da taimakon masu Aiki, ta

shiga dakin Yara, ta tashesu, ta umurce su

da suyi Sallah, ta ja su kan dining, ta zuba

musu breakfast, Dankali da liver sauce, sai

Tea a gefe kuma farfesun kayan ciki, sosai

sukaci, kafin ta ja Muhsin ta fara mai Wanka,

sannan ta chuda Zinatu, ta shirya su cikin

Uniform dinsu, kafin ta kaisu Makaranta da

kansu bayan tace lokacin break zaa kawo

musu Abinci, su fada me suke so, Muhsin

yace Indomie and Boiled Egg, Zinatu tace

Friedrice da coslow, tace “Alright zata kawo

musu lokacin break ” da ta dawo Gida tayi

nata wanka, ta lek’a dakin da aka sauke

Hajjo, har k’asa ta durkusa ta gaidata tace

“Mama Ina kwana, ya kwanan bakunta?”

Hajjo ta amsa da faraarta tace “Mama ki fito

muyi Kalaci” tare suka fita, Ziyada ta sauko

shirye cikin wasu riga da skirt na Material, ta

gaidasu duka, ta tambayi su Zeenah, Aynarh

tace “haba ai sun dade makaranta”. Sukayi

breakfast tare tace ma Ziyada ita zata

sauketa Makaranta, sannan ta wuce Aiki, ta

ba yan aiki umurnin karfe 9;30 a gama

Abincin Zeena da Muhsin zata zo ta dauka,

bayan tace da Hajjo ta saki jikinta sai ta

dawo ba dadewa zatayi ba, Sukayi ma juna

Sallama ta musu fatan a dawi Lafiya, Hajjo

ta kwadaitu da halin Aynarh, har tana cewa

InshaAllah in komai ya lafa zata sa Abba ya

aureta, don ta lura yana sonta itama.

Yau ma kamar kullum dukkan su Uku suka

fita, ko wanne da abunda yaje nema, Daddy

yan bugabuganshi yaje, Mummy neman

mafita take, Majeed kuwa yaje bada ciguyar

me sayen Gida ne, Zaid najin kanshi a sama,

shi kadai a Gida, wani tunani yazo mai, zai

samu dama cin uban Mairo hankali kwance,

waya ya dauko ya latso Armstrong.

Ringing daya ya dauka, be tsaya amsa

gaisuwan Amstrong ba yace “Bring me

Cocaine” Amstrong ya san iyakacin Zaid

Giya, ko sigari be sha, yau shine da cewa a

kawo mai Cocaine? Me zaiyi dashi?

Amstrong yace “what for if i may ask?”a

fusace yace “stop asking questions and do

as i say, Now” ya kashe wayan, ya kalli Tea

da Bread din da Majeed ya kawo mai kafin

ya fita yayi tsaki, ta ya zai fara shan wannan

abun? Sake latso Armstrong yayi yace “ya

taho mai da breakfast”.

2pm

Lecture daya tayi ta dawo Gidan Anty Ainarh,

Waya suke tayi tun bayan Sallahr Azahar,

fake feelings dinshi yake ta karanto mata, ta

yarda da duk wani kalamanshi, duk maganar

da yayi ya samu zama a zuciyarta, har ta

sanar dashi cewa yau zatayi maganar shi da

Yayanta, ita tana so a musu aure as soon as

possible” Zaid ya yi shiru yana jin haushita,

wai ta ya zai fara auren yarinyar nan? Ya fa

lura dagaske take, mts, kawai bari ya sa su

Amstrong su mata fyade, nan da nan

Zuciyarshi tayi mai gardama, ba zai bari

hakan ya faru ba, to ko meyasa? Be son

dogon tunani zuciyarshi ta sake mai wani

tunanin, ko dai ya aureta din yayi making life

dinta miserable, daga baya sai ya saketa ya

wulakanta ta, yace “Wallahi kaman kin san a

matse nake nima, please kiyi saurin gaya

mishi, zan turo magabata na, nan ya cigaba

da gaya mata kalan son da yake mata” ita

kuma tayi ta shiga yanayin Masoya.

Kalaman da ya mata amfani dasu yau sun

matuk’ar Girgiza mata Zuciya, a ranta takeji,

ba ta da Miji sai ZSA dinta, har tana ji in

bata aureshi nan da nan ba, wani

mummunan abu zai samu zuciyarta, tana Jin

kunyan YaMaji, amma dole shi zata samu ta

sanar mawa, tunda Zaid yace “ta gabatar da

shi.

Dakin Mummy ya shiga ya daga katifa ya

ajiye package din Cocaine din a karkashin

Gadon, murmushin mugunta yayi, yace ” dole

kiyi zaman gidan Yari, kama mutum da

Cocaine a Nigeria babbam laifi ne wanda

yake daidai da kisan mutum” ya fita cikin

farinciki, zuwa Anjima zai kira Police

Headquater ya gaya musu yaga wata dealer

ta kawo Cocaine Gidan Alhaji Abba Abu” ya

fita daga dakin da farincikin yau zai kara

k’untata ma Mairo, ya koma Dakin Majeed

ya latso Wayarshi ya soma magana cike da

gadara da isa;

“Labaran, zan turo maka numbern Alhaji

Abba Abu, zaka kirashi, zaka ce mishi kaji

labarin yana son saida Gidanshi, ka gaya

mishi zaka siya da Gidan da Komai Miliyan

50, zaka bashi Sati daya yayi settling, zaka

zo kuyi magana face to face” be tsaya jin

abunda zaice ba ya kashe wayan.

Da Marece Sun dawo Gida dukkansu, Majeed

na gaya ma Daddy “duk a wulakance ake

taya Gidan, daga masu cewa Miliyan 25, sai

masu cewa Miliyan 20” Daddy yace

“Maganar banza maganar wofi, ko Lokacin

da Marigayi Sada ya gina Gidan nan ai ya

kai Miliyan 20 din, balle yanzu da komai

tsada yake, don sun ga ana bukatar kudin ne

ya sa suke ma Gidan Tayin banza” Mairo taji

wani dum a Zuciyarta, Abba har ya tuna

Gidan Sada ne? Wai ba dai Asirin nan ya

fara karyewa ba, wai Ya? Abubuwa na ta

6are mata, ta dai share tace “shiyasa nace

muku a bar zancen saida Gida, don

wulakanci, tayin banza a ke ma Gidan”

Daddy yace “kina da abunda zaki biya Alhaji

Nakowa?” tayi tsaki “ku rabu da dan iskan

nan, daukaka kara zanyi” Daddy yace “kina

da Matsala, Gida ko yau aka samu me siye

miliyan 30 wallahi sai na saida mishi, fadan

da yafi karfin ka ka maidashi wasa, mu dai

san mun rabu dasu” shiru dai tayi don ta san

yanzu abunda ya sa kanshi, shi yakeyi.

Majeed yace “dazun naje Gidan Aunty

Aynarh, duk yaran na gaisheku” Daddy yayi

murmushi yace duk suna lafiya ko? Sun sake

jikinsu ko?” Majeed ya Murmusa yace “har

ce ma Zeenatu nayi tazo muje Gida wallahi

tace ba inda zata” sukayi daria banda Mairo

da ta daure Fuska, Yauwa Daddy, munyi

magana da Ziyada kan wani Yaron da ke

nemanta, yana neman izinin zuwa gunku,

don dagaske yake” Mairo tace “ba tada

hankali? Muna cikin halin haula’i shine take

neman dadako mana Aure?” Daddy yace “aa

Maryam, ai kinga bata da masaniya kan

abunda ke faruwa, kuma ai ba yanzu suka ce

suke sin auren ba, gabatar wa zaayi, kafin

komau ya lafa, sai inyi bugabuga na in mata

abunda zan iya daidai gwargwado, don yafi

da yarinya ta samu Miji a Aurar da ita, kai

AbdulMajeed, kace mata ta gaya maka

wanene shi, in anyi bincike, in mun yaba da

halayen shi, sai ya turo Magabatanshi”.

Majeed yace “Daddy, Bincike ko bazai mana

wuya ba, saboda ansan Yaron a Africa

gabaki daya” Wuf mairo tace “wanene?”

Majees yace “Zaid Sadam Abdu Gatan

Marayu” Mummy da Daddy lokaci daya suka

ce “Gatan marayu dai?” Majees ya jinjina kai,

Daddy yace “Aiko mun je mishi gaisuwan

Babanshi wata rana da zamuzo Kano” Mairo

dadi ya lullubeta, shikenan karshen

wahalarsu yazo, Dukiya da abunda ya tara

ya linka Alhaji nakow so dubu dari, ta kasa

boye farincikinta tace “Ai yayi sauri yazo

wallahi, ko ina diyata ta ganshi? Allah me

iko” tuni Daddy da Majeed suka gano inda ta

dosa Daddy yace “Maryam, ki fita idona, ba

auren Jari zanma da diyata ba, da shi ya

ganta yace yanaso da ban amince mai ba sai

ya nemi so gurin yarinya, amma tunda ita

tace tana so, zanyi Binciken Yaro, duk da

Zahirin yaro muka sani Babanshi mutumin

Kirkine, in muka gano yana da wani hali ba

za mu yarda ba, dole suyi hakuri da juna,

abunda kike tunani ba haka zai faru ba, in

abu ya tabbata Aure zamuyi ma yarinya ba

maganin Matsalolin mu ba” Mairo a fusace

tace “wai ni Daddy me kaji nace?” Daddy

yace na dai gaya miki, ki fita Idona” tashi

tayi fuuu ta wuce daki rai bace.

Alhaji Labaran ya kira Daddy, ya karanto mai

duk abunda Zaid ya gaya mai banda Kudin

da zai biya, yace “zai zo ya ga Gida, sai suyi

ciniki” Daddy yayi hamdala yace “kuzo kuga

Gida Gobe, in Gida ya musu, sai ayi Ciniki”.

Sukayi Sallama, ya gaya ma Majeed yanda

sukayi, Majeed yace ” to Alhamdulilah, Allah

ya sa su siya da daraja”.

Da daddare, Zaid ya kira PoliceHeadquater,

ya basu bayanin Ganin da ya ma Matar

Gidan da Cocaine, ya musu kwatancen Gidan

Alhaji Abba Abu, nan da nan aka cika Motar

Yan Sanda da Police sukayo Gidan Alhaji

Abba Abu, suna Parlo Gabaki daya suna cin

tuwo, Police suka shigo Gidan, gabansu ya

fadi, Babban dan sanda yace “Ina Hajia

Mairo Abba?” Mairo tace “ya akayi? Daga

ina?” yace “mun samu labarin cewa kin shigo

da Cocaine Garin Kano, yanzu ma haka yana

dakin baccin ki”

Zaro ido sukayi duka, a tare suka Maimaita

“Cocaine?” “inji uban wa yace haka?”

Inspectore yace “Kina iya fito mana da su, a

sallameki tare da fahimtar juna, amma ba ma

hukuma wuya zai kara miki charges ga

laifinki, tun kafin mu kai ga bincikarki, ki fito

dasu, muna da Na’ura me bincikar kayan

maye(cocaine detector), indai yana Gidan

nan, duk inda suke zamu ganesu, ya ba

sauran umurnin kuna Detector din su hau

bincikar Gidan, haka suka bar bazu suka hau

bincike da Injin din.

A Dakinsu Mairo, ba inda ba a duba ba, na

daga k’ark’ashin Gado, saman ceiling, toilet,

Wardrobe, ko ina, duk wani lungu da sak’on

dakin Mairo sai da aka duba, amma baa ga

komai ba, an bincika ko wani Daki na gidan,

Najwa ma na daki taga an shigo bincike duk

tabi ta tsorata Majeed yace ” ta kwantar da

hankalinta, bincike suke” haka ma dakin

Majeed, aka binciki jikin Nura da ke baccin

karya, da gan sai dakin yara, da dakin

Zaineema, ko ina na cikin Gidan sai da aka

bincika, har da jikinsu sai da aka sa naurar

nan aka bincikesu, sai da suka zagaya baya

Boysquaters amma shiru, kowa ya dawo yayi

reporting “All Clear Sir” Inspector da Mamaki

yace “are you sure?” Daddy yace “you know

we can sue you for this?(kunsan muna iya

kai k’ararku Kotu saboda haka?)” “Ka bar

yaniskan Daddy, sai Kotu ta shiga

tsakaninmu, in banda cin zarafi, a rasa inda

za a zo neman Cocaine sai Gidan nan?” ta ci

kwalar Inspector din “Danubanka sai ka

nemo min Cocaine a cikin Gidan nan, saboda

kun raina mu, binciken ku zai kawo ku nan?

To muje ka kara bincikar mu, ko in kwale ma

jikina har ciki kagani ko na boye a chan” da

kyar Majeed ya raba Mommy da Inspector,

Inspector ya basu hakuri, ya sanar dasu

cewa waya aka musu aka basu kwatancen

Gidan, aka tabbatar musu cewa Akwai

Cocaine a dakin Hajiar” Daddy yace

“Shikenan, bawani abu, but next time, dont

barge in to people’s house without an

Evidence” suka sake basu hakuri suka wuce.

Mairo ta hau haki, Wallahi Alhaji Nakowa ne,

shine da iskancin nan, aiko sai na mai

Wulakanci, da ni yake zancen, Daddy yace

“Maryam, tunda dai basu ci nasara akan mu

ba, sai mu gode ma Allah, don tsakanina da

Allah na mugun tsorata, sai mu sake kula da

lura, koma waye, Allah ya fisu” Majeed yace

“Nagode ma Allah yaran nan ba sa nan, da

hankalinsu a tashe yake”. Allah ya kara tsare

mu suka amsa da Amin banda Mairo da ke

ta huci.

Zaid ya zube ya zauna dirshen a k’asa, lately

things are not going as he planned, karo na

uku kenan, yana shirya abu yana rugujewa,

amma yana da tabbacin wannan, da kanshi

ya daga katifa ya saka Cocaine dinnan, ko

dai basu bincika da kyau bane? Amma da

detector sukayi amfani, ya san yanda abun

ke aiki, ko da nesa da kilometer 10 ne zaiyi

detecting wurin, Zuciyar shi ta raya mai

“wani ya dauke ya salwantar kamar yanda

yake bata maka duk wani shiri” A Fili yace

“to waye?” shi yasan lokacin da yake

shirinshi ba kowa a Gidan, to ko Aljannu ne?

Kai Impossible, in ma daukewa akayi wani ne

ya dauke, wanin da ya san duk shirin da

yakeyi, koma waye zai biya abunda yayi,

cocaine dinnan ya kai kusan Miliyan in

saidawa zaayi, don ma abun ko a jikinshi, da

wani ne da yayi kukan asara, kwalliya be

biya kudin sabulu ba, zai gano ko waye, ko

da Aljanni ne, zai gane be da wayau.

*****

*KAFIN DAREN*

Tana lura da duk wani taku na Nura, ta ga

ya shigo da wani package a Hannu, hankali

kwance ya sa makulli ya bude k’ofar Dakin,

ya shiga beyi Minti biyu ba, ya fito, shikadai

ya fito ba package din, a ranta tace to meye

ciki? Kila wani sharrin zai k’ulla musu, ya sa

Mukulli ya sake kullewa ya soma kiraye

kirayen waya a Parlor yana bada Orders

wurare dabandaban, ta lura shi din wani

babba ne, yanda yake waya yana bada

umurnin kudi kaza ayi kaza dashi, to meyasa

yake yin haka? Ko wani laifi suka mishi yake

son daukar fansa? Haka dai tayi lamo tana

ta sakawa da kwancewa, babban burinta ta

dauko package dinnan ta ga ko menene.

Ba zata iya shiga dakin ba, saboda dakin

kulle yake, tana wannan zantutuka har aka

kira Azahar tayi Sallah, Jim kadan taji Nura

na waya, da Alamu da me Gadi yake waya,

don da sauri Nura ya shige dakin Majeed,

kila sanar mai yayi Madam ta dawo.

Mummy na dawowa dakinta ta bude ta

shiga, chan ta fito ta shiga kitchen don daura

musu Abinci.

STORY CONTINU

Start from the beginning

“This my only Chance” cewar Najwa da sauri

ta bude kofar ta lek’a window taga Mummy

a kitchen tayi wuf ta shige dakin, ta fara

neme neme a drawer ta duba har cikin

wardrob bata ga komai ba, ta saka stool ta

duba saman wardrob bakomai, hankalinta ya

kai kan karkashin Gado, ta na dubawa kuwa

ta ga Package din, ta zaroshi da kyar, taji

alamun tafian Mummy, ta san halinta, zata

iya cewa itace ma ta kawo ko me ke ciki, da

sauri ta bude Window ta wurga abun, ya fadi

ta baya, ta rufe da sauri tayi hanyar fita

sukayi kicibus da Mommyn, gaban Najwa ya

yanke ya fadi, Mommy ta bita da kallon

tuhuma, tace “Me kike yi a dakin nan?”

Najwa tace “zuwa nayi na gyara muku ashe

a gyare yake” Mommy ta bita da kallon

rashin yarda tace “in na duba abuna ban

gani ba kece” Najwa tace “Nayarda” Mommy

tace wuce ki ban wuri “Munafuka” Najwa tayi

sauri zata wuce, Mairo ta sake mata

rankwashi a tsakiyar Kai, Najwa ta danyi

kara tare da guntun hawaye ta fita da sauri

ta fada daki, tana luluya kanta saboda

azaba.

Saida ta gama kukan zafin kanta kafin ta

tashi ta zagaya bayan window din dakinsu

Mummy, daukan package din tayi ta zagaya

baya, chan BQ, a hankali ta bude package

din, wasu Garin powder ne kusan leda biyar

anyi sealing dinshi, ko ma meye ne tasan ba

abu me kyau bane, pit toilet din wurin ta

bude ta shiga, ta bude masai din, ta jefa

chan cikin shadda ta rufe ta fito, ta wanke

hannuwanta ta koma cikin Gida.

Wannan Kenan.

*************

Murmushi tayi a ranta tace “atleast na rage

ma Jaan wani bacin rai, ashe dama Cocaine

ne?Allah ka shiga tsakanin mu da mugaye,

ta gyara kwanciyarta ta koma baccinta.

Bacin rai ya hana Zaid bacci, jira yake safiya

tayi ya gano waye ke mishi abubuwan da

yake mai.

Kamar Kullum su 3 sun fita, Zaid ya fita

wurin Maigadi rai a bace, “Kai, bayan su

AbdulMajeed akwai wani a Gidan nan ne?”

Maigadi ya girgiza kai alamun aa, yace ka

tabbata yaran gabaki daya aka tafi dasu?”

Maigadi yace “eh, akan idona naga Hajjo,

Ziyada, Zaineema, Muhsin da Zinatu suka bi

Hajia Ainau, duk sun tafi” Zaid yace “kai,

Akwai wani a tare damu, ya zaayi sai nayi

shiri, sai a bata min shiri, ko Aljani ne yau

sai ya bar Gidan nan” a hankali Maigadi yace

“Najwa” Zaid ya Kallo shi yace “wa?” “Najwa

na cikin Gidan nan tabbas, na kan ganta tayi

hanyar BQ” Zaid yayi murmushin takaici,

itace ta san sirrinshi, itace ta ke rusa mai

plan, fuska daure yace”wacece ita?” Maigadi

yace “Bakuwar Majeed ce, Hajia bata sonta

dai” cikin bacin rai Zaid yace “Ko ma wacece

sai tayi nadamar shiga Gonata” yayi cikin

gidan a Fusace.

“Maama i miss you sosai wallahi” bam taji

an bugo k’ofarta, gabanta ya yanke ya fadi,

ganin Nura gabanta, ranshi 6ace, kallon juna

suke ido cikin ido, tsanar junansu a

zuciyoyinsu, duk da ta tsorata da lamarinshi,

don shi din abun tsoro ne, Handsfree ta saka

ta cigaba da cewa “Maama, idan an ma

mutum laifi, ko an zalunceshi, ko an

kwareshi me ya kamata yayi?” Maama tace

“Sai Yayi hak’uri, sai ya bude zuciyarshi, sai

Allah ya saka mai” Kan Zaid ya sara ya

buga, ya san me muryar nan, definitely ya

san voice dinnan, Najwa ta cigaba da cewa

“Maama daukan fansa fa?” Maama tace “ai

baa so mutum ya dau hukunci a hannunshi,

is either ya kai kara gurin hukuma su bi mai

hakkinshi, ko kuma ya bar ma Allah, shine

kadai baya zalunci, shi kadai ne adali me

Adalci” Najwa tace “Maama, misali Daukar

Fansa ya maida ni abun tsoro fa?” Muryan

Maama ya chanza tace “Najwa, ba zan yafe

miki ba in Daukar fansa ya chanzaki for any

reason, i pray ba wani abunda zai saki

chanzawa daga halayenki da na sanki dashi,

duk da na san tambaya kawai kike don

neman ilimi, maaff karane ke lie seekhana (ki

koyi yafe ma mutane)”.

Ba zai cigaba da jin Maganganun nan masu

kama da saukar aradu a tsakiyar kanshi ba,

ba zai jure jin Maganganun su ba wanda ya

tsargu da shi suke, da sauri ya fizge wayar

hannunta tare dNasoyana, yana huci, Najwa

ta samu karfin guiwa tace ” Ka fadi ranka, i

know you can talk” da mamaki ya kalleta,

“how long have you been stalking me?(tun

yaushe kike bibiyata)” murmushi tayi tace

“Tun randa kazo Gidan nan” “what happened

yesterday was you right?” tace “Mummy na

ne kaji muke waya da ita, kaji abunda ya

kamata kayi, in laifi aka maka, ba ta haka ya

kamata ka biyo ba, ka barsu da Allah, ko kai

kara wurin hukuma, Allah ba Azzalumin kowa

bane”,

So yayi ya mata lagalaga ya nuna mishi

kalar Asarar da ta mai wurin mata jinajina,

saidai ranshi ba zai bari ba, saboda me?

Saboda mace ce, cewar ranshi, in ma yace

zai buge ta me zaiji? Tsaki ya buga

yace”stay away from me” da karfin hali tayi

daria sosai tace “ka fara tsoro na ne? Too

early, ai duk wani shirin da kayi nike warware

maka, duk shirin da zakayi nan gaba zan

warware maka, as long as ba zaka gaji da

hada mugunta ba, nima ba zan gaji da

warware maka muguntanka ba har sai asirin

ka ya tonu”.

Hannu ya sa ya kwasheta da Mari, ya sake

marinta ta dayan bangaren, tare da nunata

da dan yatsa, ” Stay the f*ck away from me,

kika sake shiga harkata, I will Kill you,

Believe That”. Ya fita a fusace tare da buga

k’ofar, Najwa ta zube kan Gado tare da

fashewa da kuka mai taba zuciya.

*******

Assalam Alaikum Masoyan ADAY, nasan

kun dade kuna jiran Post dinnan, hakurin

nan dai zan cigaba da baku, shi zakuma ku

cigaba dayi, da kunsan tun yaushe nake

typing page dinnan da kun sha mamaki, sai

yau Allah ya sa na gama page din. Dalili

daya ne na rashin samun Post akai akai,

MAKARANTA, makaranta ya samu gaba

wallahi, Semester yazo gangara, abubuwa

sunyi zafi, nakusa fara Jarabawa, in kuma

nace zan cigaba da muku typing zan shiga

Hakkina, kuma Karatuna gaskia shine a

gaba, hakan yasa zan saka Aya a wannan

Page din, bayan Hutun Makaranta, zuwa

Decemeber, zan cigaba daga inda na tsaya

In Allah ya kaimu rai da lafiya, a lokacin ne

zaku samu post a kai akai cikin kwanciyan

hankali ba tare da wani excuse ba da Yardan

Allah. So ina fatana zaku fahimce ni, kuma

ku kasance tare dani, tare da adduoin

samun nasarar da saar Jarabawa, don shi

kadai ne son da zaku nuna min. Nagode

Allah ya kaimu lokacin….

R

anar da muke Jira tazo, Najwa da Zaid Ido

da Ido

Zaid zai auri Ziyada?

Ya rayuwar su zata kasance bayan sun

koma Gidan Hajjo? Kamar Mairo zata fara

k’osan saidawa, lol, idk.

Me zai faru in Paapa da Maama suka dawo

Nigeria?

Ya Zaid zaiji in ya san Mahaifanshi na da

rai?

Maama zata yafe ma Zaid in ta san

abubuwan rashin imanin da yayi da sunan

rashinsu?

Najwa kuwa zata cigaba da son Majeed in ta

gano abunda Mommynsa ta ma Iyayenta?

Tambayoyi da yawa wanda amsar su kadai

zaizo ne bayan Kun kasance tare dani.

Remember Patience is a virtue. I heart you

all.

#1love

#ADAY

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg2⃣8⃣

 

A fusace ya fita ya shige Dakinsu, kanshi na harbawa, ya sa hannunsa biyu ya rik’e, dakin ke juya mai, a daddafe ya isa ga Bango, Muryar nan, Muryar Matar da yayi waya da ita, ta tuna mai da Maaman shi, kanshi yayi zafi sosai.

Jigab ya zauna a kan Kujera, ya ciro wayarshi ya latso Armstrong,  ringing daya ya dauka, cikin sanyin murya  yace “Arm, come pick me up” zai bar Gidan nan,  to me zai tsaya yi?  Wannan yarinya ta gama kwance mishi komai,  this game is over,  no not yet,  tunda  bai gama da Ziyada ba,  bai Mallaki Gidan ba, but zamanshi ya k’are a gidan a matsayin wani Nura ko kurma,  zai fito musu a asalinshi.

 

Wayarta ya sake ringing a karo na biyu,  hawayenta ta share tare da janyo wayar ta kara a kunne “Hello” jim akayi kafin akace “Najwa,  Lafiya  kuwa?  Yana jin muryanki haka,  are you OK?” kamar jira take ta fashe da kuka,  hankalin Maama ya tashi sosai,  ta hau  tambayarta me ya faru,  da kyar ta ce “wani ne ya mareni” a dan rude tace “Mari Najwa?  Me kika mai ya mareki, dama gidan nan ana cutar dake?” sai da Najwa ta tattaro natsuwarta kafin tace “Maama, ba sa min komai,  akwai wani da ya shigo gidan shi,  shibda sister  dinshi, suka yi faking identity dinsu,  Sunanshi Nura,  he pretended to be deaf and dumb, Majeed brought them in,  Maama,  nura is upto no good,  so da yawa Ina kamashi yana waya  a baya,  so da yawa ina kamashi yana basu umurni”  nan ta kwashe mata magananun da ta ji Nura nayi har na Cocaine,  da yanda  ta taimaki su Majeed.

 

Maama ta na sauraren Najwa,  ta jinjina kai,  tace “Tabbas, Mugu ne Nuran nan,  ya kware da mugunta, best thing to do,  ki gaya ma Abdulmajeed,  ki gaya musu dawa suke  zaune,  yana nufar su da Sharri, ke kuma ki kula da kanki,  ba imani gareshi ba” Najwa tace “Maama ki min addua,  i’m scared” Maama tace “ki dawo India Please,  in dai don Bhaiya dinki ne,  wallahi na hakura,  na rungumi Kaddara,  i cant afford to lose you too,  ba zan iya daukan wani rashin ba” saida Najwa ta kwantar mata da hankali kafin sukayi sallama.

 

Yazo fita ya ci karo da Abdulmajeed,  guntun tsaki yayi, Majeed ya dago da murmushi yace “Mallam Nura,  ina zaka?” ya kamo hannunshi kamar karamin yaro ya jashi zuwa ciki,  cikin zafin nama Zaid ya kwace hannunshi,  Majeed ya dube shi da mamaki kafin ya dan danne,  ya sake kamo hannunshi yace “yi hakuri Abokina,  kar ka fita,  baka san kowa ba,  ka kara hakuri har Naeelah ta dawo” a karo na biyu Zaid ya finkice hannunshi,  Majeed da mamaki ya lulubeshi, Nura kurma be taba mai haka ba,  amana kanwarshi ta bashi, gashi kuma Nuran so yake ya fita ya zaiyi?  Bari ya mishi dan dabara.

Majeed  be hakura ba ya sake sakar mai Sansanyan Murmushi,  yace “Kayi Hakuri,  muje muci abinci” ya karashe da riko hannunshi da k’arfi,  Zaid cikin zafin nama yace “stay the f**k away” a razane Majeed yayi baya,  in kunnenshi ya jiye mai daidai to Nura Kurma Magana yayi,  gabanshi ya fara dukan tara tara,  Zaid ya buga tsaki ya fuce daga Gudan,  shi ko Majeed ko yatsa ya kasa dagawa.

 

Da kyar ya tattara nutsuwanshi ya bi bayan Zaid,  sai dai kafin ya isa gate, ya ga Nura ya shige wata mota sun wuce,  kan Majeed ya daure,  ya rasa meke faruwa,  muryan Najwa yaji “Jaan” ya juyo gareta,  kallo daya ta mishi ta karanci rashin fahimta a tare dashi,  yana son bayani, ta sake fadin “Jaan” cikin sanyin jiki ya amsa mata da “pureheart” ta murmusa tace “Ka shigo ciki,  ina so na gaya maka wani abu” ba musu yayi hanyar cikin Parlo,  suka samu wuri suka zauna,  wayarta ta latso recording din maganganunsu da Nura,  inda take ce mishi “ta san shi ba kurma bane” da lokacin da Nura yayi barazanar kashe Najwa in ta sake shiga sabgarshi” jikin Majeed ya fara rawa,  meyasa?  Meyasa Nura da Naeela suka mishi karya?  Me suke so a tare dasu?  Me suka mudu da suka zabi cutar dasu? Ganin haka yasa Najwa fara magana,  nan ta bashi labarin duk abubuwan da ta sani game da Nura,  kafin ta dora da cewa;

 

“Nura ba abunda yace bane shi,  Makaryaci ne,  saboda ya maka k’arya, be chanchan tausayinka ba,  i think ya zo gidan nan ne don ya cimma wani buri nashi, sai mu gode ma Allah da yasa basu kaiga cutar da ku ba,  Allah ya fisu,  Allah shi zai cigaba da kareku”

 

Majeed ya furzar da naunauyar ajiyar zuciya yace “Pure Heart, ina so na san dalilinsa na yi mana haka?  Ko yana da wani unfinished bussiness ne da mu? I want to know why?  I only wanted  to help,  amma meyasa?” Najwa tace “Nasan taimakonsu kayi,  amma ya kamata ka zama me kula,  duniyar mu a yau,  daga taimako kake kawo wanda zi cutar da kai, mugode ma Allah da Allah be daura su kanku na,  sai ma ya daura ku kansu,  asirinsi ya tonu,  Allah ya sa karshen kenan” ya kura mata ido,  kaunarta na fuzgar shi,  yace “hakan ba zai kasance ba,  ba tare da taimakonki ba, Pure Heart,  Ke Alheri Ce a rayuwata,  nagode kwarai Allah ya bar mu tare” ta rufe fuskarta tana daria tana amsa adduar shi.

 

Da su Mummy suka dawo Majeed ya basu labarin  Nura Kurma,  da duk abunda Najwa ta gaya mai,  Mairo ta rafka uban salati ta hau karkada kafa kamar wata zautatta,  dama ace tana nan,  da sai ta lakada ma Nura na jaki,  da sai ta zaune mai ruwan hanji taji dalilin yi musu haka,  ta kalli Majeed tace “to dan agaji,  me taimakon gaggawa,  gobe  ma ka sake kawo mana mutanen da baka sani ba,  duk suzo a halaka mu a banza,  in banda Allah ya takaita mana wahala,  ya tona asirinshi,  da har yanzu muna gwagwarmaya a Kotu ace an ganni da Cocaine cikin gida,   amma Nuran nan Allah ya tsine mai,  Allah ka mishi abunda yaso ya mana” Daddy yace “Tunda be ci nasara ba,  ai ina ganin gode ma Allah zamuyi da ya daura mu kanshi ko?  Sai mu sake kula,  mu iya takun mu,  Abdulmajeed  na tabbata Allah ya ga zuciyarka,  da niyyarka,  shiyasa ya karemu,  Allah ya cigaba da karemu,  Allah ya maka Albarka” suka amsa da “Ameen” kamar an tsunguleta tace “ba kwa tunanin Alhaji Nakowa ya turo wannan Nuran ya zama spy dinshi? ” Daddy ya mike tare da fadin “zato zunubi ko da ya zama gaskia,  koma dai menene muna da Allah,  Alhaji Nakowa kuwa kafin karshen watan nan zamu sallameshi” Mummy  ta dan muskuta tace “ta yaya?” a takaice Daddy yace “an samu mai siyan Gidan” Mummy ta zaro Ido  “Wai dagaske Gidan  zaa saida?” ba tare da ya juyo ba yace “InshaAllahu” ya wuce daki,  Majeed na ganin haka shima ya shige nashi dakin ya bar Mummy da cizar yatsa.

**

 

Dadi kashe Ziyada yau Zaid zaizo Gidan Aunty Ayanarh,  a zahirance zak san tana cikin nishadi mara misaltuwa, biye mata Aunty Aynarh tayi suka hau mai shirin kayan Abinci kalakala,  bayan Maghrib ta mai kwatancen gidan Aunty Aynarh(bata san ya san Gidan ba) ,  ta shiga toilet ta tsantsara kwalliya,  gab da Isha’i sai ga Zaid,  Waiyo Allahn Ziyada,  ji take kamar ta mutu  don  dadi,  Allah ne ya dora mata  son gatan Marayu,  shi kadai ya san yanda take sonshi,  bakinta ya ki rufuwa ba,  kamar ba Ziyada Miskila ba,  ta mai jagora har tsakiyan Parlorn,  Muhsin da Zeenatu suna zaune suna kallon Cartoon Network,  Zaid ya dinga faking Murmushi,  yana musu magana shi a dole kanneneshi, Zeenah tuni ta sake jikinta dashi don ta na son dan gayu,  Aunty Aynarh suka sauko da Zaineema da Hajjo,  a yanzu Zaineema  ta sake da Aunty Aynarh,  suka gaisa da Zaid,  Zaid ya gaishesuyana kwakulo murmushi, Hajjo take kallonshi kuri a ido,  ba tantama yana kama da Abba,  kuma suna  yanayi da Majeed, Zaid ya dauke kai ganin irin kallon da Hajjo ke binshi d shi,  Aunty Aynarh ta kada kansu Zeenah suka hau sama suna yaba Zaid.

 

Abinci ta shiga zuba mai,  ya dan yatsina fuska shi ba zai ci ba, bata san Zaid be da yarda ba,  baya cin abincin Gidan Mutane, ta marairaice fuska “da hannuna fa na dafa” ya kwakulo Murmushin da be kai fatar bakinshi ba yace “sai da naci abinci na fito” “please kaci ko yaya ne” ranshi ya baci,  be son yawan magana,  da yaga zata takura mai,  sai ya sake kwakulo Murmushin  da ita a ganinta ba murmushin wani mahaluki da ya kai nashi inganci yace “kar ki damu babe,  da shi zan tafi inci zuwa  anjima, wanda ya rage da safe inyi warming inci” dadi kashe Ziyada, yayi saurin cewa zai turo magabatanshi ran friday,  ta sanar da Iyayenta, kamar ta mutu don dadi,  ta karanto mai numbern Majeed  tace “ka kirashi kuyi magana” nan gabata  ya kira Majeed cike da kwantar da kai Zaid ya mashi bayanin ko shi  waye da abunda ke tafe dashi,  Majeed ya ji dadi,  saboda yayi bincike kan Zaid,  yaji abubean Khair game dashi,  ya amsa mai da cewa “Zan tuntubi Zuzu,  in ta kara tabbatar min da kai take so,  kana iya turo Magabatan naka ran Jumaa” Murmushin yake Zaid yayi,  sukayi Sallama.

 

Zaid ya kalli Ziyada yace “Zuzu” ta dago a kunyace tace “fa YaMaji kadai ke ce min haka” ya sake sakar mata fake murmushin shi yace “gaskia ne,  nima ai ina da sunan da nikadai ke ce miki haka, “my happiness myforever” ta sa hannunta biyu ta rufe tana daria,  kaunarshi na fuzgarta,  Salon Soyayyarshi na burgeta,  nan suka  shiga musayarkalaman soyayya wanda Armstrong  ke karanto ma Zaid ta bluetooth din kunnenshi.

 

Har wurin 9 suna tare,  da zai tafi ta kirasu Aunty  don  su mai Sallama, ya ciro rafar dubu daya ya ba su Zinatu su siya Chocolates,  dadi da murna suna tsalle suna cewa “thank you Uncle Zee”.

 

Washegari, Alhaji Labaran da wasu mutane biyu suka zo mansion din,  Majeed da Alhaji Abba suka tarbe su hannu bibbiyu,  suka shiga nuna musu kai  ina na Gidan, Hajia Mairo kamar ta fashe don takaici,  sai huci take kamar zakanya,  Alh Labaran yace “Ahh gida yayi kyau sosai,  nawa aka ma gida kudi?” Alhaji Abba yace “Miliyan arbain” Alhaji  labaran yace “in baka talatin mana” Alhaji Abba yace “ka dai bada arbain din” haka sukayi ta ciniki har suka Amince a milliyan talatin da biyar” nan take Alhaji Labaran ya basu kudinsu cif ta hanyar cheque, aka bashi Takardun gida duk sukayi signing gaban shaidu,  ya kuma basu sati daya su kimtsa don zai tare  da Iyalanshi shima,  Alhaji Abba yayi godia  suka rabu cikin mutunta juna.

Daddy ya mik’a ma Abdulmajeed Cheque din yace suje suyi cashing a bank,  hajia Mairo ta fashe da kuka duk suka juyo suka kalleta,  Daddy  yace “yadai Maryam?” cikin kuka tace “yanzu shikenan  kun sayar da gidan nan? Yanzu shikenan  mun rasa gidan nan?  Yanzu shikenan?” Daddy yace “Maryam,  kin fiye rigima,  yanzu in ba a sayar da Gidan nan ba,  ta ya kike so a biya Alhaji Nakowa hakkinshi?  Wannan ruwa fa ke kika ballo mana shi, kuma da kike tada hankalinki,  ai muna da rufin asiri,  Allah ya sa muna  da gidan Mama, ba abunda gidan yayi,  Abdulmajeed ya tabbatar da hakan,  shara kadai Gidan ke bukata, barin gidan nam ba karshen rayuwarmu bane, da sauran kudin miliyan biyar sai mu fara bussiness duka,  mu rufa ma kanmu asiri ba sai munyi karya ba,  so banga abun tada hankali ba” sukayi gaba ita kuma ta dinga cizgar kuka.

 

Suna isa Bank suka bada cheque bayan verification da komai aka musu cashing kudadensu, a cikin largest sized Ghana Mustgo guda uku, da taimako jamian banki suka fito  suka sa a booth, suka juyo,  a cikin Mota Majeed ke cema Alhaji Abba “Daddy,  ina ga a kira Alhaji Nakowa yazo a je Kotun,  barin kudin a hannu hadari ne” Daddy yace “haka ne, bari in kirashi” Majeed ya cigaba da tukinshi, yana sauraron Daddy na waya da Alhaji  Nakowa;

“Eh  Alhaji,  ga kudin nan a shirye,  sai ka shirya kazo kano a je kotu mu biyaka a gaban shari’ah” Alhaji Nakowa be kai ga bashi amsa ba,  Majeed yaci wani wawan birki k’iiii, “inallilahi wa ina ilaihir rajiun”cewar Daddy  ganin wasu garada majiya karfi sun fito daga wata mota fuskarsu rife da mask,  hanyensu rik’e da Bindigogi, Majeed be ankare da me ke faruwa ba sai da ya ji bindiga kan kwakwalwar kanshi,  cikinshi ya bada k’ululu,  da kaukausar murya yaji ance “ku fito” da karfin hali Majeed yace “saboda  me?” da hargowa mutumin yace  “saboda me? Zaka fito ko sai na tarwatsa maka kai da bullet din cikin bindigata?” zai sake magana Daddy jiki na bari yace “Shiru Majeed,  fita” jim Majeed yayi kafin ya fita hannunshi kan bayan kanshi, haka ma Daddy,  sauran su ka shiga bincikar Motar,  har suka fito da manya manyan jakunkuna Yunkuro Majeed yayi don tsaida su,  babban cikin ya harbi k’asa don tabbatar mai da cewa akwai Bullet ba bindigar bogi bace,  Daddy yayi saurin  kama Majeed,  duk jikinsu rawa yake,  suna ji suna gani suka shige motarsu da kudaddensu,  Majeed ya fashe da wani kuka mai karfi,  ya zube a k’asa,  Daddy  kasa motsi yayi,  mutane don rainin wayau sai lokacin sukazo suna lallashinsu,  wani yace “saboda  ya ga suna da bindiga ne shiyasa beyi yunkurin taimakonsu ba” basu ce musu uffan ba,  Daddy ya cicibo Majeed ya tura shi cikin Mota, shima jiki a sake ya shiga driver  seat ya ja motar ba me cema kowa komai tsakanin shi da Majeed, nearby Police Station Daddy yayi.

 

Suka fita don zuwa bada report, a cikin Police station din ne Daddy ya nemi ganin On duty,  duk ciki ba wasu police din kirki, a tsiyace polisawan ke kallon Daddy, Daddy yace “Oga, danAllah ku taimaka mana,  yanzu yan fashi suka tare mu suka karbe mana kudadenmu” da rainin  wayau suke kallonshi,  har wani inspector yace “kuje ku siyo paper da biro wanda zaayi report dashi” Majeed ya dago rinannun idanuwanshi yace “mu siyo paper  da  biro? Seriously? Wasu irin  maakaita ne ku? Kuji tsoron Allah” wani kofur ya daga musu murya ta hanyar  cewa “Kai Yaro,  ka iya bakinka” ganin zasu bata musu lokaci  Majeed ya riko hannun Daddy  yace “mu tafi Daddy,  wadannan mutanen  ba abunda zasu iya mana,  ku kuma kuji tsoron Allah” ba su jira komai ba,  suka fito jiki a sanyaye,  sukayi hanyar Gida.

 

Da kyar suka koma Gida,  kafan su na nauyi suka shiga gidan,  Mairo na ganinsu gaban ta ya fadi,  a jikinta taji wani abu ya faru,  da sauri ta karaso gunsu tana tambayar abunda ya faru,  cikin sanyin jiki Daddy ya karanto mata abunda ya faru,  Ihu ta kwallara da karfi kafin ta zuve k’asa sumammiya,  duk suka yo kanta, Najwa da ke daki ta fito a guje, Majeed  ya cicibota ya rungume yana hawaye,  daddy tsaye yayi kansu,  Najwa na ganin  haka tayi fridge ta dauko ruwa,  ta bude ta fetsa mata,  Attishawa Mummy tayi,  tana farfadowa ta sake tantsawa ihu,  Majeed ya rikota,  ya rungumeta yana shafa bayanta har sai da ta natsu,  cikin kuka take cewa;

 

“Wallahi karyan Manahuki, karya kake Alhaji Nakowa,  nasan aikin ka ne,  nasan yin  ka ne haka,  karya kake ka Aiko  a mana fashi,  in ba haka ba wa yasan da kudin?” Daddy yace “aa Maryam,  banda zargi, na dai kirashi lokacin  da muka fito daga  bank nace yazo kano aje Kotu,  kafin ya ban amsa sukazo,  so ban tunanin shine” Mummy tace “kaiya Daddy, baka san waye Alhaji Nakowa ba,  ba a shaidarshi,  mutumin nan Shaidan ne me suffan mutune,  Wallahi  Gobe  zan ma Abuja dirar Mikiya”.  Daddy yace “aa Maryam, kar ki zarge shi,  ba muda wani hujja,  i think zanje chan Police Headquater, muga ko za a dace”

Majeed yayi saurin cewa “Ba abunda zasu iya  mana Daddy,  ai yanzu mu ba kowa bane,  bamu da kudi,  yanzu ai talaka be da wani k’ima a idon dunia,  talaka baida wani gata sai Allah,  shikenan mun rasa kudin nan, Daddy kudin nan sun tafi,  Allah in wani abu mukayi maka kake hukunta mu ta wannan hanyar,  Allah ka yafe mana,  Allah ka Iyakance mana,  Allah ka kawo mana Sauk’i,  Allah ka bamu ikon cin jarabawar nan” Daddy ya dan matse kwallah,  yace Ameen Abdulmajeed,  Allah Ameen Ya Rabb”. Najwa tayi saurin shigewa daki tana kuka,  tausayinsu ya rifeta gabaki daya.

 

Bayan wasu yan kwanaki

 

A yau suka dawo Gidan Hajjo da zama,  bayan an kai ruwa rana da Mummy,  a cewarta ba zata dawo ba,  Alhaji labaran da Alhaji Nakowa  suka hada baki suka ha’ince su,  har gaban Kotu,  Alhaji  Nakowa yayi rantsuwa kan be da masaniyar abunda ya faru,  Alhaji Labaran ma haka,  da haka Kotu ta kara musu  lokaci har wata 5 kan su  biya Alhaji Nakowa  kudinshi don yace be yafe ba,  Gida  kuma su tashi don Alhaji  Labaran na da bukatar tarewa da Iyalansa.

Hakan yasa  Daddy da Majeed sukayi ta lallaba Mairo har ta yarda suka koma Gidan Hajjo,  kallo daya zaka  musu ka san cewa suna shan wahalar rayuwa,  komai na babban Gidan,  harta Motocin su biyu sun saida,  gadajensu da komai suka  saida,  kudin ko miliyan shidda be rufe ba,  haka suka damk’a ma Alhaji Nakowa sukace gashi su fara rage bashi da miliyan biyar, duk da suna da tabbacin nan da shekara 5 ba zasu iya hada Miliyan 25 ba,  amma ana so su hada miliyan biyar cikin kwanakin da basu kai shekara ba? Amma basu san gaibu ba,  Allah Aalam,  shi kadai ya san yanda zaiyi dasu,  but  for now,  dole  su aje komai a gefe su kama sana’a,  su gina sabuwar rayuwarsu.

 

Tafiya ta kama Aunty Aynarh,  zataje Abuja inda zaa mata Promotion Aptitude test,  ta kira Daddy ta sanar mai,  da karfin hali ya mata addua yace “zai turo Majeed ya kwashi yaran,  mungode Allah ya saka  da Alheri” tace “Aa Alhaji Abba,  ba wai ina nufin azo a dauke su bane,  na gaya mane don kawai ka min  Addua,  amma menene don nayi tafi na barsu?” Daddy yace “ba wani abu bane,  amma ina ganin ya kamata  su dawo Gida hakan nan,  komai  ya lafa da yardan Allah, mungode Allah ya bar zumunci” ba yanda batayi ba amma yace “aa gwara su dawo su rungumi  kaddararsu,  gwara su dawo su ci damaran zama  haka har karshen  rayuwarsu har sai Allah ya kawo mana sauki” numfashin ta ta ja ta sakar tana me tausyinshi,  ta ji labarin yanda suka sayar da Motocinshi da duk wata kaddarar Gidanshi,  ta na ganin zata  iya taimaka  mishi ta hanyar rage mishi dawainiyar Yaranshi,  amma kuma gaskia ne abunda  ya fada tace “zan kawo su bayan Maghrib InshaAllah” ya mata godia sukayi Sallama.

*

 

***

 

Zaune suke cikin Parlorn Abba Abu’s Mansion, kallon wakeken Parlorn yake yana murmushi, bejin soki burutsun da Armstrong yake mai,  hankalinshi na chan gun tunani, komai na tafiyan mishi daidai,  komai na tafiyan mishi kamar yanda ya tsara, amma cikin zuciyanshi yana jin yana kewan wani abu,  kamar wani abu a cikin zuciyanshi is empty,  like something  is missing, “to meye?” Ya fada a bayyane,  Armstrong  ya kalleshi,  ya lura Ogan nashi yana cikin damuwa yace “Sup Boss?” kamar jiranshi Zaid yake yace “Arm,  i dont know whats happening to me,  but i’m feeling empty” Arnstrong ya kalleshi yace  “You feeling  Empty? In this bighouse?(kaji ka bakomai? A cikin wannan babban gidan?) ” hannu biyu Zaid ya sa yana mai bayani yanda yake so ya fahince shi “Arm, Its  like i’m missing something,  like a lame person,  like a human with no ear, or eye (ina ji kamar ba ni ba,  kamar akwai wani abun da babu a jikina,  ina jina kamar wani gurgu,  kamar mutum mara kunne ko ido)” Armstrong  ya kalleshi sosai yace  “But why? All you ever wanted was this house,  and its yours why do you feel like something  is missing?(amma saboda me?  Wannan gidan ne burinka,  kuma yanzu naka ne,  meyasa kakeji kamar baka cika ba? ) ” Hannu biyu zaid ya sa ya dafe kanshi kamar zaiyi kuka yace “I really dont know”.

 

Shiru sukayi na wani lokaci kafin Armstrong cikin sanyin  jiki yace “You are inlove boss” wani darian rainin wayau Zaid yayi wanda tsawon shekarunsu tare Armstrong be taba yin irinshi ba “Hahahha What?” Armstronng  yace “you wont believe it,  but you love thay your cousin, shes the one you are missing(ba zaka yarda ba,  amma kana son Yaruwarka,  ita ce kake rashi)”  da karfi Zaid yace “LOL, Arm you are delusional, take this, go take your baby{booze} (Arm kana hauka, karba,  je ka sha giyarka)” ya ciro rafar dubu ya jefo mishi,  Arm ya chafe yana daria ya mike yace “Think about it”   Zaid ya dan kausasa murya yace “Out” da sauri Armstrong  ya fita yana daria.

 

A ganinshi ya mallaki Gidan  nan ya gama cikar burinshi,  a ganinshi zaman su a Gidan Hajjo sabon  shafi ne na talauci, da karfi da yaji ya tallautasu, hakan ya ci ace ya sa shi farinciki,  duk wani burinsa ya cika, ya ga bayansu, ya ga karshensu, amma  akwai sauran rina akaba,  a hankali ya furta “Ziyada”.

 

Yau Kwanan su 9 yau basu yi waya ba,  tun randa yaje gidan Aunty Ainarh,  gani yake ya samu Gidan to neman me zai cigaba  da yi mata? Yayi zaton ya gama aikinshi na dasa mata Soyayyarshi  a zuciyarta, yasan yanzu tana cikin damuwa da takejin wayarshi a kashe , a kan idonshi tayi ta kiranshi baya da dauka,  karshe ya kashe wayar da yake kiranta da shi,  baya son damuwa sai gashi tunanin Ziyada na sashi damuwa, ya dayki  maganar Armstrong kamar Mara kan gado,  be dauki  maganaar da wata amafani ba,  tsaki ya buga,  zuciyarshi tace “ai shes not heartbroken yet,  rabuwa da ita ta haka bazai yi making wani  effect ba, ya rabu da ita ta hanyar da zai  taba zuciyoyin Abba Abu’s duka, ya wulakanta ta, ya tozarata ta,  ta hanya daya ce hanyar ‘Aure’,  Zai Aureta ya gallaza mata,  ya gana mata azaba karshe  ya mata sakin cin mutunci bayan ya zubar mata da k’ima da daraja a idon mutane,  da wannan  zai gama da babin Abba Abu gabaki daya,  Murmushin mugunta ya sake a baiyane yace “Sai na Aureki Ziyada Abba Abu”.

******

 

We are back people,  i’ve missed you so much bibilicious freaking fans,  i appreciate  each and every single one of you #1love.

 

Ehen,  lets see how many votes and comments this page will  get for the first time after a long time.  Vote and Comment Line by Line.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg2⃣9⃣

 

Kiran Alhaji Ado Mali ya shigo wayar Zaid,  kamar jiranshi  yake  ya daga da sauri sai kuma ya rasa me zaice mai,  daga bangaren Alhaji Ado yace “Allah ya ji k’an Gatan Marayu” dadi ya ziryaci Zaid,  a duk lokacin da aka ma babanshi addua ya kan tsinci kanshi cikin jin dadi da Annashuwa, a kasaitance yace “Ameen Baba Ado” “Muna Lafiya Gatan Marayu na biyu?” Zaid da ya matsu da ya zaiyane mai damuwanshi  yace”Eh  Baba Ado” suka danyi shiru na wasu dakiku kafin  Alhaji Ado yace “dazun naga  missed call dinka,  lokacin ina tare da mai girma shugaban k’asa” Zaid ya rasa ya zai fara magana,  chan kuma yace “uhm,  dama gidan da nake zuwa sukace in kira Iyayena”  sai da Alhaji  Ado ya dade yana nazarin Zaid kafin ya  fahimci inda  zancen sa ya nufa yace “Zaid,  kana nufin inda kake neman yarinya aka ce ka turo  magabatanka?” dan tsaki yayi mara sauti kafin yace “eh” Baba Ado yace “Alhamdulilah, kana Porthacourt ne?” a takaice Zaid yace “Ina Kano” Alhaji Ado yace “ina Abuja,  amma gobe sai in biyo jirgi inzo  Kano,  zan sanar da Alhaji Umar,   in yanada lokaci  sai muje tare” Zaid yace “Nagode Baba, Allah ya k’ara girma” suka ajiye wayan, ya kanji natsuwa in yana magana da Alhaji Ado, ya kan tuna babanshi,  yanayinsu harta maganansu iri daya.

 

Alhaji Ado Mali Shahararen dan kasuwa me sarrafa gwal tsakanin Mali,  Senegal da Nigeria, aminin Marigayi Alhaji Sadam Audu gatan Marayu ne,  farkon zuwan Alhaji Ado Nigeria da Gatan Marayu suka fara hulda,  haka har Aminta ta shiga tsakaninsu,  yanda Alhaji Sadam Ke som Zaid  haka Alhaji Ado ke sonshi,  don dai shi Zaid din dan kutsu ne be dauke shi uba ba kuma bai zuwa inda yake,  amma sosai  yake ganin mutuncin Baba Ado.

 

Yayi mamaki kwarai da ya tuntunbi Baba Ado da maganan Ziyada,  sai yanzu ya ke tambayan kanshi  dalilin da ya sashi kiran  Baba Ado,  ya ga Auren ba auren soyayya bane,  auren daukar fansa ne,  meyasa be yi hayan Iyayen da zasu je gidansu Ziyada ba? Auren ba Aure bane,  na wasu  lokkuta ne,  meyasa be nemo iyayen bogi ba sai Babban Mutum kamar Baba Ado,  wanda a yanzu yake ganin shine babanshi.

 

“Saboda kana sonta,  saboda ka na son gina Auren ku ta hanya Madaidaiciya,  ba ka son harkar  karya a maganar aurenku,  kana iya  bin ko wacce hanya don cikar burinka ba tare da ka damu da illar bin hanyar nan ba, amma ta kan Ziyada,  ba zaka iya ba,  ba zaka fara rayuwar aurenku da karya ba” Cewar Zuciyar Zaid.

Ya runtse ido da Dan k’arfi yace “Rubbish,  you are soo stupid for thinking  of this” ya buga tsaki, ya cigaba  da surutanshi shi kadai.

 

Da kwatancen AbdulMajeed Aunty Aynarh ta kawo su Gidan Hajjo, ta juyo ta kallesu tace “ku fito ko?”  Zeenatu tace “where is this place?” Aunty Aynarh ta murmusa, Ziyada da Zaineema suka kalli Gidan

su ma suna tunanin ina ne nan, don da wayonsu ba su zo gidan ba, Hajjo tace “sun dawo nan din ne?” Aunty Aynarh ta gyada kai, kafin wani ya k’ara magana AbdulMajeed ya fito daga gidan, gabansu ya yanke ya fadi, duk da duhu ya fara yi,  hakan be sasu kasa ganeshi ba,  duk ya tsamure, ya kara tsawo, fuskarshi ta sake tsawo saboda rama, kamar wanda yayi sati yana jinya, Ziyada ta sa hannu ta bude kofar mota ta karasa ta tsaya a gabanshi, tsura mai idanuwanta tayi,  baki na rawa tace “YaMaji, baka da lafiya ne?” murmushi yake k’okarin yi mata, ya girgiza kai ganin hawaye kwancen cikin idonta yace “its going to be Alright” ya ja hannunta suka karasa gabansu Hajjo, da Murmushi yake gaidasu bayan ya rungume kanenshi, Aynar da hajjo sukace “Majeed baka lafiya ne?” murmushi ya kwakulo yace “lafiya lau nake” gudun kar su sake watso mai tambaya yace “ku mu shiga Gida” Zeenatu ta tirje  tace “ina ne nan?” Majeed yayi murmushi yace “sabon gidanmu”.

 

Suka bi Gidan da kallo gabaki dayansu,  ganin  rashin yarda a cikin idanuwansu ya sa shi cewa “Ku muje ko” yayi gaba,  ba su da wani zabin da ya wuce su bishi a baya suna kallon Gidan, ba karamin gida bane,  kuma ba babba ne,  irin gidajen da din nan ne na block,  a lokacin da sai masu kudi ke zama a ireiren Gidan,  amma da yake yanzu zamani ya chanza,  kuma tsohon gidane,  ba za a sa Gidan a ko da irin gidajen lowcost ba, suka shiga da sallama,  tabarma suka gani shimfide Daddy da Mummy na zauna kai,  chan gefe kuma Najwa ke rakube,  Mummy ta tashi da sauri ta rungumo yayanta,  Daddy ya tashi yana musu sannu da zuwa.  Aunty Aynarh ta lumshe idanuwa ta bude,  har ranta takejin murmushin da Alhaji  Abba yake watso mata,  sosai ya gaida Hajjo kafin ya maida kanshi zuwa ga Hajia Aynarh.

 

Ran Zinatu a bace tace “Mummy ina ne nan?” Mummy ta ja numfashi da k’arfi, duk suka zuba mata ido,  Zaineema ta kalli Majeed tace “Yaya meyasa muke nan?” baki ma rawa Mairo tace “Erhm,  zamu zauna a nan ne na wani lokaci,  ana gyara a Gidanmu,  in an gama zamu koma chan” Majeed ya dafe kai yace “Mummy,  hakan be da amfani” ya durukusa ya dauki Muhsin,  ya ja hannun Zinatu ya wuce dasu daki,  yace “oya Sleep,  gobe akwai school”.

 

Ya dawo inda ya bar su a tsakar gida, Hajia Aynarh  ta lura zasuyi magana,  ta mike tace “barim wuce Gida” Daddy yace “tun yanzu? ” tace “eh gobe nake so na wuce  Abuja da safe,  so ina so na huta” Daddy yace “ya kamata ki hita, Allah sa a dace,  a yi test a saa” ta amsa da “Ameen, Hajia Mairo  to ga amanar yarana na baki har sai na dawo” Mummy da ta cika tayi pam tun daga shigowar Hajia  Ayanah,  da firan da sukayi da daddy wanda take gani kamar cin fuska ne ta balla mata harara tare da buga tsaki” su Ziyada  basu ji dadi ba, Hajiya Ayanar ta murmusa tace “Zaineema Ziyada ku kula min da kanku,  sai na dawo ko?  Ina sonku domin Allah” Zaineema ta mike  ta rungumeta,  Ziyada ma haka,  suna mata godia da addua,  ta durkusa gaban Hajjo  tace “Mama da na dawo zan zo in dauke ki” Hajjo tayi daria ta yi godia tare da sa mata Albarka,  sukayi bankwana,  ta juya ta kalli Mummy,  daidai yanda ita  kadai zata ganta ta kashe mata ido, tayi gaba,  Daddy da Majeed suka bi bayanta,  waiyo Allah,  Mummy ji tayi kamar ta fasa ihu,  don bariki ita zaace ta kula da yaranta?  Har sai wata bayarabiyar banza tace ta kula da yaranta? Gashi da Mijinta da Yaronta duk sun bi bayanta kamar wata zariya,  hmm  Hajia Aynar baki sanni ba,  zanyi lokacin ki a sannu.

 

Suka shigo da kayayyakin yan hutu bayan Daddy yayi sallama da ita,  rafar dari biyu ta ba Majeed,  Daddy ya hanashi karba,  ba yanda batayi ya karba ba yak’i, a cewarshi abunda ta musu ya isa hakan nan,  ba yanda ta iya haka ta maida kudinta sukayi  Sallama suka shiga gida da kayan.  Kan tabarmar suka zauna,  Ziyada ta samu karfin halin cewa “YaMaji,  wani abu ya faru da ba ma nan, kallo daya zaa muku a san cewa duk kuna dauke da damuwa,  me ya faru? Ina ne nan kuma?” Majeed ya lura Mummy  zatayi magan,  kuma yayi amanna da ba gaskia zata fada musu,  yayi karaf yace “This is our new home” suka bishi da ido,  yace “mun tura ku Gidan Aunty Ainarh ne sabida ba ma so kuyi experiencing wasu abubuwan da zasuyi affecting dinku a rayuwarku, Zaineema,  Ziyada ku ba yara bane,  kun san k’addara, kun san dai nothing  is permanent in life right?  Zan iya cewa ba kullum ake kwana a gado ba,  yau dadi gobe  akasin haka,   abubuwa da yawa sun faru,  tun kuna gida har tafiyar ku gidan Aunty Ainarh,  ganin in kun sani hankalinku zai tashi,  kuma ba ma son  kusa kanku cikin damuwa musamman ke Zaineema  da kikayi experiencing  mummuna kaddara,  kunji kunji…. ” ya  kwashe komai ya gaya musu,  tun  farko har karshe,  tun daga shiga kotun farko,  da yanda akayi da baban nana,  da yanda kotu ta yanke hukunci,  da cin Amanar nura kurma,  da yanda cocaine detectors sukazo neman cocaine a gidan,  da saida gidansu da ciro kudi a bank da tare su da akayi a ka karbe kudin da yanda suka tsinci kansu a nan,  da yazo k’arshe,  ko wannen su fuskarshi tayi harta shi me bada labarin,  Daddy ma yayi hawaye,  Mairo dai hannun ta rungume a kirji,  tana karkada kafarta,  tana hango kanta tana kuntata ma duk wani da ya kuntata mata da iyalanta.

Najwa dai kuka takeyi da jin labarin yanda yake haka,  bata taba zaton  haka sukayi suffering ba,  tausayinsu ya kamasu.

 

Hajjo da kuka yaci karfinta ta shige daki,  bata son kuka gaban Jikoki da yaranta,  Zaineema ta rarrafa gun Mummy tace “Mummy,  i’m so sorry,  ba musan da hakan ba,  da kun gaya mana,  we are your Children,  kamata yayi mu kasance tare da juna a lokaci irin  haka ba,  ku yafe mana,  kuna nan cikin kunci mu muna chan cikin jin dadi” Ziyada ma ta rarrafa gun Daddy tace “eh,  kamata yayi ku sanar damu,  we should be with eachother, ku dinga sanar da mu komai,  i’m sorry,  kun shiga cikin kunci ku kadai” ta fashe da kuka me karfi,  Daddy ya janyato ya rungume yana shafa bayanta,  itama Zaineema  ta fada jikin Mummy,  duk suka hau lallashinsu,   Najwa ta kalli Majeed,  shima ita yake kallo, da damuwa take kallonshi, shi kuma kokarin yi maa Murmushi yake, hawaye ta gani sun gangaro kan kumatunshi,  ji tayi dama tana da halin rungumoshi ta lalashe shi, so take ta gaya mai “komai zai yi daidai,  komai zai zo karshe,  komai zai wuce ayi kamar baayi ba ” tana so ta lallashe shi,  haka suka tsaya har sai da Daddy yace “ku mu shiga ciki,  nan sauro,  ga wadannan kwarin masu bin hasken lantern din  nan cizonsu zafi, ku tashi ku shiga dda kayanku ciki” Zaineema tace “wai ba wuta ne?” Majeed yace “gobe InshaAllah  zanje gun Nepa,  don da alamun an yanke wutan Gidan nan” hawaye ya zo ma Ziyada da sauri ta tashi tayi cikin daki,  ba zata tuna when last taga sun zauna  cikin duhu,  da wayanta ba zata tuna ba,  gen dinsu standby ne,  da an dauke yake kunna kanshi, amma yau sune suke haske wuri da torchlight din waya,  wannan shine chanjin Rayuwa.

 

Washe Gari.

 

Bayan sun yi Asuba Mummy ta tashi don hada ma yara ruwan wanka da kalacin da zasuyi kafin su tafi makaranta,  kitchen ta so ta shiga,  amma kitchen din be shiguwa,  irin kitchen din tsakar  gida ne,  duk yanar gizo ya baibaya kofar,  ciki k’ura, ta shiga sai ta jawo ma kanta Athma, ta dan fara waigewaige a tsakar gida,  wani katon tukunya ta gani wanda Hajjo kan dafa Zogalar sanaarta, sai wani ledan Omo da ya bushe a gefe tun ragowar Hajjo, Drum ta bude taga ruwa duk ya kare,  dama ba ruwan famfo, gindin Rijiya ta karasa,  ta jawo guga ta fara jan ruwa,  har sai da ta cika drum din nan,  kafin ta wanke tukunyar,  ta harhado leda a bola,  ta hada itace ta kunna wuta,  faifai ta dauko tana hura wutan da karfi kasancewar ba kanazir,  ta jima tana hura wutan,  ta shagala da hura wutan, idonta yayi jazir,  hawaye ya fara diga, waigawan da zatayi idonta ya sauka kan ‘yayanta,  Zaineema da Ziyada,  rungume suke da junansu,  Imani na ratsa su,  fitowarsu kenan don shiga gaida Daddy da Mummynsu suka ga Mummy na ta aikin wahala, rashin karfin jiki ya hanasu zuwa su karbeta,  basu san meye takeyi haka ba,  sun san dai ta dibo ruwa a rijiya,  kuka suke sosai,  da sauri ta karaso gunsu tana kwakulo Murmushi “My Babies,  kun tashi lafia?” Ziyada ta runtse ido ganin yanda idanun Mumnynsu yayi ja,  Zaineema tace “Mummy me kike yi haka?” Mummy  tace “wuta zan hada a murhu,  in samusu ruwan wanka da na tea, yara zasu tafi makaranta” Zaineema cikin daga murya tace “haka murhun yake? Kina ta hurawa idonki na fitar da hawaye? Mummy kina–” kasa  karashewa tayi ta fashe da kuka mai tsuma rai, ta rungume Zaineema tana lalashi.

 

Daidai nan Majeed da Daddy suka shigo gidan,  dama in sukaje Massalaci  sai  gari ya waye suke dawowa gida,  ganin su cirko cirko yasa su karasa gunsu da sauri,  idanun Ziyada runtse suke gam, Majeed ya tallafo kumatunta,  yace “Zuzu,  ya akayi ne?”  a hankali ta bude idanunta ta nuna murhun dake chan gefe tace “YaMaji,  ji abunda Mummy take hadawa,  wai sunanshi Murhu, wai dashi zata hada wuta ta sa ruwan zafin da zamu sha tea muyi wanka muje makaranta,  YaMaji,  tana hurawa idanunta na ruwa,  tana hawaye,  duniya juyi juyi, YaMaji wai yau Mummynmu ke diban ruwa a rijiya,  kaga drum din da ta cika chan,  Ya Maji wai Mummynmu,  Mummynmu fa” suka fashe da kuka a tare, Mummy tana jin kukan yaranta a cikin kanta, zuciyarta ta karaya, tasan yanzu suka fara Kuka,  basu ga komai ba,  rayuwarsu ta chanza,  sai sun koya dauke kai ga duk sabon yanayin da suka tsinci kansu, ganin kukan ba me tsayawa bane Daddy yace “akwai sanyi,  ku mu shiha ciki” hanayensu suka ja suka shiga ciki.

 

BAYAN KWANA BIYU

 

Duk wasu chanjikkanshi Aljihunshi sun k’are, be san ta wani hanya zasu fara dafa abinci a Gidan  ba,  Kosai da Koko suke siya su ci da safe,  ko kuma ya siyo ruwan zafi da kayan shayi su sha tea,  da rana suyi takeaway din abinci me saukin kudi, da daddare ma haka, a talauce a rana suna kashe dubu hudu, dole ya nemi aiki, ko wani iri ne, ko da kuwa Welda ne ko kafinta, ya maga akwai shagon kafintoci a anguwan nan,  zaije ya nemi aiki a wurin,  ko da yankan katako ne,  shidai burinshi su biyashi, yanzu kawai hanyan tsira yake nema musu, zuciyanshi na zafi in ya kalli kannenshi,  da Iyayenshi,  musamman kananan,  yana tausayin Muhsin da Zinatu,  sune yara,  ba su san rayuwa ba,  ba su saba da wannan rayuwar ba,  ba haka suka taso ba,  su cikin daula suka taso,  basu san rashi ba, ko don su dole ya nemo aiki,  be damu ba ko da aikin gyaran takalma zaiyi,  ko yasar kashi,  shi dai hanyar samu zai nema.

 

Majeed ya yanken hukuncin zuwa wani shagon Kapitoci da ke gefen gidan Hajjo ya nemi aiki, be gaya ma kowa ba, ya fita wurin karfe 10, dole fa ya nemi aikin da zai rike Gidansu, Babanshi ya tsufa, ya zama weak, dole shi din zai mike tsaye a kansu.  Da ya isa shagon  ya tarda Ogan,  ya gaisheshi cikin mutuntawa,  Ogan  yace “lafiya” Abdulmajeed  ya murmusa yace “Sunana Abdulmajeed,  ina neman Alfarman fara aiki a shagon nan,  ko wani iri ne” Ogan ya kalleshi galala,  yace “ina da maaikata,  bana bukatan sabbin Maaikata” Kafa biyu Majeed ya durk’usa ya  na rokonshi da ya taimaka  mai,  yace mishi zai iya ko wani irin aiki ne,  da Ogan ya ga majeed na cikin bukata dai yace “toh, zaka dinga goge min katakai da san paper,  kwana biyar muke aiki,  banda Asabar da lahadi,  in kulluma kake so a biyaka to,  in kuma sai karshen Sati ne to,  a rana zan  baka dari biyu da hamsi,  a kwana biyar kuma dubu biyu da dari biyar,  zan baka shawaran ka bari sai karshen sati,  don kaji kudin da dan kauri ko ya kace?” Majeed be da bakin magana,  salati yake yi a zuciyarshi,  imani na sake shiganshi,  dari biyu da hamsin a rana? Shi Abdulmajeed?” Ogan yace “Kayi  shiru,  ko bai maka  bane?” da sauri Majeed  yace “aa yayi Allah ya sa musu Albarka”.

 

Sun ta kiran wayarshi be dauka ba,  duk sun damu,  sai gashi chan ya shigo bayan Azahar da ledojin Abinci,  duk suka bishi da ido,  ya mika ma kowa nashi,  Mummy ta kafe shi da idanunta tace “ina kaje boy?” yayi shiru,  sake tambayarshi  tayi yace “ina gun aiki” da mamaki  sukace ina ne gun aiki?  Yaushe ka fara aiki?” yau,  wani Capentry shop ne chan kusa da masallaci” baki bude suke kallonshi,  Hajjo tace “Shagon Yushau?” Majeed yace “eh chan ne” Hajjo tace “me ya ja maka zuwa aiki gun Yushau?  Be da kirki fa,  a wulakance yake daukan maaikatansa,  kowa ya sanshi be da mutunci” Majeed yayi Murmushi  yace “ba ruwana dashi,  aiki zan mishi ya biyani kudina” Mummy tace “Me zaka mishi?  Kuma nawa zai biyaka?” Majeed yace “ba muyi maganan wannan  ba” cikin kakkausan Murya Mummy tace “Abdulmajeed” duk suka zuba mata ido,  a tsawon saninsu Mummy bata kiran sunan Abdulmajeed,  ko Majeed bata ce mishi,  ganin  ba wasa a fuskarta Mummy Majeed yace “Zan dinga goge katako da sanpaper ne,  kuma zai biyani 2500 a duk karshen wata”.

 

Mairo hankalin ta ya tashi tace “dari biyu da hamsin a rana? Wallahi bazakayi ba,  sai dai duk mu mutu” Majeed cikin  lallashi yace “Mummy, wannan ba lokacin muhawara bane, we are trying to survive,  is not about our pride,  ba zaiyiwu mu zauna haka ba ban aiki,  a sannu ake farawa” tace “Kafi karfin haka Boy,  wallahi  kafi karafin Kafinta” yace “aa wallahi,  Mummy in ban karbi aikin nan ba,  wata rana zamu mutu don yunwa da kunci,  and kuma sai dai inyi yawo tsirara da in  ga ranar nan,  ko wani aiki ne zanyi,  ko da kwasan kashi ne, indai zaku kasance cikin koshin lafiya”  duk sukayi shiru kamar ruwa ya cinyesu,  Daddy kunyar Yaranshi  yakeyi,  be musu planning kalar rayuwar nan ba,  kana naka Allah na nashi.

 

Ziyada tace “gaskia ne YaMaji, its not about our pride,  Survival muke so,  Allah  ya saka maka da Alheri,  and ina so ka sani,  ba kai kadai bane Da a cikin Gidan ba,  ba kai kadai bane kake son farincikin Gidan nan ba,  ba kai kadai kake son daukar hidimar Gidan  nan,  muma yayane, you dont have to go through all this alone,  zan shigo ciki” Majeed ya murmusa yace “Zuzu,  i understand  you want to help,  kar ki manta kina karatu,  what can you possibly do?” Ziyada ta murmusa  tace “Zan nemi aikin aikatau shara da wanke wanke a wani gida,  ko inje restaurant in nemi aiki,  ko na wanke wanke ko na Abinci” Da k’arfi Mummy tace “God Forbid,  over My Dead Body, Wallahi ba zai taba yiwuwa ba,  sai bayan raina zakuyi irin Aikin nan,  Wallahi ba ku isa ba,  sai dai in na mutu zakuyi aikatau” kuka takeyi sosai,  ba kasafai ake ganin kukanta ba,  amma Yaranta ne,  yaranta fa,  suke maganar Aikatau,  duk suka fashe da Kuka,  Hajjo ta na kuka tace “tunda Zogalar nan tayi tsawo sosai,  sai in tsinko in cigaba da dafawa ina saidawa” Daddy yace “Aa Umma,  nima saidai in mutuwa zanyi kafin ki koma Tallar Zogale”.

 

Najwa ta tashi ta shiga daki da sauri,  ta na tausayin su,  bata zo lokacin  da suke cikin ganiyar kudi ba,  amma ta san cewa they dont deserve this,  tasan cewa family din basu san kunci ba,  ta san cewa wani Azalumi ne ya tarwatsa su,  taji tsanar Azalummin nan,  tana mishi fatan halaka,  ta share hawayenta ta shiga cikin kayanta ta ciro envelop,  ta mike ta fita,  suna nan yanda ta barsu,  kusa da Majeed taje wanda ya hada kai da guiwa yanda zai jita tace “Jaaan” ya dago,  ta mika mai Envelop din, kallonta ya tsaya yi kafin ya mik’e tsaye,  ba tare da ya karba ba,  yace “menene nan Pure Heart” Murmushi  tayi tace “kudin da su Maama suka turo min ne,  take it,  nasan ba zai maida muku jin dadin da kuka saba ba,  its just 300 dollars,  ba zai muku komai ba,  but atleast zai rage abubuwa  da yawa” Majeed ya hadi miyau kafin yace “Aa Pure Heart i cant accept this,  naki ne,  ba zamu karba ba” cikin dan daga murya tace “Jaan,  me kakeyi haka? Meye haka?  Dama baka daukeni yanda na daukeka ba?  I thought  mun zama daya,  i thought damuwarka damuwata ne,  yanda ka maida damuwata naka, ka taimaka min tun randa na fara ganinka zuwa yau,  menene don ina son yin hakan nima?  We are a Team Jaan,  you help me i help you,  thats how it supposed to be,  bawai kai always on my aid ba, and you wont allow me to be on your aid now,  it hurts,  ba dadi,  kasa naji kamar banda amfani,  ka sa naji kamar sakara” duk suka zuba mata ido tana ma Majeed fada,  barin ma Mairo,  ba suyi zaton tana magana haka ba,  ita bata ma san tanayi ba,  maganar Zuciarta kawai take fiddo fili,  cikin sanyin Murya Majeed yace “Pure Heart!”.

*******

 

Hello Bibilicious Freaking fans,  ana gwarama a legas, duniya juyi juyi kwado ya fada a ruwan Zafi,  wa zai taba zaton Hajia  Mairo ta iya jan ruwa a rijiya?  Harda hura wuta a murhu,  Allah Mai iko.

 

Oya yanda na faranta muku rai da wannan page din ku danna wani dan tauraro da ke kallonku a kasan page dinnan,  and kuyi sharhi akan ko wani layi,  lol,  what i meant to say is,  vote and comment line by line..

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa.

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣0⃣

 

Ta dago rinannun  idanunta ta kalleshi,  yace “ba zan karba ba,  naki ne,  kema kina da bukatansu” tace “na sani,  amma a yanzu kunfini bukkatarsu,  so kawai ka karba” ta tsareshibda idanunta,  bata bashi kofar yi mata gardama ba,  ajiyar zuciya ya sauke da karfi,  yace “Fine,  100 dollar kawai zan amsa,  kuma shima da Allah ya hore min zan maido miki da kudinki, i wont hear more,  otherwise forget it(ba zan ji komai ba,  in ba haka ba kuma ki manta da maganan kudin)”.

 

Ba ta ce komai ba ya zari 100 dollars,  Daddy yace “Najwa Mungode Allah  ya biyaki” Murmushi tayi,  hawaye yazo mata tayi daku da sauri, Daddy ya kalli Mummy yace “to kin gani  Maryam,  kina ta kyarar yarinyar nan,  gashi ta taimaka mana” Mummy  ta tabe baki tace “tunda tazo Gidan,  ta taba biyan kudin abinci ko kudin dakin da take kwana ko kudin  wani abu? Ai in akayi calculating daga randa tazo zuwa yau in a hotel take zai fi 35000 din,  dama duka dollars din aka karba” duk suka bita da kallon how can someone  be like this?  Daya bayan daya suke sabewa suna shiga daki  Mairo ta bisu da ido ta watsa hannayenta sama tace “to me nace?”.

 

Washegari.

 

Abdulmajeed be koma bacci ba bayan Asuba,  ya hau firdo tarkacen Hajjo na kitchen,  ya share kitchen din tas,  ya jawo ruwa a rijiya,  duk da gabanshi na faduwa,  da fargaba da ya leka zurfin rijiyar,  be taba jan ruwa a rijiya ba tun da Mumnynsa ta haifeshi, sai da ya cika drum kafin ya wanke kitchen  din tas.

Najwa ta fito zata  shiga toilet taga Abdulmajeed na ta cin aiki,  batace mai komai ba ta shiga toilet ta yi fitsarinta ta fito ta je ta mai tsaye,  yaji alamun mutum a tsaye kanshi,  ya dago  kai be san saada Murmushi  ya subuce mai ba,  ya ajiye tsintsiyar hannunshi ya mike tsaye yana kallonta,  bakinta ta turo ta juya dayan gefen wai ita fushi take dashi,  Murmushi  yayi sosai,  Allah  ya san yana son Najwa, har cikin ranshi yake jinta,  a hankali ya tako har gabanta,  ba tare da yace mata komai ba ya daura hanayenshi biyu kan kunnuwanshi, cikin murya me kama da rada yace mata “i’m sorry pureHearty na,  kuma kar kiyi fushi dani” idanuwanta cikin nashi,  a ranta tace “how can he be so cute?” a fili kuwa ta k’ara daure fuska tare da juyawa dayan bangaren,  be saduda ba ya sake juyowa inda take ya shagwabe fuska kamar dan yaro,  sai taga ya mata kama da Muhsin yace “kuma in baki daina fushi dani ba,  zanje in hau saman transformer ayi ruwan sama kuma in makale,  haka” ya mata alama da hannu,  bata san lokacin da ta fashe da dariya ba,  shima dariyan yayi yace “there, the smile is all i want purehearty” bata san lokacin  da ta sake mai Murmushin da yake matukar so ba,  sun dan jima suna exchanging looks,  kafin suka ji muryan Ziyada  da Zaineema nacewa “Excuse us” firgigit sukayi suna kallon kofan kitchen din,  Ziyada tace “YaMaji are we interrupting something?” Kasa magana sukayi sai blushing da suke, Zaineema  tace “Ziyada wai are these two inlove?” Ziyada zatayi  magana Abdulmajeed  yace “Shuttup Zuzu, ni tsaranku ne? ” suka fashe da daria,  Najwa ina zata sa kanta don kunya,  Zaineema tace “zo nan Najwa” Najwa kanta a k’asa zata  karasa gun Zaineema  Abdulmajeed  ya sha gabanta yace “ba inda zaki PureHeart,  ku kuma wallahi  zanci  mutuncinku” sukayi daria duka,  Ziyada tace “wai aiki kakeyi?” yace “No ku koma daki” Zaineema tace “wallahi aiki kakeyi,  ya kamata a gyara gidan ma” Abdulmajeed  yace “ku wuce daki zan gyara” Ziyada tace “Sam sai dai muyi a tare” da kyar ya yarda ya raba musu aiki.

 

Sanitation sukayi na Gidan gabaki daya duk wasu yana na saman ceiling sai da suka cire, wurin 10 sun  gama komai,  Zuwa yayi wanka,  ya fita yayi changing dollar din,  dubu 35,900 ne,  ya shiga kasuwa ya musu siyayya,  kama da  richo,  kanazir,  kayan shayi, kwalin indomie,  bobo da biscuit na yan makaranta,  sabulun wanka da na wanki,  da dai kayan amfani daidai kudinsu,  ya biya ya siyo lantern, ya biya ya bada kudin nepa dubu sha daya,  ya siyo bulb na wuta,  kudin da ya rage dai dubu bakwai,  ya dawo gida a kan adaidaita sahu da kaya nikiniki, kamar wanda ya dawo daga Dubai haka suka tareshi,  suka ta yashe baki abun zattausayi,  haka suka jera komai inda ya kamata,  nan suka ga kyan Gidan,  Mumny ta dage ta zira lagwani a jikin risho,  aka dura kanazir a risho din,  aka daura Abincin Rana.

****

 

Be san meyasa ba ya shiga damuwa,  kiran wayarta yayi a karo na kusan ba adadi,  wayarta kashe,  rabon da yayi waya da ita  tun randa tace mishi zasu koma Gidansu, ba wai ya damu bane,  yace ma zuciyarshi,  kawai ina so in ga ta yanda zan k’untata mata, ban damu da ita ba,  ban damu da komanta ba,  all i want is revenge, ya buga tsaki,  ya dauki keys din motarshi ya fita daga dakin,  Guest house din Baba Ado ya nufa, straight ahead Gidan ya shiga, kasancewar an sanshi ba wanda ya tambayeshi ko an san da zuwanshi ,  da Sallama ya shiga Parlorn,  Baba Ado na zaune kan wat kujera ta alfarma yana karanta wata Jarida,  Zaid ya taka cikin takun kasaita har gabanshi ya durkusa ya shafi k’afanshi,  shi kuma baba Ado ya dafa kanshi (haka ne gaisuwan yan Mali yake) Jaridar hannunshi ya ajiye,  ya mikar da Zaid suna kallon juna,  kafin nan ya rungumeshi.

 

Kafin kace komai tuni an cika ma Zaid gaba da kayan motsa baki, sai da ya bata lokaci kafin ya dauka grapes daya ya fara tauna a kasaitance,  kasancewar  Baba Ado ya san Zaid ciki da bai,  ya san halinshi,  ya san yanda zai tafiyar dashi, yace mai “Ka sanar dasu zamu zo yau din?” kamar ba zai amsa ba chan yace “Wayarta a kashe yake” Baba Ado ya dago ya kalleshi,  yace “kenan basu san zamuzo ba?” dan gajeren tsaki yayi yace “Wayarta kashe yake” Baba Ado yayi jim, kafin yace “to ya zaayi kenan? Na kira abokan babanka biyu sunce mu hadu karfe hudu,  Alhaji  Hamisu ma musamman ya hau jirgi daga Porthacourt yazo Kano” Zaid yace “Zakuje ai” “ba su san da zuwanmu ba din?” Zaid yace “ai ba wani abu bane,  suna Gida” Baba Ado yace  “amma dai be kamata  ba Zaid” da sauri Zaid yace “Please Baba Ado,  banson a samu matsala, banson Auren ya wuce Friday din nan, ka taimakeni” Baba Ado ya murmusa,  a zatonshi Zaid na kaunar yarinyar nr da har ba zai iya kara daukan wasu lokuttan ba tare da ya aureta ba, kuma dai abun farincikimsu ne tunda Zaid da bakinsa yace yana son auren,  gwara su mishi kafin ya chanza raayi.  Baba Ado ya ja numfashi yace “Zamuje Gidan Bayan Laasar”.

 

Bayan Laasar.

 

Abdulmajeed  da Daddy suna hanyan dawowa Gida daga Masallaci,  daga nesa suka ga Motoci kusan  guda Biyar a daidai kofar Gidan Hajjo,  Daddy ya kalli Abdulmajeed, yace “baki mukayi?” Abdulmajeed yace “da Alama” daga nesa Daddy ya hango Baba Ado,  kasancewar Babban mutum Sananne yace “Abdulmajeed  kamar Alhaji Ado Mali na GG” Abdulmajeed da mamaki yace “shine Daddy,  ko Lafia?” Daddy  yace “kace me neman Ziyada dan Marigayi Gatan Marayu ne ko?” Abdulmajeed  yace “Eh,  Zaid sadam sunanshi” Daddy yace “to ba abun mamaki bane, kowa yasan Alhaji Sadam da Alhaji Ado Aminanna juna ne,  kila neman auren Ziyada sukazo” Abdulmajeed ya jinjina kai suka karasa gunsu,   da Sallama, ta cikin Mota Zaid ke kallonsu cike da tsana,  ji yake kamar ya fita ya makure su,  a karo na biyu tun bayan da sukazo mai taaziyar Babanshi zasu hadu gaba da gaba,  yana jin Daddy da daya daga cikin Abokin Baba Ado suna gaisawa,  Abdulmajeed ya gaishesu cikin girmamawa,  Baba Ado yace “Alhaji Abba Abu dama wurinka mukazo” Daddy  jiki na rawa yace “mu shiga daga ciki”.

 

Abdulmajeed  yayi saurin  shiga Gida yace “ku koma daki, anyi baki” Mairo tace “su wanene?” Abdulmajeed  yayi  Murmushi  yace “masu neman  auren Zuzu ne” dam gaban Ziyada ya fadi,  Mummy ta yashe hakori ta na gyara zani tana tura yaran su fita daga palo tana cewa “Gatan Marayun ne?” Abdulmajeed  yace “magabatanshi ne” daki suka koma,  Ziyada ta rasa me takeji,  dadi ne?  ko tsoro? Mummy tace “Diyata kwantar da hankalinki mu mun dangwalo arziki” shiru  suka mata kowa da tunanin da yake.

 

Zaune suka a cikin Parlo,  ba abunda kakeji sai gaurayen daddan k’amshin turarensu, su 4 ne zaune,  sai Daddy na biyar,  Abdulmajeed  ya fita don siyo musu Lemu, nan suka sake sabon gaisuwa,  Baba Ado ya fara magana kamar haka ;

“Da farko muna neman afuwan zuwa ba tare da saninku ba,  ko kuma ince izininku ba” Daddy yace “haba bakomai wallahi” Baba Ado ya cigaba da cewa “Alhaji Abba Abu, sunana Alhaji Ado na Mali, Amintakarmu da Marigayi Alhaji  Sadam Audullahi ya sa muke jin kanmu kamar yanuwana jini, Yaronshi Zaid wanda ake ma lakabi da gatan Marayu na biyu na neman diyar gurinka Ziyada,  be da wanda zai shige mai gaba kamar mu,  duk nan da kake ganin mu ba wanda be ci Albarkacin Gatan Marayu ba,  ya mana abunda ba zamu taba mantawa ba, ba wannan ba, Yaronmu ya gano fure a Gidanka,  kuma yana so a bashi damar tsinka” sukayi dariya gabaki daya.

 

Daddy ya muskuta yace “To Alhamdulilah,  nayi farinciki matuk’a da wannan zance,  babban abun farinciki  shine kasancewar dan Baban Gida kamar dan Gidan Gatan Marayu na neman diyata da aure,  ba wanda ba zaiso hada iri da Alhaji Sadam Audu ba,  kowa ya sanshi datijjon kirki ne,  ban taba ganinshi ba,  amma abubuwan Alherin da yayi na isko mu, kuma ko bayan rasuwarshi danshi ya cigaba daga inda ya tsaya,  Alhaji Sadam Audu is a legend,  he is Dead,  but his legacy still lives, so babban abun Alfahari na be wuce ganin diyata ta auri Yaron Baban Mutum kamar Marigayi Alhaji Sadam ba,  amma wani hanzari ba gudu ba,  duk yanda nake son wannan abu ya kasance,  ba zai wuce da Amincewar yarinya ba,  in bata amince dashi ba,  to ba yanda zaayi sai dai ayi hakuri,  don banda niyyar aura ma yarana wanda ba sa so” Alhaji Ado yaji dadin Dattakon Alhaji Abba,  yace “haka ne,  yi ma yara auren Dole ba fa’ida,  amma ina da tabbacin suna son juna, shi dan gurinmu ya tabbatar mana da hakan,  yana waje barin kirashi ya sake tabbatar mana da hakan” ya zaro wayarshi ya latsa ma Zaid kira,  ringing  daya Zaid ya dauka “Eh Hello, ka shigo ciki” be tsaya jiran abunda Zaid zaice ba ya kashe wayar.

 

Zaid yayi jim yana kallan wayar,  takaicin Baba Ado yaji,  don me zai kirashi? Me zaije ya musu? ” Idi yace “Oga ka shiga kawai,  Allah ya soka Baba Ado ya baka Manyan kaya kasa, lafiya lau ne, ka shiga kawai,  remember  gaban sirikin ka kake,  banda kallonsu cikin ido,  kuma a kasa zaka zauna” tsaki Zaid ya buga da karfi ya bude kofa ya ma su Amrstrong banging da karfi,  suko suka fashe da daria,  cikin Gidan yayi,  gidan ba bakonshi bane, takalmominsu ya gani daga waje,  yayi Sallam ya shiga suka amsa mai,  a k’asa ya zauna kamar yanda Idi yace, murya cikiciki ya gaida Daddy,  Daddy da faraarsa ya amsa.

 

Baba Ado yace “MashaAllah,  Alhaji Abba ga Yaronmu,  durfane gabanka, yazo neman auren diyarka,  be zo a matsayin Gatan Marayu na biyu ba, yazo ne a matsayin  Zaid Sadam me son diyarka Ziyada” kan Zaid a kasa,  yanda yake magana sai yake jin wani nauyi na sauka a kansa,  anya zai iya kuddirinsa? Kafin Daddy ya bada amsa Abdulmajeed ya shigo dauke da Lemuka su coke fanta mirinda a talauce (waya ce maka suna shan irin wanan? lol).

 

Alhaji  Abba yace “ga Baban dana,  yayan Ziyada  ne,  sunanshi Abdulmajeed” Abdulmajeed  ya dirr lemukan a k’asa ya sake gaidasu,  suka amsa da faraa,  Daddy yace “AbdulMajeed,  je ka kira min Mummynku da Ziyada,  inshort ka kira min kowa da kowa har Mama” Abdulmajeed  ya mike a ladabce ya fita,  a dakin Hajjo ya iskesu duka,  yace “Mummy kuzo Daddy na kira” jiki na rawa Mummy ta zaro  mayafin da bata san ko na waye ba zata fita Abdulmajeed  ya tareta,  yace “tsaya Mummy,  gabaki daya zamuje,  Zaineema ku muje,  Hajjo har ku” duk  suka tashi  suna neman mayafin sakawa banda Ziyada da ta takure wuri daya,  Abdulmajeed  ya kallota ya bude drawer ya ciro wani k’aton gyale ya rufe mata jiki yace “come on zuzu, ba zaki bar surikanki suyi ta jiranki ba ko?” ta mike  jiki ba kwari,  Abdulmajeed ya ja hannunta suka fita, duk suka rufa musu baya banda Najwa da ta ke  gyara inda su Muhsin suka 6ata.

 

Sallama sukayi suka shiga,  suka amsa  da faraarsu,  duk suka samu wuri suka zauna, kan Ziyada a k’asa,  Baba Ado ya nuna ta da yatsa yace “ga Amaryanmu nan” ta sake sadda kanta k’asa,  Daddy yace “haka ne, nan Iyalai na ne dukkansu,  Wannan itace Mahaifiyata,  wannan kuma Mai dakina” ya nuna Mairo da hannu,  ita ko sai faraa take watsa musu”  wannan kamar yanda na gaya muku shine babban da na AbdulMajeed,  sai me bi mishi Zaineema,  sannan Ziyada,  Zinatu ke bi mata sai auta Muhsin” Alhaji Ado yace “MashaAllah,  Allah ya ja kwanan zuria,  matuka kun burgeni,  ka nuna mana dattako da karamci,

Hak’ika hankalin mu zai kwanta ganin gidan da yaronmu ya dauko mata” Daddy  yace “haka ne,  amma bari mu ji ta bakinsu ko?”.

 

Alhaji Bello yace “Zaid,  shin wannan itace ka zaba ta zame maka abokiyar rayuwa har karshen rayuwarka?” be san dalilin da yasashi faduwar gaba ba,  yayi shiru gabanshi  na dukan chalugude,  baba Ado yace “Zaid?” da sauri yace “Eh itace”. Daddy  ya juyo kan Ziyada yace “Ziyada kin amince in bada aurenki ga Zaid? Kar kiji nauyi ko wani abu in ba kya so,  sai in basu hakuri,  ki fada min ranki,  farincikin ku ya fiye min komai” Ziyada ta sadda kanta kasa, Daddy yayi maganan duniya amma tayi shiru ba tare da ta tanka ba,  yace “ko ba kya so?” nan ma shiru tayi,  Alhaji Bello yace “Ziyada magana zakiyi kinji?  Ba zamu gane me ke cikin ranki ba in ba magana ko alama kika mana ba, kina son sa,  ko ba kya sonsa?” shiru tayi har yanzu ba tace  komai ba,  Mummy ji take kamar  ta gwala kan Ziyada da bango, Alhaji Sani yace “kun san dai ma’anar shirun budurwar kirki,  yana nufin ta amince kenan” Alhaji Kabir yace “aa kar ayi saurin yanke hukunci,  duk tambayar da aka mata shiru tayi,  ya kamata musan amsarta,  muna iya bata lokaci tayi tunanita gaya mana sirrin da ke ranta”.

 

Abdulmajeed  yace “Erhm,  in zan dan iya magana da ita,  zan samo mana amsar da takasa fada” Daddy yace “Eh Abdulmajeed  kuje kuyi magana” hannunta yaja suka fita daga Parlorn, Daddy ya musu alamu da su bisu, su Mummy suka tashi suka tafi,  be san meyasa yaji gabanshi na faduwa ba,  what if tace bata sonsa? Plan dinshi ya zube kenan?  Plan kadai?  Cewar zuciyarshi,  da sauri yace “eh,  plan dina ne kawai,  be san mesa ba amma sai ya tsinci kanshi da yin adduan Allah  ya sa ta amince.

 

“Zuzu lookat me, talk to me,  kina sonshi? ” cewar Abdulmajeed,  da sauri ta kallo yayanta tace “YaMaji,  a cikin halin da muke ciki,  maganar aurena shine karshen abunda ya kamata ayi,  muna cikin halin ha’ulai,  Ya Maji–” ya katseta da cewa “shhhh,  ki amsa ni,  kina sonshi?” rungumeshi tayi da sauri tana gyada kanta a jikinshi,  yayi daria yace “abunda nake sonji kenan” ya juya ya tafi yayi Parlor,  ya rada ma Daddynsu a kunne,  Daddy  yace “to Alhamdulilah,  yarinya  ta Amince” duk sukayi hamdala suna faraa,  Zaid ya sauke numfashi a hankali yana gode ma Allah.

 

Alhaji  Ado yace “Alhaji Abba ka bamu?” Daddy yayi daria yace “na baku” sukayi daria sukace “mun karba kuma mungode,  muna so ayi Auren Ran Juma’a me zuwa in Allah ya kaimu” Daddy suka kalli juna da AbdulMajeed,  Daddy yace “Alhaji,  da wuri haka? Ni ina zaton sai daga baya zaa sa bikin kuma zaa sa a kalla wata 10” Alhaji  Ado ya zaro ido yace “Wata Goma dai? Me zaa jira Alhaji tunda yara na san junansu,  ka bamu kuma mun karba? Me zaa jira?” Daddy yace “haka ne,  amma akwai wata yar matsala da ta auku,  ina neman Alfarma a bamu lokaci mu maganceta kafin ayi ma maganar daurin auren yaran” Alhaji  Ado yace “nasan kana so kama diyarka kayan daki,  nasan kana so nyna bajintarka a matsayinka na Baban yarinya,  nasan kana so kamata kayan daki kamar yanda ko wani uba yakr ma diyarsa,  amma Ba fin karfi,  ba nuna isa ba, ba ma bukatar komai,  Yarinya muke so kuma kun bamu,  ita ral muke so a daura aure Yaro ya dauki matarshi ya kaita Gidanta” Daddy zaiyi magana Alhaji Ado ya katseshi da cewa” Gatan Marayu na farko ya kan daura ma Yara 100 aure a rana wanda be sani ba fa,  ya musu lefe ya musu kayan daki, to me kake tsammamin zai ma Yaronshi in ya tashi aure? Ka na tunanin zai barsu su siya koda kara ne?” Daddy yayi jim kafin ya kalli Abdulmajeed  neman shawara,  da ido ya gyada mai kai Alamun ya amince,  Daddy yace “haka ne, toh Allah ya saka da Alheri,  Allah ya kaimu Jumaa din” Alhaji Ado yace “Ameen,  ba shishigi ba,  amma  wata irin matsala ce da kuke son magancewa?” Daddy yace “ba wata damuwa bace,  kar ku damu” Alhaji Ado yace “haba Alhaji, tunda ka bamu diya ai an zama daya, ka gaya mana ko menene”.

 

Daddy ya yi shiru kafin yace “Akwai Alhaji Nakowa da muka samu sabani dashi— tiryan tiryan ya kwashe labarinsu da Alhaji Nakowa zuwa yau” Allahu Akbar, Zaid dai duk wani guiltiness ya kamashi,  be taba jin tausayin mutanen nan ba ko kadan amma yau da Daddy ke bada labarin sai yaji wani bangare na zuciyarshi na tausaya musu,  da sauri gudan zuciarshi ke mai gargadi da kar ka sake kaji tausayin Azzaluman nan da suka maka katangar karfe da mahaifanka,  da sauri ya yakice tausan da ke ranshi,  be ankara ba sai ji yayi Alhaji Ado na cewa “Alhaji Abba,  tunda yanzu an zama daya zan bada Miliyan 30 din ku biyasu” Daddy yace “gaskia ba zan amince ba,  abun ai sai yayi yawa,  gaskia ba zan yarda ba,  abin da kukayi ma mun gode  Allah bada Lada” Alhaji Ado yace “Haba Alhaji Abba,  ashe baka yarda an zama dayan ba,  to in ba mu ma Zaid  ba wa za mu mawa,  na gaya maka duk nan ba wanda be ci albarkacin Gatan  Marayu ba,  duk abunda muka mishi ko danshi bamu fadi ba wallahi” Zaid kamar ya makure Baba Ado,  ya sanshi da kafiya,  biya musu bashin nan na nufin basu da wata damuwa,  meyasa yake da shishigi ne?  Tsaki yake ta bugawa a ranshi yana cewa shifa baba adon nan da matsala yake,  shi kuwa Daddy ya san cewa in suka rasa tallafin nan ba wanda zai sake tallafa musu, this is the only chance they have,  amma be bi san zucianshu ba yace “duk da haka , kuyi hakuri we are not your responsibility,  in sunyi aure duk abund zai mata ba me hanashi matarshi ce”.

 

Ganin ba zai amince ba dabara tazo ma Baba Ado,  yace “to in ranta maka mana? Da bashi a kan mutane irin Alhaji Nakowa gwara gida ko? Zan ranta maka,  in ka samu sai ka biyani” Daddy yace “to ina iya amince ma rance,  amma gaskia  ba kyauta ba,  kuma 25million ne,  don mun basu 5, zan dinga biyanka a hankali a hankali” Zaid  kamar yayi Ihu  don haushi,  yasan siyasa Alhaji Ado ya mai,  ya san ba zai taba karban kudin ba,  shikenan ya yanke musu wahala,  kamar yayi kuka,  nan dai suka cigaba da tataunawansu cike da mutunta juna,  Alhaji Ado yace “gobe zaayi banking a biya Alhaji Nakowa kudinshi, Alhaji Bello yace  bayan daurin Aure zaayi gagarumin walima” Alhaji Sani ya ciro rafar 1000 guda uku yace “ga Sadakin Amarya” duk abubuwan da akeyi bakinciki ya turnike Zaid,  shifa neman aure yace su zo su mishi ba san iyawa ba,  be san lokacin da ya mike ya fita ya bar parlorn ba,  ba su damu da shi ba don ba su ma lura da ya  fita ba,  ba jimawa suka tafi.

 

A GURGUJE

Mairo harda takawa tayi don Dadi da taji sun dangwalo Arziki,  har ce ma Ziyada take ta zo ta hau bayanta ta goyata ta share mata hawaye,  a zuciyarta take hasko yanda rayuwa zata canza mata,  zata fito gari ta taka duk  wanda ya tabata,  zata gurza ma makiyanta rashin mutunci,  Ziyada kam farinciki damke a ranta zata auri farincikin ranta, wai ita zata zama Mrs Zaid Sadam in two days,  she cant wait.  Bata so yin wani gayya ba,  amma Mummy tace sai tayi gayan friends dinta duk da ba wai yawa ne dasu ba,  a cewar Mummy ya zaayi ta auri Mutum kamar Zaid amma ba wanda ya sani? Dole ta gayyato kawayenta,  haka dai ta hada BC ta tura ma Friends dinta. Itama Mummy aka wuce gidan tsohuwar kawarta hajia Aliya tana bude mata hanci ita zata zama sirikar Zaid Sadam.

Alhaji  Nakowa yayi mamakin ganin Cheque da yayi daga account  din Ado Mali wai da sunan biya ma Alhaji Abba Bashi wanda daga Kotu aka turo mishi   ba haka yaso ba,  so yayi ya kuntata ma su Hajia Mairo,  amma ya ya iya?  Karawa da Alhaji Ado Mali kamar karawar kifi ne da mage.

 

JUMA’A

 

Bayan Sallahn Juma’ah ne a babban Masallacin Jumaa na Central Mosque dubbanin Jamaa suka shaida auren Zaid Sadam Audu da Amaryarsa Ziyada  Abba Abu a bisa sadaki Naira dubu dari uku.

 

Wasa farin Girki.

 

•••••••

 

Gyara: Dear Bibilicious freaking fans,  akwai wani gyara da wata baiwar Allah ta min, attimes ina using Abdulmajeed wasu lokuta kuma Majeed, Malamai suna waazi akan Kiran sunayen Allah hakan Nan batare da sa Abdul din ba, mu kuma mu kan yanke ko don gayu ko don gajeratawa,  amma hakan baban kuskure ne, to mu dinga kokari muna cikita sunan AbdulMajeed, from now henceforth zamu dinga karasa sunan,  in aka ga akasin haka to kuskure ne da kuma sabo,  ina fatab zamu gyara Nagode. .

 

Yekpa Anyi aure fa,  akwai Walima Party anjima,  you are all invited.

 

Akwai gwarama fa,  this is the begining of an end,  stay tuned,  yanda nake kokarin typing  haka,  kuma dont Forget to Vote and Comment line by line.

 

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa. 💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣0⃣

 

Ta dago rinannun  idanunta ta kalleshi,  yace “ba zan karba ba,  naki ne,  kema kina da bukatansu” tace “na sani,  amma a yanzu kunfini bukkatarsu,  so kawai ka karba” ta tsareshibda idanunta,  bata bashi kofar yi mata gardama ba,  ajiyar zuciya ya sauke da karfi,  yace “Fine,  100 dollar kawai zan amsa,  kuma shima da Allah ya hore min zan maido miki da kudinki, i wont hear more,  otherwise forget it(ba zan ji komai ba,  in ba haka ba kuma ki manta da maganan kudin)”.

 

Ba ta ce komai ba ya zari 100 dollars,  Daddy yace “Najwa Mungode Allah  ya biyaki” Murmushi tayi,  hawaye yazo mata tayi daku da sauri, Daddy ya kalli Mummy yace “to kin gani  Maryam,  kina ta kyarar yarinyar nan,  gashi ta taimaka mana” Mummy  ta tabe baki tace “tunda tazo Gidan,  ta taba biyan kudin abinci ko kudin dakin da take kwana ko kudin  wani abu? Ai in akayi calculating daga randa tazo zuwa yau in a hotel take zai fi 35000 din,  dama duka dollars din aka karba” duk suka bita da kallon how can someone  be like this?  Daya bayan daya suke sabewa suna shiga daki  Mairo ta bisu da ido ta watsa hannayenta sama tace “to me nace?”.

 

Washegari.

 

Abdulmajeed be koma bacci ba bayan Asuba,  ya hau firdo tarkacen Hajjo na kitchen,  ya share kitchen din tas,  ya jawo ruwa a rijiya,  duk da gabanshi na faduwa,  da fargaba da ya leka zurfin rijiyar,  be taba jan ruwa a rijiya ba tun da Mumnynsa ta haifeshi, sai da ya cika drum kafin ya wanke kitchen  din tas.

Najwa ta fito zata  shiga toilet taga Abdulmajeed na ta cin aiki,  batace mai komai ba ta shiga toilet ta yi fitsarinta ta fito ta je ta mai tsaye,  yaji alamun mutum a tsaye kanshi,  ya dago  kai be san saada Murmushi  ya subuce mai ba,  ya ajiye tsintsiyar hannunshi ya mike tsaye yana kallonta,  bakinta ta turo ta juya dayan gefen wai ita fushi take dashi,  Murmushi  yayi sosai,  Allah  ya san yana son Najwa, har cikin ranshi yake jinta,  a hankali ya tako har gabanta,  ba tare da yace mata komai ba ya daura hanayenshi biyu kan kunnuwanshi, cikin murya me kama da rada yace mata “i’m sorry pureHearty na,  kuma kar kiyi fushi dani” idanuwanta cikin nashi,  a ranta tace “how can he be so cute?” a fili kuwa ta k’ara daure fuska tare da juyawa dayan bangaren,  be saduda ba ya sake juyowa inda take ya shagwabe fuska kamar dan yaro,  sai taga ya mata kama da Muhsin yace “kuma in baki daina fushi dani ba,  zanje in hau saman transformer ayi ruwan sama kuma in makale,  haka” ya mata alama da hannu,  bata san lokacin da ta fashe da dariya ba,  shima dariyan yayi yace “there, the smile is all i want purehearty” bata san lokacin  da ta sake mai Murmushin da yake matukar so ba,  sun dan jima suna exchanging looks,  kafin suka ji muryan Ziyada  da Zaineema nacewa “Excuse us” firgigit sukayi suna kallon kofan kitchen din,  Ziyada tace “YaMaji are we interrupting something?” Kasa magana sukayi sai blushing da suke, Zaineema  tace “Ziyada wai are these two inlove?” Ziyada zatayi  magana Abdulmajeed  yace “Shuttup Zuzu, ni tsaranku ne? ” suka fashe da daria,  Najwa ina zata sa kanta don kunya,  Zaineema tace “zo nan Najwa” Najwa kanta a k’asa zata  karasa gun Zaineema  Abdulmajeed  ya sha gabanta yace “ba inda zaki PureHeart,  ku kuma wallahi  zanci  mutuncinku” sukayi daria duka,  Ziyada tace “wai aiki kakeyi?” yace “No ku koma daki” Zaineema tace “wallahi aiki kakeyi,  ya kamata a gyara gidan ma” Abdulmajeed  yace “ku wuce daki zan gyara” Ziyada tace “Sam sai dai muyi a tare” da kyar ya yarda ya raba musu aiki.

 

Sanitation sukayi na Gidan gabaki daya duk wasu yana na saman ceiling sai da suka cire, wurin 10 sun  gama komai,  Zuwa yayi wanka,  ya fita yayi changing dollar din,  dubu 35,900 ne,  ya shiga kasuwa ya musu siyayya,  kama da  richo,  kanazir,  kayan shayi, kwalin indomie,  bobo da biscuit na yan makaranta,  sabulun wanka da na wanki,  da dai kayan amfani daidai kudinsu,  ya biya ya siyo lantern, ya biya ya bada kudin nepa dubu sha daya,  ya siyo bulb na wuta,  kudin da ya rage dai dubu bakwai,  ya dawo gida a kan adaidaita sahu da kaya nikiniki, kamar wanda ya dawo daga Dubai haka suka tareshi,  suka ta yashe baki abun zattausayi,  haka suka jera komai inda ya kamata,  nan suka ga kyan Gidan,  Mumny ta dage ta zira lagwani a jikin risho,  aka dura kanazir a risho din,  aka daura Abincin Rana.

****

 

Be san meyasa ba ya shiga damuwa,  kiran wayarta yayi a karo na kusan ba adadi,  wayarta kashe,  rabon da yayi waya da ita  tun randa tace mishi zasu koma Gidansu, ba wai ya damu bane,  yace ma zuciyarshi,  kawai ina so in ga ta yanda zan k’untata mata, ban damu da ita ba,  ban damu da komanta ba,  all i want is revenge, ya buga tsaki,  ya dauki keys din motarshi ya fita daga dakin,  Guest house din Baba Ado ya nufa, straight ahead Gidan ya shiga, kasancewar an sanshi ba wanda ya tambayeshi ko an san da zuwanshi ,  da Sallama ya shiga Parlorn,  Baba Ado na zaune kan wat kujera ta alfarma yana karanta wata Jarida,  Zaid ya taka cikin takun kasaita har gabanshi ya durkusa ya shafi k’afanshi,  shi kuma baba Ado ya dafa kanshi (haka ne gaisuwan yan Mali yake) Jaridar hannunshi ya ajiye,  ya mikar da Zaid suna kallon juna,  kafin nan ya rungumeshi.

 

Kafin kace komai tuni an cika ma Zaid gaba da kayan motsa baki, sai da ya bata lokaci kafin ya dauka grapes daya ya fara tauna a kasaitance,  kasancewar  Baba Ado ya san Zaid ciki da bai,  ya san halinshi,  ya san yanda zai tafiyar dashi, yace mai “Ka sanar dasu zamu zo yau din?” kamar ba zai amsa ba chan yace “Wayarta a kashe yake” Baba Ado ya dago ya kalleshi,  yace “kenan basu san zamuzo ba?” dan gajeren tsaki yayi yace “Wayarta kashe yake” Baba Ado yayi jim, kafin yace “to ya zaayi kenan? Na kira abokan babanka biyu sunce mu hadu karfe hudu,  Alhaji  Hamisu ma musamman ya hau jirgi daga Porthacourt yazo Kano” Zaid yace “Zakuje ai” “ba su san da zuwanmu ba din?” Zaid yace “ai ba wani abu bane,  suna Gida” Baba Ado yace  “amma dai be kamata  ba Zaid” da sauri Zaid yace “Please Baba Ado,  banson a samu matsala, banson Auren ya wuce Friday din nan, ka taimakeni” Baba Ado ya murmusa,  a zatonshi Zaid na kaunar yarinyar nr da har ba zai iya kara daukan wasu lokuttan ba tare da ya aureta ba, kuma dai abun farincikimsu ne tunda Zaid da bakinsa yace yana son auren,  gwara su mishi kafin ya chanza raayi.  Baba Ado ya ja numfashi yace “Zamuje Gidan Bayan Laasar”.

 

Bayan Laasar.

 

Abdulmajeed  da Daddy suna hanyan dawowa Gida daga Masallaci,  daga nesa suka ga Motoci kusan  guda Biyar a daidai kofar Gidan Hajjo,  Daddy ya kalli Abdulmajeed, yace “baki mukayi?” Abdulmajeed yace “da Alama” daga nesa Daddy ya hango Baba Ado,  kasancewar Babban mutum Sananne yace “Abdulmajeed  kamar Alhaji Ado Mali na GG” Abdulmajeed da mamaki yace “shine Daddy,  ko Lafia?” Daddy  yace “kace me neman Ziyada dan Marigayi Gatan Marayu ne ko?” Abdulmajeed  yace “Eh,  Zaid sadam sunanshi” Daddy yace “to ba abun mamaki bane, kowa yasan Alhaji Sadam da Alhaji Ado Aminanna juna ne,  kila neman auren Ziyada sukazo” Abdulmajeed ya jinjina kai suka karasa gunsu,   da Sallama, ta cikin Mota Zaid ke kallonsu cike da tsana,  ji yake kamar ya fita ya makure su,  a karo na biyu tun bayan da sukazo mai taaziyar Babanshi zasu hadu gaba da gaba,  yana jin Daddy da daya daga cikin Abokin Baba Ado suna gaisawa,  Abdulmajeed ya gaishesu cikin girmamawa,  Baba Ado yace “Alhaji Abba Abu dama wurinka mukazo” Daddy  jiki na rawa yace “mu shiga daga ciki”.

 

Abdulmajeed  yayi saurin  shiga Gida yace “ku koma daki, anyi baki” Mairo tace “su wanene?” Abdulmajeed  yayi  Murmushi  yace “masu neman  auren Zuzu ne” dam gaban Ziyada ya fadi,  Mummy ta yashe hakori ta na gyara zani tana tura yaran su fita daga palo tana cewa “Gatan Marayun ne?” Abdulmajeed  yace “magabatanshi ne” daki suka koma,  Ziyada ta rasa me takeji,  dadi ne?  ko tsoro? Mummy tace “Diyata kwantar da hankalinki mu mun dangwalo arziki” shiru  suka mata kowa da tunanin da yake.

 

Zaune suka a cikin Parlo,  ba abunda kakeji sai gaurayen daddan k’amshin turarensu, su 4 ne zaune,  sai Daddy na biyar,  Abdulmajeed  ya fita don siyo musu Lemu, nan suka sake sabon gaisuwa,  Baba Ado ya fara magana kamar haka ;

“Da farko muna neman afuwan zuwa ba tare da saninku ba,  ko kuma ince izininku ba” Daddy yace “haba bakomai wallahi” Baba Ado ya cigaba da cewa “Alhaji Abba Abu, sunana Alhaji Ado na Mali, Amintakarmu da Marigayi Alhaji  Sadam Audullahi ya sa muke jin kanmu kamar yanuwana jini, Yaronshi Zaid wanda ake ma lakabi da gatan Marayu na biyu na neman diyar gurinka Ziyada,  be da wanda zai shige mai gaba kamar mu,  duk nan da kake ganin mu ba wanda be ci Albarkacin Gatan Marayu ba,  ya mana abunda ba zamu taba mantawa ba, ba wannan ba, Yaronmu ya gano fure a Gidanka,  kuma yana so a bashi damar tsinka” sukayi dariya gabaki daya.

 

Daddy ya muskuta yace “To Alhamdulilah,  nayi farinciki matuk’a da wannan zance,  babban abun farinciki  shine kasancewar dan Baban Gida kamar dan Gidan Gatan Marayu na neman diyata da aure,  ba wanda ba zaiso hada iri da Alhaji Sadam Audu ba,  kowa ya sanshi datijjon kirki ne,  ban taba ganinshi ba,  amma abubuwan Alherin da yayi na isko mu, kuma ko bayan rasuwarshi danshi ya cigaba daga inda ya tsaya,  Alhaji Sadam Audu is a legend,  he is Dead,  but his legacy still lives, so babban abun Alfahari na be wuce ganin diyata ta auri Yaron Baban Mutum kamar Marigayi Alhaji Sadam ba,  amma wani hanzari ba gudu ba,  duk yanda nake son wannan abu ya kasance,  ba zai wuce da Amincewar yarinya ba,  in bata amince dashi ba,  to ba yanda zaayi sai dai ayi hakuri,  don banda niyyar aura ma yarana wanda ba sa so” Alhaji Ado yaji dadin Dattakon Alhaji Abba,  yace “haka ne,  yi ma yara auren Dole ba fa’ida,  amma ina da tabbacin suna son juna, shi dan gurinmu ya tabbatar mana da hakan,  yana waje barin kirashi ya sake tabbatar mana da hakan” ya zaro wayarshi ya latsa ma Zaid kira,  ringing  daya Zaid ya dauka “Eh Hello, ka shigo ciki” be tsaya jiran abunda Zaid zaice ba ya kashe wayar.

 

Zaid yayi jim yana kallan wayar,  takaicin Baba Ado yaji,  don me zai kirashi? Me zaije ya musu? ” Idi yace “Oga ka shiga kawai,  Allah ya soka Baba Ado ya baka Manyan kaya kasa, lafiya lau ne, ka shiga kawai,  remember  gaban sirikin ka kake,  banda kallonsu cikin ido,  kuma a kasa zaka zauna” tsaki Zaid ya buga da karfi ya bude kofa ya ma su Amrstrong banging da karfi,  suko suka fashe da daria,  cikin Gidan yayi,  gidan ba bakonshi bane, takalmominsu ya gani daga waje,  yayi Sallam ya shiga suka amsa mai,  a k’asa ya zauna kamar yanda Idi yace, murya cikiciki ya gaida Daddy,  Daddy da faraarsa ya amsa.

 

Baba Ado yace “MashaAllah,  Alhaji Abba ga Yaronmu,  durfane gabanka, yazo neman auren diyarka,  be zo a matsayin Gatan Marayu na biyu ba, yazo ne a matsayin  Zaid Sadam me son diyarka Ziyada” kan Zaid a kasa,  yanda yake magana sai yake jin wani nauyi na sauka a kansa,  anya zai iya kuddirinsa? Kafin Daddy ya bada amsa Abdulmajeed ya shigo dauke da Lemuka su coke fanta mirinda a talauce (waya ce maka suna shan irin wanan? lol).

 

Alhaji  Abba yace “ga Baban dana,  yayan Ziyada  ne,  sunanshi Abdulmajeed” Abdulmajeed  ya dirr lemukan a k’asa ya sake gaidasu,  suka amsa da faraa,  Daddy yace “AbdulMajeed,  je ka kira min Mummynku da Ziyada,  inshort ka kira min kowa da kowa har Mama” Abdulmajeed  ya mike a ladabce ya fita,  a dakin Hajjo ya iskesu duka,  yace “Mummy kuzo Daddy na kira” jiki na rawa Mummy ta zaro  mayafin da bata san ko na waye ba zata fita Abdulmajeed  ya tareta,  yace “tsaya Mummy,  gabaki daya zamuje,  Zaineema ku muje,  Hajjo har ku” duk  suka tashi  suna neman mayafin sakawa banda Ziyada da ta takure wuri daya,  Abdulmajeed  ya kallota ya bude drawer ya ciro wani k’aton gyale ya rufe mata jiki yace “come on zuzu, ba zaki bar surikanki suyi ta jiranki ba ko?” ta mike  jiki ba kwari,  Abdulmajeed ya ja hannunta suka fita, duk suka rufa musu baya banda Najwa da ta ke  gyara inda su Muhsin suka 6ata.

 

Sallama sukayi suka shiga,  suka amsa  da faraarsu,  duk suka samu wuri suka zauna, kan Ziyada a k’asa,  Baba Ado ya nuna ta da yatsa yace “ga Amaryanmu nan” ta sake sadda kanta k’asa,  Daddy yace “haka ne, nan Iyalai na ne dukkansu,  Wannan itace Mahaifiyata,  wannan kuma Mai dakina” ya nuna Mairo da hannu,  ita ko sai faraa take watsa musu”  wannan kamar yanda na gaya muku shine babban da na AbdulMajeed,  sai me bi mishi Zaineema,  sannan Ziyada,  Zinatu ke bi mata sai auta Muhsin” Alhaji Ado yace “MashaAllah,  Allah ya ja kwanan zuria,  matuka kun burgeni,  ka nuna mana dattako da karamci,

Hak’ika hankalin mu zai kwanta ganin gidan da yaronmu ya dauko mata” Daddy  yace “haka ne,  amma bari mu ji ta bakinsu ko?”.

 

Alhaji Bello yace “Zaid,  shin wannan itace ka zaba ta zame maka abokiyar rayuwa har karshen rayuwarka?” be san dalilin da yasashi faduwar gaba ba,  yayi shiru gabanshi  na dukan chalugude,  baba Ado yace “Zaid?” da sauri yace “Eh itace”. Daddy  ya juyo kan Ziyada yace “Ziyada kin amince in bada aurenki ga Zaid? Kar kiji nauyi ko wani abu in ba kya so,  sai in basu hakuri,  ki fada min ranki,  farincikin ku ya fiye min komai” Ziyada ta sadda kanta kasa, Daddy yayi maganan duniya amma tayi shiru ba tare da ta tanka ba,  yace “ko ba kya so?” nan ma shiru tayi,  Alhaji Bello yace “Ziyada magana zakiyi kinji?  Ba zamu gane me ke cikin ranki ba in ba magana ko alama kika mana ba, kina son sa,  ko ba kya sonsa?” shiru tayi har yanzu ba tace  komai ba,  Mummy ji take kamar  ta gwala kan Ziyada da bango, Alhaji Sani yace “kun san dai ma’anar shirun budurwar kirki,  yana nufin ta amince kenan” Alhaji Kabir yace “aa kar ayi saurin yanke hukunci,  duk tambayar da aka mata shiru tayi,  ya kamata musan amsarta,  muna iya bata lokaci tayi tunanita gaya mana sirrin da ke ranta”.

 

Abdulmajeed  yace “Erhm,  in zan dan iya magana da ita,  zan samo mana amsar da takasa fada” Daddy yace “Eh Abdulmajeed  kuje kuyi magana” hannunta yaja suka fita daga Parlorn, Daddy ya musu alamu da su bisu, su Mummy suka tashi suka tafi,  be san meyasa yaji gabanshi na faduwa ba,  what if tace bata sonsa? Plan dinshi ya zube kenan?  Plan kadai?  Cewar zuciyarshi,  da sauri yace “eh,  plan dina ne kawai,  be san mesa ba amma sai ya tsinci kanshi da yin adduan Allah  ya sa ta amince.

 

“Zuzu lookat me, talk to me,  kina sonshi? ” cewar Abdulmajeed,  da sauri ta kallo yayanta tace “YaMaji,  a cikin halin da muke ciki,  maganar aurena shine karshen abunda ya kamata ayi,  muna cikin halin ha’ulai,  Ya Maji–” ya katseta da cewa “shhhh,  ki amsa ni,  kina sonshi?” rungumeshi tayi da sauri tana gyada kanta a jikinshi,  yayi daria yace “abunda nake sonji kenan” ya juya ya tafi yayi Parlor,  ya rada ma Daddynsu a kunne,  Daddy  yace “to Alhamdulilah,  yarinya  ta Amince” duk sukayi hamdala suna faraa,  Zaid ya sauke numfashi a hankali yana gode ma Allah.

 

Alhaji  Ado yace “Alhaji Abba ka bamu?” Daddy yayi daria yace “na baku” sukayi daria sukace “mun karba kuma mungode,  muna so ayi Auren Ran Juma’a me zuwa in Allah ya kaimu” Daddy suka kalli juna da AbdulMajeed,  Daddy yace “Alhaji,  da wuri haka? Ni ina zaton sai daga baya zaa sa bikin kuma zaa sa a kalla wata 10” Alhaji  Ado ya zaro ido yace “Wata Goma dai? Me zaa jira Alhaji tunda yara na san junansu,  ka bamu kuma mun karba? Me zaa jira?” Daddy yace “haka ne,  amma akwai wata yar matsala da ta auku,  ina neman Alfarma a bamu lokaci mu maganceta kafin ayi ma maganar daurin auren yaran” Alhaji  Ado yace “nasan kana so kama diyarka kayan daki,  nasan kana so nyna bajintarka a matsayinka na Baban yarinya,  nasan kana so kamata kayan daki kamar yanda ko wani uba yakr ma diyarsa,  amma Ba fin karfi,  ba nuna isa ba, ba ma bukatar komai,  Yarinya muke so kuma kun bamu,  ita ral muke so a daura aure Yaro ya dauki matarshi ya kaita Gidanta” Daddy zaiyi magana Alhaji Ado ya katseshi da cewa” Gatan Marayu na farko ya kan daura ma Yara 100 aure a rana wanda be sani ba fa,  ya musu lefe ya musu kayan daki, to me kake tsammamin zai ma Yaronshi in ya tashi aure? Ka na tunanin zai barsu su siya koda kara ne?” Daddy yayi jim kafin ya kalli Abdulmajeed  neman shawara,  da ido ya gyada mai kai Alamun ya amince,  Daddy yace “haka ne, toh Allah ya saka da Alheri,  Allah ya kaimu Jumaa din” Alhaji Ado yace “Ameen,  ba shishigi ba,  amma  wata irin matsala ce da kuke son magancewa?” Daddy yace “ba wata damuwa bace,  kar ku damu” Alhaji Ado yace “haba Alhaji, tunda ka bamu diya ai an zama daya, ka gaya mana ko menene”.

 

Daddy ya yi shiru kafin yace “Akwai Alhaji Nakowa da muka samu sabani dashi— tiryan tiryan ya kwashe labarinsu da Alhaji Nakowa zuwa yau” Allahu Akbar, Zaid dai duk wani guiltiness ya kamashi,  be taba jin tausayin mutanen nan ba ko kadan amma yau da Daddy ke bada labarin sai yaji wani bangare na zuciyarshi na tausaya musu,  da sauri gudan zuciarshi ke mai gargadi da kar ka sake kaji tausayin Azzaluman nan da suka maka katangar karfe da mahaifanka,  da sauri ya yakice tausan da ke ranshi,  be ankara ba sai ji yayi Alhaji Ado na cewa “Alhaji Abba,  tunda yanzu an zama daya zan bada Miliyan 30 din ku biyasu” Daddy yace “gaskia ba zan amince ba,  abun ai sai yayi yawa,  gaskia ba zan yarda ba,  abin da kukayi ma mun gode  Allah bada Lada” Alhaji Ado yace “Haba Alhaji Abba,  ashe baka yarda an zama dayan ba,  to in ba mu ma Zaid  ba wa za mu mawa,  na gaya maka duk nan ba wanda be ci albarkacin Gatan  Marayu ba,  duk abunda muka mishi ko danshi bamu fadi ba wallahi” Zaid kamar ya makure Baba Ado,  ya sanshi da kafiya,  biya musu bashin nan na nufin basu da wata damuwa,  meyasa yake da shishigi ne?  Tsaki yake ta bugawa a ranshi yana cewa shifa baba adon nan da matsala yake,  shi kuwa Daddy ya san cewa in suka rasa tallafin nan ba wanda zai sake tallafa musu, this is the only chance they have,  amma be bi san zucianshu ba yace “duk da haka , kuyi hakuri we are not your responsibility,  in sunyi aure duk abund zai mata ba me hanashi matarshi ce”.

 

Ganin ba zai amince ba dabara tazo ma Baba Ado,  yace “to in ranta maka mana? Da bashi a kan mutane irin Alhaji Nakowa gwara gida ko? Zan ranta maka,  in ka samu sai ka biyani” Daddy yace “to ina iya amince ma rance,  amma gaskia  ba kyauta ba,  kuma 25million ne,  don mun basu 5, zan dinga biyanka a hankali a hankali” Zaid  kamar yayi Ihu  don haushi,  yasan siyasa Alhaji Ado ya mai,  ya san ba zai taba karban kudin ba,  shikenan ya yanke musu wahala,  kamar yayi kuka,  nan dai suka cigaba da tataunawansu cike da mutunta juna,  Alhaji Ado yace “gobe zaayi banking a biya Alhaji Nakowa kudinshi, Alhaji Bello yace  bayan daurin Aure zaayi gagarumin walima” Alhaji Sani ya ciro rafar 1000 guda uku yace “ga Sadakin Amarya” duk abubuwan da akeyi bakinciki ya turnike Zaid,  shifa neman aure yace su zo su mishi ba san iyawa ba,  be san lokacin da ya mike ya fita ya bar parlorn ba,  ba su damu da shi ba don ba su ma lura da ya  fita ba,  ba jimawa suka tafi.

 

A GURGUJE

Mairo harda takawa tayi don Dadi da taji sun dangwalo Arziki,  har ce ma Ziyada take ta zo ta hau bayanta ta goyata ta share mata hawaye,  a zuciyarta take hasko yanda rayuwa zata canza mata,  zata fito gari ta taka duk  wanda ya tabata,  zata gurza ma makiyanta rashin mutunci,  Ziyada kam farinciki damke a ranta zata auri farincikin ranta, wai ita zata zama Mrs Zaid Sadam in two days,  she cant wait.  Bata so yin wani gayya ba,  amma Mummy tace sai tayi gayan friends dinta duk da ba wai yawa ne dasu ba,  a cewar Mummy ya zaayi ta auri Mutum kamar Zaid amma ba wanda ya sani? Dole ta gayyato kawayenta,  haka dai ta hada BC ta tura ma Friends dinta. Itama Mummy aka wuce gidan tsohuwar kawarta hajia Aliya tana bude mata hanci ita zata zama sirikar Zaid Sadam.

Alhaji  Nakowa yayi mamakin ganin Cheque da yayi daga account  din Ado Mali wai da sunan biya ma Alhaji Abba Bashi wanda daga Kotu aka turo mishi   ba haka yaso ba,  so yayi ya kuntata ma su Hajia Mairo,  amma ya ya iya?  Karawa da Alhaji Ado Mali kamar karawar kifi ne da mage.

 

JUMA’A

 

Bayan Sallahn Juma’ah ne a babban Masallacin Jumaa na Central Mosque dubbanin Jamaa suka shaida auren Zaid Sadam Audu da Amaryarsa Ziyada  Abba Abu a bisa sadaki Naira dubu dari uku.

 

Wasa farin Girki.

 

•••••••

 

Gyara: Dear Bibilicious freaking fans,  akwai wani gyara da wata baiwar Allah ta min, attimes ina using Abdulmajeed wasu lokuta kuma Majeed, Malamai suna waazi akan Kiran sunayen Allah hakan Nan batare da sa Abdul din ba, mu kuma mu kan yanke ko don gayu ko don gajeratawa,  amma hakan baban kuskure ne, to mu dinga kokari muna cikita sunan AbdulMajeed, from now henceforth zamu dinga karasa sunan,  in aka ga akasin haka to kuskure ne da kuma sabo,  ina fatab zamu gyara Nagode. .

 

Yekpa Anyi aure fa,  akwai Walima Party anjima,  you are all invited.

 

Akwai gwarama fa,  this is the begining of an end,  stay tuned,  yanda nake kokarin typing  haka,  kuma dont Forget to Vote and Comment line by line.

 

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa.

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣1⃣

 

Kafin a daura auren ji yayi kamar yaje ya hana wannan daurin auren,  ji  yayi kamar ya harbe Baba  Ado da yafi  kowa Zak’ewa a gurin, da aka daura Auren kuwa gabanshi ya tsananta faduwa,  wai yau shine aka daura ma aure? Zai rantse yaji girmana da ke shiga kanshi,  yaji kulawa da nauyin Ziyada a kanshi,  to wayace muku auren  zaiyi lasting? Wulakantata kawai zanyi na saketa,

Ya  san Central Mosque ne na garin Kano,  dole ta cika balle sallahr jumaa ce,  amma ya tabbata rabi da kwatan mutanen sunzo ne domin daurin auren gatan marayu kuma daga gari daban daban, besan abun ya baza duniya ba sai da ya ga an fito ana tayashi murna,  duk wasu abokan babanshi na nesa da na kusa zai rantse daidayyaku ne be gani ba.  Kowa burinshi ya gaisa da Zaid ya mai fatan Alheri,  a wannan fanin ne yayi nadamar sanar da Baba Ado tun farko,  dama zuwa yayi ya hayo Magabantan karya har ya aureta ya sakota Baba Ado be sani ba balle yayi mai tereren jamaa har ana chunkuson nan kamar hawan sallah.

 

Abdulmajeed  kam shima ba laifi Abokanshi na Kano sun hallarta daurin auren, har Khaleed din Zaineema yazo Kano Aliyu ya jawoshi suka zo bikin,  gaisawa sukayi kamar ba abunda ya faru tsakaninsu,Khaleed nason tambayarshi Zaineema amma besamu dama ba,  sai da suka dunguma sukaje wurin wani Reception da Baba Ado ya hada Khaleed ya samu ya kebe da AbdulMajeed  ya tambayeshi Zaineema,  Abdulmajeed  ya murmusa yace “tana nan lafiya  lau” Khaleed yace “Abdul Abba kasan inason Zaineema,  ina jin zan Maidota Gidana”Abdulmajeed  ya murmusa  yace “Kana so ka maidota ne saboda kana sonta? Ko kuma ka bar zarginta ka yarda shes innocent shiyasa  zaka maidota?” Khaleed  yayi jim yace “Zan maidata saboda ina sonta” Abdulmajeed yace “gaskia bazan yarda ba,  duk randa ka bar zarginta ka yarda cewa she was innocent ka zo ka tafi da ita” da sauri Khaleed yace “i saw someone laid on our matrimonial bed?(wani na gani kwance kan gadon aurenmu)” Abdulmajeed  yace “did you catch them lying together? Pestle and Motar? Did you?(ka gansu kwance tare? Turmi da tabarya?)” ya girgiza kai zai yi magana Abdulmajeed  yace “Khaleed,  muna  Walimar Aurene,  nan ba wurin maganar nan bane,  kaidai kawai kaje,  sai lokacin da ka yarda da ita”. Ya wuce ya cigaba da harkar gabanshi,  Alhaji Abba ma sai hulda yake da mutanen shi,  Ziyada fa?.

 

Gidan Aunty Aynarh,  shine inda Ziyada take da kawayenta na Northwest University, suna ta kai kawo,  dan luncheon Aunty Aynarh ta hada musu a parlornta ita da kawayenta da basu wuce 10 ba sai Najwa da Zaineema ,  musamman Aunty Aynarh ta dawo daga Abuja don Bikin diyar Masoyinta.  Ziyada na chan daki ita kadai,  Wayarta a hannunta take jiran  shigowar sak’on Angonta,  ta sha jin labarin ko a litattafan soyayya ko a film,  har a reality cewa ana daura aure Angwaye ke kiran  amarensu ko su yi kasu sakkon text su sanardasu babban Albishir na cewa an daura aure, wasu kanyi amfani da “Alhamdulilah an daura aure,  kin zamani na zama ke” ko kuma “Ke tawace nikadai yanzu” banda Angonta,  ita  shiru kakeji,  zuciyarta tace mata “ki mishi uzuri fa,  Babban mutum ne sananne,  kila mutane ba su barshi ba,  yana chan yana fama da mutane ina yaga lokacin neman ki?” ta gyada kai hakane,  ta mishi uzurin yana fama da mutane ne.

 

Gab da Maghrib

 

Hajia Taatuh itace Amaryar Baba Ado ta shigo Gidan Hajjo, shigarta ya nuna ma Hajia Mairo babbar mata ce,  nan da nan aka tarbeta hannu bibbiyu, ta buk’aci ganin Amarya da kawayenta, Mairo jiki na rawa ta kira Abdulmajeed  kan cewa yazo ya jagorance su Gidan Hajia Aynarh, ba jimawa sai gashi yazo, Hajia Taatuh ta zaro IV guda 20 ta ba Uwar Amarya tace akwai grande event din da zaayi wanda ita da Mijinta suka hada ma Amarya da Ango,  Mairo dadi kamar s shideta,  irin bikin da take burin ta ma yaransu ne  barin ma da ta ga Venue din a  Afficent

Bristol palace zaayi, ta dinga mata Godia ta rakasu har bakin k’ofa,  kafin ta dawo Gida ta fara shirin wanda zata gayyata,  su Her Excellency me hura mata hanci,  ta hana Amjad auren Ziyada gashi Allah ya sa ta auri wanda ya ninkasu kudi linkin ba linkin.

 

Ashe Hajia Taatuh ba ita kadai bace,  tare take da Maaikatan Meenerh Parrot’s makeup &Salon su kusan 10, don kwalliyar Amarya da k’awayenta,  Abdulmajeed ya rakata har Gidan Aunty Aynarh ya mata iso, Aunty Aynarh ta taresu hannu Bibbiyu,  aka gaisa cikin mutuntawa,  nan Hajiya Taatuh tace  ma Aunty Aynarh “ina  Amaryar? Gwara ai a shiryata kinsan su Mazan nan ba sa son jira” Aunty  Ainarh  tayi daria tace “Bismillah,  tana nan dakin” Hajia Taatuh ta kalli sauran staffs din meenaparrot saloon tace “Ku kuma ku gyara bridemaids dinnan,  a nema ma kowa  size din gown din da zaiyi fitting dinsu” suka amsa da “Yes Ma”.

 

Daya daga cikin staffs din tace “DonAllah ku bamu hadin kai muyi aikinmu,  in akwai masu Sallah kuyi Alwala yanzu tun, kuzo a fara makeup din” wata daga cikin friends  din Ziyada me suna Nusaiba tace “nawa kuke makeup din?” tace “karki damu thanks to Hajia Taatuh,  its free,  mu zamu miki makeup,  har kayan da zaki sa kije Walima din mu zamu baki,  kuma bawai in an gama ba zaki dawo mana dashi,  no its yours,  dukkan ku nan bridemaids akwai kayan da zaku sa Anko ne” nan suka fara faraa,  suka shiga toilet masu wanke fuska nayi,  masu alwala nayi,  kasancewar Najwa na fashin Sallah yasa bata tashi ba, Matar tace “bari mu fara da ke” kafin Najwa tace wani abu,  har an aje makeup kit gabanta,  bata da wani choice da ya wuce  zama aka fara yanyara mata Makeup,  casual makeup dai haka,  sauran ma suka zo aka cigaba da yi musu, harta Zaineema ba a barta a baya ba, daga nan wata Official  ta bude wani dan Akwati, Ankon wasu riguna suka gani Peach and push pink and white gown,  tace “Please kowa ta dau daya” duk suka kalli juna kafin beaulinbilmoh ta sa hannu ta dauka,  sauran suka daddauka har Najwa da Zaineema, da yake Meela karamin jiki gareta tace “ni ya zaayi wanna riga ta min,  ai ta min yawa” matar ta murmusa tace “kar ki damu Maxi gown ce, da me karamin jiki da me babban jiki duk zai musu daidai,  akwai abun daurewa da zaiyi fitting dinki,  da taimakon officials dinnan yan matan Amarya  suka fito chas abunsu, nan suka cigaba da daukan kansu hotuna don sunyi kyau sosai.

 

Fadin kyaun da Ziyada tayi bata lokaci ne,  duk wani kyaun da aka san amarya nayi ranar bikinta to Ziyada tayi irinshi har ta gaji, makeup  din da aka mata ya dace da ovalshaped fuskarta, sanye take da peach fitted gown da maroon Ashoke wanda yaji dauri a kanta,  wuyanta sanye da manyan Marjani wanda  daga kallo kasan sunji kudi, sai black net wanda tayi mayafi dashi,  kafanta sanye yake da  maroon highhills, hannunta kuwa rike yake da maroon clutch(purse).  Sosai Ziyada tayi kyau kuma ta fito a Amaryarta,  Aunty Aynarh ta fito daga dakinta itama ba a barta a baya ba sai da ta sa aka jagireta (lols) itama harda ita a makeup din,  dakin da ake shirya Ziyada ta shiga,  nan take ta shiga nanata “MashaAllah Ziyadatu,  kinyi kyau sosai” Murmushi  kawai takeyi,  nan tayi ta daukanta hoto,  hannunta Hajia Taatuh  taja suka sauka k’asa inda bridemaids suke,  suna ganin Ziyada ai sai suka sa ihu don haduwar da tayi,  itama idanuwanta ta dago ta kallesu,  ta bisu da Murmushi  don su ma sun mata kyau, nan fa aka hadu akayi ta selfie,  Najwa ta ma Amarya Hoto ta tura ma Maama ta whatsapp,   Maama ta ma Ziyada Adduan zaman lafiya a gidan Mijinta.

 

Waya Hajia Taatuh tayi inda ta bada umurnin azo a kwashe kawayen Amarya,  ta kuma kira Baba Ado ta sanar dashi ya kira Zaid yazo ya dau Amaryarshi,  cikin mintuna da ba su wuce  20 ba,  Motoci suka zo a ka kwashi Kawayen Amarya har Zaineema da Najwa don duk sun saje cikin kawayen Amarya,  direct Afficient bristol Palace suka  nufa,  aka bar daga Amarya sai Hajia Taatuh sai Aunty Aynar da maikatan ta a Gidan,suna faman jiran zuwan Zaid.

 

“In har Zan saka abu kak’i Zaid,  to haka zalika Alhaji Sadam zai saka abu kak’i” Zaid ya dago rinannun idanuwanshi ya watsa ma Baba Ado wani kallo, ya naji kamar ya harbe Alhaji Ado ya huta,  yayi babban Nadaman sako Alhaji Ado cikin lamarin auren nan, don bala’i sai da ya ganoshi a hotel din ds ya killace kanshi dom be son takura,  ya biyoshi hotel din,  gashi wai yanzu yana takura mai sai yaje wani Walima kuma wai shi zai  dauko Amaryarsa ya kaita,  har don yaki Baba Ado zaice da babanshi yake?” Baba Ado be damu da mugun kallon da Zaid ke watsa mai ba yace “Eh,  indai ka watsa min kasa a ido to kamar ka watsa ma gatan marayu ne,  don yanzu nine a matsayinshi,  in kuma zaka  watsa mai k’asa a ido to kar kayi abunda nake so” ina ma zai iya ihu ya huce takaicin tsohon nan, tsaki yayi ya finciki jakar da aka aje mai na kayan da zai sa ya shige toilet din wakeken dakin Hotel din, tsaki ya buga,  shifa ya gaji da sa wannan Babbar rigar,  dazu da daurin aure shi aka tilasta mai ya saka yanzu ma haka,  gwara ma na yanzu be da nauyi,  bakin yadi ne me aiki maroon,  ya ciro hula k’ube ya sa, agogo da zoben cikin jakkan duka haka ya saka.   sosai Zaid yayi kyau,  ya fito daga toilet din har yanzu Baba Ado yana nan inda ya barshi,  a zuciyarshi  yace “jarababben tsoho,  ko baba ya rasa abokai ne oho” ba tare da yace mai kala ba ya fita,  Baba Ado ya murmusa  ya bi bayanshi,  Zaid din ne sai ana mai haka.

 

Benz din da ya ga an faka ya bude ya shiga baya,  na direban ya dan leka inda yaga Baba Ado tsaye,  Alhaji Ado ya gyada mai  kai, Driver ya ja motar ya fita daga farfajiyar hotel din, bakinciki dankare a zuciyar Zaid, text ya ma Armstrong “where the fu*k are you?(kana ina?)” a halin da yake ciki be iya magana don yana iya bude baki ya fashe da kuka,  Driver be tsaya ko ina ba sai Gidan Aunty Aynarh,  ba bata lokaci aka sanar da Hajia Taatuh, suka fitoda Amarya,  Driver  ya fito,  dayan bangaren baya ya bude  aka tura Ziyada ciki,  Hajia Taatuh bata damu tayi magana da Zaid ba don ta san be da kirki,  indai tashi ne zatayi abunda takeyi ai da batayi ba,  amma saboda Mijinta takeyi,  da marigayi Baban Zaid din,  ta rufe kofar motar ta kalli Steve Driver tace “we’ll be right behind you” Driver ya sara mata ya shiga mota ya fita daga gidan Hajia Aynarh.

 

Lumshe idanuwanta tayi a lokacin da ta shaki daddadan kamshin Zaid,  duk da bata kalleshi ba kanta a kasa yake, zata iya rantsewa yana walkiya don kyau,  taga kayan jikinshi baki ne, ta san yayi kyau har ya gaji,  dole ma yayi kyau, to ya ma ba zai yi kyau ba? Yana fari? Ta san yin kyanshi farilla ne,  Tana so ta dago kai ta kalleshi ko don taji dadi,  tana so ya sakar mata da murmushin da yake  mata,  amma ta kasa ta na jin nauyi,  wai tsaya ya mata magana? Ko sallamarta ya amsa? ai ya kamata suyi magana, shi ya a kamata ya mata magana, itace Amarya fa, a ranta tace “ka min magana my Forever, kace min komai,  koma meye ka cemin please” sun hau titi sosai be tanka ta ba,  bata san lokacin da tace “Ina wuni ba” duk yanda yaso ya amsata yak’i,  don yanzu haushin da yakeji ya danne daukar fansanshi.

 

Bata damu ba tayi shiru, kanta a kasa har sukazo wurin Event din,Aunty Aynarh ma sun iso, wuri yayi guri, taro yayi taro, kowa ya hallara, chan na  hango Alhaji Abba Abu da makaraban shi, Baba Ado ma haka,  daga wani bangaren kuma Mairo ce sai fadi takeyi don ta samu yan kwarako su hajia Aliya, chan na hango su Sholingaye da Mrs Splendid suna fadi don sun zo bikin yan gata,  hanayen su dankare da zoben zinari wuyansu kuwa Sark’an gwal ne,  yan ZBI members ma ba a bar su a baya ba, ga hafseen inda rai da cutielurv sai zara ido suke burinsu a fara chop,  wurin dai shak’e makil da duk wasu masoya na ADAY.

 

MC tagwaye ne MC,  bayan ya bada labari aka dan dara ya sanar da kowa a mik’e saboda shigowar Amarya da Ango,  duk aka mik’e a na jiran shigowar su,  kasancewar  baza ayi Bridal Train ba daga Amarya sai Ango zasu shigo.

Daga waje,  Armstrong ne yazo daidai saitun kunne Zaid yana mai rada kan “Please dont make any scene here,  i beg you” da kyar Zaid ya fito daga Mota, Aunty taatuh ta dan gano “something is not right,  sai kace ba auren soyayya ba?  Duk tasan shi Zaid din wani irin mutum ne,  amma abubuwan  da ta lura dashi na nufin wani abu” share wa tayi dai suka fito da Ziyada.

 

A jere suke tafia,  duk  da ba su rike hannye ba sunyi kyau sun bada maana matuka, shiga hall din sukayi,  sansanyar waka me taushi me ratsa zucian masoya ya karade hall din,  tafia suke a kasaitance,  shaharrarun masu hotuna kamar AhmedZol da GeorgeOkoro suka fara aikinsu,  Amarya da Ango suka cigaba da tafiya har mazauninsu suka zauna, abun yayi ban shaawa,  ba wanda ya take musu baya.

Tun shigowarsu Najwa ta kura ma Zaid ido,  bata san dalilin faduwar gabanta ba,  ta san fuskar nan, tabbas ta san fuskar nan a wani wuri to a ina?.

Daidai llll wani matakalan benen da zai sadasu da kujerun da aka tanada dominsu Ziyada tayi missing step daya,  tangartangar tayi zata fadi, be san lokacin da yayi saurin tarban ta ta baya ba tare da fadin “i got you” sai da ta gyara tsayuwarta kafin ya saketa,  daga baya kuma ranshi ya baci,  duk yaji haushin abun da yayi,  don me be barta ta sha kasa ba? Dama ya barta ta fadi” duk ya bi ya tsani  kanshi,  juyawa kawai zaiyi ya bar gurin nan,  ba zai iya ba.

 

Ji yayi kafanshi ya mai nauyi,kamar an sa magnet an rike mai kafa,  sai da Ziyada ta rigashi zama kafin ya karasa ya zauna kan kujerar alfarmar gefenta,  nan aka shiga yi musu  hotuna,  fuskar Zaid a daure, amma da yake shi mai kyau ne,  baa gane labarin dake kan fuskarshi.

Nan MC tagwaye ya cigaba da gudanar da program of events, a ka gayyaci Amarya da kawayenta suzo suyi rawa,  nan aka dinga yaba kyaun kawayen Amarya da suka fito cikin maxi gowns dinsu,  sun bada kala da suka sa Amarya a tsakiya, daga bisani aka kira Mothers din Amarya nan Mairo da kawayenta suka fito suna wani irin rawan bariki,  kamar ba uwar Amarya ba,  Abdulmajeed  ina ma k’asa ta bude  ya shiga don kunya,  rawan da Mairo keyi ba girma dai,  abun kunya,  sai da Hajia Aynarh ta rada mata a kunne  “kedai ba girma,  ji wannan rawan da kike gaban surukai,  wannan ba wayewa bace” Mairo kamar ta faska mata mari a ciki,  amma ganin zata jawo abun kunya  don public suke, kuma press na nan yasata yin Murmushi  sai abun yayi kama da suna shiri.

 

A ka kira Zaid da Ziyada Zsquare kamar yanda MC tagwaye  ya laka musu, ganin yanda yake shan kamshi ya sa batayi yunkurin tashi ba,  sai da ya tashi don karan kanshi, kafin itama ta tashi,  suka je sukayi tsaye a dancing floor, wak’an *Rihanna work* aka samu su, ba wanda ke rawa cikinsu, tsaye dai sukayi, wakan taushi sai tashi yakeyi, kamar an bashi umurni ya sa hannu cikin aljihu ya ciro bandir din naira dubu, kamar yanda yaga akayi dazun ya shiga zuba mata a jiki, ya karar ya sake ciro wani ya lika mata.  Wannan abun da yayi ya burge Mairo,  nan ta shiga hura hanci burinta ya gama cika,  ko ba komai Zaid ya siya mata mutunci gun  kawayenta. MC tagwaye yace “Mr Zaid,  lead your wife here,  its time to cut your Wedding cake” ya nuna musu Cake dake daga gefe, Zaid yaji takaici, amma  ji yake kamar ana ingizashi,  baya kasa yin gardama ga duk abunda akace yayi a hall dinnan,  anya mutanen nan sun barshi haka, duk yanda yakeso ya bar gurin ya kasa,  besan ya akayi ba amma ya tsinci kanshi da kamo hannunta ya ja su  suka nufa inda 3steppedcake dinsu yake,  da taimakon  mutane suka  yanka cake din,  aka ce su ciyar da juna,  nan fa daya,  babu yanda zaayi yaci abunda be san wa yayi shi ba,  ya yanka ya matsa kusa da ita daidai kunenta yace “i’m sorry i cant eat this,  bansan wa ya yi ba” ya sa mata cake din a baki,  a kunyace ta karba ta sa a baki, akace “Ziyada,  feed your husband” gabanta ya fadi,  kar fa ya bata kunya,  idonta ya kai kan wani Bottle water da cup, tunda baya cin abunda be san waya yishinba,  shes sure zai sha ruwan da ya saba sha,  a yangace ta karasa gun ta dauko Robar ruwan da Kofi,  a ranta tana adduar kar Zaid ya bouncer ta,  ta bude ta tsiyaya a cup,  a yangance ta kai cup din bakin shi, kamar bazai karba ba ya karba, ji kake raf raf tafin mutane,  sosai hakan ya bada maana, MC yace “Zaid yaje ya bar matarshi,  don zaa gayyata Family dinta dancing floor” kamar jira yake ya wuce yaje ya zauna,  kamar MC ya sani be ce abokan Ango suzo suyi rawa ba,  don be da Abokai,  kila sai dai su Baba Ado  su fito a madadin abokan lol.

 

Aliyu Abokin Abdulmajeed  ya ja AbdulMajeed  har inda su Zaineema suke da Najwa don da cewa yayi ba zaije ba, Abdulmajeed ya riko hannun Hajjo, Zaineema  ta rike hannun Zinatu da tun dazun ake rawa,  Zinatu ta kamo hannun Muhsin suka nufa Dancing floor inda Ziyada ke jiran zuwansu,  har sun kusa  isa gun Muhsin ya kwace hannunshi daga hannun Zinatu ya  ruga a guje inda Najwa ke zaune ya ja hannun Najwa,  Najwa na girgiza mai kai tana “please Muhsin let me go” yace “No,  you are family” bata da wani zabi da ya wuce ta bi bayanshi,  nan suka  rike hanaye suna zagaye Ziyada Aunty Aynarh ta zo ta musu liki,  Mairo ma haka, da kyar Daddy yayi joining dinsu, ganin Family dinta wuri daya cikin farinciki ya sata fashewa da kuka ta rungumo YaMajinta,  rungumeta yayi yana lallashi,  shhh kar ki bata kwalliyanki mana” Zinatu ma ta fashe da kuka,  duk tauri rai na Mairo sai da tayi hawaye,  da kyar aka lallashesu suka koma mazauninsu.

Sai next agenda wato REFRESHMENTS.

Ehen,  lokaci yayi na chop, babban makasudin zuwan yan ZBI da bibiliciouswattpadiansfans kenan,  sai da aka fara da Appetizer

 

 

Kafin aka gabatar daAbinci kala kusan 4, da chapman,  abundai sai wanda ya gani.

 

 

Walima dai yayi walima Zaid ya mike shi ya gaji,  ya ma yi kokari cewar Baba Ado,  ban yi zaton zai tsaya haka ba, tana ganin ya mike itama ta mike,  to ina zai tafi ya barta,  kafarshi kafarta, suka bar hall din,  Yan ZBI suka bukaci a sa musi wakar Ado Gwanja, nan suka shiga kwaso Shoki.

 

Yana tafia ya zaro wayarshi,  “Come get me home Arm?” Ziyada ta yi turus,  to ai ba zata bishi ba, murya a disashe tace “MyForever” chak ya tsaya,  tace “ina zaka?” be amsata ba yayi gaba abunshi turus ta tsaya “me  hakan ke nufi?  “Ya gaji ne,  kila kanshi ke ciwo” cewar wani sassan zuciyarta,  da sauri ta mai uzurin gajia ne,  zuciarta na gaya mata Zaid ya chanza,  amma bata so ta yarda,  tafi so ta mai uzuri,  Armstrong  yaji tausayinta ya karaso gunta,  yace da su Idi ya shiga ya gaya ma Aunty Taatuh Amarya na waje.  Hakan ko akayi,  Aunty Taatuh najin takaicin  yanda Zaid ya bar Amarya Waje,  Thank God  ma ba wanda ya lura da ita,  ta ma Aunty Aynarh Magana kan cewa tazo su maida Amarya Gida.  Haka dai aka watse aka bar Dj da yan ZBI members (lols).

 

WasheGari Asabar.

 

Misalin karfe 10 na safe,  Aunty Ainarh  ta sa Ziyada da Najwa da Zaineema a Mota ta kaisu Gidan  Hajjo,  gaban Daddynta da Mummynta aka direta don yayi mata fada,  karfe 12 Hajia Taatuh zata zo su tafi da Amarya.

Zuciyar Daddy na nauyi ya fara magana “Ziyadatu Diyata, Ziyada me kawaici da dauke ido,  na san ki da hankali,  na san ki da kawar da ido, ina rokon ki da kiyi hakuri a duk halin da zaki tsinci kanki,  hakuri shine abu na farko da zan tunasarceki dashi,  biyayya kuwa shinr ribar zaman aure,  na sanki da biyayya ki bi mijinki sau da k’afa,  nan Daddy ya shiga yi ma Ziyada nasiha me ratsa jiki,  Daddy na kuka,  Mumny na kuka Ziyada nayi, Daddy ya lallashe su ya tashi ya fita,  Abdulmajeed  ya shigo  ya rungumota yana lallashi,  kuka take kamar ranta zai fita, nan Hajjo ta dinga mata Nasiha,  Aunty Ainarh ta dora mata da nata wanda ta koya mata hanyar tafiyar da miji in yayi fushi,  har zuwan Hajia Taatuh da wasu kawayenta,  nan Mairo ta sa darun cewa da ita zaa kai Amarya, ana ta bata baki amma ina,

Daddy da ya ji kanshi nayin wani juyi yanzu yanzu ya fito rai a bace yace “Haba Maryam,  don rashin kawaici ke zaki kai diyarki dakin Miji?  Ke ba ki san kawaici ba ai? Duk kokarin da Hajia Aynar keyi ba ki gani ba?  To kije din in gani,  Mutuniyar Banza mutuniyar hofi,  Hajia Aynarh,  mun wakilta ki,  ki kai Ziyada dakin Mijinta” Kirrrrrrre kan Mummy yayi kara,  ina wuk’a ta chaka ma kanta don bakinciki,  ba ta da lokacin tunanin wulakancin da Alhaji  Abba ya mata a gaban mutane,  babban bakincikinta rabuwarta da diyarta,  da karfi  ta fashe da kuka ta yi daki da gudu ta fada kan Gado,  tana ji zata iya rabuwa da duk wani jin dadin rayuwa in har ba zaa rabata da yayanta ba,  Hajjon dai ce taje tana lallashinta tana tausasata.

 

Hajia Aynarh  ta ja Ziyada zuwa Farar Mota Kirar Benz din da Hajia Taatuh tazo dashi, bayan mota suka shiga Driver ya ja su suka dunguma syka nufa Gidan Amarya,  Ziyada kanta a k’asa tana kuka, an dade ana tafiya har sai da suka zo Janbulo  Hajia Aynarh  ta dinga bin hanyar da ido,  a ranta tace “Allah sarki,  ashe Anguwar su na da zata zauna” bata gama tunani ba sai da ta ga anyi parking daidai Gidan Alhaji Abba Abu na da,  kanta be gama daukan meke faruwa ba taji muryar Hajia Taatuh  na cewa “Hajia mun iso,  ga Gidan nan” Hajia Aynar ta zaro ido tace “ina?” Hajia Taatuh  ta sake gwada Gidan Alhaji Abba Abu,  Hajia Aynarh tayi jim,  zuciyarta tace “kar kiyi mamaki,  kila da ake neman me siya ya siya ba tare da ya san gidan sirrikanshi bane” Zuciyarta tace “kai,  ta ya zai siya Gidan Sirrikai ba tare da ya sani ba?  Ta ya hakan zai faru? Something is not right?” ganin tunani ba inda zai kaita tayi shiru, Hajia Aynarh ta radata mata tayi adduar shiga Gida,  ba tare da ta dago ba tayi,  suka shiga da ita har main palor,  Hajia Taatuh ta ja hannun Ziyada har dakin Mairo” Hajia Aynarh sai binta takeyi da ido,   meke faruwa ne, ta kasa gane komai,  da alamu kuma Hajia Taatuh bata san ko meke faruwa ba,  koma meye zataji daga bakin Alhaji Abba in ta koma Gida, Hajia Taatuh  tace “Hajia Aynar mu zagaa ki ga Gidan Amaryanko?” tace “haba ai naga kamar Maigidan na nan,  ma dawo mu ga Gidan Amarya da kyau daga baya” suka murmusa,  suka ma Ziyada Sallama suka fita,  tana jin fitarsu ta fashe da kuka cikin mayafinta.

 

Sai da taji kanta na neman fashewa ta hakura ta janye mayafinta,  gabanta ya fadi da idonta ya sauka kan dakin da take ciki,  chanzawar kayan dakin ba zai taba sa ta manta dakin Mahaifiyarta ba,  ta  waiga taga toilet a inda yake,  da sauri ta diro daga kan sabon gadonta tayi hanyar fita,  kanta ya kwance da ta tabbata a inda take,  a baiyane tace “Gidan mu?” ta dinga bin ko ina da ido,  Gidanmu? Gidanmu ne nan,  Mijinta ya siya Gidansu? Meke faruwa? Gidan Mahaifanta ne yanzu ya zama Gidan Aurenta?   Don cin fuska aka kawota dakin Mahaifiyarta  a matsayin dakin aurenta? Anya ya san nan gidannsu ne?  Ai ba ta taba kawoshi Gidan ba,  be taba zuwa gidan ba,  amma ya akayi haka?  Daman su YaMaji shi suka saida ma Gidan? Meke shirin faruwa ne? Is this  a coincidence?  Tamabayoyi da yawa a kanta wanda Mijinta kadai ne zai iya bata amsarsu,  da karfi tace “ZAID”.

 

•••••

Ghen!  Ghen!! Bibilicious freaking fans meye haka Zaid  keyi?  Wani irin cin fuska ne wannan? Hmmmm.

Drop all your thoughts here

Vote and Comment line by line.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa.

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣2⃣

 

Hajiya Taatuh na rabuwa da Hajia Aynarh ta kira Alhaji Ado tace mishi “sun kai amarya yanzu za taje Airport ta wuce Abuja, shima ya sanar da ita zai biya Bauchi yau amma InshaAllah gobe zai dawo Abuja suka ma juna fatan Alheri kafin suka katse wayar.

 

Anty Aynarh ta nufa Gidan Alhaji Abba na yanzu don ta sanar dashi an kai Ziyada gidanta, kuma ta dauka motar ta da ta bari a gidan da zasu kai amarya, ko da ta isa bata san hayaniyan Mairo sai ta kirashi a waya tace tana waje, ba a dau lokaci ba sai gashi ya fito da Murmushi, bayan sun gaisa ya tambayeta Ziyada tace “Tana chan lafiya, Gida yayi kyau, kuma abun mamaki Gidan da kuka tashi nan ne gidan” Daddy yayi jim kafin yace “ikon Allah, kila Alhaji Labaran Zaidun ya sayar ma Gidan, don Zaid din be san mu da gidan ba” Anty Aynarh tace “nima dai nayi mamaki” Daddy yace “amma ba wani abu bane, Allah ya basu zaman lafiya duk daya ne, ba zan dai gaya ma wannan mahaukaciyar ba don tana  iya zuwa ta rokeshi ya bamu Gidan” Hajia Aynarh tayi daria tace “Lalala, Alhaji Abba ba ruwana wallahi” Daddy ya Murmusa yana jin kansa wasai, tun jiya yake jinshi kamar an zare mai wani haki daga kafa yace “Nagode kwarai Hajia Aynarh, kin tabbata masoyiyata, tunda kin maida yarana kamar naki, banda gida, banda mota, banda kudin aurenki, da ina da ko da biyu daga cikin jerin abubuwan nan ne da na fito cikin sahun Masu neman Aurenki, Hajia Aynar ta runtse ido, wani irin dadi na shiga duk wani sasan jikinta, abunda ta dade ta na tsumaye kusan shekara 20 tana so taji wannan maganar daga bakin Alhaji Abba,ta tabbata ko meye Hajia Mairo ta mishi na mallaka ya fara kuncewa, tayi tsumayen kalaman kauna daga bakin shi, a kanshi ta kasa zaman Gidan Aure saboda sonshi, Aure biyu ta kaso don Alhaji Abba ya aureta, ta sa mayafin gyalenta ta rufe ido, wai ita kunya, yayi dariya yace ” Zanyi kokari in ga na mallaki ko da biyu daga cikin abubuwan nan inzo na aureki, ta juya mishi ido, tace “Idan na ara maka kudin Aurena zaka aureni?” yace “Aa, ni da kaina zanyi aikin neman kudin da zan aureki, ke gimbiya ce, ba zaa aureki da kudin bashi ba, tace “ina iya ara maka kudin sadaki, in ka samu ka biyani, Gida kuma da Amincewarka zaka barni a gidana, abu na, naka ne, na sha gaya ma da dadewa” kasa magana yayi ya murmusa, daidai fitowar AbdulMajeed daga Gida, Daddy ya yafito shi yace “Zo ka kai Auntynka Gida, ta gaji” cike da ladabi yace “To Daddy” Aunty Aynarh ta kura ma Daddy ido, shima kallonta yakeyi, har Majeed yaji kunyan kallon da suke wurga ma junansu da angani an san na so ne, a ranshi yace “ai in Mummy ta fito yanzu ai mun bonu duka” don kansu suka bar kallon junansu, ta mika ma AbdulMajeed Key, suka shiga mota suka wuce Daddy be shiga gida ba sai da yaga sun kule, a hanya ne Anty Aynarh ke sanar da AbdulMajeed inda aka kai Ziyada,  sosai ya jinjina maganar amma daga karshe ya musu fatan Alheri.

••••••

 

Da k’arfi ta sake kwala mai kira “Zaid” nan ma shiru ba amsa,  da baya da baya take tafia har ta ci karo da Dakinsu na da,  ta bude da karfi,  wayam baya nan,  kamar zararra ta nufi dakin AbdulMajeed ta wangale nan ma baya nan,  da gudu ta nufi dakin Daddynsu ta banka da k’arfi,  nan ta sauke naunauyar ajiyar zucia ganin  Zaid sanye cikin wasu Farar riga da Wando fari 3quater, yana zaune kan Kingsized bed yana latsa laptop dinsa,  ganinshi ya sa ta jin sanyi,  wani sabon so da kaunarshi na shiga duk wani lungu da  sakon jikinta, a daddafe ta karasa  ta hau kan Gadon,  ko kallo daya bata samu ya mata ba,  cigabawa yayi da harkar gabanshi.

 

Ta kasa karantar yanayin da yake ciki,  meyasa yake yin haka?  Ko gajiar bikin ce be sakeshi ba?  Yanda yake wayoyinsa cikin kwanciyar hankali ba tare da ya dago ido ya kalleta bane ya sata mamaki ainun,  kamar ba shi ba,  kamar ba Zaid dinta ba, bakinta na mata nauyi,  da kyar ta samu ta juya harshenta “My Forever” yanda kasan ba da shi takeyi ba,  yayi banza da ita,  a ranta tace “ko dai be ji ba?” ta sake kiranshi da “Zaid” nan ma shiru yayi mata, wannan shine “hakuri” da Daddynta yake ce mata ta yi? Wannan shine kawar da kai din da ake ta mata magana a kai? Tun baaje ko ina ba? Dama haka maza suke da sunyi aure? Ba haka yake ba da, kamar ba loving and caring Zaid dinta ba,  wanda bata taba so ba sai a kanshi,  wanda shine ya koya mata yanda zata soshi?  Duk ya rikide ya chanza,  bata so tayi imagining wani abu is about to go wrong,  bata so tayi tunanin chanjin nan da wani manufa,  bata so tayi tunanin komai,  gwara tayi ta mai uzuri, da sauri zuciyarta tace “ko dai yana da aljanu? Don sharetan da yakeyi ta tabbata ba yin kansa bane,   Ko moodswing ne? Ai ana haka,  wani lokacin kaji baka son yi ma kowa magana,  to kila hakan ne,  bari ta bashi space,  ko anjima zai dawo daidai.

 

Mikewa tayi zata bar dakin ta tsinkayi muryansa a sama “Ina Wayarki?” da sauri tace “Yana daki” muryarsa cike da umurni yace “dauko” da sauri ta fita Daki ta shiga dakinta ta bude jakkarta ta dauko wayar, komawa tayi dakin da ta bar Zaid ta mika mishi wayan, amsa yayi da karfi kamar fizge, ta kalloshi da sauri, a gaban idonta ya kashe wayar ya jefa cikin aljihunsa ya cigaba da latsar wayarsa da laptop, gabanta ya fadi, me hakan ke nufi? Me Zaid ke nufi? Me yakeyi haka? For how long zata cigaba da mishi uzuri? Bakinta na rawa tace “Meyasa ka kashe min waya? Meyasa ka kawoni Gidan nan? Shin baka san Gidanmu bane nan?” Zaid ya fashe da wani irin dariyan da daga ji kasan cewa bana lafiya bane,  kafin yace “thats what you dont know,  This is my house,  it has always been My house(shine abinda baki sani ba,  wannan Gida  na ne,  dama chan Gida na ne” ta ja baya tana kallonshi, a iya sanninta,  ta san wannan gidansu ne,  shiyasa suka saida gidansu na Abuja suka dawo Kano,  yana nufin da ya siya gidan ne ya zama nashi.

 

Ita yanzu ba ma wannana ba, Maaurata ne su, burinta ya cika,  ta auri Masoyinta abun sonta, be kamata su fara da haka ba, ta sautar da murya tace “My Forever, me ya faru ne?  Kana jin yunwa? In dafa maka abinci?” Zaid ya zaro ido yace “Abinci? Abincin diyar Hajiya Mairo? Allah ya tsareni da cin Abincin Mahainta,  nasan ko an baki maganin da zaki saka mun inci in mutu  ku gaji Dukiyana, No thanks?”.  Yanzu abun kuma ya fara ba Ziyada tsoro,  tsoro fal ranta,  ta zaro ido,  kanta na juya magananunshi,  jikinta yayi sanyi, tace “haba My Forever,  wani irin magana kake haka? Ta ya zan samaka magani ka mutu?  Ya zaayi in kashe Mijina? DanAllah ka bar irin wannan tunanin” ta karashe cikin sanyin jiki tare da kamo hannunsa,  kamar wuta ya tabe shi da sauri ya janye hannunsa tare da mikewa,  kar ki sake tunkaro ni,  kar ki sake gigin tabani,  jinin Hajiya Mairo Najasa ne,  ke najasa ce, in kuma shaawar da kika kwaso kike son a rage miki ina da Yara Christians sai in hadaku su zo su biya miki bukkatarki” be karashe maganarshi ba ta sa hannu ta kwashe shi da Mari, Murmushi  Zaid yayi tare da shafar fuskarshi,  abunda tayi yanzu ya harbi tunaninta,  Marinshi tayi, Marin Mijinta ta tayi,  kawai  sai  ta fashe da kuka, “donAllah kayi hakuri, ban san nayi ba” be tanka ta ba ya hau kan gado,  da murmushi dauke kan fuskarshi,  duk sai ta sha jinin jikinta,  rarrafawa tayi kan Gadon tace “ka min magana,  ka yafe  min, in ba zaka iya ba ka rama,  ga fuskata nan,  ka rama” banza yayi da ita ya dauko wayarshi da mukuli ya sa a aljihu,  fita yayi daga dakin ta bishi saurisauri gudugudu, a tsakar gida ya kwalawa Sule kira,  daga dakin Maigadi wani ya fito sanye da kayan uniform,  yace “Kar wanda ya sake ya shigo min gida,  kar kuma wanda ya sake ya fitar min daga gida,  kana jina?” jiki na rawa yace ” Eh Oga,  nagane” Zaid ya kalleshi sama da kasa yace “Wannan  in Mairo tazo ai bugeka zatayi ta shigo,  ya latso idi a waya ringing daya ya dauka “Idi,  kaje Police Headquater kace nace ina son tsaro a Gida” da fita zaiyi amma ya fasa,  ya koma cikin gidan,  itama ta bishi,  wannan wani irin masifa ne?  A ce ko kwana ba tayi a gidanta ba amma ta fara haduwa da bacin rai?”.

 

Kan Kujera ya zauna ya kira Gidan Marayu na Kaduna yana waya,  tana zaune dan nesa dashi tana karantar halaiyarshi,  komai nashi yayi  ne,  ji yanda yake magana cike da isa,  ta kasa gane me yake nufi da ita,  amma ai ta ji labarin yanda angwaye ke rawan jiki a kan Amarensu,  ita meyasa nata ya sha bambam? Suna zaune Idi ya kira Zaid ya ce mishi ga Police  nan da Civil defense, kamar ta sani ta bi bayanshi  da ta ga ya mike ya fita tsakar gida,  nan ta ga garada sun kai sha biyu da uniform din tsaro,  duk suka shiga kwasan gaisuwa be karba musu ba ya shiga basu umurni kamar haka;

“Ban yarda a shigo min Gida ba,  ban yarda na ciki su fita ba,  i mean ko waye kar a barshi ya shiga,  i want tight security here”.  A tare suka ansa da “Yes Sir”.

Nan take ya kira Armstrong, ringing daya ya dauka “book our tickets,  we are leaving for Porthacourt  now” Zaid ya wuce ta ya shige ciki,  da gudu ta bi bayanshi, ta bishi har daki inda yake hada Naurarshi cikin jakka, baki na rawa tace “Porthacourt? Chan zamu?” banza yayi ya kyaleta,  tace “kayi wa darajan manzonAllah ka min magana” ya dago ya kalleta, zaiyi magana kuma ya fasa,  tace “please, You are not leaving me here are you?” nan ma shiru ya mata,  tace “ka ban wayata ina so nayi magana da Yayana” nan ma shiru,  da sauri tace “Don girman Allah ka kaini Gida wurin Mummy na,  ka kaini wurin iyayena” tsaki yayi a k’arshe ma ya finciki jakarshi me kama da school bag ya rataya ya fita ya bar mata daki.

 

A guje ta kwasa ta bishi,  a tsakiyar farlo ta cimma shi,  ta rungumoshi tare da fashewa da kuka,  jimmm yayi yana tsintar kanshi cikin kunan rai,  be san  dalili ba,  kukanta ne ya sashi kuka?  Ko haushin ta taba shi?  Sosai ta rungumeshi,  ta matse shi ta baya, tana kuka har hawayenta na zuba akan farar rigar bodyhug dinshi,  cikin kuka take cewa  “me ya faru damu?  Me ya samu soyayar mu?  Me na maka? Meyasa kake min haka? A iya sanina banyi maka wani abu ba, all i did was to love you,  i didnt do anything wrong,  Sonka kawai nakeyi,  shin So dama laifi ne? Ina Alkawarin Soyayyar da ka min?” zaiyi karya in yace Jikinshi be mutu ba,  zaiyi karya in yace be jin duk wani kalamanta, murya dishidishi yace “ki sakeni” kara matseshi tayi tana girgiza kanta a jikinshi tana cewa “ba zan sake ka ba, sai ka gaya min  what change,  sai ka gaya min what happened  to us” da kyar ya tattaro wani courage ya daka mata tsawa yace “Ziyaaaaaa,  Let Go” lumshe idanunta tayi,  daidai da saukowan hawaye masu dumi,  duk  da tana cikin tashin hankali,  wallahi taji  kiran nan da yayi mata da wani suna da ba wani mahalukin da ya taba kiranta dashi “Ziyaaaa” sake kwantawa tayi a bayanshi ta girgiza kai tace “No,  i wont let go,  Never (ba zan barka ba,  ba zan taba barinka ba)”.

Shikenan ta gama kashe jiki,  be so be so ya yarda,  amma tausayinta yaji,  karo na farko  da tausayin wani abu ya darshe shi.

 

“Your Plans,  dont let het ruin it” Sashen zuciyarshi ta tunasarshe shi,  da karfi ya banbareta daga jikinshi ya yasar da ita a kasa yace “kar ki sake tabani,  kina so kisan what changed? Zan gaya miki,  ban taba sonki ba,  i cant love you” dariya me hade da kuka takeyi tace “karya kakeyi,  biglie,  ban yarda ba ba zan kuma yarda ba,  kana sona,  shiyasa ka sa akayi bikinmu cikin kurarren lokaci,  you  cant wait to have me,  shiyasa aka aura maka ni cikin kwana biyu,  kana sona, so mai yawa, you love me that much” Zaid ya girgiza kai irin na tausaya makin nan yace “You are even more stupid than i thought, dont you get it? Ko da yake diyar Mamanki ce ke, bakwa ganewa, to barin gaya miki Na aureki ne don na Wulakanta ki, na tozarta ki, na Aureki ne don na dau fansa, wanda so far ina ganin da kyau, na Aureki ne don na kuntata miki da mahaifanki, baki fara ganin wulakancin ba? Na kawo ki Gidan da kuke takama naku ne a da, it was never yours, i took back whats rightfully mine”.

 

Girgiza kanta takeyi tana kuka tace ” Karyane, wallahi kana sona, i refuse to believe all this, ka nuna min ingantacen so, ba zan yarda ba, in ma kana da wani unfinished bussiness da su Mummy ne, i dont care, ku zauna kuyi settling din kanku, ku yafe ma juna, amma kar ka min haka , donAllah kar ka min haka” Zaid yayi fuskan tausayi yace “Awwwn, My Poor Wife, ba kyason Mijinki ya barki ai?  Congrats Ba zan barki ba, amma zaki so mu rabu, duk da ba zan rabu dake ba sai na tabbatar na muku tabon da ba zaku taba mance ni ba” ya tsugguna ya dau jakkarshi ya fice daga parlorn ita kuwa rushewa tayi da wani irin kuka mai ratsa zuciya.

 

A cikin Mota ya zauna ya dinga sauke ajiyar zuciya da karfi, kanshi ya dau chargi, In ranshi ya baci, abu daya kawai ke kwantar mai da hankali in ya shiga irin yanayin nam, da sauri ya fita ya bude booth, Akwatin Armstrong ya bude, Gwangwanin Giya sun kai goma daga gani masu tsada ne, ya dauko daya da karfi bude lid din zai kafa kai ya sha.

“Zaid Alkawarin da ka mun kenan?” Ya rantse da Allah muryan Babanshi Sadam yaji a kwanyar kanshi, da wani irin murya kamar fatalwa, da sauri ya wurgar da Giyar hannunshi ya fada Mota  ya latsa horn aka bude mishi gate da sauri, ya fincika Motar da karfi ya fita daga Gidan, Driver dinshi da Odile suka shiga wata Motar suka bi bayanshi a guje.

Saida ya kusa Minti 50 yana zagaye garin Kano, kafin ya samu ya dawo daidai, daga bisani ya buga tsaki da karfi? Meye hakan to?” Armstrong ya kira ya bashi umurnin ya wuce Airport Direct.

°°°°°°°

Har wurin k’arfe biyu tana nan yashe a inda Angonta ya barta,  zuciyarta na tukukin zafi,  bata son yarda da duk wasu magananunshi,  zata cigaba da mai uzuri har ya dawo gareta,  a yanda ta fahimci maganganunshi, Akwai wata boyayyen zance tsakaninshi da Iyayenta,  a yanda yake yada mata habaici ta gane Iyayenta sun taba mishi wani laifi, to me zasu mishi?  Zaid fa ba zai wuce tsaran YaMaji ba,  in kuma laifi suka mishi ko wani nashi meyasa zasu yarda ya aureta,  to menene? duk yanda taso gano kullaliyar da ke ciki ta kasa,  su kadai zasu gaya mata meke faruwa,  da sauri ta tashi ta nufa daki dan kiran Mommy a waya,  tana son jin komai, abubuwan da suka faru a baya kafin a haifeta,  turus ta tsaya da ta tuna wayarta na hannun Zaid,  ba kuma ta isa ta fita ba,  hawayenta sun kare karkaf,  ta fada toilet don yin Alwala don ko Azahar batayi ba.

****

 

A cikin Jirgi Armstrong  ya lura da Zaid  yayi nisa cikin tunaninshi,  ya dan tabo shi yace “Are you OK?” Zaid ya danyi tsaki yace “I’m fine” arm yace “You want to talk about it?” Zaid a fusace yace “Shut the f**kup Arm” Armstrong ya daga hannunshi sama yace “Sorry,  naye shiru”.

Duk yanda be so yayi tunaninta ya kasa,  kawai ya dauko earphone babba ya sa a kunnenshi ya kura volume duk dai don ya manta da tunanin da zuciyarshi keyi.

 

Bayan kwana biyu….

PORTHACOURT 10am

 

A daddafe yayi kwana biyun nan,  wani hali take ciki?  Me takeyi?  Ba wai don ya damu ba fa,  kar ma ayi zaton ya damu, kamar an tsunguleshi ya tashi  a zabure,  ya kira Arm,  yace “book a flight to Kano”Armstrong  yace “why?” a fadance Zaid yace “Stop Asking question  stupid,  book the goddam flight” Armstrong  yace “OK i got you” ya kashe wayan ya kira waya,  chan ya sake kiranshi yace “Sorry boss,  they’d be no flight to Kano today(saidai  kayi hakuri,  ba jirgin kano yau)” ran Zaid a bace yace “Seriously? Then get my Private Jet” Armstrong  zaiyi magana Zaid ya katse shi da cewa “Arm if you wont get me to Kano i’ll find someone who will(Arm in ba zaka kaini kano ba,  zan nemo wanda zai kaini)” cikin  sanyin jiki Amstrong yace “OK boss” Amstrong ya kashe wayan yana mamakin meke samun Zaid,  duk ya sukurkuce lokaci guda,  ya zabure yana abubuwa kamar someone that is desperate,  da wannan tunanin ya iso Gidan Zaid, Driver ya kai su inda Private Jet din ZSA yake,  kasancewar Amstrong ya iya tuk’a Jet,  shi ya tuk’a Jet din,  a hanya Amstrong  ke tambayan Zaid meyasa yake son komawa Kano da gaggawa,  Zaid yace saboda yaje a cigana da kuntata ma Ziyada,  in ba sa tare zata fi sakewa, tafi walawa,  shikuma be son ganin ta sakata ta wala, amma in yana nan zata takura ta zama cikin kunci. Armstrong ya tabe  baki,  yayi shiru da bakinshi don kar yace wani abu a hayyayako mai.

 

KANO 1pm

Abin duniya yayi ma Mairo cunkuso, komai ya tsaya mata cak ta rasa meke mata dadi. Banda tunani kala kala bata komai. Hankalinta na tashi a duk lokacin da ta kira wayar Ziyada taji switched  off, Tun auren Ziyada batasan inda aka kaita ba, tayi tunanin duniya ta gano amma ta kasa. Ta gaji da Kira wayan Ziyada don baya shiga, nan fa ta rinka surfa ma MTN zagi kala kala tana kwashe masu albarka.

Duk da haka ba ta daina trying number dinba, a hakan har charging wayanta ya kare kap. Garin masifa da rawar jiki taje ta ƙone charger saida hayaƙi mai firgitarwa ya fito.

Gefe ta koma ta rukuba tana huci, abin duniya yana damunta,  ta tambayi daddy da Abdulmajeed duk sunce basu san inda Gidan Ziyada yake ba,  duk da sun san ko ba dade ko ba jima sai ta san inda diyarta ke zaune,  Wani dabara ya fado mata taje wajen dangin oduduwa watau Hajia Ainau domin tabbas tasan inda take,  ita ta kaita dakin Miji.

Da farko tayi kememe da shawarar amma kuma saita tuna batada wani tudun dafawa, gwiwa a sanyaye ta rinka fizgan jiki har Gidan Hajia Aynarh,  ita wallahi bari dai ta gano gida ziyada, sai tace ma Zaid tana bukatar Mota don abun kunya ne a ce tana surikar Gatan Marayu kuma tana hawa Keke Napep  .

 

Babu kunya ba tsoron Allah tayi ma Hajia Aynarh  sallama a dakile  da mamaki Hajia Ainau take kallonta bata taba zaton Hajia Mairo  ta san gidanta ba,  nan ta murtuke fuska ta amsa mata sallamar ciki ciki.

“Ina wuni ina gajiya?” Hajia Mairo tace don tana son suyi su gama ta tafi gidan diyarta,

“lau” kawai Hajia Ainau tace saita cigaba da abinda takeyi wato shan kankana, batayi mata tayi ba banda danna waya na rashin dalili data soma,  don  har ranta tana kishin Hajia Aynarh.

Hajia Mairo idan ranta yayi dubu ya ɓaci amma saita danne saboda ita take neman taimako wajenta. Murya yana rawa ta tambaya Hajia Ainau inda Ziyada take.

 

“Nima ban sani ba” Hajia Ainau ta amsa mata a takaice,   Kakalo murmushi Mairo tayi saita ce, “Haba Hajia kiyi hakuri mana Dan Allah ki fada min inda take, wallahi inasan ganinta ne. ‘Yata ce kwana biyu kenan ina kiranta a kashe,  dole nake shiga damuwan rashinta,  ki gaya min please”

Ita kam Ainau halin ko ta kula tayi sai laste laste take na na’ urar bature. Mairo kam sai magiya takeyi har saida H. Ainau tace mata cikin izgili “jeki tsohon gidanku tana chan” a zatonta Gatse Hajia Aynarh takr mata,  tace “DanAllah  ki gaya min,  tana ina?” tace “Haba Hajia Mairo, ya zaki zo kina min ihu akai,  nace miki tana tsohon gidanku na GRA,  me kike so kiji bayan nan?  DanAllah ki rabu dani”

“Ban gane tsohon gidan mu ba” ta faɗa ido a warware gabanta na bugun taratara

Hajia Ainau bata ce mata ci kanki ba, nan tabama banza ajiyar ta.

Saurisauri gudu gudu Mummy ta fita daga gidan ta taro Adaidaita  tace a kaita GRA,  kuma tsakani ga Allah  ko kudin Napep  din bata dashi,  in taje ta bada.

***

A cikin kwanaki biyun nan,  wanda ya san Ziyada ya ganta ba zai ganeta ba cikin wannan yanayin,  duk ta rame ta jeme,  akwai abinci a gidan,  amma bata iya ci ko ta dafa,  bata bacci don fargaba ta ya zata kwana a gidan nan ita kadai,  sai dai bacci barawo ya saceta,  ta sha kokarin guduwa marasa imanin nan ba sa barinta fita ,  ba hanyar guduwa,  hawayenta har sun kafe,  kukan ma bata iyayi,  Ziyada dai ta koma abar tausayi, tana kan daddumarta tana Addua taji alamun an bude kofar parlo,  a guje  ta kwasa ta fita  parlon,  ganin Zaid tayi sanye cikin riga top  da ta waje da wando jeans Zai rufe kofa.

 

 

Ajiyar zuciya ta sake a guje ta rugo gunshi ta runkukumeshi tare da fashewa da kuka,”My Forever,  kar ka sake bari na ni kadai DonAllah” be son kukan nan,  aa yana so,  ta cigaba,  it gives him joy, hannu ya sa ya tureta ya wuce daki,  binshi take a baya tana tambayarshi  me zata dafa mai,  ya shiga daki ya buga mata kofa a fuska.

***

Isowarta ke da wuya,  ta ci karo da gidan makil da masu tsaro,  tace ma me Napep barin anso maka kudinka, yace “to Hajia kiyi sauri” ta wuce tana sababi,  tazo shiga aka dakatar da ita,  tace “Kai gafara chan,  matsa min in shiga” wani yace “baa shiga Hajia” cike da masifa tace “ban gane baa shiga ba” yace “Umurni ne  daga Oga,  yace kar a bar ko waye ya shiga” Hajia Mairo  ta dara tace “ni ai ba kowa bace,  ku bude ni surukar shi,  matsayin uwarsa nake” dayan yace “ku bude mata” dayan yace “baka da hankali ne? Bakaji Oga yace kar a bar kowa ya shigo  ba,  ko yanzu da zai shiga sai da ya kara jadadda mana” sukace hakane,  Mairo tace “kai bansan iskancin banza ku bude  min na shiga,  ko wallahi na sa ya koreku” daya yace “Hajia da kin kirashi kince mai kina kofar gida” nan fa daya,  da tana da numbernshi ai da taji dadi,  kuma numbern Ziayda be shiga,  tace “wayar ba chaji kaidai  kaje ka ce mishi ga Mamansu a waje” suka ce to gwara hakan, shiga dayan yayi ya dinga kwankwasa parlo,  Zaid da Ziyada  a tare suka karasa Parlorn,  shi ya na tunanin waye ke kwankwasa mai kofa,  ita kuma tana rokon Allah yasa wani dan gidansu ne.

Officer yace “Sorry Oga,  Bakuwa kukayi” yace “Uban me nace muku?  Nace kar ku bari ko waye ya shigo ko?” yace “bawanda ya shigo,  dama tace mamar matarka ce, kuma surikarka,  shine nace bari a sanar da kai” ran Zaid bace yace “ba ce muku nayi kowaye ya zo kar ku bari ya shigo ba?” police ya kalli Ziyada sai yaji ta bashi tausayi yace “Oga Mahaifiyar Matarka fa ce” cikin tsawa wanda ya tabbata Mairo taji  yace “koma uwar wacece” Jikina rawa ya juya yana cewa “OK Sir”.  Zaid ya waiga yaga Ziyada na kukan hawaye,  ya murmusa  a ranshi yace “its time” Zai ci mutuncin Uwa gaban diyarta,  ya juya gun mai tsaron yace “Ko kuma Kai,  barta ta shigo” Ziyada ta daka tsallen murna,  tana farinciki zata ga uwarta” Zaid ko Murmushin gefen kumatu yayi.

****

 

Ghen Ghen,  Zaid and Mairo,  Round one Fight.

Me kuke tunanin zai faru?

Me zakuce game da abunda Zaid ke ma Ziyada,  nima na sha hawaye na,  amma Zaid akwai dan…

 

Vote and Comment line by line,  God Bless you as you do.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

 

 

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣2⃣

 

Hajiya Taatuh na rabuwa da Hajia Aynarh ta kira Alhaji Ado tace mishi “sun kai amarya yanzu za taje Airport ta wuce Abuja, shima ya sanar da ita zai biya Bauchi yau amma InshaAllah gobe zai dawo Abuja suka ma juna fatan Alheri kafin suka katse wayar.

 

Anty Aynarh ta nufa Gidan Alhaji Abba na yanzu don ta sanar dashi an kai Ziyada gidanta, kuma ta dauka motar ta da ta bari a gidan da zasu kai amarya, ko da ta isa bata san hayaniyan Mairo sai ta kirashi a waya tace tana waje, ba a dau lokaci ba sai gashi ya fito da Murmushi, bayan sun gaisa ya tambayeta Ziyada tace “Tana chan lafiya, Gida yayi kyau, kuma abun mamaki Gidan da kuka tashi nan ne gidan” Daddy yayi jim kafin yace “ikon Allah, kila Alhaji Labaran Zaidun ya sayar ma Gidan, don Zaid din be san mu da gidan ba” Anty Aynarh tace “nima dai nayi mamaki” Daddy yace “amma ba wani abu bane, Allah ya basu zaman lafiya duk daya ne, ba zan dai gaya ma wannan mahaukaciyar ba don tana  iya zuwa ta rokeshi ya bamu Gidan” Hajia Aynarh tayi daria tace “Lalala, Alhaji Abba ba ruwana wallahi” Daddy ya Murmusa yana jin kansa wasai, tun jiya yake jinshi kamar an zare mai wani haki daga kafa yace “Nagode kwarai Hajia Aynarh, kin tabbata masoyiyata, tunda kin maida yarana kamar naki, banda gida, banda mota, banda kudin aurenki, da ina da ko da biyu daga cikin jerin abubuwan nan ne da na fito cikin sahun Masu neman Aurenki, Hajia Aynar ta runtse ido, wani irin dadi na shiga duk wani sasan jikinta, abunda ta dade ta na tsumaye kusan shekara 20 tana so taji wannan maganar daga bakin Alhaji Abba,ta tabbata ko meye Hajia Mairo ta mishi na mallaka ya fara kuncewa, tayi tsumayen kalaman kauna daga bakin shi, a kanshi ta kasa zaman Gidan Aure saboda sonshi, Aure biyu ta kaso don Alhaji Abba ya aureta, ta sa mayafin gyalenta ta rufe ido, wai ita kunya, yayi dariya yace ” Zanyi kokari in ga na mallaki ko da biyu daga cikin abubuwan nan inzo na aureki, ta juya mishi ido, tace “Idan na ara maka kudin Aurena zaka aureni?” yace “Aa, ni da kaina zanyi aikin neman kudin da zan aureki, ke gimbiya ce, ba zaa aureki da kudin bashi ba, tace “ina iya ara maka kudin sadaki, in ka samu ka biyani, Gida kuma da Amincewarka zaka barni a gidana, abu na, naka ne, na sha gaya ma da dadewa” kasa magana yayi ya murmusa, daidai fitowar AbdulMajeed daga Gida, Daddy ya yafito shi yace “Zo ka kai Auntynka Gida, ta gaji” cike da ladabi yace “To Daddy” Aunty Aynarh ta kura ma Daddy ido, shima kallonta yakeyi, har Majeed yaji kunyan kallon da suke wurga ma junansu da angani an san na so ne, a ranshi yace “ai in Mummy ta fito yanzu ai mun bonu duka” don kansu suka bar kallon junansu, ta mika ma AbdulMajeed Key, suka shiga mota suka wuce Daddy be shiga gida ba sai da yaga sun kule, a hanya ne Anty Aynarh ke sanar da AbdulMajeed inda aka kai Ziyada,  sosai ya jinjina maganar amma daga karshe ya musu fatan Alheri.

••••••

 

Da k’arfi ta sake kwala mai kira “Zaid” nan ma shiru ba amsa,  da baya da baya take tafia har ta ci karo da Dakinsu na da,  ta bude da karfi,  wayam baya nan,  kamar zararra ta nufi dakin AbdulMajeed ta wangale nan ma baya nan,  da gudu ta nufi dakin Daddynsu ta banka da k’arfi,  nan ta sauke naunauyar ajiyar zucia ganin  Zaid sanye cikin wasu Farar riga da Wando fari 3quater, yana zaune kan Kingsized bed yana latsa laptop dinsa,  ganinshi ya sa ta jin sanyi,  wani sabon so da kaunarshi na shiga duk wani lungu da  sakon jikinta, a daddafe ta karasa  ta hau kan Gadon,  ko kallo daya bata samu ya mata ba,  cigabawa yayi da harkar gabanshi.

 

Ta kasa karantar yanayin da yake ciki,  meyasa yake yin haka?  Ko gajiar bikin ce be sakeshi ba?  Yanda yake wayoyinsa cikin kwanciyar hankali ba tare da ya dago ido ya kalleta bane ya sata mamaki ainun,  kamar ba shi ba,  kamar ba Zaid dinta ba, bakinta na mata nauyi,  da kyar ta samu ta juya harshenta “My Forever” yanda kasan ba da shi takeyi ba,  yayi banza da ita,  a ranta tace “ko dai be ji ba?” ta sake kiranshi da “Zaid” nan ma shiru yayi mata, wannan shine “hakuri” da Daddynta yake ce mata ta yi? Wannan shine kawar da kai din da ake ta mata magana a kai? Tun baaje ko ina ba? Dama haka maza suke da sunyi aure? Ba haka yake ba da, kamar ba loving and caring Zaid dinta ba,  wanda bata taba so ba sai a kanshi,  wanda shine ya koya mata yanda zata soshi?  Duk ya rikide ya chanza,  bata so tayi imagining wani abu is about to go wrong,  bata so tayi tunanin chanjin nan da wani manufa,  bata so tayi tunanin komai,  gwara tayi ta mai uzuri, da sauri zuciyarta tace “ko dai yana da aljanu? Don sharetan da yakeyi ta tabbata ba yin kansa bane,   Ko moodswing ne? Ai ana haka,  wani lokacin kaji baka son yi ma kowa magana,  to kila hakan ne,  bari ta bashi space,  ko anjima zai dawo daidai.

 

Mikewa tayi zata bar dakin ta tsinkayi muryansa a sama “Ina Wayarki?” da sauri tace “Yana daki” muryarsa cike da umurni yace “dauko” da sauri ta fita Daki ta shiga dakinta ta bude jakkarta ta dauko wayar, komawa tayi dakin da ta bar Zaid ta mika mishi wayan, amsa yayi da karfi kamar fizge, ta kalloshi da sauri, a gaban idonta ya kashe wayar ya jefa cikin aljihunsa ya cigaba da latsar wayarsa da laptop, gabanta ya fadi, me hakan ke nufi? Me Zaid ke nufi? Me yakeyi haka? For how long zata cigaba da mishi uzuri? Bakinta na rawa tace “Meyasa ka kashe min waya? Meyasa ka kawoni Gidan nan? Shin baka san Gidanmu bane nan?” Zaid ya fashe da wani irin dariyan da daga ji kasan cewa bana lafiya bane,  kafin yace “thats what you dont know,  This is my house,  it has always been My house(shine abinda baki sani ba,  wannan Gida  na ne,  dama chan Gida na ne” ta ja baya tana kallonshi, a iya sanninta,  ta san wannan gidansu ne,  shiyasa suka saida gidansu na Abuja suka dawo Kano,  yana nufin da ya siya gidan ne ya zama nashi.

 

Ita yanzu ba ma wannana ba, Maaurata ne su, burinta ya cika,  ta auri Masoyinta abun sonta, be kamata su fara da haka ba, ta sautar da murya tace “My Forever, me ya faru ne?  Kana jin yunwa? In dafa maka abinci?” Zaid ya zaro ido yace “Abinci? Abincin diyar Hajiya Mairo? Allah ya tsareni da cin Abincin Mahainta,  nasan ko an baki maganin da zaki saka mun inci in mutu  ku gaji Dukiyana, No thanks?”.  Yanzu abun kuma ya fara ba Ziyada tsoro,  tsoro fal ranta,  ta zaro ido,  kanta na juya magananunshi,  jikinta yayi sanyi, tace “haba My Forever,  wani irin magana kake haka? Ta ya zan samaka magani ka mutu?  Ya zaayi in kashe Mijina? DanAllah ka bar irin wannan tunanin” ta karashe cikin sanyin jiki tare da kamo hannunsa,  kamar wuta ya tabe shi da sauri ya janye hannunsa tare da mikewa,  kar ki sake tunkaro ni,  kar ki sake gigin tabani,  jinin Hajiya Mairo Najasa ne,  ke najasa ce, in kuma shaawar da kika kwaso kike son a rage miki ina da Yara Christians sai in hadaku su zo su biya miki bukkatarki” be karashe maganarshi ba ta sa hannu ta kwashe shi da Mari, Murmushi  Zaid yayi tare da shafar fuskarshi,  abunda tayi yanzu ya harbi tunaninta,  Marinshi tayi, Marin Mijinta ta tayi,  kawai  sai  ta fashe da kuka, “donAllah kayi hakuri, ban san nayi ba” be tanka ta ba ya hau kan gado,  da murmushi dauke kan fuskarshi,  duk sai ta sha jinin jikinta,  rarrafawa tayi kan Gadon tace “ka min magana,  ka yafe  min, in ba zaka iya ba ka rama,  ga fuskata nan,  ka rama” banza yayi da ita ya dauko wayarshi da mukuli ya sa a aljihu,  fita yayi daga dakin ta bishi saurisauri gudugudu, a tsakar gida ya kwalawa Sule kira,  daga dakin Maigadi wani ya fito sanye da kayan uniform,  yace “Kar wanda ya sake ya shigo min gida,  kar kuma wanda ya sake ya fitar min daga gida,  kana jina?” jiki na rawa yace ” Eh Oga,  nagane” Zaid ya kalleshi sama da kasa yace “Wannan  in Mairo tazo ai bugeka zatayi ta shigo,  ya latso idi a waya ringing daya ya dauka “Idi,  kaje Police Headquater kace nace ina son tsaro a Gida” da fita zaiyi amma ya fasa,  ya koma cikin gidan,  itama ta bishi,  wannan wani irin masifa ne?  A ce ko kwana ba tayi a gidanta ba amma ta fara haduwa da bacin rai?”.

 

Kan Kujera ya zauna ya kira Gidan Marayu na Kaduna yana waya,  tana zaune dan nesa dashi tana karantar halaiyarshi,  komai nashi yayi  ne,  ji yanda yake magana cike da isa,  ta kasa gane me yake nufi da ita,  amma ai ta ji labarin yanda angwaye ke rawan jiki a kan Amarensu,  ita meyasa nata ya sha bambam? Suna zaune Idi ya kira Zaid ya ce mishi ga Police  nan da Civil defense, kamar ta sani ta bi bayanshi  da ta ga ya mike ya fita tsakar gida,  nan ta ga garada sun kai sha biyu da uniform din tsaro,  duk suka shiga kwasan gaisuwa be karba musu ba ya shiga basu umurni kamar haka;

“Ban yarda a shigo min Gida ba,  ban yarda na ciki su fita ba,  i mean ko waye kar a barshi ya shiga,  i want tight security here”.  A tare suka ansa da “Yes Sir”.

Nan take ya kira Armstrong, ringing daya ya dauka “book our tickets,  we are leaving for Porthacourt  now” Zaid ya wuce ta ya shige ciki,  da gudu ta bi bayanshi, ta bishi har daki inda yake hada Naurarshi cikin jakka, baki na rawa tace “Porthacourt? Chan zamu?” banza yayi ya kyaleta,  tace “kayi wa darajan manzonAllah ka min magana” ya dago ya kalleta, zaiyi magana kuma ya fasa,  tace “please, You are not leaving me here are you?” nan ma shiru ya mata,  tace “ka ban wayata ina so nayi magana da Yayana” nan ma shiru,  da sauri tace “Don girman Allah ka kaini Gida wurin Mummy na,  ka kaini wurin iyayena” tsaki yayi a k’arshe ma ya finciki jakarshi me kama da school bag ya rataya ya fita ya bar mata daki.

 

A guje ta kwasa ta bishi,  a tsakiyar farlo ta cimma shi,  ta rungumoshi tare da fashewa da kuka,  jimmm yayi yana tsintar kanshi cikin kunan rai,  be san  dalili ba,  kukanta ne ya sashi kuka?  Ko haushin ta taba shi?  Sosai ta rungumeshi,  ta matse shi ta baya, tana kuka har hawayenta na zuba akan farar rigar bodyhug dinshi,  cikin kuka take cewa  “me ya faru damu?  Me ya samu soyayar mu?  Me na maka? Meyasa kake min haka? A iya sanina banyi maka wani abu ba, all i did was to love you,  i didnt do anything wrong,  Sonka kawai nakeyi,  shin So dama laifi ne? Ina Alkawarin Soyayyar da ka min?” zaiyi karya in yace Jikinshi be mutu ba,  zaiyi karya in yace be jin duk wani kalamanta, murya dishidishi yace “ki sakeni” kara matseshi tayi tana girgiza kanta a jikinshi tana cewa “ba zan sake ka ba, sai ka gaya min  what change,  sai ka gaya min what happened  to us” da kyar ya tattaro wani courage ya daka mata tsawa yace “Ziyaaaaaa,  Let Go” lumshe idanunta tayi,  daidai da saukowan hawaye masu dumi,  duk  da tana cikin tashin hankali,  wallahi taji  kiran nan da yayi mata da wani suna da ba wani mahalukin da ya taba kiranta dashi “Ziyaaaa” sake kwantawa tayi a bayanshi ta girgiza kai tace “No,  i wont let go,  Never (ba zan barka ba,  ba zan taba barinka ba)”.

Shikenan ta gama kashe jiki,  be so be so ya yarda,  amma tausayinta yaji,  karo na farko  da tausayin wani abu ya darshe shi.

 

“Your Plans,  dont let het ruin it” Sashen zuciyarshi ta tunasarshe shi,  da karfi ya banbareta daga jikinshi ya yasar da ita a kasa yace “kar ki sake tabani,  kina so kisan what changed? Zan gaya miki,  ban taba sonki ba,  i cant love you” dariya me hade da kuka takeyi tace “karya kakeyi,  biglie,  ban yarda ba ba zan kuma yarda ba,  kana sona,  shiyasa ka sa akayi bikinmu cikin kurarren lokaci,  you  cant wait to have me,  shiyasa aka aura maka ni cikin kwana biyu,  kana sona, so mai yawa, you love me that much” Zaid ya girgiza kai irin na tausaya makin nan yace “You are even more stupid than i thought, dont you get it? Ko da yake diyar Mamanki ce ke, bakwa ganewa, to barin gaya miki Na aureki ne don na Wulakanta ki, na tozarta ki, na Aureki ne don na dau fansa, wanda so far ina ganin da kyau, na Aureki ne don na kuntata miki da mahaifanki, baki fara ganin wulakancin ba? Na kawo ki Gidan da kuke takama naku ne a da, it was never yours, i took back whats rightfully mine”.

 

Girgiza kanta takeyi tana kuka tace ” Karyane, wallahi kana sona, i refuse to believe all this, ka nuna min ingantacen so, ba zan yarda ba, in ma kana da wani unfinished bussiness da su Mummy ne, i dont care, ku zauna kuyi settling din kanku, ku yafe ma juna, amma kar ka min haka , donAllah kar ka min haka” Zaid yayi fuskan tausayi yace “Awwwn, My Poor Wife, ba kyason Mijinki ya barki ai?  Congrats Ba zan barki ba, amma zaki so mu rabu, duk da ba zan rabu dake ba sai na tabbatar na muku tabon da ba zaku taba mance ni ba” ya tsugguna ya dau jakkarshi ya fice daga parlorn ita kuwa rushewa tayi da wani irin kuka mai ratsa zuciya.

 

A cikin Mota ya zauna ya dinga sauke ajiyar zuciya da karfi, kanshi ya dau chargi, In ranshi ya baci, abu daya kawai ke kwantar mai da hankali in ya shiga irin yanayin nam, da sauri ya fita ya bude booth, Akwatin Armstrong ya bude, Gwangwanin Giya sun kai goma daga gani masu tsada ne, ya dauko daya da karfi bude lid din zai kafa kai ya sha.

“Zaid Alkawarin da ka mun kenan?” Ya rantse da Allah muryan Babanshi Sadam yaji a kwanyar kanshi, da wani irin murya kamar fatalwa, da sauri ya wurgar da Giyar hannunshi ya fada Mota  ya latsa horn aka bude mishi gate da sauri, ya fincika Motar da karfi ya fita daga Gidan, Driver dinshi da Odile suka shiga wata Motar suka bi bayanshi a guje.

Saida ya kusa Minti 50 yana zagaye garin Kano, kafin ya samu ya dawo daidai, daga bisani ya buga tsaki da karfi? Meye hakan to?” Armstrong ya kira ya bashi umurnin ya wuce Airport Direct.

°°°°°°°

Har wurin k’arfe biyu tana nan yashe a inda Angonta ya barta,  zuciyarta na tukukin zafi,  bata son yarda da duk wasu magananunshi,  zata cigaba da mai uzuri har ya dawo gareta,  a yanda ta fahimci maganganunshi, Akwai wata boyayyen zance tsakaninshi da Iyayenta,  a yanda yake yada mata habaici ta gane Iyayenta sun taba mishi wani laifi, to me zasu mishi?  Zaid fa ba zai wuce tsaran YaMaji ba,  in kuma laifi suka mishi ko wani nashi meyasa zasu yarda ya aureta,  to menene? duk yanda taso gano kullaliyar da ke ciki ta kasa,  su kadai zasu gaya mata meke faruwa,  da sauri ta tashi ta nufa daki dan kiran Mommy a waya,  tana son jin komai, abubuwan da suka faru a baya kafin a haifeta,  turus ta tsaya da ta tuna wayarta na hannun Zaid,  ba kuma ta isa ta fita ba,  hawayenta sun kare karkaf,  ta fada toilet don yin Alwala don ko Azahar batayi ba.

****

 

A cikin Jirgi Armstrong  ya lura da Zaid  yayi nisa cikin tunaninshi,  ya dan tabo shi yace “Are you OK?” Zaid ya danyi tsaki yace “I’m fine” arm yace “You want to talk about it?” Zaid a fusace yace “Shut the f**kup Arm” Armstrong ya daga hannunshi sama yace “Sorry,  naye shiru”.

Duk yanda be so yayi tunaninta ya kasa,  kawai ya dauko earphone babba ya sa a kunnenshi ya kura volume duk dai don ya manta da tunanin da zuciyarshi keyi.

 

Bayan kwana biyu….

PORTHACOURT 10am

 

A daddafe yayi kwana biyun nan,  wani hali take ciki?  Me takeyi?  Ba wai don ya damu ba fa,  kar ma ayi zaton ya damu, kamar an tsunguleshi ya tashi  a zabure,  ya kira Arm,  yace “book a flight to Kano”Armstrong  yace “why?” a fadance Zaid yace “Stop Asking question  stupid,  book the goddam flight” Armstrong  yace “OK i got you” ya kashe wayan ya kira waya,  chan ya sake kiranshi yace “Sorry boss,  they’d be no flight to Kano today(saidai  kayi hakuri,  ba jirgin kano yau)” ran Zaid a bace yace “Seriously? Then get my Private Jet” Armstrong  zaiyi magana Zaid ya katse shi da cewa “Arm if you wont get me to Kano i’ll find someone who will(Arm in ba zaka kaini kano ba,  zan nemo wanda zai kaini)” cikin  sanyin jiki Amstrong yace “OK boss” Amstrong ya kashe wayan yana mamakin meke samun Zaid,  duk ya sukurkuce lokaci guda,  ya zabure yana abubuwa kamar someone that is desperate,  da wannan tunanin ya iso Gidan Zaid, Driver ya kai su inda Private Jet din ZSA yake,  kasancewar Amstrong ya iya tuk’a Jet,  shi ya tuk’a Jet din,  a hanya Amstrong  ke tambayan Zaid meyasa yake son komawa Kano da gaggawa,  Zaid yace saboda yaje a cigana da kuntata ma Ziyada,  in ba sa tare zata fi sakewa, tafi walawa,  shikuma be son ganin ta sakata ta wala, amma in yana nan zata takura ta zama cikin kunci. Armstrong ya tabe  baki,  yayi shiru da bakinshi don kar yace wani abu a hayyayako mai.

 

KANO 1pm

Abin duniya yayi ma Mairo cunkuso, komai ya tsaya mata cak ta rasa meke mata dadi. Banda tunani kala kala bata komai. Hankalinta na tashi a duk lokacin da ta kira wayar Ziyada taji switched  off, Tun auren Ziyada batasan inda aka kaita ba, tayi tunanin duniya ta gano amma ta kasa. Ta gaji da Kira wayan Ziyada don baya shiga, nan fa ta rinka surfa ma MTN zagi kala kala tana kwashe masu albarka.

Duk da haka ba ta daina trying number dinba, a hakan har charging wayanta ya kare kap. Garin masifa da rawar jiki taje ta ƙone charger saida hayaƙi mai firgitarwa ya fito.

Gefe ta koma ta rukuba tana huci, abin duniya yana damunta,  ta tambayi daddy da Abdulmajeed duk sunce basu san inda Gidan Ziyada yake ba,  duk da sun san ko ba dade ko ba jima sai ta san inda diyarta ke zaune,  Wani dabara ya fado mata taje wajen dangin oduduwa watau Hajia Ainau domin tabbas tasan inda take,  ita ta kaita dakin Miji.

Da farko tayi kememe da shawarar amma kuma saita tuna batada wani tudun dafawa, gwiwa a sanyaye ta rinka fizgan jiki har Gidan Hajia Aynarh,  ita wallahi bari dai ta gano gida ziyada, sai tace ma Zaid tana bukatar Mota don abun kunya ne a ce tana surikar Gatan Marayu kuma tana hawa Keke Napep  .

 

Babu kunya ba tsoron Allah tayi ma Hajia Aynarh  sallama a dakile  da mamaki Hajia Ainau take kallonta bata taba zaton Hajia Mairo  ta san gidanta ba,  nan ta murtuke fuska ta amsa mata sallamar ciki ciki.

“Ina wuni ina gajiya?” Hajia Mairo tace don tana son suyi su gama ta tafi gidan diyarta,

“lau” kawai Hajia Ainau tace saita cigaba da abinda takeyi wato shan kankana, batayi mata tayi ba banda danna waya na rashin dalili data soma,  don  har ranta tana kishin Hajia Aynarh.

Hajia Mairo idan ranta yayi dubu ya ɓaci amma saita danne saboda ita take neman taimako wajenta. Murya yana rawa ta tambaya Hajia Ainau inda Ziyada take.

 

“Nima ban sani ba” Hajia Ainau ta amsa mata a takaice,   Kakalo murmushi Mairo tayi saita ce, “Haba Hajia kiyi hakuri mana Dan Allah ki fada min inda take, wallahi inasan ganinta ne. ‘Yata ce kwana biyu kenan ina kiranta a kashe,  dole nake shiga damuwan rashinta,  ki gaya min please”

Ita kam Ainau halin ko ta kula tayi sai laste laste take na na’ urar bature. Mairo kam sai magiya takeyi har saida H. Ainau tace mata cikin izgili “jeki tsohon gidanku tana chan” a zatonta Gatse Hajia Aynarh takr mata,  tace “DanAllah  ki gaya min,  tana ina?” tace “Haba Hajia Mairo, ya zaki zo kina min ihu akai,  nace miki tana tsohon gidanku na GRA,  me kike so kiji bayan nan?  DanAllah ki rabu dani”

“Ban gane tsohon gidan mu ba” ta faɗa ido a warware gabanta na bugun taratara

Hajia Ainau bata ce mata ci kanki ba, nan tabama banza ajiyar ta.

Saurisauri gudu gudu Mummy ta fita daga gidan ta taro Adaidaita  tace a kaita GRA,  kuma tsakani ga Allah  ko kudin Napep  din bata dashi,  in taje ta bada.

***

A cikin kwanaki biyun nan,  wanda ya san Ziyada ya ganta ba zai ganeta ba cikin wannan yanayin,  duk ta rame ta jeme,  akwai abinci a gidan,  amma bata iya ci ko ta dafa,  bata bacci don fargaba ta ya zata kwana a gidan nan ita kadai,  sai dai bacci barawo ya saceta,  ta sha kokarin guduwa marasa imanin nan ba sa barinta fita ,  ba hanyar guduwa,  hawayenta har sun kafe,  kukan ma bata iyayi,  Ziyada dai ta koma abar tausayi, tana kan daddumarta tana Addua taji alamun an bude kofar parlo,  a guje  ta kwasa ta fita  parlon,  ganin Zaid tayi sanye cikin riga top  da ta waje da wando jeans Zai rufe kofa.

 

 

Ajiyar zuciya ta sake a guje ta rugo gunshi ta runkukumeshi tare da fashewa da kuka,”My Forever,  kar ka sake bari na ni kadai DonAllah” be son kukan nan,  aa yana so,  ta cigaba,  it gives him joy, hannu ya sa ya tureta ya wuce daki,  binshi take a baya tana tambayarshi  me zata dafa mai,  ya shiga daki ya buga mata kofa a fuska.

***

Isowarta ke da wuya,  ta ci karo da gidan makil da masu tsaro,  tace ma me Napep barin anso maka kudinka, yace “to Hajia kiyi sauri” ta wuce tana sababi,  tazo shiga aka dakatar da ita,  tace “Kai gafara chan,  matsa min in shiga” wani yace “baa shiga Hajia” cike da masifa tace “ban gane baa shiga ba” yace “Umurni ne  daga Oga,  yace kar a bar ko waye ya shiga” Hajia Mairo  ta dara tace “ni ai ba kowa bace,  ku bude ni surukar shi,  matsayin uwarsa nake” dayan yace “ku bude mata” dayan yace “baka da hankali ne? Bakaji Oga yace kar a bar kowa ya shigo  ba,  ko yanzu da zai shiga sai da ya kara jadadda mana” sukace hakane,  Mairo tace “kai bansan iskancin banza ku bude  min na shiga,  ko wallahi na sa ya koreku” daya yace “Hajia da kin kirashi kince mai kina kofar gida” nan fa daya,  da tana da numbernshi ai da taji dadi,  kuma numbern Ziayda be shiga,  tace “wayar ba chaji kaidai  kaje ka ce mishi ga Mamansu a waje” suka ce to gwara hakan, shiga dayan yayi ya dinga kwankwasa parlo,  Zaid da Ziyada  a tare suka karasa Parlorn,  shi ya na tunanin waye ke kwankwasa mai kofa,  ita kuma tana rokon Allah yasa wani dan gidansu ne.

Officer yace “Sorry Oga,  Bakuwa kukayi” yace “Uban me nace muku?  Nace kar ku bari ko waye ya shigo ko?” yace “bawanda ya shigo,  dama tace mamar matarka ce, kuma surikarka,  shine nace bari a sanar da kai” ran Zaid bace yace “ba ce muku nayi kowaye ya zo kar ku bari ya shigo ba?” police ya kalli Ziyada sai yaji ta bashi tausayi yace “Oga Mahaifiyar Matarka fa ce” cikin tsawa wanda ya tabbata Mairo taji  yace “koma uwar wacece” Jikina rawa ya juya yana cewa “OK Sir”.  Zaid ya waiga yaga Ziyada na kukan hawaye,  ya murmusa  a ranshi yace “its time” Zai ci mutuncin Uwa gaban diyarta,  ya juya gun mai tsaron yace “Ko kuma Kai,  barta ta shigo” Ziyada ta daka tsallen murna,  tana farinciki zata ga uwarta” Zaid ko Murmushin gefen kumatu yayi.

****

 

Ghen Ghen,  Zaid and Mairo,  Round one Fight.

Me kuke tunanin zai faru?

Me zakuce game da abunda Zaid ke ma Ziyada,  nima na sha hawaye na,  amma Zaid akwai dan…

 

Vote and Comment line by line,  God Bless you as you do.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

 

 

Biebee Isa

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

BIEBEE ISA

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣3⃣

 

Bude mata Gidan aka yi, ta sa kafa tana hararrarsu tana mita, “da kun san ni wacece da baku hanani shiga ba tun farko” ba su ce mata komai ba taji muryan me Napep yana cewa “Hajia,kiyi sauri donAllah” daga hannu tayi daga inda take tace “kar ka min ihu, yanzu zan aiko ma da kudinka” ta shiga fuuu tana rafka Sallama har Parlo ba ta bar Sallama ba, tana shiga ta ji an rungumeta, itama sai ta rungumeta tana farincikin jin dumin diyarta a jikinta, tana fadin “Ziyadata an zama Mace, kinyi gidan kanki, wani abun Allah ma Gidan Ubanki aka kawo ki Cikin Rashin Sani, kila in aka gaya mai ya bamu abun mu, ku kuma ya nema muku wani wurin Zama” Kuka Ziyada ta fashe dashi ta na sake rukunkumeta, Mummy tace “Ya Isa Ziyada, nima nayi missing dinki” da kyar ta samu ta bambare Ziyada daga Jikinta, Kallo daya ta mata tace “Barauban nan” ta zaro ido gami da fadin “Me ya sameki Ziyada? Ciwo kikayi?” dan guntun Murmushi tayi tace “Aa Mummy, ba komai” Mairk ta sake kallonta sama da kasa tace “To wadannan kasusuwan wuyan na uban meye? Kwana 3 kawai kamar shekara uku? Kinga yanda kika zabge kuwa? Kamar ana dibanki ana miya dake? Ba kya cin Abinci ne?” Ziyada ta fashe da kuka tazo fadawa Jikin Mairo, Mairo ta ja baya, tace “ba kuka ba, me ya sameki? Ki min magana, ba ki da lafiya ne?” Ziyada na hawaye tana girgiza kai alamun ba komai, Mairo tace “In baki gaya min damuwarki ba wa za ji gaya ma wa? Kina Missing din gida ko? Kin sa tunanin mu gaba kin hana kanki sukuni, to ai ko wacce mace dole ta bar Gida, ki kwantar da hankalinki, gobe zan sa YaMajinki ya kawo miki su Muhsin da Zinatu, yanzu dai je dauko min kudin Napep, na bar shi a waje, ai ina nan har Dare”. Ziyada ta girgiza kai tace “ai banda kudi” Mummy tayi wata ‘yar dariya, “Habadai baki da kudi, kice dai baki da chanji”

“0ya je kar6o min wurin Mijinki”.

 

Ziyada na so tace ma Mummy ga Zaid nan fa zaune amma Mummy sai sakin layi take, kamar ance ma Mairo ta kalli chan, Mummy na kallon chan cikin Parlo ta ga Zaid Zaune kan Kujera 3sitter ya hada kafa daya kan daya yana kallonsu, kululu cikinta ya kutsa, haka kurum taji faduwar gaba, kallon Mijin Ziyada da tayi daga nesa sai ta ga ya mata kama da wani kamar Abbanta, wayancewa tayi ta yashe hakora inda ta karasa gunshi tana ashe ga Alhajin nan, zama zatayi yayi saurin dakatar da ita ta hanyar cewa “Dakata, kar ki zauna min a kan kujera” Mairo tayi sauran kallonshi ta ga fuskarshi cike da gargadi, Ziyada ta karaso da sauri tace “zo Mummy, zo muje Dakina” Zaid yayi karaf yace “Haba Ziyaaaa, ya zaayi zatayi magana da Sirikinta kice tazo ku shiga daki? Hajia Mairo ai akwai maganar da zamuyi ko?” Mummy ta dara ba tare da damuwan ya kirata da Hajia  Mairo ba, ita ko Ziyada taji haushin rashin karan da Zaid ya mata, in be iya kiranta da Mummy ai gwara yace mata Hajia kawai, banda sunanta, Mummy tace “sosai ma, akwai maganganun da nake so muyi” yace “Yauwa Hajia Mairo, fadi matsalolinki in magance miki su”.

 

Zaman Dirshen tayi a k’asa kamar me rok’on gafara, Ziyada tayi saurin rintse idanu don yanda Mummy ta zube k’asa kamar Marokiya, ta fara magana “Alhaji, kamar yanda ka sani, mun samu karayar Azziki, Akwai wani manafuki Alhaji Nakowa ya kala min sharri wai ya biyoni bashin 30million bayan karya yake, sai da abu ya kaimu ga Kotu, abubuwa da yawa sun faru, har muka saida wannan Gidan da kuke ciki, ashe kai ka siya bamu sani ba, bayan wannan Yarona wato Yayansu Ziyada ba ya aiki, Babansu ma ba yayi, ko mota bamu da, yanzu duk chunkushe muke a gidan kakarsu, inda kuka zo da manyanka, a takaice dai muna cikin wani hali, babu yayi yawa, Amma Allah me share kukan bayinsa ne, ya turo mana kai a cikin Rayuwarmu, me zamu tambaya bayan baiwar da ya mana na sakoka cikin gidan Rayuwarmu?.”

 

Zaid da ke sauraron duk wani zancenta  ya Murmusa, abun nema ya samu, yace “Gidan nan na waye kafin ku saida?” da Murmushi tace “Na mu ne” Zaid yace “Ina nufin Mamalakin gidan” tace “Gidan Maigidana nane” Zaid ya ciza hakori “Are you sure?” da sauri tace “Eh, Gidanshi ne bamuyi shekara da dawowa dindindin ba, Abuja da muke zama, saboda rayuwa sai muka saida gidanmu na Abujan muka dawo Gida, ai da yake mun dade a Bariki, gwara a dawo Gida”. Ta karashe tana daria. Zaid yace ” So wurin wa ku ka   karbi Gidan, ko ku kuka gina shi, ba ku kashe wasu kun musu haye ba?” Mairo ta kalleshi a firgice, ta girgiza kai baki na rawa tace “Aa, tun asali namu ne”.

 

Zaid da ranshi ya baci amma sai ya danne yace ” Yanzu kina so na sama ma Yaronki da Mijinki aiki, kina so na dawo muku da Gidanku, kina so na siya muku Mota, na dawo muku da duk wani abunda kuka rasa, Saboda me?” tayi daria taxe “Sabida ka isa, saboda in kayi haka ba zai taba hakki daga cikin dukikiyoyin da abunda ka tara ba, sabida kafi karfin haka, balle kuma kai Mijin Ziyada ne, zaka fiddo Family dinta daga cikin halin da suke ciki” yayi murmushi yace “kina burgeni Hajia Mairo, kina da wayau” ta fara yashe hak’ora, ya cigaba da cewa “Amma ke wawuya ce” da Ziyada da Mairo suka kalleshi a lokaci guda ido a zare.

 

Ya cigaba da cewa “Ke Wawuya ce in kikayi tunanin zan taba daukar tsinke

na baku, Ke wawuya ce in kika taba tunanin zan taba taimakon ku ko da dukiyana na zuba kasa sabida yawa, Ke Wawuya ce in dama kin taba daukan Gidan nan a matsayin naku, it was Never Yours, and it will never be yours, none of anything you had was yours, nothing was ever Yours, and you are nothing but a fake manipulating,conniving,hypocritical bi**h (Gidan nan ba naku bane, be taba zama naku ba, ba kuma zai taba zama naku ba, ba wani abunda kuke dashi da da naku ne, ba ku da komai, kema ba kowa bace face Makaryaciya, Munafuka me cin amanar wanda take tare dasu,me zamba cikin aminci)”.

 

Cikin Zafin nama Ziyada ta ruga da gudu kicin,wuka ta dauko tayo kan Zaid da gudu zata chaka mai, har ta daga hannu zata chaka mai ya kama hannun ya murde mata shi da sauri ta sake wukan tare da kara, ya murde mata hannu ta baya ya sako kanshi kan wuyanta.

Hajia Mairo ta rugo gunta yace “kika matso nan sai na sa an harbeki wallahi” hankalinta tashe,  takasa fahintar maganganun Mijin Diyarta,  tsakani ga Allah bata san inda ya dosa ba, idonshi ta kalla taga ya kada yayi jazur,  rashin imani tagani kwance a idonshi,  tsaf zai iya sa a harbeta, ta daga hanayenta sama tace “ba zan zo ba,  amma please dont hurt her”.

 

Be bi ta kan Mummy ba ya fisge dankwalin kan Ziyada yayi cilli dashi  yana shishinar kanta,yana mata magana a kunne “Kina so ki kasheni? Don na fadi gaskia?  Don ina tona ma Uwarki Asiri? ba zaki iya ji ba ko My Forever? Ba zaki iya jin gaskian wacece Hajia Mairo ba, saboda you cant take it, but wallahi sai kinji, Your Mom is a Monster,  zata iya yin komai don Kudi da Shahara,  she can kill for money wealth and fame,  No she already Did, she’s a Killer,  she’s a murderer,  zata iya Kashe Yaro sa’an Zinatu,  or maybe Muhsin”.  Tashin hankalin da tunda uwata take ciki bata taba shiga irinshi ba ta shiga yau,  ba zata iya dauka ba.

 

Luuu Ziyada ta fadi kasa a jikin Zaid,  sakinta yayi ya ruga Fridge da sauri ya dauko ruwan sanyi,  kafa ya sa ya hambare Mairo da ke kan Ziyada tana kuka da k’arfi. Ya kwarara ma Ziyada ruwan Sanyi a jiki,  Ajiyar zuciya ta sake da karfi kafin ta daura da kuka me sauti,  dagata yayi ya na girgiza kai “No,  No My Forever, no, ki tashi ki gaya mata dalilin  da ya sa na aureki,  tashi ki gaya mata” Ziyada kuka takeyi ta kasa magana,  sake ta yayi ta fadi k’asa.

 

Ya kalli Mummy yace “Hajia Mairo,  barin gaya miki dalilin da ya sa na auri Ziyadarki, na aureta ne  Saboda na k’untata mata,  na kuntata maku gabaki daya,  na aureta ne saboda na mata wulakanci, wulakanci nake mata,  ran da aka kawo min ita rannan na tafi Porthacourt,  bayan na karbe wayarta,   am sure kin kirata kinji wayar kashe,  kafin na tafi na saka securities,  inda na bada Umurnin kar wanda ya shigo min gida,  itama kar a barta ta fita,  ki tambayeta gata nan,na san hurting your kids means hurting you, and hurting  you gives me Joy and Happiness (na san in an taba yaranki kamar an tabaki ne, ganin cikin  wuya da rinsti na sani farinciki da annashuwa)  babban farincikina shine na ganki ke da Iyalenki cikin Bakinciki da kunci,  everything that has happened  to you,  i enjoyed every  bit of it(duk abubuwan  da suka faru da ku,  naji dadin ko wanne daga ciki)”.

 

Mairo tace “Meyasa kake haka?  Me na maka?  Me muka maka? In laifi muka maka,  dan Adam Ajizi ne, sai mu rokeka gafara,  me yayi zafi haka Zaid?  Babanka Marigayi Sadam mutumin kirki ne,  meyasa kake haka?”.

Pillow ya dauka ya wurga mata a fuska ya nunata da hannu,  “kar na sake jin kin furta babana da dattin bakinki, baki san komai game dashi ba”

Zaid ya kalli Ziyada yace “Na sani,  Ahap i knew it,  Mamanki Dakikiya ce, ta ya zaayi ta san me ta min bayan  shes the dumbest person that ever lived(tafi kowa dakikanci a duniyar  nan) .

 

Ziyada bata taba zaton Zaid be da hankali ba sai yau, zubewa tayi a gabanshi tana kuka mai ratsa zuciya ta rungumo kafarshi, tace “Zaid, na rokeka da sunayen Allah kyawawa,  na hadaka da girma da zatin Allah ka bari,  Ya Isa haka, Enough  is Enough,  bansan meke tsakaninka da Mummy ba, ban damu ba ko ta saka mutun gabas ta yankashi ba,  ban damu da sannin zunubanta ba, we all are sinners(dukkan mu masu zunubai ne) ,   whatever she did she’s still my Mother and you will show her some respect,  ka barta hakan nan,  you can hurt me if you want for all i care,  but stay away from my Family, Please,  na rokeka don darajan Magabantanka da suka rasu”.

 

Be son meyasa ba,  maganganunta sunyi tasiri a zuciyarshi,  kanshi yayi nauyi ya dafe kanshi da hannu bibbiyu kafin ya furzar da huci me zafi,  “its not worth it” yace ma zuciyarshi, *Ziyada*,  yana da ita,  matarshi ce,  zai aje ta kusa dashi,  yayi duk abunda ya ga dama da ita, ba wanda ya isa ya hana,  Ajiye Ziyada a gurinshi zai fi bakanta mata rai,  zata dandani zafin raba ‘ya da Mahaifiya, kamar yanda ta rabashi da nata iyayen,  gwara shi ya san sun mutu ba zasu dawo ba,  amma ita zata dandani jin zafin rashin diyarta alhalin tana raye, tunanin ya take?  Wani hali take ciki?  zai kasheta, zai rabasu,  ba zata sake ganinta ba.

 

Da wannan tunanin ya matso daf da Mairo yace “ki tashi,  ki tashi ki bar min Gida,  kar na sake ganinki kusa da Gidana,  ka.  naku a Unguwar nan,  kika bari wani yazo Unguwar nan,  zan sani,  and i will come for you all”

Mairo tayi Jim, tace “ka sake Ziyada,  na tafi da ita,  zamuyi disappearing daga rayuwarka,  ba zamu taba showing kanmu a gabanka ba” Murmushi  ZAID yayi yace “Ni na nemeku,  ba ku kuka nemeni ba,  you cant disappear from my life, Sakin Ziyada kike so nayi?  Zan saketa a lokacin da naga dama,  but for now,  she stays with me,  so ki bar Gidan nan at once,  kafin a fiddaki dole”.

 

Ita ta san gardama da Zaid aikin banza ne,  kai shi kotu kamar ta hak’a kabbarinta ne ta shiga da kanta,  bata da wani karfi ko wani abun da zai sa tayi going against him,  karawa dashi kamar suicide ne,  ba zatayi wannan gangancin ba balle da ta san Ziyada na hannunshi,  ba zatayi kuskuren nan ba,  Kan guiwowinta ta zube tana kuka, Ziyada tace “Mummy ki tashi  please” tace “Ziyada,  zanyi komai a kanku,  durkusawa gabnshi ba komai bane,  Zaid ina rokonka, kayi hakuri,  ka yafe min, na hadaka da Allah kayi hakuri,  kar ka rabani da Diyata,  kaji tausyain wannan Uwar,  Diyarta kawai take so a kusa da ita,  kafi mu karfi,  kafi mu iko,  ka tausaya mana, zan jure rashin komai,  banda rashin ‘yayana, komai kake so zan maka,  kar ka rabani da ita please”.

 

Anzo gurin, Ran Zaid bace idanun nan sun kada sunyi Jazir cikin tsawa yace “Ashe ba dadi?  Iye ashe ba dadi?  Ashe da zafi? An rabaki da diyarki,  ashe abun da ciwo?  To ai abunda kikayi ne aka miki,  Tarihi ne ke maimaita kanshi, Ha!  Karma issa bitch huh?(K’aikayi ne ya koma kan Mashek’iya ko? ) Thats what u do,  in kin manta barin tuna miki,  You turn Brothers  against Eachother(Kin raba kan yanuwa) , you turn Child against his own Mother (kin juya Da Kan Uwarsa Mahaifiya)  You Seperate Child from his parents by killing them(Kin raba Da da Mahaifanshi,  ta hanyar kashesu),  so don an rabaki da Diyarki i think ba wani abu bane its fair Enough”

Saura kadan fitsari ya kubce mata, wasu abubuwan  da suka faru shekaru sama da 20 suka fado mata,  cikin sakwan da be wuce talatin ba ta gama nazarin maganganunshi,  brothers against brothers yana nufin Abba da Sada kenan, Son Against his own Mother yana nufin  ta juya Abba kan Hajjo kenan,  da kuma Seperating Child from their parents wato ta raba Zaid da Iyayenshi, amma ita ta san bata kashe kowa ba,  wanda taso kashewa kuma ai guduwa– bata karasa tunaninta ba ta dago rinannun idanunta ta kalleshi, bakinta ta rufe da hannu bibbiyu tana girgiza kai a hankali ta furta *”ZAID. “*

 

Murmushi ya sakar mata,  da sauri sauri ta dinga ja da baya da baya ta fita a guje Ziyada zata bi bayanta yayi saurin chafkota,  ya hadata da jikinshi,  da sauri ta ture shi tace “Mugu Azzulmi,  Allah ka saka mana” ta ruga daki a guje ta sa key  ta fada a gado tana cizgar Kukan da bata taba zaton ta taba irinshi ba tunda uwata ta haifeta.

 

Tafiya take kamar Guguwa,  bata san inda take jefe kafarta ba,  kamar wata Mahaukaciya sai sambatu take; “Hajiya Ji mana” cewar Mai Napep din da tunda ta fito daga Gidan yake binta,  banza tayi dashi,  Parking Adaidaitan shi yayi ya fito,  ya biyota,  pincikota yayi suna fuskantar juna yace “Ko ki  ban Kudina wallahi tallahi ko na miki zindir na miki wanka da ruwan kwata a nan gurun” Mairo ta tsura mai ido,  bata gane kalaman da ke fitowa daga bakinshi,  kawai sai ta juya ta barshi,  Mai Adaidaita  cikin Zafin nama ya sha gabanta ya dauketa da Mari, nace “ki ban Kudina ko na miki bugun burauba” Hawaye suka shiga sunturi a kunatun Hajia Mairo,  ta kalli yaron sama da kasa,  ko ya Girma Zaineema  da kadan ne, amma sai ya daga hannu ya mareta?” ta girgiza  kai tayi gaba,  Mai Adaidaita ya sake hasala,  ya finciko Mayafinta ya wurgar k’asa,  yace “kin zata wasa nakeyi ko? Wallahi zindir zan miki in baki ban kudina ba” nan ya shiga kiciniyar cire mata Riga, daidai nan wata Dalleliyar Mota ta tsaya a gefensu,  “kai Assha,  Lafiya?” cewar wani Magidanci da ya fito daga Motar,  Mairo Kunya kamar ta bude kasa ta shiga,  Mai Adaidaita yace “Kawai Alhaji,  wannan Matar ta sa na dauko ta daga Sharadda Phase 2 na kawota nan,  sai  cewa tayi bari ta shiga ta kawo min kudina,  na fi karfin Minti 40 tsaye nan ima jiranta,  yanzu ko ta fito ta kama gabanta ina cewa ta ban Kudina tayi banza dani” Mutumin ya girgiza kai yace “nawa ne Kudinka?” yace “600 ne” Mutumin ya zaro dubu daya ya bashi,  Mai Adaidaita  ya ciro dari 4, ya bashi,  ya kalli Mairo yace “Allah  ya soki wallahi” Mutumin yace “shikenan dai tunda an biyaka” ya shige Napep dinshi ya ja ya wuce,  Mutumin ya kalli Mummy yace “Hajia, ya akayi ne?” Mummy ta dago ta kalleshi,  a tsorace mutumin ya zaro ido yace “Subhanallah, Hajia Mairo, dama kece?  Ya akayi haka?” ta rasa abunyi sai kawai ta fashe mai da kuka,  yace “Inallilahi,  Hajia,  kiyi hakuri kiyi shiru,  ina Alhaji Abba?” ta daiyi shiru,  ina Abdulmajeed,  nan ba amsa,  yace “to ki shiga in kaiki Gida” ta tirje taki motsi,  da Baban Ikhy ya ga zata bata mai lokaci kuma Jiranshi ake a wani gu,  sai ya ciro Kudi dubu 2 ya makala mata a hannu,  yace “sauri nake,  zan kira Alhaji Abba, ki samu Napep  ki hau danAllah” ya shige Motarshi ya tada ya wuce yana waigenta ta Madubi.

 

Baban Ikhy Makocinsu Daddy ne a lakacin suna Anguwar nan,  ko da zasu tashi,  ko sallama Mairo bata shiga tayi ba,  sai da wata rana Baban Ikhyn ya kira Daddy yace “ya bar ganinsu a Masallaci ko sunyi tafia ne?” cike da kunya Daddy ya gaya mai ai tashi sukayi,  abun yazo cikin gaggawa shisa ba wanda ya sani.

Akan hanya Baban Ikhy ya kira Daddy ya sanar mishi da abunda ya gani game da Mairo,  Daddy  yayi Godia sukayi Sallama, dama Hajia Aynar ta sanar dashi yanda sukayi da Mairo,  a ranshi yace “nasan a rina shiyasa naki gaya miki inda take tun farko,  ba inda zani,  ina nan zaki dawo”.  Gyara zamanshi yayi ya cigaba da karatun Jarida.

 

Kusan Awa 2 suka shude Mairo bata dawo gida ba,  har Daddy ya soma damuwa, ya gaya ma AbdulMajeed abunda ake ciki,  hankalinsu ya tashi,  yace “Daddy da tun dazun ka fada da na hau Adaidaita  naje,  kasan Mummy in abu na damunta” Daddy yace yanzu dai muje, Zaineema da sauran yaran sukace zasu bisu,  Daddy  yace “aa ku bari muje,  ku tsaya a nan incase ta dawo sai ku sanar damu” suka gyada kai cikin damuwa,  Zinatu  kam har ta fara kuka,  Najwa na lallashinta, a daidai kofar shiga da fita  Gidan Mummy ta shigo,  suna ganinta suka hada baki gun cewa “Alhamdulilah” kamar jira take ta saka Ihu mai karfin tsiya tare da zubewa kasa tana tirjiya,  cikin tashin hankali duk sukayi kanta.

••••••••

 

Ghen Ghen, To kunga abunda ya faru a Page dinnan,  Me zakuce game da karon Zaid da Mairo?

Ko Mairo ta Haukace ne?

 

Yeah, Yeah I know Zaid baya kyautawa Ziyada,nima ban jin dadi, amma Zaid zai shiga hankalinshi soon i promise,  me zai karkato da hankalin Zaid kan Ziyada?  Guesses?

 

Wai ina Labarin Mutanen India?

 

#NajwaMajeed?

 

Heheheh i cant wait to start typing the next Page, but i’ll type IF naga number of Votes na Increasing.

Vote and Comment Line by Line.

 

#1love

#ADAY

#Bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa.

 

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIEBEE ISA

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣4⃣

 

Bin bayan Motan Baban Ikhi tayi da kallo kamar tana kallon TV har sai da ta daina ganin kurar Motar, kan dakalin wani Gida ta zauna ta rafka uban tagumi ta shiga duniar tunani;

Maganganun Mijin Ziyada marasa kan Gado, yana maganan ta kashe mutane, duk iskancinta ai bata taba kashe rai ba, da yake magana kamar ya santa, ai ko a da ita ta san bata kashe Sada da Yesmin ba, ba zata iya kashesu ba, ta san ta musu Kurciya sun bar k’asar gabaki daya kuma ba zasu taba dawowa ba, Zaidun Yesmin kuma tana da tabbacin mutuwarsa daga bakin Mallaminta wanda shine ya ma su Sada Kurciya, Iyakacin abunda ta san tayi kenan, so bata ga ta inda hakan ya shafe shi mijin Ziyadan ba.

 

Tambayoyi zuciyarta ta fara jefo mata”To shi wannan Zaid din wanene? Meye hadinshi da su? Ta ya akayi ya san Tarihinta? Ko dai Coincidence ne?” da sauri ta karkada kanta “Babu yanda zaayi ace wannan shine Zaidun Sada, Guiltiness kadai ke addabar Zuciyarta, ba wani Zaidun Sada, wannan be da wata alaka da Dan K’anin Mijinta, kowa ya san Mahaifinshi Sadam Audu Gatan Marayu, ba shi bane ta fada tana jin hakan na zama a Zuciyarta, Zuciyarta ma bata so ta sa abun a ranta ballantana ta yarda da hasashen da a baiyane yake, Zuciyarta ta karyata mata duk wani tunanin da yake kawo mata, ga zahiri tana gani, amma ta rintse ido tace ba haka ba, Zuciyarta na gaya mata karya, taki yarda ta amince da gaskiar da yake a baiyane, bata so ta yarda da zahirin gaskia, Zuciyarta ta dinga gaya mata abubuwan da take so ta yarda dasu.

 

To shi wannan Zaid din me yake so? Meyasa ya gaya mata bakaken maganganu? Meyasa ya ke son rabata da Ziyada? Hankalinta ya tashi ainun da ta tuna Ziyada na gurinshi, kuma yana so ya musu farraqu, hankalinta ya tashi da ta tuna Zaid ya fi karfinsu, Zaid fa qya linka Alhaji Nakowa so dubu dari, ta kasa karawa da Alhaji Nakowa ina zata fara da Gatan Marayun da Arzikinshi ya karade Afrika gabaki daya? Tata ta kare,

Nan hankalinta ya sake tashi, ita ba wannan ba, ita dai ta samu Ziyada ta dawo garesu, hankalinta ba zai taba kwanciya ba sanin Ziyada na tare da wannan Mutumin me kyaun dan Maciji, hankali tashe ta nufa Gida don su samo Mafita.

****

 

“Mummy Don Allah kiyi shiru, ki bar Ihun nan haka”cewar Abdulmajeed cikin damuwa, kamar an kara ingizata ta kara fasa wani ihun, Hajjo tace “Hajia, komai yayi zafi maganinshi ALLAH, ki yi ta sallalami, ko menene zai zo miki da sauki, Daddy ko ya gama kulewa matuka da wannan iface ifacen da mummy keyi ya zata ganin Ziyada a gidansu na da ne ya sata hauka haka, cikin bacin rai yace “Haba Maryam, Haba Maryam, me kikeyi haka? Ke wai yaushe zaki girma ne da in abu ya sameki ki daina Ihu? Kin tasa yara gaba kina Ihu, me kikeso ki yi? ki daga musu hankali? Nima ki daga min?” cikin kuka tace “don ba kaga Halin da Ziyada take ciki bane da baka tsaya nan kana min fada ba” da sauri suka hada bakingun cewa “Me ya samu Ziyada?”duk suka maida hankalinsu gunta ta ja majina tace “Mun aura ma Mugu ita, ya na son raba mu da ita, bayan ya siya Gidanmu dan cin fuska ya kaita Gidan, yanzu kuma ya saka jamian tsaro, wai kar wanda ya zo mishi Gida ita ma ba zata fita ba, kuma ya karbe wayarta”..

 

Jikin Majeed ya fara rawa, Daddy ya samu bakin cewa “to saboda me?” Mairo ta karbe tace “Ohon ma Shegen, wasu surutai yake tayi marasa kan Gado, ba ku ji bakaken maganganun da yake ta gaya min ba kamar na kashe mai wani, tsanarmu a fuskarshi nake ganinshi, ya yaudare mu da halaiyanshi na gari, ashe kyaun dan maciji ne, gabanshi fari cikinshi bakikirin,da alamu dan shayeshaye ne don sai da yayi tatul ya zo ya tata min rashin mutunci, Ziyada harda Suma”.

 

Abdulmajeed hankali tashe yace “to wai duk saboda me? Me muka mishi Mummy? Ko be yarda damu bane? Ko zaton makwadaita yake mana shiyasa yake son ya rabamu da ita? Wallahi ba ruwanmu da abunda ya tara, in gani yake Auren kudi mukayi mata wallahi yayi kuskure, Mummy ni fa ban ma gane ba” Mairo tace “da ba gabana akayi ba da nace karya ne, ni bansan meyasa yake haka ba, bansan me muka mishi ba, wai randa aka kaita Porthacourt ya tafi, Ziyada kadai ta kwana cikin wanann wakeken Gidan” Daddy ya jinjina kai cikin tausaya ma diyarshi yace “ga Ziyada da tsoro baiwar Allah”.

Mummy tace “wai be taba sonta ba, wai be aureta don so ba, ya aureta ne don ya mata wulakanci” Daddy yace “Maganar banza da wofi, in ya san be sonta meyasa ya Azazzala sai ya aureta cikin kwana biyu? Meyasa ya tado manya masu fada a ji a Nigeria suzo neman mishi Aurenta? Kuma na san in ba da dagaske yake ba Alhaji Ado ba zai bata lokacinshi ya dauko Aminanshi suzo neman aurenshi ba, ba kuma za su kashe kudinsu a banza ba, har dai bashi suka biya mana na Miliyan25 muka rabu da Alhaji Nakowa for what? Ba don shi sukayi ba? Nidai banda komai balle ace wani abu suke nema a guna shiyasa suka zo neman Diya wurina, in Kudi ne ai su ne Kudi, to maganar be aureta don So ba be tashi ba, in laifi aka mai ai sai ya fada ayi sulhu, in kuma misunderstanding ne sai a zauna a tattauna har a gano inda matsalar take, amma Koma dai menene harda Yarinta”.

 

Abdulmajeed yace “nidai bari inje Gidan inga halin da Ziyada take ciki” Mairo tace “wallahi wahalar banza zaka sha, tunda kaga na dawo ba tare da Ziyada ba kasan cewa abun yafi karfina, Ihun nan da kuka ga ina yi, na takaici ne, na takaicin diyar mu na cikin wani hali bamu da yanda zamu fito da ita, bamu da abun da zamu iya yi, sai dai mu nemi sauki daga gareshi”. Nan sukayi jugunjugum, har dai Abdulmajeed ya mike yace “hankali na ba zai kwanta ba har sai na san halin da take ciki” Daddy yace “Muje mu ga” Mairo tace “sai kun dawo” tana rungume zinatu da duk suke ta hawaye ita da Zaineema da Hajjo.

 

Tausayin Ziyada ya kama Najwa da ke rungume da Muhsin tunda Mummy ta shigo tana ihu shima ya fara kuka, itama Najwar kwalla take, Muhsin ya tashi yaje gun Mummynsa ita kuma Najwa ta shige daki don ta basu gu don jajanta ma juna, Daki ta koma tana tausaya ma Ziyada, mamakin Mijin Ziyada take, wai dama shi ya siya Gidan, don rashin kirki ya kai diyar chan? Kuma yana son rabata da danginta, kuma ya wulakanta Mummy? Ziyada harda Suma kuma har yace be taba sonta ba yanda Ziyada take mutuwar sonshi? “How can someone be So Heartless?” ina ma zata iya fitar da ita daga kangin da take ciki, saboda Ziyada ta taimaka mata a wurare da dama, ita haka take bata son taga wanda take tare dashi ya shiga damuwa, haka kurum ta fashe da kuka sanin yarinyar da take sonta kuma kanwa ga Jaan dinta na cikin wani hali kuma ba abunda zata iya yi game da hakan, sosai take kuka kamar laifinta ne, a wannan hali Maaman ta ta kirata.

 

I N D I A

 

Maama ta bude murya tace “Papi, kayi sauri ka fito, lokacin waya da Najwa yayi” jim kadan sai ga Paapa ya fito tare da shagwabe fuska yace “haka jiya kika kirata bana nan, sai dai daga baya na kirata kuma har ta fara bacci” tayi daria tace “sorry Papi, gani nayi ba zan iya jiranka ka dawo daga Aiki ba, amma daga yau ba zamuyi waya baka nan ba” yace “yauwa Yesmeenah, oya kirata” ta danna kiran wayan Najwa gami da sa handsfree.

Haka suke a daidai wannan lokacin suke kiranta su ji ya take, in tana da bukatar wani abu, sun fi so su kirata don ita ba zata juri kiran India ba don charges din akwai yawa, ringing biyu ta dauka da Sallama,

Jin muryarta a disashe yasa Maama tambayarta meke samunta? Ko bata lafiya ne? A takaice ta ba Maama labarin halin da Ziyada da Family dinta ke ciki, sosai Maama ta jinjina labarin, tana me tausayawa ma Ziyada kuma tana me kyamatar Mijin Ziyadar ta kuma lallashi Najwa tace ta bar damuwa, ta tayata da addua shi ta fi bukata.

 

Najwa ta gyada kai kamar Maaman na gabanta ta share hawayenta tace “Maama kiyi Hakuri, kuyi hakuri Please, i am so sorry, i’m useless wallahi, its like kamar nazo hutu ne Nigeria, har yau na kasa cika promise din da na miki, bansan ta inda zan fara ba, abubuwa da yawa sun faru, i’m lost, duk sanda nayi niyyan fita fara neman Bhaiyya na, sai wani abu ya faru da su Abdulmajeed, shine dama zai taimaka min, and its not right suna cikin wani hali kuma in fito mai da bukatana, ina so komai yayi settling ne, ku kars hakuri”.

Maama tace “Najwa Diyata, Allah ya miki Albarka, Allah ya saka miki da Aljanna Firdausi, amma ina so ki dawo Gida, na hakura, hawayena kike so su tsaya? To wallahi sun tsaya, in ba so kike hawaye na ya cigaba da flowing ba to ki dawo Gida, hankalina zai kwanta in kina tare dani, hankalina be taba kwanciya ba tunda na san cewa kina Nigeria cikin mutane irin su Mijin Ziyada, na yafe please, come back home” ta karashe tana shesheka, itama Najwan Kuka takeyi tace “Maama, Please hang on a little longer, zan dawo Gida Safe InshaAllah, i’m in safe hands, zuwa Karshen Month dinnan in ban ganshi ba zan Dawo Gida, I promise”.

Paapa yace “Najwa, Nigeria na da 36states, and atleast 774 localgovernment area, ta ina kike son fara neman shi? Da me zaki fara nemanshi? Hoto? Wannan hoton fa Zane ne, wa zai ganeshi? Ki ji Maamanki Najwa ki dawo Gida, ana ta wuceki a School, ki dawo Please” Najwa cike da tausayi da son Mahaifanta tace “Paapa, support dinka nakeso, ka kwantar ma Maama hankali, i know he is still out there lonely and alone, ku dan karamin time din da nace, karshen Month din nan, in ban ganshi ba, i am coming home, i promise, Kaji Paapa na? ” Paapa ya suake Ajiyar zuciya tare da kallon matarshi ta gyada mai kai alamun ta amince, yace “You have till end of this Month” da dan dariyarta tace “Thank You Paapa, I love you Both”.

*

N I G E R I A

 

Tunda ta shiga daki take ta cizgar kuka kamar zata fitar da idanunta saboda Kuka, wannan wani irin Rayuwa ce? Wannan wani irin abu ne? Bata taba zaton akwai Mutane Irin Zaid ba, tana jinshi ya shigo, tayi banza dashi, duk da Zuciyarta na mata kuna, bata so tana shareshi, da tana da yanda zatayi ta cizge son shi daga ranta da tayi hakan, “tashi ki zauna” ta ju muryarshi cike da umurni, burus tayi dashi, “in baki tashi zaune kin bar Kukan nan ba, zan ma Ya Gidanku abunda ya fi na yau” da sauri ta tashi zaune tana sharar hawaye tana girgiza kanta “DonAllah kar ka musu Komai, na tashi” a wulakance ya kalleta ya watsar, ya fita daga dakin.

Komawa nashi dakin yayi ya zauna, ba wai kukan ne ke damunshi ba fa, kawai ta cika mai kunni da ihu ne, be son damuwa, wayarshi ya dauka yana Waya.

 

Tunda suka iso Unguwar suka hango Motan Jamian tsaro a gaban Gidan, Daddy ya kalli AbdulMajeed, suka karasa garesu da Sallama, musulmin cikin ne ya amsa, Daddy yace “munzo ganin MaiGidan ne” yace “to ku kirashi a waya” AbdulMajeed yace “kuce mai Mahaifi da Wan Matarshi ne” yace “Aa ai ku zaku kirashi kuce mai kuna Kofar Gida, mu ba ruwanmu, Aikinmu shine hana fita da fice a gidan nan, ko waye yazo, dazun ma dan shi yace a bar Mamarta ta shiga shiyasa aka barta, amma da ba haka ba” Daddy yace “ku taimaka ku sanar dashi zuwanmu” nan sukayi biris da lamarin, Wayarshi Daddy ya ciro don kiran Alhaji Ado ya sanar da shi halin da ake ciki, amma wayarsa Kashe(kasancewar ya bar kasar). Sun kusa Awa Biyu a kofar Gidan, ganin mutanen nan ba wani tausayi ko imani tattare da su yasa Daddy Lallaba AbdulMajeed kan su tafi, ba don ya so ba su ka tsaida Adaidaita suka bar Unguwar.

 

Bayan Maghrib

 

Ganin kuka ba zai fissheta ba ya sa ta tashi ta fada wanka, tayi alwalan maghrib kafin ta fito ta shafa mayyukan da ke gaban dressing mirror dinta, bude daya daga cikin Akwatinan da Anty Taatuh ta shigo dasu a ranar da aka kawota tayi, bata taba budewa ba sai yau, dama ina kwanciyan hankalin dubawa, Akwatin cike yake da dogayen riguna, da kananun kaya irin na matan turawan nan, ta bi wata riga  navy blue color me torches din re da kallo, ta dauka ta daga ta na duba tsawon jikin Madubin Wardrobe dinta, iyakar rigar guiwarta, hannun dan guntu ne, ta ina zata fara sa rigar nan? Ai da kunya, ta ma saka taje wurinshi ya wulakanta ta? Amma fa na zaiyiwu su cigaba da zama haka ba har karshen rayuwarsu, dole ita zata kokarta wurin karkato hankalin Mijinta gareta duk da ba abu bane me sauki, ta kan gani a littafan hausa Mazaje masu tsaurin raayi, ta hakan ake shawo kan wasu, tasan this is reality, amma zata gwada ko Allah ya sa ta dace, tana son Mijinta, kuma zata iya hakuri dashi in dai har zasu zauna lafiya.

 

Saka rigar tayi ta daura zani a kai tayi sallahr Maghriba, tana kan dardumarta taji kiran Sallahn Isha’i, ta tashi tayi Sallahr ishai, ta hada da shafa’i da wutir, ta zauna tana jera ma Allah Kirari, tana adduar Allah ya kawo karshen komi ya basu zaman lafiya da Mijinta, Allah kuma ya kwabe Fitina tsakaninsu, a karshe kuma ta kara da Allah ya daidaita tsakanin su” ta shafa. Ta mike ta linke hijab da zanin da tayi sallah. Ta sake shafe jikinta da turarruka masu k’amshi ta gyara fuskarta, dan jambaki ta zizara a baki, ta sake kallon kanta a mirror, sosai rigar yabi jikinta, ita ta san tana da kyau, ko da bata shafa jambaki ba, ina ga ta shafa.

Sai da ta shiga Kitchen ta dafo ruwan zafi  da kayan shayin da ta gani a wajen, bayan ya tafasa ta sa a wani Jug me kyau, ta dauko saucer kalan jug din ta hada mai, ta dauko tayi dankin Oga.

Nan gabanta ya fadi da ta tuno wurin wanda zata je, jiki na rawa ta fita daga dakinta, tana karanto adduar shiga gida bismillahi walajna.. Bata san ko ya dace ta karanta shi ba ita dai ta karanta, ta murda k’ofan da Sallama.

*

 

Ko Darduman da ya idar da Sallah be ninke ba ya hau kan Gado yana Waya, inda aka kirashi daga Maaikatarsa ta Bauchi, wai ana bukatar shi a Maaikatar saboda wasu clients da suka samu daga London, karamin tsaki yayi yace “kuma dole sai ni? Ba gaka ba? Or Zan turo Faisal” Cike da ladabi mutumin yace “Oga sai dai kayi hakuri, sunyi insisting sai sunga CEO din company din ne” Zaid ya buga tsaki yace “matsalarsu, in representative dina ba zaiyi tending dinsu ba, they should forget it” yace “Oga, zaiyi causing dinmu Millions of Pounds” Zaid cikin daga Murya yace “I dont care” Manager ya kwantar da kai yace “this is the Company your Dad spent his time and energy Building, ba zaka sa muyi asarar nan ba” Zaid ya rintse Ido ya bude ya sauke su kan Ziyada da ta shigo yanzun da Sallama hannunta rike da tray, kallonta yakeyi kallon kurilla, be san me yakr tunani ba, ji yayi Manager na cewa “Oga, are you there?” cikin sanyin murya Zaid yace “Yes i’ll see you Tomorrow” ya kashe waya ya mik’e tsaye ya na kallon Ziyada, kallo yake binta da shi, kallon da be san na menene ba, takawa yakeyi a hankali har yazo gabanta, sansanyar murmushi take binshi dashi, tana murnan Zaid ya fara dawowa kan hanya.

 

Ba ta ankara ba sai jin wani irin Zafin da bata taba sanin akwai irinshi ba akan kafarta, wani tsalle tayi ta ja baya, sai a sannan take jin muryan Zaid na cewa “kar ki sake shigo min daki, dan gulma harda hado min Tea, waya san irin Asirin da ke ciki? Da da ki ka kawo ni kike son na sha? Ki kara gobe a jiki zan watsa miki, sai sannan ta lura da ba sakin Jug din tayi ya fadi a kasa ba, shi Zaid din ne ya dauka ya kwarara mata a k’afa, murmushin takaici tayi ta share hawayen da ke fuskarta ta kalleshi da jajjayen idanunta tace “Ba a horo da Wuta Zaid” ta ajiye tray din kan wani drawer da ke gun, ta fita daga dakin da gudu, binta yayi da wani irin kallon da be san na meye ba.

 

Toilet ta nufa ta sake ma kafarta ruwan sanyi, tun daga guiwanta har kasan kafafunta, kuka take me taba zuciya ganin yanda kafar tayi Ja, tasan in ta shafa ko ta sosa kafar zai tashi ya ja ruwa, kuka take tayi, bata da abunyi da ya wuce ta zuba ma wurin ruwa, akwai radadi, ta dau lokaci me yawa a toilet kafin ta fito ta cire rigar jikinta ta saka Nightgown, ta kuddura a ranta, in Allah yayi duniya don Manzo ta fita harkan Zaid kenan, Allahn da ya jarrabeta da sonshi shi zai yaye mata” tana jin zafi ta hau Gado ta kwanciyarta tare da jan bargo a jikinta, tun tana kuka har bata san Lokacin da bacci barawo ya saceta ba.

***

 

2:35am

 

*”ZAID” yaji wata kakausar murya na kiranshi, ya dago ya kalli fuskar a razane, fuskar da ba zai taba mantawa bane, fuskar Babanshi , Gatanshi, baki na rawa yace “Baba” cikin tsawa yace “kar ka sake ka kirani da wannan sunan, ni ba Babanka bane, ban taba haihuwa ba, banda da, dana sani na barka a inda na tsinceka, da na sani, da ban baka duk wani jin dadi na rayuwa ba, na baka gata, na baka suna na, na baka duk abunda kake bukata don ka zama good example gurin mutane na kasa da kai,  ban raineka ba, ban baka duk abubuwan nan ba don ka zama Jahili ba, ban bar maka tarin dukiyata ba don kayi amfani dashi wurin hanyar banza ba, nuna karfi da isa a kan na k’asa da kai ba, kana amfani da dukiyar dana bar maka ta hanyar banza, Zaid i’m so disappointed in you” Kuka Zaid keyi kamar ranshi zai fita, “Babana, ka min afuwa, ka yafe min, na tuba wallahi” Kuka sosai Zaid keyi, daga bisani yace “zan yafe ma da sharadi daya” da sauri Zaid yace “ko ma menene zanyi wallahi” Baba yace “ka chanza halinka for good, ka rungumi kaddararka, ka nemo yafiyan wanda ka sa6ama wa, matarka, she’s innocent” kafin yace wani abu bat Baba ya 6ace mai*.

 

Daidai nan Zaid ya farka daga baccin da yakeyi, duk da AC da ya karade dakin Zaid be fasa zufa ba, zufa yakeyi sosai, kunna hasken wayanshi yayi ya duba lokaci, Yasan Mafarki ba gaskia bane, amma meyasa zaiyi mafarki da Baba? Hankalinshi ya tashi, da ya tuna yanda sukayi da Baba, a hankali ya sauko daga kan Gado ya zura takalmanshi ya fita daga dakin, dakin Ziyada ya nufa, yaci saa a bude yake, ya kunna hasken dakin ya karade ko ina, chan karshen gado ya ga ta rakube tana bacci, jefi jefi tana sauke ajiyar zuciya me nauyi, wani abu da be san meye ba ya dirsa a Zuciyarshi, a hankali ya hau kan Gadon ya yaye bargon da ke rufe a jikinta, ya kai dubanshi kan kafarta, nan yaga kafar ta fara jan ruwa, da sauri ya sauka ya je dakinshi ya bude firstaid box ya dauko wani ointment, ya dawo da dan sauri ya hau kan gadon, k’afarta ya daura kan cinyarshi ya shiga shafa mata Man a kafa, ya dau lokaci yana yin haka, kafin wani abu ya cizgeshi yayi saurin jayen kafan ya aje kan gado, ya gyara mata kwanciya ya rufeya da bargo ya kashe wuta ya fita.

 

Kafin safe kafar Ziyada ya ja ruwa ya tashi, ita kadai ta ja kafarta toilet don hawayen sin dauke, tayi alwalar asuba, a zaune tayi sallah saboda sujada, da kyar ta kasa komawa tayi bacci saboda kafanta na zugi, har wurin karfe 10, ganin yunwa zai mata lahani ya sa ta fitowa tana jan kafa, daidai nan Zaid ya fito da jakka me kama da School bag, idonshi kan k’afarta, tana ganinshi ta kara saurin tafiyarta tana cije baki ta shige kitchen, tsayawa yayi na kusan minti 2, kafin yayi tsaki ya wuce ya shiga Motarshi inda Driver ke jiranshi, zai tafi Airport inda jirginsu zai tashi karfe 11 zuwa bauchi.

 

B A U C H I

6PM

 

Duk wasu reports din da ake karanto mai hankalinshi be gun, burinshi ya ganta, be san halin da take ciki ba, be san ya k’afarta yake ba, mikewa yayi kamar an tsunguleshi, zumbur yayi hanyar fita daga conference room din, da sauri Manager ya bishi, yace “Sir, you cant leave now, we are in the middle of a meeting(ba zaka iya fita ba, muna tsakiyan meeting)” Zaid cike da damuwa yace “sorry, i cant do this, i’ve got to go(yi hakuri ba zan iya ba, tafiya zanyi)” Manager yace “Turawan nan are already here, be kamata ace an tara su ba kuma a ki gabatar da taron, babanka ya so kwangilar nan, sai yanzu ta samu, da ya na nan, bana tunanin akwai wani uzurin da zai hanashi aiwatar da taron” Zaid ya kalleshi, haka mutanen nan suke, in har suna so yayi wani abu sai su fara sako Babanshi a ciki, yace abunda zanje yi “Baban ne ya sani yi” Manager yace “Me kenan?” Cigaba da tafiya yayi Manager na binshi a baya Zaid yace “ka koma kace musu nace i’m sorry i cant hold the meeting, there’s been an emergency, i need to go home to my wife, kasan su turawa yanda suke so da girmama matayensu, i’m sure they’d understand” ya cigaba da waya  “Hello Faisal, book me a flight to Kano” Faisal yace”anya akwai jirgin Kano yanzu kuwa?” Zaid ya buga tsaki yace “Never Mind” Faisal yace “Ya zakayi kenan? Sai gobe?” a takaice yace “Nope, zan tuk’a kaina zuwa Kano” Faisal yace “DonAllah aa, dare yayi, ka jira inzo na kaika, kasan Baba be son kana tuk’i in har ba cikin gari bane” Dif Zaid ya kashe wayan yana Mitan “komai Baba Komai Baba Arrgh” daidai nan ya isa gaban entrance din Reception Company, Motoci ne kala 5 a jere suna jiran fitowarshi, Zaid ya nufa inda ya shiga da zaizo ya mika ma Driver hannu Alamun ya bashi Key, zai mai Gardama Zaid ya buga mai Harara, ba Arziki Driver ya ciro Key ya bashi, ya shiga Mota ya kalle su yace kar wanda ya biyoni, ya burka motan ya fita a Sittin.

 

Yanda Hanyar Bauchi zuwa Kano a ke samun gargada, haka Zaid ya dauka hanyar nan bayan ya kashe wayoyinsa don ma su Faisal kar su ishe shi da kira, kwarara gudu kawai yakeyi, ya dade beyi tuki da nisa ba, saboda tsaron lafiyanshi ba a bari yayi tuki da kanshi, iyakanshi cikin Gari, kuma duk fitan da zaiyi da convoy dinshi yakeyi, in ya fita personally to da Armstrong ne ko Idi, saidai in yanaso yayi basaja sai ya basu umurnin kar su biyo shi sai yayi nisan 100km, Zaid beyi Sallah Maghrib da Ishai ba sai da ya iso Ningi, komi beci ba ya sake daukan hanya, Tafiya dai na Allah ne, shi ya kawoshi Lafiya. Sai karfe 11:27pm iso garin Kano.

 

Jami’an tsaro sunyi mamakin ganinshi a wannan lokacin, be iya jira su bude mai Gate ya fita ya shiga Gidan sauri sauri gudu gudu, ya sa mukulli ya bude parlorn ya shiga dakinta a kwance ya ganta tana rawan sanyi duk da bargon da ke jikinta.

A baiyane yace”what have i done?” da gudu ya hau kan Gadon,ya yaye bargon, wani irin hucin zafi ya bugeshi, ya sa hannu ya tattarota gabaki daya jikinshi, bata da karfi da kasala, amma cike da karfin Hali take tureshi daga jikinta tana cewa “ka sakeni, kar ka tabani, ka barni in mutu ni” kara rungumota yake sakeyi  ita ma bata fasa tureshi ba, cikin wata irin Murya yace “Ziyaaaaaa”

….

 

Late night Post, Sorry, kuyi Blaming NEPA,

 

*Zaid back to his senses?*

 

*Ta ya kuke son Zaid yayi nadama?*

 

*Me zuzu zatayi in ta san cewa shine sanadiyar duk wani hawayen da ita da family dinta suka taba zubarwa?*

 

*Me kuke ganin zaiyi da zata yafe mai da irin cin fuskar da yayi mata da Family dinta?*

 

*Meye zai faru da Zsquare in kwai ya fashe?*

 

*Me zai faru da Mairo in kwai ya fashe?*

 

*Najwa zata amince da Jaan dinta in ta san cewa Mahaifiyarshi ce Ummulabaisin duk wani abunda ya faru da Mahaifanta*?

 

*Duk zaku samu answers dinku in less than 6 pages to come(yesso ADAY is coming to an end)*.

 

You know what to do with the Star down there right?

 

#1love

#ADAY

#Bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa.

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

BIYasme

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣5⃣

 

Cikin wata irin Murya yace “Ziyaaaaaa, Keep Calm Please” tureshi tayi da duk wani karfin da Allah ya bata, ta mik’e zaune, tace “meye haka?” kallanshi tayi cikin ido kafin tayi wata dariar takaici, tace “Damuwa a idonka? Karya ne, parts of your tricks? (Wasu daga cikin shirin ka? ) I wont fall again, Allah ya tsarei ni” ta kwanta tare da k’udundunewa.

Girgiza kai yayi da sauri, yana so ya mata bayani, amma be san be zaice ba, yana so ta fahimci abinda ke ranshi, be damu ba in ta sani, be damu in Armstrong zai kalleshi yayi daria yace “I told you so Boss” be damu ba in zai sauka kasa yayi gravelling don ta amince dashi, ba tricking dinta zaiyi ba, daga Bauchi fa yayi risking rayuwarshi and all don kawai yazo ya ganta ya ga ya take, amma abubuwan da ya mata a yan kwanakin nan, yasan ba zata amince da shi ba, tsaki yayi, ya shiga toilet ya dibo ruwan sanyi a dan bowl, ya fito, fita yayi ya dauko hand towel a dakinshi, ya dawo dakinta, tana nan yanda ya barta.

 

Riga da Skirt na atamfa ke jikinta, Saboda Fever din da ya kamta bata samu kuzarin cirewa ba, ya juyota cikin zafin nama tace “nace kar ka tabani, in ba yankani zakayi ba so kar ka tabani” be kulata ba ya kama zip din rigarta zai zage, tayi saurin buge hannunshi, ta koma ta kwanta, ranshi ya fara baci, meye haka takeyi? He only wants to help, ba wani abu ba, yace “ina so na goge miki jiki da ruwan sanyi don kiji dadi” idonta runtse tace “bana so” a ranta kuwa tace “sai kace ya damu” yace “am not trying to see your body, i just want to help” murmushin takaici tayi, a ranta tace “so yake in amince dashi ya samu damar wulakanta ni a fili kuwa sai tace “I dont want your Help” Zaid ya gama kai koluluwa gurin k’ulluwa yace “Ziyaa, ko ki bari na taimaka miki, ko in je Gidanku in ma Family dinki wani abunda ba zasu taba mancewa ba” idonta a runtse hawaye na bin kuncinta tace “in ka tashi ka kashesu”.

 

Da mamaki ya kalleta, she’s in pain abunda ya sani kenan, kar yayi taking advantage ya kara mata wani pain, tashi yayi ya fita daga dakin rai ba dadi, da ta san daga inda ya taho a mota don ita, da ta san risk din da ya dauka yayi tafian dare, da bata mishi haka ba, sha zafin ciwo ne, ya koma dakin shi, saidai ya kasa bacci, waje ya fita ya dauko Laptop dinshi da aka shigo mai da Motarsa, ya dawo Parlo ya kunna yana latsawa, saidai hankalinsa be san abunda yake yi ba, tsaki yayi ya tashi zai koma dakinta, sai ya fasa, sunturi yake a parlo, har wurin karfe 1 yana abu daya, ya yanke hukunci komawa dakin, kila tayi bacci.

 

Yana kuna wutar dakin ya ganta ta na kaukau da jiki, da sauri ya karasa gunta yana fadin “Ohhhh, Ziyaa, yoi are soooo stubborn” hawa yayi kan gadon ya jawo Bowl din ruwan da ya ajiye kan mirror da towel din, dagota yayi ya kwantar kan cinyarshi, ya sa hannu ya zuge zif din, sosai jikinta yayi zafi, tana jin hannunshi a fatar jikinta, bata yi yunkurin hanashi ba, don bata da karfin hanashi, tana ji tana gani ya dinga tsoma towel din nan yana matsewa ya daura mata a jiki, tun daga kanta, zuwa wuya, baya da kirjinta, tashin hankalin da yake ciki ba zai bari ya kare ma surar jikinta kallo ba, Drawer dinta ya bude ya duduba akwati, ba Sweater ko wani riga me kauri, da sauri ya nufa daki ya dauko Wani Sweater dinshi Hoody, da Wayarsa, sai da ya samata Sweater dinshi kafin ya latsa numbern Dr Emran, ya tambayeshi maganin da ya kamata ya ba Ziyada, ya mishi texting, be da lokacin aiken wani, gani yake ba zaa mai sauri ba, haka ya dauka key ya fita da sauri yace “ku bude min Gate” daya yace “Oga 1am fa” Zaid be tanka shi ba ya karasa gun Mota ya kunna, ganin haka aka bude mishi, Wasu securities suka shiga wata Mota suka bi bayanshi.

 

Ba su wuce 30mins ba suka dawo, sauri sauri gudu gudu yake abubuwanshi, ya fito daga mota ya shiga gida ya dauko ruwa ya shiga dakinta, bata yi bacci ba, ya dagota ya bude mata maganin kamar yanda akayi prescribing ya sa mata a baki, ba gardama ta karba ta sha, kafin ta koma ta kwanta ointment ya kara shafa ma kafanta ya gyara mata kwanciya ya ja bargo ya rufeta, yana kallonta har bayan wani lokaci bacci ya soma daukarta.

Be san lokacin da ya kwanta gefenta, daga bisani ya rungumota yana jin dadin kasancewar su haka, da wuya a ga Zaid na bacci, baya baccin da ya wuce 2hrs, and his very sensitive, duk yanda yake bacci ko yayane ya ji motsi ko ba na mutum ba sai ya farka, amma be san lokacin da ya fara bacci ba yanzu, be so wani dalili ya rabasu.

 

Da k’arfe 5 da wani abu Zaid ya farka sakamon jin Ziyada na zufa, ya taba jikinta, yaga zufa takeyi alamun Fever din ya sauka, dadi ya ziyarce shi, ya dan zame jikinshi kadan, a hankali ya cire mata Sweater, tare da goge mata zufan jikinta, be damu ba, da hannu ya goge mata, ya kunna AC kadan. Fita yayi ya wuce daki, lokacin Asuba yayi haka yayi alwala yayi Sallah, abun mamaki nan inda yayi sallahn ya buge da bacci kamar an bashi maganin bacci.

 

Da Yunwa ta tashi, rabonta da Abinci tun kalacin safe, gari ya waye, Subhanallah batayi Asuba ba, jin jikinta tayi garau sai dai yunwa, she was sick yesterday, amma yau jinta take kamar ba ita bace ke kwance jiya magashiyan, da sauri ta shiga toilet tayi Alwala, Sallah ta fito tayi tana gode ma Allah da ya kara mata da lafiya, Toilet ta sake fadawa tayo wanka ta fito ta chanza kaya, bari ta gyara Gado kafin ta fita neman abunda zataci, tana daga Bargo taga Sweater me laushin gaske, Haba! Tun da ta tashi takejin kamshin Zaid, a hankali abubuwan da suka faru jiya suka soma dawo mata, ta tuna yanda yake mata magana da damuwa kwance a muryarshi, anya kuwa? Ko duk hakan na cikin shirin da yake mata, kai, ba zata yarda dashi ba, inaa, gyara dakin tayi ta chanza bedsheet, ta linke bargo, ta fita ta wuce kitchen.

 

Komai akwai a kitchen, tayi mamakin yanda komai na kitchen din ke karuwa, store ta nufa tana kallo, me zata ci? Me zatayi? Ita ba wai girkin ke mata wuya ba, me zata dafa ne ke bata wuya, guntun tsaki tayi ta dibo Dankalin da be wuce 15 ba amma irin manyan nan ne, ta fita kitchen dashi, daidai sink ta tsaya ta dauko peeler, ta shiga ferewa, bata dau lokaci ba ta gama, kamar cubes ta shiga datsawa, a haka ta soya Dankalin, ta fasa kwai ta soya, ta hada ruwan zafi tayi Tea.

Buruntu ya sashi fitowa ds sauri yayi Kitchen, tsaye ya ganta tana hada breakfast dinta kan tray, wani Murmushin da be san daga ina ba ya subuce mai, kallonshi tayi so daya ta kawar da kai, ta gabanshi ta raba ta wuce fuskarta ba wata Annuri, Tofa! Bayan ta ya bi, ko har yanzu bata jin dadi ne? Amma she looks perfectly Ok, ta warke da bata zo Kitchen ba, da sauri ya bita daki, tana zaune Kan Gado tana cin Dankalinta da Kwai cikin kwanciyar hankali, daga nesa ya hango dankalin nan, don kwadayi na kwadayi, a halin yanzu be taba gannin abunda yake son ci ba kamar abunda Zuzu keci, a hankali ya karaso gunta, a hankali yace “Ziya, Ya jikin? Ina fatan kin samu sauki?” banza ta ba ajiyarshi ta cigaba da cin dankalinta kamar ba ayi wani halitta a gun ba, be hakura ba ya sake cewa “Ina fatan ba abunda ke miki ciwo?”.

 

Ya dan murmusa a ranshi yace “tana fushi ne, haha tana so na, zan ga inda fushin zai karashe” cikin kashe murya, da ya san zai narkar mata da zuciya yace “Haba My Forever, dont you want to talk to your Forever?” tsaki ta buga sosai da sai da yaji tsakin a tsakiyar kanshi, shi ake ma Tsaki yau? Banda ita, wa ya isa ya mai tsaki ya barshi, lallai Ziyada ta ciri tuta, tsugunna yayi gabanta, ya dauki fork din da ta aje ta dauki cup din shayinta har ya sa fork din ya dangwalo dankali da shi ya ga tayi saurin ajiye cup din shayin ta yi saurin kwacewa daga hannunshi, har ta dan bashi tsoro yanda ya ga ta zabura, shima da sauri ya mike yace “Yadai?” Kamar jira take tace “Poison, ko Asiri kana so ka mutu da wuri ne? Ko kana so na mallakeka ne? Da hankalinka zakaci abincin da akayi Asiri don mallakeka? Haba mana, kar ka zama wani mara wayau mana”.

 

Sosai da mamaki yake kallonta, duk ta chanza, ta rikide ta koma wata da be sani ba, ya san cewa tabbas magana ta gaya mai, yanda kasan Me Ciki haka yake jin kanshi, so yake yaci dankalinta, wani abu ke ingiza shi, dan kawar da kai yayi, besan meyasa yake jin shi wani dolodolo gabanta ba, share maganar da tayi yayi yace “Ziya, bani inci please, nima Yunwa nakeji, kuma shine zaki dafa ke kadai, kuma kinsan cewa ba ke kadai ke cikin gidan nan ba?” ya karashe cikin karyar da murya, da karfi tace “Heheh, Ni in dafa ma Abinci? You are sick in the head, lokacin dana so kaci abinci na ya wuce, ni banson Almubuzaranci, amma da na baka abinci na, gwara na zubdashi a kasa na taka”.

 

Ranshi ya fara baci yace “Ki bani ko ranki ya baci, this is my House” ta danyi guntun dariya tace “bacin rai? Na nawa kuma sai dai kar a kuma, and this is your House but this is my room, baka isa ka sani abun da ban yi niyya ba, banda lokacinka, a lokacin da ka barar min da ruwan zafi a kafa, a lokacin duk wani k’ima, mutunci, daraja da wata So ya bare tare da ruwan zafin and Abu na karshe, ina so ka sani raina ya gama baci ta kanka” ranshi bace da mamakinta be so ya yarda da abunda tace, be so ya sake jin wani abu daga bakinta, don me zatace tabar son shi? Ya zaayi ta bar sonshi? The whole Him, for God sake he’s Zaid Freaking Sadam Audu, ba ta san yanda mata ke mutuwan mai ba? Matan da sun fita da komai, sai yaji kamar ta ci mai fuska, kamar dan shekara 4ya mareshi zai iya daukan rejection dinnan ba.

 

Da karfi yace “Shuttup, kar ki sa na miki abunda ba zakiji dadinshi ba” dariar da ya tsana tayi tace “bana tsoronka, bana shakkanka, thanks to you ni ba mafadaciya bace, ka koya min fada, ni ba mara kunya bace, ka koya min rashin kunya, so mu zuba ni da kai, duk wanda ya gaji yayi sanadiyar dayan, ko gawa ta ko taka, ko ka barmin Gidan, ko ni na bar ma Gidan, don na tsaneka wallahi, i hate you Zaid, nayi nadaman saninka, kaci amanar Soyayya, kaci amanata kuma ban yafe ba” abun mamaki juyawa yayi ya fita daga dakin a guje kamar dan Yaro.

A zaton ta wani abu yaje daukowa don ya bugeta, amma taga shiru, haka ta zauna ta cigaba da cin abincinta ta fita ta kai kayan kitchen, zuciyarta bushe, ba a haifi wanda zai wulakanta Family dinta ta raga mishi ba, So kadai zai hanata gurza mai rashin mutunci, amma yanzu ta sa Martaban Family dinta a gaba, ta zabi hakan akan Farincikinta, ba zata sake bari Zaid ya wulakanta ta ba ko Family dinta, ba za ta fita ba ba kuma zaa zo gunta ba ko? Ba wani abu, muje zuwa” har tayi hanyar daki, kuma ta fasa ta koma Parlo ta zauna ta kunna Zeeworld ta hau kallo ba tare da ta damu ba.

Bayan Wasu Awannni.

 

Daki ta shiga domin yin Sallahn Azahar, tana cikin yi sai ta ji shigowarshi, sai da ta idar ta dade tana Addua, da ya ga bata da niyyar shafawa sai ya dauko Magungunan jiya ya matso kusa da ita yayi tsugunni a gabanta, ballowa yayi ya kai bakinta, ta kawar da kai, ya sake kai mata, ta sake kawar da kai, ya dai daure yace “kisha magani please” a dan tsiwace tace ” ba zan sha ba”, ranshi ya baci sosai, Masifa ya fara mata “Ke Mallama, ki kama kanki kinaji ko, kinga ina lallaba ki zaki fara kawo min raini? Toh ki kiyayi kanki, ki cece mu daga bacin rai dukkanmu, ke ke ciwo amma na fiki damuwa, jiya baki san wanda ke kanki ba, an samu kin fara jin sauki kuma zaki fara wani iskancin banza kice ba zaki sha magani ba, har kin isa ki sa na fita k’arfe dayan dare don siyo miki magani kuma ki k’i sha? Wallahi baki isa ba, ki karbi maganin nan ki sha kar na saba miki” jiki na rawa, dama wasa guri gareshi, da sauri ta karba ta sha ta karashe da murguda mai baki, Kyau ya ga ta mai, be san Murmushi yake ba, ita kuma tayi kicinkicin da fuska. K’afarta ya jawo ya sa a jikinshi, tana kallo ya matsa wani mai me kama da vaseline a hannunshi, ya shiga shafa mata sama sama don kunar ya fara bushewa, ya dago kai ya kalleta, yace “Ki daina sawa ina miki Masifa, ki dinga yin abunda nake so kinji” bata ce mai k’ala ba ila kawar da kanta da tayi, be damu ba ya tashi ya fita ba tare da ya damu da shariyar da take mishi ba.

 

Binshi tayi da idanuwa, So take gani a Idonshi, Kula da damuwa take gani a idonshi, na gaske ne? Ko kuma na sa ta fada cikin wani tarkon, tsaki tayi tace “banda lokacin yarda da kai, in ma dagaske kake, in ma karya kake, duk karya na dauke su, kalamanka na yaudara ne” magana takeyi kamar yana gabanta.

**

Waya General Manager ya mishi, kan cewa Mutanen nan fa ba su tafi ba, suna jiran shi Yau by 8 zaayi meeting, tsaki yayi yace “ba zai samu zuwa ba, in dole sai ya je za suyi agreeing to contract din su tafi baya so” chan kuma yayi wani tunani yace “No, kace musu i’ll see them by 8” kashe waya yayi ya Kira Armstrong yace “ya mai booking two flights zuwa Bauchi. Fita yayi ya koma dakin Ziyada ya ga bata nan, ya lek’a Kitchen ya ganta tsaye tana dafa Indomie kwara daya, Murmushi yayi, yace “ki shirya za muyi tafiya yau” kallonshi tayi ta watsar, ta matsa kusa da inda ake ajiye plates ta juye Indomie dinta ta dauka yaji ta koma daki ta barshi tsaye kamar Sakarai.

 

Daki ta je ta zauna ta ci Indomie dinta tas, ta shiga ta kai plate, ta dawo ta kwanta kan Gado, don bacci takeji, baccin nan har bayan Laasar, Zaid ya shigo dakin don su tafi Jirgin zai tashi da karfe 5, ganinta yayi kwance kan Gado, ya dan hau ya bubbugata yace “Ziyaa, bacci kikeyi? Kinyi Laasar ma kuwa? Tashi kiyi Sallah mu tafi, yi sauri, ba musu ta tashi tashiga toilet, yana nan zaune ta fito daure da Alwalanta, ta dauko Hijab a nitse tayi laasar dinta, lazimi ta fara wanda sai da ta dau minti 10 tanayi, kuma bata da niyyar tsayawa, cewa yayi “Tashi mu tafi kar muyi missing Flight dinmu, ina kayan da kika shirya a sa a Mota?” bata tanka shi ba sai Mikewan da tayi, hawa Gadon ta sakeyi ta kwanta tare da jawo bargo, da sauri ya yaye mata bargon yace “Tashi please, in bacci zakiyi sai kiyi a hanya, tashi mu tafi” gyara kwanciyarta ta tayi ta fincike bargon ta rufe Jikinta da shi, da mamaki yace “Haba Ziyaa, na fi 20 mins in jiranki, kuma na gaya miki flight din mu is 5, yaushe mukaje Port din?” ki tashi donAllah, ya isheta da magana tace “kayi tafiarka Mallam, don ni ina nan, ba inda zani” baki ya sake yana kallonta, chan yace “Haha, tashi, nice Joke, tashi mu tafi” ta dan juyo tana kallonshi tace “Joke? Zakaga Joke” ta sake komawa ta kwanta.

 

Nazarinta Zaid ya tsaya yi, dagaske take ba zata ba, bayan ta sa ya jirata, kuma tace ba zata ba, aiko bata isa ba, ya mik’e ya bude drawer dinta da k’arfi, dan karamin akwati ya zaro ya shiga harhada kayanta a ciki, ta cikin bargo take kallonshi, ya fita ya ajiye Akwatin Kofar Parlo, ya kwalawa Mudi kira, da sauri Mudi ya dauki Akwatin yayi cikin Mota, komawa dakin yayi yace “Ziyaa, kar ranki ya baci, tashi mu tafi” ta murguda baki tace “sai kayi, na ce maka ba inda zani ko?” kakkabe hannunshi yayi kamar akwai datti a kai, bata ankara ba sai ji tayi ya janyota ya dagata sama ya dorata kan kafadarshi, mutsu mutsu ta fara yi tana fadin “meye haka? Put me down” cilla cilla take tayi tana wulwula kafa tana bugun shi a baya, ko a jikinshi shi dai fita yayi da ita, ko dankwali babu a kanta, haka ya tusa ta Mota ya zagaya ya shiga dayan side din ya tuka ya fita daga Gidan, Securities suka bishi a baya.

 

Fuskarta murtuk’e tace “wai meye haka? Ka ajiye ni, nace ba zani ba, ko dole ne? Haan naci na meye?” shi dai be ce mata uffan ba, tayi ta masifarta yayo banza da ita, da taga dai dagaske din tafiya zasuyi don sun dau hanyar Airport, tace “sai ka tsaya in dauka mayafin da zan rufe kaina, tunda kai ba kada Ilimin Addini, baka san ya kamata ba, baka da kishin Matarka, zaka bari garadan da Muharammamta suga jikinta da gashin kanta” kiii ya ci burki a gangaren titi yana kallonta, rai bace yace “Nine banda Ilimin Addini?” ko tsoro babu tace “Hakan nake nufi, Jahili ne kai a addini, in ba haka ba, ta ya zaka fito dani haka” zaiyi magana kuma ya fasa, ya bude kofa ya fita ya bude Booth inda ya sa kaya, ya dauko Akwatin gaba ki daya ya zagayo dashi daidai ita ya ajiye tare da bude, mamakin sauyin shi take, ta shiga dudduba kayan da ya zabo mata, tsaki tayi, duk ba wasu kayan mutunci, duk fitted gowns ne, chan dai ta zaro wani Mayafi ta yafa a jiki tunda kanta, ta maida kafafuwanta Mota, be ce mata komai ba ya zige zip din, dama masu tsaranshi sun fito suna tambayan lafiya, banza yayi dasu, da suka zo taimaka mishi gurin daukan Akwatin ya buga musu tsawa wai yana da hannu, da sauri suka koma motocinsu shi kuma ya rufe ya dawo ya kunna mota ya figa da karfi, Ziyada ta buga tsaki da k’arfi tace “kai dai ka sani” be tanka ta ba don ya lura ta koyi rashin kunya, be ce komai ba har suka iso Airport inda zai jirgi zai jirasu, kamar dama su ake jira, suna isa jirginsu ya tashi.

 

B A U C H I 6:15pm

 

Already su Faisal na Airport din bauchi suna Jiransu, Ziyada ta dinga murza hanayenta biyu a Saboda sanyi, Zaid ya lura da hakan, dukkansu ba me Rigar sanyi, sakalo hannunshi yayi a hannunta, kamar ta fizge kawai sai dai ta share kar ta basar da shi gaban yaranshi, ganin Motoci kusan 5 don tarban Zaid ya sa Ziyada jinjina kai, lallai kudi na inda suke, suka shiha Motar tsakiya Faisal na gaba, Faisal yace ma Zaid “Barka da zuwa Boss” a kasaitance a amsa mai, Ziyada ta bi Zaid da kallon yanda yake shan kamshi yana magana, Faisalyace “Barka da Zuwa beehive Madam” Ziyada ta murmusa tace “Ina wuni” Wannan Murmushin ya bata ran Zaid sosai, wato shine ba zata ma Murmushi ba amma ta iya ma wani? Faisal ya kalli Zaid ta mirror yaga yanda ya hade rai, sai yayi saurin fara karanto mai Updates daga jikin Tab dinshi, kafin yace “Boss, Company ko Masauki?” ya kalli Ziyada, kafin yace “mu fara zuwa Hotels din” Faisal ya kalli driver yace “Muje Zaranda Hotel”.

 

Cikin wasu Mintuna suka iso wani Wakeken Hotel, me suna Zaranda Hotel, suka fito, Faisal ya raka su har zuwa gaban dakin da ya musu booking, wani kuma ya kwaso kayan Ziyada da Jakkar Zaid, Faisal ya bude dakin dayan kuma ya shigar musu da kaya, Ziyada ta dinga bin dakin da kallo, tunda take bata taba kwana Hotel ba, yau zata kwanan hotel, zama tayi kan kujera, Zaid ya kalleta yace “Kina jin Yunwa ai?” banza da shi tayi, yayi maganan duniya kan ta fadi me take son ci tayi banza dashi ta kyale, haka ya hakura ya bude Wardrobe ya dauka towel ya shiga toilet yayi wanka da Alwala, ya fito daure da guntun towel, da sauri ta kawar da kanta, yana karasowa dakin ta shiga toilet da sauri don dauro Alwala.

Sai da ta bata lokaci kafin don ta tabbatar ya shirya, tana fitowa taga ya kabbara Sallah, itama ta nemi Mayafi ta kabbara Sallah, sai da suka idar da Sallah ya kalleta yace “zanje Meeting, please in kina jin Yunwa, ga Waya chan ki danna 1 roomservice ki fada duk abunda kike so su kawo miki, take care of yourself please” be tsaya jin rashin kunyarta ba ya dauki bag ya rataya ya fita. Kamar jira take, yana fita ta kira roomservice tace a kawo mata Chips da liversauce” ba a wuce 15 mins ba akayi knocking aka kawo mata service dinta, tana gama ci ta chanza kaya, ta kunna TV ta fara kallo, har wurin past 10, kafin ta kashe kayan Kallon ta kwanta, ba bacci takeji ba, ta dai gaji ne, ga tsoron da bata san na meye ba.

 

Wurin 10:30 sai ga Zaid ya bude ya shigo da Sallama, ya kunna wuta, ganin Plate yayi alamun taci abinci, ya sauke ajiyan zuciya, ya kalli Gado, ya ga ta kwanta, a gajiye yake, a gun Meeting din sai rushing yake don ya dawo ya ganta, harda ya hakura a ka gama and it was succesful..

Kulle kofan yayi ya soma Zare kayanshi a hankali ya chanza zuwa Pyjamas, ya kashe Wuta ya dauko Laptop dinsa ya hau kan Gado, kamar jira take ya hau Gadon tayi zunbur ta tashi, da hasken Laptop dinsa yake kallonta yanda ta tsura mai ido yace “Yadai?” tace bangane ba, ya zaka hau min Gado? ” da mamaki yace “to ina kike so na kwanta Kujera?” tace “ba dai dakin nan ba, ta ya zamu kwana daki daya?” Murmushi yayi yace “to ya kike so inyi?” a takaice tace “ka kama wani Dakin” ya kalleta yace “banda kudin kama wani dakin” galala tace “kaidin? Ni mallam ka fitar min a daki, ba zan kwana daki daya da kai ba, ko ka fita ko na fita” Zaid ya kalleta sosai yace “kiyi hakuri ki kwanta, barin koma kujera, ba bacci ma zan ba, zanyi wani aiki ne” cike da karfin hali tace “ni fa ba zan kwana daki daya da kai ba” ya kwantar da murya yace “kiyi hakuri, gobe sai mu raba daki, please Ziya, i dont have the strength to argue” bata tanka shi ba ta juya ta kwanta, ganin haka ya sa shi tashi ya koma kan kujera ya cigaba da latselatsenshi, Ziya ta sauke Ajiyar Zuciya, bata san ya zaayi dama ta kwana ita kadai ba, dama duk wani abu da take karfin hali ne, Thank God be fita ba, hankalinta zaifi kwanciya in ta san cewa yana dakin, bargo ta ja ba a dau lokaci ba bacci ya kwasheta.

 

INDIA

 

Yatsina fuska yayi yana ajiye cokalin shi cikin abincin da yake ci hadi da dafe kanshi dake wani irin sarawa kaman zai bude gida biyu yana kiran Allah. Hakan ya dawo da hankalin Maama dake danna wayarta tana kokarin kiran Najwa kanshi. Da sauri ta mike tana kama hannunshi da fadin “Subhanallah, lafiya?”

Hannunta Paapa ya rike dam yana jin bazai iya bude bakinshi ya fada mata abinda yake ji ba, bama zai iya magana ba a yanayin da yake jin kanshi. Gabaki daya yanda yake riko Maama yana dafe kanshi da dayan hannunshi ya rikita mata lissafi.

Bude bakinta tayi da nufin tai mishi magana taji kanta yai wata irin dokawa kaman an kwada mata karfe, ba shiri ta sake dumtse hannun mijinta dake cikin nata tana durkushewa kasa hadi da fadin “Inalillahi wa ina ilaihi raji’un” wani duhu-duhu take ganin yana lullube mata idanuwanta data runtse gam tana salati da neman taimakon Allah jin yanda kanta ke sarawa.

A hankali duhun dake cikin idanuwanta da kanta take jin yana budewa da duk numfashin da take shak’a. Kamun wasu images da bata fahimta su fara mata yawo cikin kanta. Daki ne take gani da kujeru a cikin shi da labulaye ruwan kasa masu haske.

 

Kamun ta ga mutane guda biyu a tsaye suna hira, tana jin sautin maganarsu da dariyar da suke sai dai fuskokin su take son gani da dukkan zuciyarta, kaman sun san me take so suka juyo. Wata irin dokawa zuciyar ta tayi har cikin kunnenta. “Ammi…” Maama ta fada tana kara dumtse hannun Paapa cikin nata.

Saboda yanda kanta yake ci gaba da bugawa. A mafarki, a ido biyu, a cikin maye, zata gane dakin da tai kuruciya a cikin shi. Yola ne, asalinta, tushenta, garin iyayenta da kakaninta. Yar Yola ce ita, bude idanuwanta tayi tana jan wani irin numfashi kaman wadda tasha gudu, kamun a hankali komai ya soma dawo mata.

Da duk wani abu da zata tuna, da yanda ciwon da kanta yake yi yake sauka, har lokacin hannunta na cikin na Paapa da babu abinda yake gani sai Zaid da AbdulMajeed dan gun Yayanshi lokacin yarintar su. Sai dan uwanshi, dan uwanshi da yake kauna da dukkan zuciyar shi.

Kano yake gani da yanayin komai na rayuwar su na dawo mishi kaman film aka kunna. Kamun yaga fuskar Mairo, yaga fuskar da a yanzun yake da yakinin har mutuwarshi ta riske shi bazai taba mantawa da ita ba.

 

Musamman kalamanta da suka zauna a kirjinshi da zafi kaman garwashi, kanshi ya saki da dayan hannunshi yana dafe kirjin shi dake kuna.

*”Ina so ka dauki matarka, da wasu ‘yan kudi, ku bar k’asarnan, kuyi nesa da k’asar nan, kar ku sake waiwayen Nigeria, duk inda ka san muna iya haduwa ko ba dade ko ba jima kar kaje gun, wurare kamar Makka da Madina, Ina so ku manta da Mahaifarka, ku tashi ku tafi yanzu”* Kalamun Mairo ke dawo mishi kamar a lokacin take mishi,

Ware idanuwanshi yayi akan Maama, da ta sauke nata idanuwan cikin nashi cike taf da hawayen da suke gab da zubowa, na Paapa cike suke da yanayin da bazai misaltu ba, kamun ya mike tsaye daga kan kujerar da yake yana dago da Maama. Goshin shi ya hada da nata “Na tuna…na tuna komai…” yake fadi mata muryarshi na rawa.

 

Kai Maama take daga mishi hawayenta na zuba. “Me mukai mata? Me yasa zatai mana haka?” Saida Paapa ya hadiye wani abu daya tsaya mishi a wuya kamun yaja numfashi da fadin “Bansan dalilinta ba. Bansan me yasa ba, in akwai abinda nasani shine kowacce kaddara na faruwa da dalili…”

Hannuwa tasa ta tallabi fuskarshi cikin tata, babu abinda take so, babu abinda take muradi da duk wani abu da ta mallaka daya wuce taji kafafuwanta kan kasarta, ta sauke idanuwanta kan yan uwanta, kan yayanta, ta shaki iskar data banbanta da duniyar nan da Mairo tai musu sanadin shiga.

“Let’s go home” ta ce wasu sabbin hawayen masu dumi na zubo mata. Sumbatar goshinta Paapa yayi yana jin yanayin da bazai misaltu ba. “We are going Home. Komai yazo karshe Yesmeenah ” In hankali da nutsuwar shi sunyi dubu gida suke kira mishi.a

Kama hannunta yayi suka shiga ciki dan su fara shirye-shiryen daya kamata, kamun ai musu visa ne aiki, sun san zai dauki lokaci amma abu daya suka sani, Zasu Gida.

Tana shiga daki ta zaro wayarta Paapa yace”Wa zaki kira?” “Najwa..” ta amsa shi tana dialing number din Najwa hadi da kara wayar a Kunne.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣6⃣

 

Pappa yace “Aa Yesmeenah,  duba kiga lokaci,  yanzu 10pm daidai da kusan karfe 3am dinsu,  duk inda Najwa take tayi bacci, kuma  gaggawa na me? Mun warke daga duk abinda aka mana,  kuma zamu Gida, ki bari da safe sai ayi Waya ko?” Maama tace “Wallahi Papi baka ji dadin da nakeji bane,  kawai doki ne ya sa ni mantawa” Paapa ta murmusa yace “muje mu kwanta,  abincin ma na san ba iya ci zanyi ba” tayi dariya tace “baccin ma ba iyawa zakayi ba,  kawai mu zauna mu jira garin Allah a waye” dariya yayi,  yace “gobe InshaAllah za mu fara processing Visa” tace “Allah shi kaimu” ya dan kalleta kafin ya mik’e yace “Zama be ganmu ba, muje mu nuna ma Allah jin dadinmu ta hanyar gode mai,  muje muyi nafila” tashi tayi ta bi bayanshi suka shiga daki don nuna Godiar su ga baiwa da jin k’ai din da ya musu.

 

Suna yin Sallahr Asuba ta zaro wayarta zata kira  Najwa,  Paapa yace “Yesmeeenah.. Wai saurin me kikeyi?” ta cigaba da latsa waya tace “gwara ta san mun tuna komai,  kuma tana da uncle a Kano,  ta nemeshi” Pappa ya karbi wayan yace “Kul, kar ki sake, me kike so tayi?  Taje ta nemo Abba,  ta koma gunshi da zama Mairo ta san cewa diyar mu ce ta salwantar da ita?  Kinsan me tama Zaid?  Kinsan ko ta Salwantar da Zaid kamar yanda ta mana?  Kinsan ko yana raye ko yana mace? Ba mu san me ta mishi ba,  ba musan me zata mata ba in ta ganota, tunda dama ba kaunar mu take ba” Maama tayi shiru kafin ta jinjina kai,  tabbas hakane,  yanzu in Mairo ta gano Najwa,  Allah kadai ya san abunda zatayi  mata tunda ba imani ne da ita ba, Pappa yace “Zamu gaya ma Najwa, mun tuna komai,  zamu gaya mata zamu zo Gida, thats all,  koma meke nan,  in mun isa sai mugani”.

 

K A N O

NIGERIA 8am

 

Tun lokacin da ta tashi ko breakfast ba tayi ba ta dauki kudi ta fita,  yau ta sha alwashin zata fare neman Yayanta,  Cyber Cafe ta shiga,  inda tace musu zatayi amfani da system,  ta siya Time ta zauna ta fara searching Zaid Sada Abu,  clicking taga sunaye da yawa sukayi appearing,  mafi yawanci sunayen Larabawa ne, daga k’asa ta ga ansa Search for Zaid Sadam Audu The Youngest Multi Billionaire in Africa(bincika Zaid Sadam Audu, Matashin maltibilonaire na Afrika) ta shiga nan din duk da tasan ba shi din bane. Tamfatsesen hoton Zaid ya kusa mamaye screen din computer

A ranta tace “Mijin Ziyada ne, ta ji labarin Yana da kudi sosai,  amma bata san shine multi bilionaire a Africa ba,  no wonder yake musu Mugunta ba tare da an dauka Mataki ba,  kallon hoton takeyi,  ta shagala da kallon idanuwanshi da yanayin  hancinshi da yanayin bakinshi, tabbas ta san fuskar nan,  akwai inda ta san fuskar nan,  a ina? Zuciyarta ta tambayeta,  wata sassan Zuciyarta tace “NURA KURMA” zumbur ta gyara zama ta shiga dunian tunani, nan take ta dinga hasasso dalilanta na tunanin Nura Kurma ne, amma anya kuwa? Nura Baki ne,  wannan kuma fari ne, ganin hujjojinta na amincewa da shine sun fi karfi,  da sauri tace “Yes, Shine,  ai ko shi Nura Kurman is fake,  karya yakeyi,  shi ba abunda yace shine ba,  ba kurma bane,  wani abu yake so tare da su Mummy,  kila ya ga bayyamsu don ta tuna mugayen Ayukkan da yake ta aikata tuna karawansu,  sanda take wargaza mai duk wani shirin da yayi,  tun daga cocaine,  da wannan  abunda zai yi sanadiyar karewan Mairo,  da maganunshi na cewa ta fira daga harkarshi,  dalilinta ya bar gidan,  saboda ta gane cewa ba kurma bane, shiyasa ya bullo ta Auren  Ziyada  don ya k’untata musu, ina ga shine dalilin da ya sa ya yi musu basaja,  don ya matso kusa da su,  don ya samu wasu informations kansu, akwai wani babban abu tsakaninshi da su Mummy, kila akwai wani abu da suka taba mishi ko family dinshi,  in ba haka ba,  don me zai bata lokacinshi da matsayinshi kan su da ko kafar Azzikinshi ba suyi ba?  Akwai boyayyen Alamarin da ke tsakaninsu wanda ya sa yake daukan Fansa ta hanyoyinshi,  to ya akayi ba wanda ya ganeshi?” da sauri ta ba kanta amsa,  Multi Bilionaire  ne,  zai iya yin komai, komai zai iya yiwuwa a gunsa,  yanzu haka makeup ne.  Duk da zarginsa takeyi bata tabbatar ba,  amma Zuciyarta da duk wasu sassa na jikinta sun amince da hakan ne.

 

Ta kira Jaan ta gaya mai?  To tace mai me?  Ta bi diddikkin Mijin Kanwarshi? To yanzu da suka san tana cikin wani hali me sukayi? Gaya musu na nufin kara musu damuwa,  tana jin tausayinsu duka,  balle Mummy tun bayan dawowarta daga Gidan kullum sai ta zauna dabas tana sambatun kiran sunan Ziyada, da hawaye da majina sha6esha6e,  haka yaranta ke shiga damuwa,  kai amma Nura Kurma be da imani,  ko ma tace Zaid,  Mutane wasu ba sa tuna mutuwa,  wai ka k’untata ma danuwanka Musulmi kaji Me? Me zakaji? Kawai don mutum yana da komai a dunia sai ya zabi yayi Zalunci? Kai ko Kashe masa Mahaifa sukayi ai be kamata ya dinga musu haka ba,  wa ma ya san Mugunta nawa ya musu kuma yake shirin musu?  Wa ya san duk was misfortunes dake faruwa a Family din ko ba shine sila ba? Haba,  ko me suka mishi yana da karfin hadasu  da hukuma sai a musu hukunci daidai su,  ba ya dinga taking decisions a hannunshi ba,  kawai a ranta taji ta tsani halaiyar Zaid,  wannan beyi halin  Yayanta Zaid ba,  be ci a kirashi da sunan Kamili irin Yayanta ba,  wannan sai ya bata ma masu sunanshi suna,  da ba dan sunanshi irin na Mafi soyuwan Danuwanta ba,  da ta tsaneshi tsana me karfi,  yanzu zata tayashi da addua,  Allah ya shirya shi in me shiryuwa ne,  in kuma ba zai shiryu ba Alkah ya shiga tsakaninsu da su Mommy,  ya kuma kawo sanadiyar rabuwar su da Ziyada.

 

Bata gama tunaninta ba wayarta yayi k’ara,  ta ciro da sauri ganin  8:30, Maama ce,  ta dauka jiki a sanyaye,  bayan sun gaisa tace “Diyata,  me ya sameki?  Ki baki da lafiya ne?  Kina ina?” Najwa cikin sanyin jiki tace “Wallahi Maama garin binciken Zaid Bhaiya,  na gane Mijin Ziyada shine wannan Nura da yayi faking shi kurma ne?” Maama tayi saurin chabewa tace “wannan Mugun? Wanda ya so framing dinsu da Cocaine? ya akayi aka aura mata shi to? ” Najwa tace “shifa Mamma,  abun akwai confusion,  yana da kudi sosai,  yana daga cikin masu kudin Afrika,  Maama ya auri Ziyada, ya siya Gidansu ya kaita chan,  ya na gana mata azaba,  da Mumnynsu taje ya mata wulakanci,  ya hana kowa zuwa, Allah kadai ya san abunda yake ma Ziyada a chan” Maama ta ja numfashi cike da tausayawa tace “Kin ban labarin duk wasu abubuwan da ke faruwa,  Allah ya saka musu,  ke dai ba ruwanki,  na sanki da son bin diddigi, ki kula da kanki,  ki sani Muna nan zuwa Gida Nigeria, Paapanki ya tafi chan Embassy neman mana Visa,  InshaAllah muna nan zuwa cikin yan kwanaki  duk abubuwan da muka mance mun tuna su,  Zamu dawo Gida, tare zamu nema Yayanki kinji?  Ki kwantar da hankalinki ,  cikin kwanaki zamu kasance tare dukkanmu in har yana raye”.

 

Najwa cikin fariniciki mara Misaltuwa tace “Naji Dadi Maama,  Allah maji rokon Bawane,  na tabbata Mallam din da Meri Jaan ya sa shi yi muku addua ne yayi aiki” Maama da mamaki tace “tum meri Jaan?” nan da nan kunya ya cika Najwa,  bata san abunda tace ba kenan,  Maama ta murmusa  tace “vah kaun hota hai?(wanene shi?)” Najwa tayi shiru, tace “Bolo na(gaya min mana)” cike da kunya tace “AbdulMajeed” Maama ta murmusa tace “Zan zo Nigeria,  zanga wannan Abdulmajeed  din,  zan gaya mishi Nagode da kulawan da ya baki,  nagode da ya sa ki ka manta da dalilin zuwanki Nigeria kika fara Soyayya” da sauri Najwa tace “Maama,  in Paapa ya jiki fa?” Maama tace “ai zan gaya mishi, ke Soyayya kike yi,  ya miki Aure” Najwa ta dinga ma Maama magiya kan kar ta gaya ma Paapanta,  Maama ko sai  dariya take tayi daga Bisani Najwa tace “Maama ta bata Address dinsu, ko na wasu wanda zata iya tunawa,  taje taga  ko zata samu wani lead da zai hadata da Yayanta” Maama ta danyi jim ta tuna gargadin Papi inda yace  kar ta gaya ma Najwa komai game da Yayanshi ko Matarshi,  don ba su san me zasu mata ba, sai da Najwa ta kara magana kafin Maama tace “Najwa,  ba zan iya tuna kowa ba,  ai its been long,  kawai dai na san ni Yar Yola ce,  Papi kuma dan Kano, in munzo zamu tuna” Kafin Najwa tayi magana Mama ta kashe wayan,  Najwa ta bi Wayar da Kallo.

*

B A U C H I

 

Stool ya jawo ya kafa gaban Gadonta ya zauna yana kallonta,  yanda take jan numfashi tana saukarwa cikin kwanciyar hankali,  jinta yake har cikin ranshi, saboda ita,  zai zubar da duk wani kuddurinshi,  saboda ita zai manta da komai, bai taba jin son barin abinda ya faru ba, saboda ita zai manta da komai ya faru, Ziyada ta chanzashi,  ko kuma yace ya chanza saboda Ziyada.

 

Wani abu yake ji game da ita me wuyar fasaltuwa,  be taba tsintar kanshi a wannan yanayin ba,  ko yanayin da yake ji na daukar fansa bai kai wannan karfi ba, bai kai yanda zuciyarshi take dokawa kamana zata fito daga kirjinshi da tunanin ta ba, be taba jin wani abu ko wata ta burgeshi ba,  be taba jin abunda yake ji ba gun Na’eela da ta nuna mishi So kamar ta ciro Zuciyarta ta bashi, sai yanzun ya fahimta, sai yanzun yake jin tausayinta.

 

Bai taba jin hakan gun duk wasu yan mata masu nuna mai alamun So,  ko kuma masu furta mai So,  ba wai don ba su da kyau ba,  ko kuma ba su da abunda zai birgeshi, aa yanmata ne nagani na fada,  bama na Gida Nigeria ba, har France inda yayi karatu,  ba ma nan ba,  da wuya yaje wani k’asa ba tare da ya samu Masoya ba, to be taba jin abunda yake ji kan Ziyada ba,  Ziyaaa…. Yana Sonta,  Eh!  Yana Sonta, yana k’aunarta Sosai,  be san sanda Sonta ya shigeshi ba,  aa yasani,  Feeling din da yake ji kanta tun farko wanda ya ke ganin kamar don daukar  fansa ne Gaskia ne,  Gaskia ne yana sonta tun Farko,  gaskia ne K’aunarta yakeyi,  be damu ba da wanda ya sani,  zai fada a gaban kowa,  yana sonta,  zai nuna ma kowa yana sonta,  Itace Farincikinshi,  Itace Jigon rayuwarshi.

 

Ya sha dauka zuciyarshi zata buga ne ta doka ma macen da tafi ziyada aji da komai. Musamman yanda yake da control akan komai na rayuwarshi, sai yanzun da zuciyarshi ta kwace daga control dinsa tukunna. Hannuwanshi duka biyun yasa ya dafe kanshi yana jan iska cikin salon son shakar iskar da babu Ziyada  a cikinta.

Ta farka, ba tai da bude idanuwanta ba,  jikinta ya bata ana kallonta. A nutse ta bude idanuwanta da suka rine zuwa ja saboda baccin da tayi tana sauke su cikin na Zaid, yanayin da take gani yasa zuciyar ta matsewa. Karya take ma kanta, karya take idan tace babu wani bangare dake numfasawa ba tare da Zaid  a kirjinta ba.

Sai dai yanayin idanuwanshi sun dauke hankalinta daga abinda take ji. Me take gani a idanuwanshi? Dana sani? Anya kuwa? Sanya tayi  ta ja jiki  tana tashi zaune tare da sauko da kafafuwanta kasa, har lokacin baice mata komai ba saima idanuwanshi dake kafe kanta.

 

Kofar bandaki tayi,   Har takama handle din zata murda cikin muryarshi data kara mata so da kaunar sa yace “Ziyadaa…” Lumshe idanuwanta tayi zuciyarta na wani irin dokawa. Kunnuwanta na amsa mata sunanta daya kira. Kwakwalwarta na son tuna ko ta taba jin asalin Sunanta akan labbanshi.

Da duk wani abu da take dashi a jikinta take son juyawa ta kalli fuskarshi, kafin wata zuciya ta gargadeta “Da gaske yarda zakiyi dashi? Sake yarda zakiyi?  Sake fadawa tarkonshi zakiyi?  Wanne tabbas kike dashi bazai saki komawa tsumbul a soyayyarshi ya sake wulakanta ki ba?

 

Tura bandakin tayi ta shiga,  Har zuciyar Zaid  yaji wani irin abu da bai taba jiba,  yanda take shasshare shi,  Duk  wadannan abubuwan  baki ne a wajenshi,  Yau shi  yake magana ake shareshi,  yau shi ke kiran mutum amma baida darajar dako a juyo balle har a amsa mai,  shifa ne Zaid Sadam Audu,  Shi fane wanda tarin shi ke sa mutum ya shiga taitayinshi,   Baisan sanda murmushi ya kwace mishi ba. Rayuwa ce ta bashi nishadi, yanda komai ke canzawa na sake bashi mamaki.

Bayan Mintuna 20 ta Fito daga bandakin sanye da wasu riga da skirt da ta shiga dasu toilet,  tazo ta gabanshi zata wuce caraf ya riko hannun ta, kiciniyar kwacewa take,  Zaid  ya girgiza mata kai “Don’t, karki fara,  bana cikin yanayin dazan iya daukar shirmenki” ranta taji ya baci, babu karya a abinda take gani dazun, dan har yanzun akwai dana sani a idanuwanshi, amman jin kan nan babu inda yaje,  yi tayi kamar zata fincike hannunta yace “Please” ya sake fadi yana jefa daga shi har ita cikin mamakin fadin kalmar.

Ware idanuwanta tayi “Me kace?” dan murmushi yayi da yai mata wani irin kyau kamar takai dan yatsanta kan labbanshi kamun ya bude baki yana lalata koma menene yake faruwa da fadin “Karkiyi pushing luck dinki, subutan baki ne, kamar yanda na sha gaya miki, I am Zaid Freaking Sadam Audu,  its not in me to Apologise or Plead” tsaki tayi tare da  fisge hannuwanta tana wucewa ta kyale shi.

 

Kan gado ta koma ta zauna tana juya mishi baya. Tana jin Idanuwanshi akanta, kamun ya tashi ya karasa gefen da take ya zauna. Wani numfashi mai nauyi ya sauke “Yunwa nake ji” a tsawance tace “Sai akace yunwarka ta dame ni?” shagwabe fuska yayi yana ware mata idanuwanshi cikin wani yanayi da bata taba zaton ganin shi ba. Kamun ya kamo hannunta ya dora kan cikin shi “Incase baki fahimta ba, ko kadan banda energy din rikicin ki. Yunwa nake ji” ya sake maimaitawa.

Kwace hannunta tayi tana murza inda ya rike tana jin kaman yabar tambari a jiki. Baice mata komai ba ya mike yana me fita daga dakin. Ta sauke ajiyar zuciya, sam ba zata yarda ta kara fadawa tarkon shi ba. Baifi mintina biyar ba ya dawo, bata kalle shi ba, idanuwanta kafe a kasa.

Bayan Minti 35 da shigowanshi,  sai ga room service yayi knocking,  Zaid ya fita ya karbo ordern da yaje da kanshi ya musu,  don kwadayi irin Dankalin da ta soya Jiya a gida ne,  musamman ya fita yaje kitchen din ya musu bayanin yanda yake son dankalin ya kasance.

Kan Carpet ya zube ya tankwashe kafafunshi,

Yana so yace mata ta sauko su karya amman baida karfin yin gardama, ba kuma yajin zai iya jure ita tai mishi gardama, gabaki daya zuciyarshi ta gama narke mata. Ziyada kam bata san abinda yasa taji tana son ya sake mata magana ba don tunda ya shigo be sake kulata ba, Wata irin kewar muryarshi take ji,  ga kuma Yunwar da takeji.

 

Jin kaman tana kallonshi yasa shi juyawa da fadin “Ki sakko mu karya” duk ya wani canza, abubuwan da yake yi yau kaman bashi ba take gani. Sosai take jin kaman Zaid din ta na farko, kaman Zaid  din dayai amfani dashi ya yaudareta, kamun koma menene yake mata magana a zuciyarta ya fara ta sauka daga kan gadon. Shiru suke karyawar har suka gama.

Kallon  ta Zaid  yayi yana sauke numfashi “Zan fita, may be zan kai karfe biyu ban dawo ba. Akwai Business din da nake son handling. Ki kula da kanki kamun in dawo, can I trust you to do that for me?” bata san lokacin da dariya ta kubce mata ba. “Yaushe ka soma fadamun fitarka ko lokacin da zaka dawo? Yaushe ma ka fara damuwa da halin da nake ciki?” runtsa idanuwanshi yayi yana jin maganganunta na mishi zafi. Mikewa yayi kawai yana kai kofa. “Baka da amsa ko? Ko wannan ma na cikin wata yaudarar taka?” ta fadi a tsawace.

 

Da wani irin zafin nama ya dawo dakin yana sa hannunshi daya ya dagota dashi kamun ya hada goshin su waje daya yana wani irin sauke numfashi cikin bacin ran da sai da Ziyada  ta tsorata, idanuwanshi a runtse yana shakar kamshin da take, murya can kasan makoshi yace “Stop it, ki daina gwada hakurina, bazai mana kyau ba” duk yanda take jin zuciyarta na dokawa bai hanata fadin “Kome zai faru? Me zakai mun wanda bakai mun ba?” bude idanuwanshi yayi cikin nata.

 

“Sona zan dawo dashi a zuciyarki, sona zan dawo dashi cikin idanuwanki. Batare da izininki ba, saboda zan iya hakan, saboda na gaji da ganin akasin hakan, sabosa nagaji da komai, ke kuma kin ki ganewa, saboda me ba zaki gane hakan ba?” ba abinda take tsammani bane daga bakin shi, dan haka duk wasu kalamai sun tsaya mata, komai ya kwance mata be bi ta kanta ba yace “Please, just,ki kula da kanki” ya karasa yana sakinta hadi da ficewa ya doko kofar kaman ita tai mishi laifin.

Durkushewa ziyada tayi tana fitar da numfashi “Gab kake da dawomun da komai sabo, dan Allah karka mun haka, zuciyata ba zata iya daukar wani betrayal din ba kuma” tai maganar tana jin hawaye masu dumi na taruwa cikin idanuwanta.

 

BAYAN KWANA BIYU

 

A kwana biyun nan babu wani shiri a tsakanin su da Zaid , baima kara gwada yi mata magana ba. Asalima duk wani abu dazai hada magana a tsakanin su kauce mishi yake. Ita ke ordern Abincinta,  shima yayi na shi,  kulleta yayi ya bar tankata,  Su biyun yake azabtarwa da hakan. A bangarenta tana kewar muryarshi, har fadan da suke yi kewarshi take yi. Kaman yasan tunanin shi take yi ya shigo dakin.

Kanshi tsaye inda take zaune ya karasa yana zama shima, sosai ya hade space din dake tsakanin su “Look at me” ya umarta ta yanayin da ba zata iya musa mishi ba, fuskarshi ta kalla, ya fada, idanuwanshi sunyi zuru-zuru. “Nagaji…ban taba dauka ina Son  zaman lafiya ba… Ban taba dauka zan nemi zaman lafiya a tsakanin mu ba. Kome zance bazai gyara abinda nai ba, bazai gyara abinda ya faru ba” kallon shi take tana son ganin zuciyarshi ta cikin fuskarshi. Tana son ganin duk wani alama dazai nuna mata kalamanshi karya ne, wata yaudarar yake son shirya mata ta kasa.

Duk yanda ta so shareshi ta kasa,  muryarta na rawa tace “Ina tsoro, ina tsoronka, saboda me zan sake yarda dakai?” hannunta ya kamo ya dora kan kirjinshi inda zuciyarshi take.

“Karki yarda dani, karki yarda da kalamaina, ki saurari yanda take bugawa a kan hannunki. Da farko na dauka a lillibe take da son daukar fansa. Saida ta bude naji abin da nake ji daban ne, bance ki yarda dani da wuri ba…” tana jin zuciyarshi na bugawa a tafin hannun ta da sauri da sauri. Itama tata zuciyar bugawa take, hawaye na taruwa a idanuwanta saboda kalamanshi na wargaza mata duk wani bango da take tunanin ta gina na kare zuciyarta daga shi. Runtsa idanuwanta tayi hawayenta na zubowa.

 

“O. M. G,  Ziyaa please karkiyi kuka”  rokonta yake, sosai kukan ya kwace mata, saboda tana jin tsoron shi, tana jin tsoron abinda ya faru ya sake faruwa. “Ka daina, dan Allah karka sake hurting dina, zuciyata zata tsaya, zata daina bugawa” girgiza mata kai yake yana janyota jikinshi hadi da rungumeta yana son tai shiru, saboda gabaki daya kukan da take ya birkita mishi lissafi.

 

“Bazan sake ba, kuskure nayi, bazai sake faruwa ba” yace cike da assurance yana jin kanshi daban. Yana jin mutanen dayai amfani dasu dan cin ma burinshi, Sumbatar goshinta yayi saboda baya son girman laifukanshi su danne shi da wuri haka. Bai shirya ba. Dagowa tai daga jikinshi tana goge hawayen ta. “Kabani wayata…” ta bukata, 6ata fuskarshi yayi cikin rashin fahimta “In har da gaske kake ka bani wayata. Inhar duk abinda ka fada ba yaudara bane kaban wayata” ta karasa maganar tana tsare shi da idanuwanta,  ya zata zasu iya rayuwarsu su biyu ba tare da ta bukaci wayarta ba, ya zata zai maye mata gurbin Family dinta,  su biyu ba tare da kowa ba,  amma in har hakan zai sa su zauna lafia,  in hakan zai sa ta yarda dashi zai mata.

 

Wayarta na kano, “kina son Sabuwar waya? ” ya tambaya a takaice, girgiza kai tayi tace “ni nawa nake so” Wayarshi ya zaro ya latso Idi,  tana kallon yanda yake waya yana bashi Umurni, ita fa gwadashi takeyi,  haka kawai ta ji hawaye na sake zubo mata. Akan me zuciyarta zata sake yarda dashi? Akan me ma zata amince cewar da gaske sonta yake… Juyowa yayi dungurgum kanta,  hakan ua katse mata tunanin da take. Dawowa yai inda ya tashi ya zauna “Anjima za’a kawo miki daga Kano” goge fuskarta ta sake yi, cikin sanyin murya tace “Da gaske? Are you for real?” yanayin da tai maganar da fuskarta ya sashi kwashewa da dariya.

 

Sake ware idanuwa take cikin wani sabon mamakin, dariya yake, da gaske dariya yake, hannu takai ta taba shi “Me ka sha? Ina Zaid  yake? Me kayi dashi?” da murmushi a fuskarshi ya kama hannunta yana matsawa dab da ita, yanda tana jin hucin numfashin shi a fuskarta. “Soyayyarki na sha, ga Zaid  nan, abin mamaki ko? You tame the beast of in me, kin canza ni”

 

Gani yai zata lumshe idanuwanta yai saurin hura mata iska a fuskarta “Don’t, karki boyemun” warewa idanuwanta sukai batare data shirya ba. Sun jima a hakan tana jin yanda kalamanshi da shirun shi suka hadar mata,suka wargaza duk wani katanga da ta gina a tsakanin su “I will kill you if you betray me again,  bansan yanda zanyi ba, I will google and watch how to do it on YouTube but I will, I will kill you (Zan kasheka in ka sake yaudarata) ” wannan karon dariya yake daya manta yanda ake irinta. Dariya yake da dukkan zuciyarshi. Ziyada ce ke threatening dinshi wai. Yarinyar dako fada bata iya ba kamun haduwar su. Yarinyar da ko muryarta saika saurara sosai zaka ji tashin ta. Dukkan su sun canza, rayuwa ta canza su. Soyayyarta yake ji a duk wani abu na  jikinshi.

Itama abin dariya ya bata kuma, musamman data kalli kirar Zaid  da tata, ta kalli yanda ko naushin shi tayi tsaf zata iya targada yatsunta, “Ka canza ni” ta fadi tana kallonshi “Mun canza juna” ya fadi yana kallon cikin idanuwan ta. “Kin yarda mu zauna lafiya? Kin yarda dani? Kin yarda bazan sake hurting dinki ba?” ba sai ya tambaya ba. Amman ba zata mika wuya da sauri haka ba “Bari a kawo mun wayata tukunna” girgiza kai yayi, ta yamutsa fuska “Ka daina yi kaman ba daga wajenka na koyi komai ba” murmushi kawai yayi, tasa shi surutu mai yawa yau din nan. Hannunta kawai ya kamo yana kwantar da ita a jikinshi, bata musa ba, dan su duka suna bukatar comfort din.

 

A yanda suke ta amince dashi,  Zuciya ce qanda bata da k’ashi,  Allah ne shaidarta tana son Zaid sosai,  ta kalleshi da idonshi ke a lumshe,  bata yi kokarin raba jikinsu ba tace “ina so na san dalilin da ya sa ka ma Mummy abunda ka mata,  shin ka santa a wani gu ne?  Shin ta taba maka wani abunne? Akwai wani unfinshed bussines ne tsakninku?  Meyasa ka gaya mana bak’aken Maganganu, meyasa ka Azabtar da zuciyata?” ta lura yanayinshi ya chanza,  kanta na k’irjinsa ta rantse ta ji bugun zuciyarsa ya chanza, Yana Son Ziya,  a yanzu faranta mata shine Wajibinshi, baya son ranta ya baci,  baya son ta shiga damuwa,  ba ya so ta tsani kanta saboda kuskuren Mahaifiyarta, sabida Farincikinta da kwanciyar hankalinta ba zai gaya mata Alakarahi da Mahaifiyarta ba,  kamar ba zai tanka ta ba yace “Ziyaaa,  there are certain things that are better left unsaid (Akwai wasu abubuwa da rashin fadansu shine Alheri) saboda ke zan manta da komai ya faru, ki san na baki matsayi babba,  zan sadaukar da kuddirin da na girma dashi tun ina da shekara 11 saboda ke,  Son ki ya girmi komai da nake da, so kema ki manta da komai ya faru” taji seriousness a muryanshi,  tana tsoron jin wani abun da zai ruguje mata farinciki ko nashi,  ta sake gyara kanta a jikinshi cike da shagwaba tace “”Mu koma Gida” a hankali ya bude idanuwanshi,  yace “i like it here daga ni sai ke,  no body else,  just us” gyada kai tayi kafin ta zauna da sauri tana dukkan kirjin irin shima ya tashi zaune,  haka ya zauna yana kallonta ta nuna shi da yatsa tace “Kar ka sake karya min zuciya,  kar ka yaudareni,  na baka daukkan so,  na baka dukkan kaunata, daga yau har zuwa ranar da zan ja numfashin karshena” kallonta ya tsaya yi kamar hoto,  tana jiran amsa daga bakinshi,  be san me zai ce mata ba,  dama duk wasu kalaman da yake gaya mata da Armstrong ke rubuta mai ko ya karanto mai,  be san ta yanda zai maida mata martanin kalamanta ba,  ya kuma san kalamanta na bukatar amsa,  ido ta bude tare da dan bugunshi a kirji tace “Ehem Ina jinka” gyada kai ya hau yi kamar k’adangare yace “Nima haka” Dak’una fuska tayi tace “kaima mene?” yace “abunda kika fada” turo baki tayi tace “ni gaskia ban yarda ba” be san me zai ce mata ba,  be san ya zaiyi ba,  kar ta gano be iya komai ba,  kar yayi hurting dinta inta san cewa duk abubuwan da yake gaya mata ba yin kanshi bane,  da sauri ya hade bakinshi da nata don kar ta gano gazawarshi, sun dade a wannan yanayin kafin ya saketa dukkansu idanunsu a lumshe,  bakon feeling na shigansu,  jikinsu dukka na rawa,  ba su saba ba,  ba su taba ba,  this is their first,  kalma daya ya san zai iya fada mata kuma yayi meaning dinshi, cikin wata irin murya yace “You are My Always and Forever” cikin sanyin Murya tace  “Always and Forever?” ya tallabo fuskarta da hannu bibbiyu yana gyada mata kai kamar lizard yace “Always and Forever,  i promise” da sauri ta rungumeshi tace “Allah ya dauwamar damu cikin farinciki da zaman lafiya,  Allah ya kwabe fitina tsakaninmu,  Allah ya bamu zaman lafiya da zuria dayyiba” shima rungumeta yayi yana dariya yace “Amin My Forever”.

 

Sun dau tsawan lokaci a haka kafin yace “Hello Madam,  a dagani ko?” kunya ya lullubeta sosai ina kasa ta shige don kunya,  ta boye fuskarta cikin kirjinshi,  yayi daria yana kara matseta a jikinshi,  Wayarshi yayi k’ara,  ko motsawa beyi ba, Ziyada ce ta zame jikinta daga gareshi,  ya samu ya dauka wayan “Idi ya? Alright” ya kashe wayan ya sa takalma ya bude kofar dakin,  ya amsa sakon sa Idi ya bashi,  “Yauwa” kadai Zaid yace ya maida kofa ya rufe, ya dawo kan Gado ya mika mata Wayar yace “Ga Akwalar wayarki” kallon wayar tayi ta sa hannu ta rufe bakinta saboda murna kafin ta rungume shi tace nagode sosai, I love you so muc,  ya akayi aka dauko?  Naga anyi sauri” a takaice yace “Jirgi ya hau” Awwn,  thanks my forever” ya manna mata peck a goshi, ya mike ba zai iya sauraranta tayi waya da yan gidansu ba yace “bari inyi wanka mu fita ganin gari tunda baki fita ba tunda kika zo” ta gyada mai kai ta na kunna wayar,  toilet ya shiga don yin wanka,  ita  kuwa ta latso Mummynta.

 

K A N O

 

Zaune  suke a Parlo gabaki dayansu suna shan Tea and Bread da kwai, Wayar Mummy tayi k’ara,  ganin Ziyada ta sa ta saurin ce musu Ziyada ce,  duk suka tsaida kalacin gabansu na dukkan ukuuku suna rokon Allah ya sa lafia,   dauka tayi tare da sa Handsfree,  muryan Ziyada ya karade Parlorn “Hello Mummy ina kwana” bakin Mairo har rawa yake,  tace “Ziyada,  ya kike?  Kina lafiya?  Ince mijinki be miki wani abu ba?  Yana muzguna miki?” Majeed  a chafe da “Zuzu kina jina?  Are you Alright?” Zaineema ma tace “Sis kiyi magana, kina lafiya?” Zinatu ma tace “Ya Ziyada” dariya sosai Ziyada keyi tace “Relax Guys,  i’m fine, who is missing me?  me ya faru ne,  naga you sound worried kamar an ce muku ban lafia”Mummy tace “yo ba dole ba,  sanin wnada na barki dashi ai hankalin mu dole ya tashi,  ki gaya min if hes hurting you,  Daddynki da Yamajinki sunzo gidanki an hana su shiga” Ziyada tace “ku saurareni,  Mummy,  abunda ya faru  rannan was a complete misunderstanding,  amma komai yazo karshe yanzu, yanzu munyi tafiya munzo bauchi,  yazo wani aiki ne,  amma zamu dawo nan ba da dadewa ba,  ku kwantar da hankalinku,  everything is alright kunji?” Ajiyar zuciya suka sake a tare,  Mummy ta kara da cewa “haba nidai ince,  na san Alhaji Zaid ba haka yake ba,  akasi aka samu,  kice mai ba wani abu,  komai ya wuce,  ki tabbata kin samo ma Gatan Marayu takwara kafin ki dawo Kano” kai Ziyada ta dafe saboda kunya duk sunji kunya,  Ziyada ta shaew maganan ta hanyar cewa “YaMaji ina Daddy?” Daddy yace”Ina jinki yar gidan Ya Maji” tayi daria bayan sun gaisa tace “Daddy kuyi hakuri kunzo an hanaku shiga” Daddy yace “bakomai Allah ya muku Albarka” sai da Ziyada ta gaisa da Hajjo kafin tace ina Najwa,  tace kinsanta da kadaicwa tana daki” Ziyada tayi daria tace zan kirata,  sun dade suna waya kafin sukayi sallama.

 

B A U C H I

 

Sai da ya tabbatar ta gama waya kafin ya fito daga shi sai towel,  rintse ido tayi gam,  shi ko ya mata daria ya bude jakkarshi ya shirya hankali kwance jikin nan sai kamshi yake,  yace “Oya Muje ko?” tace “wai ina?” ya kashe mata ido yace “sightseeing” ta turo baki tace “bayan baka dauko mun kaya masu kyau ba” yace “to wa ya ja?  Ba sai da nace miki ki shirya kayanki  ba?” ta murguda mai baki,  yace ” bari a kawo miki kaya,  wasu iri kike so?” tace “Doguwar riga Jallabiya” waya ya dauko ya latsa yayi waya,  ta bishi da kallo tace “wai kai komai sai dai kayi waya?” be tanka ta ba ya sakar mata murmushin gefen fuska.

Ba a dau lokaci ba aka kawo dogayen riguna a paper bag kala kala,  designs designs, sai jakka da takalmi, duk sun mata kyau,  wata Ja da ta dauke mata ido ta dauka ta shiga toilet tasa, chan sai ga ta tafito,  yatsunshi na karshe guda uku ya daga mata alamun tayi kyau tayi murmushi, suka fito daga hotel room din suka shiga lift suka sauka k’asa.

Convoy dinsu har sun taru suna jiran sakowanshi,  Faisal na daga gefe,  ya kalleshi yace “Yanzu duk motocin nan ni suke jira, DonAllah ba sai kun bimu ba,  Yankari Game reserve kadai zamu” Faisal yace “Okay Mota Uku kawai za su bi” Zaid ya marairaice yace “Daya donAllah” Faisal ya karasa gun Motar tsakiya ya bude baya ya na me kallon Ziyada yace “Biyu,  Madam Bismillah” Ziyada ta shiga tana Daria,  Zaid ya buga mai harara,  aka bude  mai shima ya shiga baya wurin Ziyada,  Faisal  ya kalli sauran drivers din ya sallamesu,  yace motar Steve kadai zata biyosu,  shima ya buda gaba ya zauna ya kalli Driver yace “YGR zamu” Driver ya ja motar  sai Yankari Game Reserve.

 

Daga Zaid sai Ziyada,  Bangaren Dabbobi suka nufa, nan Ziyada ta dinga tsalle taga wild Animals su Lion, Tiger,  Chimpanzee da sauransu,  abun ya kayatar da ita matuka, waya aka bugo ma Zaid daga Kaduna, dauka yayi yace “Hello Babangida” bayan gaisuwa Zaid ya buga Salati, da sauri yace “ba wanda ya k’one ko? Is everyone safe?,  Alhamdulilah i’ll make the call” Faisal ya matso kusa dashi yace “Oga,  is everything Alright” Zaid cikin wani yanayi yace “Gobara akayi a Gidan Marayu,  amma ba wanda ya kone suna lafia” ka kira Julius Berger,  suje su chanza Ginin Gidan a rushe inda ya k’one” suna wannan Ziyada na chan bata san me ake ba,  hankalina na kan kallon dabbobi,  ji tayi an mata sallama,  dagowa tayi ta kalleshi.

“laa,  Ya Amjad ina wuni” Amjad yace “ashe ke din ne,  ya kike ya gida ya su Mummy?” tayi murmushi  ta amsa da lafiya lau muke” yace “ke dawa kuka zo?” ta murmusa tace “ni da Mijina”  da mamaki ya zaro ido yace “ashe kinyi aure” tace aikuwa,  bata ankara ba sai ganin Zaid tayi saman kansu yana haki kamar tsohon zaki,  shi be san da wa ma take tsaye ba,  yana waya ya hangota  tana fara da wani Namiji ba shi ba,  ranshi bace,  bata lura da yanayin da yake ciki ba tace “Ga Mijina na nan” Amjad ya zaro Ido yace “ZSA” Zaid ya juyo ya kalleshi, ba yabo ba fallasa yace “Amjad” Amjad yace “Dont tell me kaine Mijin Ziyada” Zaid ya tsuke fuska be amsa shi ba,  sai Ziyada tace “Eh Shine Mijina” Amjad yayi wani irin dariya yace “Seriously Zaid Sadam Audu? Seriously kai ka auri Ziyada? Ohh now i see why you call me telling me to leave her,  ashe so kake kai ka aureta,  i was so stupid to believe  all you said” Ziyada tace “Whoa!  What are you talking about?” Zaid ya riko hannun Ziyada yace “mu tafi” Ziyada ta  tirje  tace “Me yake cewa My Forever?” Amjad yace “tsaya kiji, kin tuna randa na fara zuwa gidanku,  randa na fara ganinki?  From my looks kin san ina sonki da duk wani abunda nake dashi,  kin san na mutunmiki,  ki tambaya Mummynki yanda na fara sonki da ta nuna min pictures dinki,  bansan ya akayi ba,  ban san ya akayi  ZSA ya san cewa ina sonki ba,  bansan ya akayi ya san nazo gidanku ba,  bansan yana da numberna ba,  sai kirana yayi yace min in rabu dake,  ke yar iska ce,  ciki ki kayi shiyasa aka cireki daga Baze University,  and kuma ana tunanin kina da HIV,  ganin ki kamila ya sa zuciyana kokonto,  but ganin shi he’s always a serious man,  ban taba zatan zaiyi making dinshi up ba,  ban yi zaton yana da wani dalilin da zai min karya ba,  shiyasa kika ba tare da na ce miki komai ba na fita a lokacin,  but yanzu na gane ya shiga tsakaninmu ne don ya sameki kuma ya ci nasara tunda gashi ya aureki” tuni Hawaye ya soma kwaranyowa daga fuskarta,  kirjinta kamar zai fashe saboda bakinciki,  tafiya ta farayi bata san ina take jefa kafarta ba,  bata damu da sauran mutanen da ke kallon ta ba,  buguzum buguzum take tafiya,  a guje Zaid ya bita,  ya riko hannunta,  tana juyowa ta sauke mishi hadadden Mari a a fuskar shi,  ta juyata cigaba da tafiyarta,  bata da masaniyar inda zata,  binta ya cigaba da yi,  yana mata magana,  da karfi a juyo tace “me zakace min?  wani karya zaka min Zaid?  Daukar Karuwa ma kake min ashe bansani ba?  Dagaske Zaid?  Ni Zaid?” zai yi magana tayi saurin dakatar dashi tace  “Baka da abinda zakace  min,  Zaman mu Ya k’are,  Zargi a shigo tsakani,  dole ka sakeni Zaid,  dolenka”…

 

Whatsup Lovers? Late night post huh?  Bear with me gab muke da landing,  I heart Y’lls to pieces.

Vote and Comment

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode.

 

Biebee Isa.

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣7⃣

 

Zaid ya kai hannunshi kan fuskarshi ya shafa sajensa kamar yana goge zufa a jiki, ranshi ya 6aci, ya k’ara isa gurinta yace “Ziyaada, listen” ta waigo ta kalleshi rai a 6ace tace “Me zaka ce min? Kalaman Yaudara zaka sake watso min?” ranshi ya 6aci, inda ta san girman Laifin da tayi, inda ta san girman laifin daukar hannu ta mareshi cikin baiyanar Jamaa, da bata fara ba, ya rantse inda Armstrong na nan, ya ga Marin nan, ba zai damu in Ziyada matarshi bace zai mata ligiligi runtse ido yayi ya bude a hankali, murya cike da Umurni yace “Shiga Mota ki jirani” be bata damar gardama ba ya juya inda Amjad ke tsaye ya k’arasa yana kaiwa kusa dashi ya dunk’ule hannu ya kai fuskar Amjad wanda ke tsaye yana murmushi, beyi zaton hannun Zaid a fuskarshi ba, taba gefen bakinshi yayi cikin jin zafin, har ya fitar mai da Jini, ya yunk’uro don ramawa, yaji an rik’eshi ta baya, Odilen Zaid ne, Zaid ya kalleshi yace “Ziyada Mayata ce, kar ka sake ganinta a ko ina ka mata magana, ba ruwanka da ita, kasan meyasa baka aureta ba? Saboda kai banza ne me gajeren tunani, kuma Ziyaa,, ta fi karfin Banza mai gajeren tunani” har ya juya zai tafi ya kuma sake juyowa yace “Ehen hak’ar dama don kar ka aureta ne, kuma ba ka aureta ba, so kaga hakana ta cimma ruwa, what i’m saying is, inka sake mata kallon Yariska ko wani abu, zan sani kuma zan nemeka, kuma kasan abunda zan iyayi, so ka kula”

“Oga What do i do with him?” cewaar Odilen da me rike da Amjad, Zaid ya juya, ba tare da ya sake kallonsu ba yace “let him go, he is Stupid” ya wuce inda sukayi parking Motoci Faisal na take mishi baya, nan aka zubar da Amjad a k’asa kamar wani kayan wanki yana nadaman tsautsayin da ya kawo shi Bauchi.

 

Mota ya shiga ya ganta zaune ta hade kai da bango, ba zai mata magana ba yanzu ransu bace yake, in ta sake mishi wani abu, ba zai iya dauka ba, shi yana ma iya bugeta in ta tunzurashi, dukkansu sai huci suke kamar Zaki, ganin yayi sun dau hanyar Hotel din, ba zai iya sake kwana a hotel din ba.. A Bauchin ma gabaki daya, ji yayi garin ya fitar mai akai, ya kalli Faisal yace “Kano” Faisal ya kalli driver yace “to the Airport” Driver ya cika umurni ya dauke hanya, Ziyada sai sheshekan Kuka take, shi ko yayi banza da ita..

Suna isa Airport Faisal ya siyan musu Ticket, suka tashi Faisal ya musu fatan a sauka lafiya kafin ya kira Idi yace “su shirya, Oga na nan zuwa Kano cikin 45mins”.

A cikin Jirgin ba me kula wani, har suka iso Kano ta bar kukan amma ta cigaba da kumburi, be mata magana ba ya fita tana binshi a baya, har inda ya ke ganin Motocinshi, na tsakiyar ya shiga, bata da wani zabin da ya wuce ta shiga wannan, be damu da masu musu sannu da zuwa ba, yayi banza dasu, itace ma ke amsa su, yanda taga yayi mugun dauke kai ya sa ta shan jinin jikinta, tunaninka kala kala har suka iso Gida, be bari anyi Parking ba ya fito ya mata slamming door a fuska, binshi tayi da kallo, “wai ai maka laifi a fika zucia” ta fada fili, ta dauki jakkarta ta shiga gida.

 

Yana shiga daki ya buga kanshi da bango don ya san ba zai iya shan Giya ba, so yake yayi ihu, takaici goma da ashirin, ga Rigimar Ziyada, ga Gidan Marayunshi anyi gobara, dafe kanshi yayi a baiyane yace”Ya Illahi, have mercy” shi din me Laifi ne, shi din me zunubai ne, shi yasan ba zai iya gyara abunda yayi ba, abu daya ya sani, bazai sake maimaita mistakes dinshi ba, abu daya ya sani ba zai kara yin abunda zaiyi hurting Ziyarshi ba, zuciyarshi ta dinga mai sake sake “Least abunda yayi musu kenan, to ina ga taji manyan laifukanshi? me zai faru in taji shine sanadiyar duk wani bakincinsu?” tsoro ya kamashi sosai, be son fita balle su hadu ta tambayeshi takkadar saki, be san ya rayuwa zata kasance mai ba tare da Ziya a ciki ba, be san me zaiyi da kanshi ba in ta rabu dashi, ba zai kara hurting dinta ba, meyasa ba zata yarda da hakan ba? A shirye yake ya zama abunda take so ya zama, sosai yayi nadama, toilet ya fada don watsa ruwa, ko da ya fito kin zuwa gunta yayi don karta tada mai hankali da maganar Saki, sai ya kwanta lamo yana waya kamar munafuki duk dai don kar taji muryarshi ta san cewa yana ciki.

 

“Tun tana sa rai zai biyota daki, har dai tagaji ta fito ta shiga Kitchen don daura abincin dare, tazo fita daga kitchen shi kuna ya fito daga daki, wuceta yayi ya bar parlo da alamu fita zaiyi, kar fa ya tafi wani gari ya barta ita kadai fa kamar randa aka kawota, nadama abunda tayi ya fara shigarta, ko zatayi fushi dashi, be kamata ta daga hannu ta Mareshi a gaban yaranshi ba, be kamata ta tsinkashi haka ba, ko bakomai Mijinta ne fa, tsoro ya kamata, kar ta kasance cikin Matayen da wutansu ke daban saboda rashin kyautata ma Miji, kitchen ta shiga ta kashe gas din, jikinta yayi sanyi, yunwa takeji amma bata da karfin dafa wani abu, daki ta koma ta rafka uban tagumi, tana ji aka kira Sallahr Maghrib, ta tashi ta dauro Alwala tayi Sallah. Tana idar wa ta daura kanta kan Gado ta shiga tunani, they were happy, yau ne karon farkon da taga Soyayya ingantacciya a idon Zaid, na Awannin da sukayi suna nuna ma juna So, taji wani irin dadi mara Misaltuwa, ko ba shi bane ya roketa da ta manta da komai shima ya manta kuma don ita? Meyasa taki mai uzuri? Meyasa ta watsa shi gaban mutane? Hawaye suka fara gangarowa daga idanunta, haka har aka kira Ishai tana zaune kan dardumarta, tana isha’i tayi shafa’i da wutir.

 

Kamar me tsoron wani abu ya bude k’ofar dakin a hankali yana lekenta, jingine ya ganta da Gado, kar dai fevern tane ya dawo, fitarshi yanzu maganin da suka bari a bauchi yaje ya siyo. Hannunshi dauke ne da Ledan Magani, da Basket bag me dauke da Abinci wanda bansan daga inda Zaid ya samoshi ba, zuciyarsa ya kai nesa ya karasa gareta, murya cikiciki yace “kici Abinci, in kin gama ki sha magani, be jira cewarta ba ya juya da sauri don kar ta mishi maganar da baya so, cikin zafin nama ta mike ta is gareshi ta rungumoshi ta baya kafin ta kwantar da kanta kan bayanshi, runtse idanunshi yayi yana jin hannunta rungume ta kirjinshi, sun dade a tsaye, jin hawayenta a kan bayanshi ya juyota a hankali yana kallon cikin idanunta yana me tsoron abunda zai fito daga bakinta.

 

“Kayi hakuri” ta fada a hankali, sadda kanta kasa tayi yasa yatsun shi biyu ya dago fuskarta, suna masu kallon juna, a hankali ya girgiza kansa yace “I hate fighting you, bana so har raina” da baki ta sake ce mai “i’m Sorry” Murmushi ya sakar mata yace “Na gaya miki abubuwa da yawa sun faru ai? Na gaya miki nayi abubuwa da yawa da ba zan iya gyarawa ba sai dai ba zan sake maimaita su ba, abunda Amjad ya fada gaskia ne, ni na ce mishi haka saboda kar ya aureki, saboda ni nake son Aurenki, amma na rantse miki shine karamin abu daga cikin ayyukana, i was a monster, i did inhuman things, Na gaya miki somethings are better left unsaid saboda kwanciyar hankalinmu duka, rashin fadan shine Alheri, ban san me zai faru ba saboda fadar abubuwan nan, and To God, i’m scared to lose you, i know the curiousity would be there, but for me can you let it go? For me can you forget about everything? For me can you ignore things that are yet to come? Can you forget the past and focus about the future? (Kuma tsakani da Allah ina tsoron na rasakai, na san zaki so kiji menene, amma zaki iya sharewa don ni? Zaki iya share komai, zaki iya dode kunnuwanki ta wasu da zasu baiyana nan gaba? Zaki iya share baya mu maida hankalinmu kan gaba?)”.

 

Be jira ansarta ba ya tallabo duka fuskarta da hanayenshi biyu yace “Wallahi Tallahi na chanza saboda ke, Wallahi na ajiye abubuwa da yawa saboda ke, i want you to trust me, ina so muyi putting komai a gefe, mu biyu kadai ne na junanmu, kin manta me nace miki dazun a bauchi before all that happened? You are my Always and Forever, baki yarda bane? Please believe me, I want you to trust me, ki yarda dani Ziyaa, i’m a changed person”.

Juya kalamanshi takeyi, har ranta ta gasgata kalamanshi, In kafiri ya karbi Musulunci sai a cigaba da kiranshi Arne? In Mazinaci ya tuba ga Allah tsakaninshi da Ubangjinshi ne, wannan kuma tsakaninta da mijinta ne, ba zatayi judging dinshi a laifin da ta kamashi a baya ba, zata dauki hukuncin da zata kamashi a gaba, a hankali ta dauki hannunta ta kai daidai kumatunsa da ta mara, ta shafa a hankali ta hada idanuwansu, tace “I trust you, I trust you with my Life” bude hannayenshi yayi mata tayi sauri ta shige cikin jikinshi kyakyawan runguma ya musu.

 

Daga bisani ya rada mata a kunne cewa “I’m hungry” a hankali ta janye jikinta daga nashi ta tafi kitchen, plates da serving spoon ta dauko musu, lekawa tayi daki yana tsaye inda ta barshi “Oya dauko Lunch Bag din” dauka yayi suka fito daga parlorn suka isa dining area, ta zage zip din ta fiddo da warmers din, ta bude coolern farko Peppersoup din jan nama ne, dayan kuma hadadden Couscous ne wanda ya ji kanya lambu da hanta, ki samun Peppersoup din da yawa, sai abincin kadan, a plate daban daban tayi yanda yace ta tura mishi gabanshi, ita kuma ta zuba Couscous din da dan yawa, ta sa naman a ciki, harta zauna tayi saurin tashi don dauko ruwa a fridge, tana budewa taga Fruits da drinks kala kala, bata ganin sanda ake kawo duk wani abun amfaninsu, babban roban ruwa ta dauko da wasu Orange drinks din daga kallo kasan foreign ne, ta kai kan table, lokacin Zaid cin Couscous dinshi yake cikin kwanciyar hankali, itama ta fara cin nata, kura mai ido tayi yanda yake cin abincinshi ya burgeta, tana kallon ya ture ya janyo plate din peppersoup din, har zai fara ci ya fasa tare da k’ura ma plate din ido, kamar naman zai yi magana, ta lura da yanayin chanjin fuskar shi, ta dan taboshi tace “Yadai? Lafia? ” Murmushi yayi tare da girgiza kai yace “Duk sanda zanci Peppersoup din jan Nama, na kan tuna Babana, yanason Jan Nama, ya san fa yana da Gout amma be fasa ci ba, Doctor ya kirashi ya hanashi, sai yace ya bari ashe in ya dawo Gida yana sa a masu aiki su dafa mishi, da Dr ya gane be daina cin naman ba, sai ya kirani yace in kula da abincin da yake ci, Baba be ji dadi ba da na sani, ina zuwa duk RedMeat din da ke fridge sai da na sa aka fitar dashi a gidan, sai Kaza saboda ban san Kifi shima ya bar ci, wai kinsan me Mutumin nan keyi?” ya tambayeta yana daria, ta girgiza kai itama tana dariar ba wai don tason dariyar me yakeyi ba, ya cigaba yana cewa “Wai sai mutumin nan ya siyo Naman shi ko ya sa Masu aiki su dafa mai amma kar a gaya min, sai yaje bayan k’ofa ya ci abunshi, kullum fa haka yakeyi, har sai da na kamashi redhanded yana ci a bayan kofa, could you imagine, the Whole Alhaji Sadam Audu Gatan Marayu boye bayan kofa yana cin nama a boye?” daria suke gaba daya, bata taba ganin faraarshi ba kamar yau, yanda yake bata labari yana daria tsakaninshi da Allah ita ba wai labarin ya bata daria sosai bane, amma ganinshi cikin annashuwa yasata biye mai tana daria, tace “to ya akayi ya rabu da cin Nama? ” Zaid ya tsagaita darianshi yace “Wa? That stubborn Old Man, ai ba zai bari ba, sai da ya kasance indai ya sa a dafa mai sai dai ni na kwace na ci, kullum haka muke, a dafa mai in cinye sai in sa mishi Kaza, wai sai yace be son Kaza, ji yake kamar Dusa, ke har ranar da zai mutu sai da yaci Parpesun kan rago”.

 

Ziyada tace “Allah Sarki, Allah ya gafarta mai ya sa ya huta” Murmushi Zaid yayi ya cigaba da cin Naman, “Matarshi fa? I mean Mamanka” jimm yayi tare da tsagaita taunar naman da yakeyi kafin daga bisani yace “ban taba ganin Matarshi ba” Ziyada da mamaki tace “Bangane ba” a takaice yace “Matanshi ba donAllah suke son shi ba, yana da wani laluri da Mace ba zata iya zama dashi ba, su kance baya iya haihuwa, to duk wanda kika ga ta aureshi, to ba dan Allah bane sai dai don dukiyarshi da abun da ya tara, to tunda muka hadu be sake wani auren ba” kai ta jinjina bakinta na nauyi zatayi magana yayi saurin katseta don ya san me take son cewa, a takaice yace “i’m only his adopted Son, the son he never had, the son he always wished for(Ni Yaron da ya rika ne, nine yaron da be taba samu ba, Nine yaron da ya dade yana son samu) “.. Ya danyi jim kafin yace “My Parents are Dead”. Allah sarki, sosai ta tausaya mishi, akwai tambayoyin da take so ta mishi, amma zata share, tace “Ubangiji Allah ya gafarta musu duka, ya sa sun huta, ya sa Aljanna ce makomarsu” ya ansa da Amin, ta chigaba da cewa “akwai hikima babba a taimakon maraya, balle shi wannan Marayu sama da dubu ya inganta rayuwarsu, ya dauke su kamar nashi, ai tashi tayi kyau InshaAllah,sai dai mu roki Allah ya inganta k’abarinshi” Sosai aji dadi da adduointa, yace “Ameen, i’m sure da ya ganki da ya soki, sabida yana son duk wani abun da nake So” blushing ta fara yi a hankali tace “Kana sona?” bata san yaji ba yace “Fiye da tunaninki” kallonta ya cigaba dayi kasa kasa, da sauri ta maida kanta kan plate tana cin Abinci, har suka gama ya tashi ya koma daki ita kuma tayi clearing gun da suka ci Abinci ta danyi kallo a ZeeWorld har wurin to 11 kafin ta kashe ta koma Daki don bacci.

 

Har ta hau Gado taji shigowarshi, juyawa tayi da sauri kasancewar duhu ne ta kashe Wuta bata ganshi ba, da fitilar wayara ta haka shi, tsaye ta ganshi cikin fararen shorts da top karama, ta dan muskuta tace “Bakayi bacci ba” cikin mintunan da sukayi kama da har abada yace “Erhm Eh banyi ba” ya karaso kan Gadon ya zauna, ta tashi zaune duk da cikin duhu ne amma tana hangenshi, tace “Lafiya? Kaje daki zan kwanta” da sauri yace mata “ina jin tsoro ne” ido a ware tace “Wani irin tsoro kuma?” yace “ba zan iya kwana ni kadai ba, ina tsoron dodo ne ko me ake cewa?” Ziyada ta fahimci ya ma raina mata wayau, ta juya mai baya tayi kwanciyarta tare da jan bargo.

 

Sosai ya hau kan Gadon, Gabanta ya hau dukkan ukuuku, a bayanta ya kwanta tare da juyo da ita tana fuskantarshi, a kunnenta ya mata rada “Ni Mijinki ne, be kamata ki juya min baya ba kinji?” a hankali ta gyada kai alamun taji, kare matseta yayi yana binta da wasu kauna a jiki, ganin yanda yake matsowa jikinta ne ya sa ta daburcewa jiki na rawa tace “Zanje Makaranta” Murmushi yayi don ya san ta tsorata dashi ne yace “Yanzu zaki makaranta?” da sauri ta gyada kai tace “Gobe” a takaice yace “na cireki” za tayi magana yace “Makarantarki zaki Koma, baze ko? Chan zaki cigaba da karatunki bata iya amsa shi ba, ta mayar da idanunta ta rufe.

A nutse yake nuna mata yanda yake jinta a zuciyarshi, cikin kwanciyar hankali yake nuna mata yanda soyayyarta tai mishi illa batare dayai amfani da kalamai ba. Cikin kwanciyar hankali yake hade zuciyoyinsu da ruhinsu waje daya cikin salon da bazai mantu a wajen su ba har abada.

***

*Bayan Wasu yan Kwanakin da ba su kai Sati ba*

 

Soyayya, Aminci da Shakuwa ta darsu a cikin zuciyoyin masoyan nan biyu, burin daya ya kyautata ma daya, a zaman da sukayi da juna sun fahimci halaiyar junansu, sun sake da junansu, sabida Kwanciyar hankali Zaid ya kashe wayoyinsa don samun hutu, shi fita kasashe bude ido be dameshi ba, niyyarshi ya dauketa su tafi chan Porthacourt su danyi hutu ba tare da hayaniya ba, a yanzu ne Zaid yasan cewa ya dade yana cikin bakin duhu, a yanzu ya san cewa akwai wani abu So, a yanzu ya san cewa mutum na zama da tsana da bakinciki a ranshi in yaso, in ko ya so cirewa zai cire ya musanya da So, Allah ne shaidarshi yana son Ziyada, yana son kyautata mata kamar yanda take kyuatata mishi, shiyasa jiya da daddare da ta zo mai da bukatar suje Gidansu be ce komai ba, amma duk da baya so, ba zai hana ba, dole ya hakura suje Gidan, wurin breakfast ya gaya mata ta shirya anjima su tafi, dadi ya kamata, ta tashi ta rungimeshi tana mai godia breakfast din da basu gama ba kenan.

**

 

Aunty Aynarh ta shigo Gidan da Sallama, duk yaran su ka tashi suka rungumeta, fara’a take tayi, ta zube kasa ta gaida Hajjo, Daddy baki har wuya yaga Masoyiya, a mutunce aka gaisa, Mummy sai famar wurga mata harara take ko a jikinta, ta kalle su tace “Allah ya sa ba ku daura abincin Rana ba, na riga na mana Lunch” Zaineema ta murmusa tace “ba mu daura ba ko” tace “yauwa perfect” Key ta mik’a ma Abdulmajeed tace “Ka dauko Kayan Booth” Abdulmajeed ya karba ya kalli Najwa yace “muje ki tayani dauko kaya” tashi tayi ta bi bayanshi suka bar Parlorn, Mummy ta kalli Daddy tace “bari in daura mana Abinci kafin yara su fara jin yunwa” Daddy yace “Maryam bakiji Hajia Aynarh tace ta yo abinci damu ba?” Galala ta kalleshi, kwana biyun nan tsinkata yakeyi gaban jamaa, kar ya mata haka yanzu ta wayance tace”wai sai a kara ko?” Daddy yace “Aa, am sure Abincin da yawa, ki bari da daddare ayi, yanzu dai muci wannan” zama tayi tana wurgar Hajia Aynarh da harara, ita ko hararar mugunta take mata.

 

“PureHeart, i cant wait naga su Maama don nace su bani ke na aura” Murmushi tayi tace “suna nan tafe cikin kwanaki” yace “Allah ne shaidana, ina sonki dominsa” Murmushi tayi tace “main tumase karta hoon” idonshi ya juya sama cikin salon banji me kikace ba, tayi daria tayi gaba, ya bi bayanta yace “Nidai a bar min magana da Indiyanci” dariya tayi tace “Aunty Aynarh na jira” ya bude Booth ya fiddo kayan ciki duka har su carpet, plates da cups, sai Flask kusan kala uku, suka dau iyakan iyawansu suka kai ciki, suka dawo suka dauka sauran.

 

Carpet din suka shimfida a tsakar Gidan, suka jera komai a kai, sai da sukayi Sallahr Azahar suka fito waje kan Carpet din, daidai nan Ziyada ta shigo Gidan da Sallama, duk sukayi kanta suka yayyabeta suna murnan ganinta, Oyoyo Oyoyo, daga baya Zaid ya shigo, baki Mairo ta washe, shi kuwa kamar an aiko mai da Sakon mutuwa, faraar fusakrshi ya dauke dif, Abdulmajeed a karaso gunshi ya mika mai hannu don suyi musabaha, ba yabo ba fallasa ya karba, tare da dan durkusawa ya gaida da Daddy da Hajjo da Aunty Aynarh da ke zaune kan Carpet, duk ya bi yaran gidan da kallo inda suke gaisheshi, tausayinsu ya kamashi, Zaineema yarinyar da yaso kamar me, be manta kaunar da ke tsakaninsu ba, yarinyan da Mairo ke rankwashinshi in ya dauketa, rashin imaninshi ya sa ya rabata da Mijinta, ya zaiyi ya gyara mistake dinnan? Idonshi ya kaiga Najwa wanda take wurga mishi wani mugun kallon “na san ko waye kai” da sauri ya dauke kai yana me jin tsoronta, kar fa ta ganeshi, kar ta tona mai asiri Ziyada a rabu dashi, Allah sa bata ganeshi ba, ji muryar Mairo yayi tana cewa “Ku shigo Parlo sannunku da zuwa” Ziyada tace “Aa Mummy, bari mu zauna a nan so kike ayi picnic din banda mu?” Mairo ta tabe baki tace “ba wani picnic, dangin yarbawa ce tayi son iyawanta wai ta dafo mana Abinci, kamar munce ba mu da abinci”. Ziyada tace “Yayy, dama nayi missing Abincin Aunty Aynarh” Mairo takaici kamar ya shideta, tace “Alhaji Zaid kai ka shigo Parlo ka zauna” banza yayi da ita, ba wanda ya lura da ko gaishe da Mairo beyi ba, ya samu wuri kusa da AbdulMajeed ya zauna, wanda Hajjo ke gefenshi Najwa na nata gefen, Mairo tace “Lah, Alhaji, zaman kasa be kamace ka na, please ka shigo ciki” ko kallo bata isheshi ba, Daddy yace “Maryam ki barshi ya zauna cikin Yanuwanshi mana”

 

“‘Yanuwanshi” kalmar da Zaid ya fada kenan, ya kalli gefen shi ya ga su Hajjo da Muhsin da Zaineema zaune, dayan gefen Daddy da AbdulMajeed da Zinatu da Ziyada a zaune, sai ya ji shi kamar daya daga cikinsu, ba abunda ya kai bond din Yanuwan jini karfi, ba abunda ya kai feeling din dadi, tabbas yaji wannan connection din, ya ji shi among them, ko yaki ko ya so “they are his Family” yayi Alkawarin gyara laifinshi, “I will fix this , i will fix everything ” ya fada a ranshi..

Daddy yace “Oya a bamu mu ci” Hajia Aynarh tace “ai ga yara na nan, su zuba mana” Mairo kamar ta mutu ganin yanda Hajia Aynarh ke fi’ili gaban Daddy.

Zaineema ta bude kulolin, Faten Wake da Amala, duk wanda kake so sai a sa maka, Miyar Amalan yaji Ganda da Stock fish, Alallen kuwa ya hadu da kwai da kifin Sardine, Faten waken ma yaji dryfish da Ganda.

Tace “Daddy me zaa sa maka? Hajjo me zaki ci?” tace “a zubo min Faten Wake, mun dade bamu hadu ba” akayi daria, Daddy yace “a zuba min Amala” Mummy fa baki ta yatsina tace “Moimoi”.

Ziyada tace “YaMaji me zakici?” ya tashi daga durkuson da yayi yace “Zuzu serve your Husband, ni da kaina zan zuba abinci na” Hajia Aynarh tace “banda abunki Ziyada ana ta Miji wake ta wani YaMaji”.

Ta k’asa ta kalli Zaid din da yayi mugun dauke kai, yana iya cin Abincin Musamman da yaji cewa ba Mairo tayi shi ba, Hajia Aynarh tayi, kuma yana iya cin Amala, don yana son abincin, ita kuma bata yi zaton zaici ba shisa bata tambayeshi ba, a hankali suka hada ido yace mata “Amala” Ziyada ta murmusa, Najwa tace ita kuma a bata irin na Hajjo ba wai don ta san meye ba, amma don yayi kama da wani soup din India, kowa ya fadi abunda zaici akayi serving kowa..

 

Addua Daddy ya umurta ayi, a tare kowa yayi suka fara cin Abinci, kasancewar duk Abinci da busasshen kifi da kuma gasasshen kifi akayi, in ba ci kayi ba ba zaka gane kifi bane, yafi kama da Nama.

Ko Cokali biyu ba suyi ba numfashin Zaid da Najwa ya fara daukewa, sama sama Numfashin ya fara, AbdulMajeed da ya kafa Najwa da ido ya lura da abunda takeyi yayi saurin ajiye spoon yace “PureHeart are You OK?” Zaineema ta kalli Najwa tayi saurin mikewa tsaye Hajia Aynarh ma haka, Najwa me ya faru? Abu takeyi kamar mai neman shidewa, Ziyada ta dan waiga ta kalli Zaid, gabanta ya fadi, irin abun Najwa yakeyi, numfashin shi samasama, fuskarshi yayi ja, da sauri ta karasa gunta “My Forever, lafiya” Hankalin Mairo ya tashi ta mike ta ci kwalar Aunty Aynarh “Munafuka Algunguma, me kika sa ma Abinci? Me kika sa ma sirikina? So kike ya mutu” Aunty Aynarh ta tsure sosai tana girgiza kai tace “Wallahi bansa komai ba, Wallahi ba abunda na sa, mukai su Asibiti” Najwa ta riko hannun Hajjo tana bankarewa kamar zata mutu, Zaid ma hannu ya sa ya rike wuyanshi yana jan numfashin dake fita da kyar, fuskar nan tayi Ja, Daddy yayi saurin fita don taro A daidajta sahu a kaisu Asibiti, yana fita ya ci karo da Convoy din Zaid, Ziyada Hawaye kawai takeyi hankalinta tashe, Abdulmajeed hankali a tashe ya kalli Aunty Aynarh yace “Aunty kinsa Kifi a abincin nan?” da sauri ta gyada kai tace “duka abincin da Kifi nayi shi” Abdulmajeed ya ruga kitchen a guje, Ya shiga bincikar Kayan Miya da ya siyo dazun Tomatoes ya dauko, ko wankewa beyi ba ya fito ya mika ma Ziyada 1 yace ki bashi, lokacin sun fara fita daga hayaccinsu, fasawa yayi da bakinshi ya juye ma Najwa ruwan tumatirin a baki, haka Ziyada ta ma Zaid, a hankali a hankali numfashin su ya fara dawowa daidai, daidai nan Idi da wasu Yaran Zaid suka shigo sukayi kan Zaid wai zasu kaishi Asibiti, daga musu hannu yayi yace “i’m fine” Ziyada tace “me ya faru da kai?” Zaid yace “ina tsammanin Abincin nan akwai Fish, and i’m allergic to Fish” daidai lokacin da Najwa ta ke ce ma Hajia Aynarh “Dama bansan da kifi a cikin Abincin ba, shine naci?” Hajia Aynarh tace “I’m So Sorry, wallahi bansan ba kwa son Kifi ba, Abincin ba wanda ban sa Kifi ciki ba, kuyi hakuri donAllah” Najwa tace “Laah Aunty ba wani abu, ni in na samu irin attack dinnan da na sha tomato zanji normal, ai farkon zuwana Nigeria na taba samun attack din” Abdulmajeed yace “shiyasa na tuna Tomato ne first Aid treatment din” Zaid ya kira Idi ya zo kusa dashi, ya rada mai abu a kunne, da sauri ya fita, Aunty Aynarh duk tayi wani iri, gani take laifinta ne, Zaid ya kalle su Daddy da sukayi cirko cirko suna kallonsu yace “Baba Abba ku zauna ku cigaba da cin Abincinku, Ni kifin ne bana so, yanzu zaa kawo min wani Miyan sai in ci” Daddy ya sage yana kallon Zaid, wani abu ke bin zuciyanshi, dunia Zaidun Sada kadai ke ce mishi “Baba Abba” jiki a sake ya zauna, yace da Muhsin su cigaba daci, Daddy ya kallesu yace “sai kuka tuna min da k’anina Marigayi, kunsan shi ko kanshi Kifi ya ji sai ya fara sheshek’a?” Hajjo ta chabe tace “haka ne, ko abinci nayi da Man kifi in ya fara Amai kamar zai zazzago kayan cikinsa” Zaid ya runtse idonsa yana tausar zuciyarsa. Abincinsu su ka cigaba daci banda su 3, Zaid da Najwa da Mummy, su kadai ne basu cin Abincin, gaban Mairo ke dukan uku uku, ta kalli Najwa a kalli Zaid, tunanin da bata son yi ta fara yi, Sada be cin Kifi, Zaid din Sada be cin Kifi, Wannan dan Sada ne. Da sauri ta girgiza kanta ta tashi kamar mahaukaciya ta shige daki, daidai nan Idi yayi Sallama da Cooler a hanayensa, Gaban Oganshi ya Dire, Ziyada ta bude Miyan Kubewa danya ne da yaji Jan Nama, ta bude wani Amalan ta sa mai da miyan Kubewar, ta kalli Najwa tace “in sa miki ko? ” kai Najwa ta daga, Ziyada ta zuba mata suka cigaba da ci, Hajia Aynarh ta saukar da Ajiyar zucia ganin basuyi zargin ko tayi poisoning dinsu bane.

 

I N D I A

 

Duk wasu Process na tafia sun gama, Jirginsu zai tashi Gobe zuwa Dubai, washegari su tafi Nigeria inda zasu isa Lagos daga nan suyi Kano, Paapa da Maama sunyi Resigning a wuraren Aikinsu, an basu kudin Sallama me tsoka, harta Motocinsu da Gidan da suke zaune sun saida, Paapa ya samu wani Agent dan Kano suna communicating, nan ya tura mishi kudi ya siya mishi dankareren Gida a Tarauni, don shi baya tunanin zai koma Gidanshi na da, yafi karfin ya tada Yayanshi a gidan da yake, ya bar mai Gidan nan har abada, Maama ta dinga shiga Gidajen Neighbors dinsu tana musu sallama, Vijhay Bhaiya yayi kuka sosai, Maama tace “InshaAllah zasu zo wani lokacin” bayan sun mishi Alheri me yawa, ko da ta shiga Gidansu Kaveri nan suka bata lokaci da Maman kaveri suna jimamin rabuwansu, Kaveri kuwa bata fito ba tana daki tana cizgar Kuka.

 

N I G E R I A.

 

Rigima Ziyada ke ta ma Zaid tun tashin su yau da safe don ya sanar da ita Tafiar gaggawa ta kamashi zuwa Taraba, zai biya Kaduna ya ga Gidan Marayu kafin Jirginsu ya tashi zuwa Taraba’s state. Ziyada tace ya tafi da ita, hakuri ya bata cewar tayi hakuri, ya dawo, da ya dawo zai musu processing Visa suje any country of her choice, sannan in sun dawo Gida zasu yi Parking su koma Gidan Babanshi na Asali a Kaduna, dolenta ta hakura amma taso ta bishi don bata son yayi nisa da ita. Alfarma ta rokeshi da ya barta a koma Gida har sai ya dawo, da farko k’i yayi, yace tayi hakuri ta zauna har randa zai dawo, tace “itadai aa, ba zata iya kwana ita kadai ba ” ba yanda ya iya ya amince mata da taje Gidan, a daren da zai tafi, makale suke da juna kamar cingam, baya so ta bishi sabida bussiness zaije yi, da wuya ya samu time dinta. Washegari da kanshi ya rakata har Gida bayan an musu siyayya a Shoprite, sunfi Minti 20 a gaban Gidan cikin Mota suna manne da junansu kamar kar su rabu, shagwaba take ta zuba mai, shi ko yayi ta biye mata, “i’ll miss you i’m My Forever” rungumeta yayi yace “i’ll miss you more” sun dade a haka kafin daga baya ya rakata har Cikin Gidan, suka gaisa da yan Gidan banda Mairo da ba wanda ya lura be gaisheta ba. Daddy ya masa godian Hidiman da yakeyi dasu. Ziyada a boye ta share hawayenta da zai tafi, shima duk yaji ba dadi, ta zama wani bangare na jikinshi.

****

Najwa sunyi waya da Su Maama sun gaya mata Jirginsu zai tashi a ranar da daddare, but zasuyi transit a Dubai washegari su iso lagos, dadi ya ziyarci Najwa, ta musu fatan a iso a lafia.

 

B A Y A N K W A N A B I Y U

 

Tun daga garin Allah ya waye yake jin nauyin jikinsa, ya kanji kunnenshi yayi wani irin Yammm, hannunshi kan mai nauyi wurin dagawa, Da k’yar yaje Sallahr Asuba da taimakon AbdulMajeed ya dawo Gida, duk da shima yace be jin dadin jikin nashi, Hankalin Yaran Gidan ya tashi, Daddy da Ya Maji basu lafia, duk da ya Majin ba kwance yake ba, duk suka zauna suka rafka tagumi suna kallon Daddy. Mummy ta lallabasu suka koma dayan dakin tace “a bar Daddy ya samu bacci” da kyar suka fita suka barshi shi kadai.

kishingida yayi kan Katifarsa yana tunano abubuwa da suka shude shekaru sama da 20, ya tuna Mutuwar kaninshi da Matarshi, gawarsu da ya kasa shaidawa Saboda k’una, ya rufe kaninshi da Matarshi da hannunshi, wani side na kanshi ya buga kamar an kwala mai darma, da sauri ya girgiza kansa, runtse idanunshi yayi ya na son tunano exact abinda ya faru, sai ya gano Me ya faru da Sada da Yesmin in ba mutuwa sukayi ba? A hankali komai ya soma kwaranyo mai,

Kalamanta da abubuwan da suka faru suka so mai sintiri a kwalawa kamar a lokacin ake yinsu

“ina so ka maida sunan duk Takaddun nan daga Sunanka zuwa sunan Abba” ya tuna Sada be mata gardama ba yayi yanda tace yace “nagama” shi karan kanshi yaji mamaki, ya tuna da tsoro ya tambayeta “Meyasa? Don me zaiyi haka?” ya tuna tsawar da ta mishi tace “shuttup, baka son ka mallaka Dukiyoyin Sada?” yace “ai yana bani dukkan abun da na buk’k’ata, hakan yayi” ya tuna yanda ta girgiza kai tace “aa, beyi ba, kana son dukiyan Sada” ya tuna yanda ya maimaita abunda tace kamar karatu” beyi ba, ina son dukiyan Sada” murmushi tayi ta kallo Abba tace “good”.

Ba a kwana ba ya tuna lokacin da ya ganta tayi nisa da tunani, ya tuna tambayarta

“Maryam tunanin me kikeyi haka?”

a takaice ta bashi ansan “tunanin Kashe Sada da Yesmin nikeyi” ya tuna yanda hankalinshi ya tashi cikin rudu yace

“Saboda mene Maryam? Sun ba mu duk abunda muke da burin samu a rayuwa”

“hakane, amma zamansu a doron k’asa barazana ce a rayuwata, shiyasa na yanke hukuncin kashe su”

Ya tuna yanda ya durkusa kan guiwowinshi ya na kuka yana rokonta gafara”Kiyi Hakuri Maryam, ba sai kin kashe su ba DonAllah, Sada danuwa na ne, kuma ina sonshi sosai”

Ya tuna yanda ranta ya baci tace “sai ka za6a ko ni ko shi”

Ya tuna yanda beyi dogon tunani ba yace “ke na za6a uwar ‘yayana, ina sonki, kece farincikina, zan iya rabuwa da kowa don in zauna dake, amma Sada danuwana ne, akwai Babba Alaqa tsakaninmu, ina neman Alfarma da ki barshi raye,in bakya bukatar ganinsu zan sa shi su bar garin,amma kar a kashe su donAllah Maryam”

A kausashe tace? “in kuma hakan zai bani farinciki fa?”

Ya tuna muryarshi me cike da tsoro da rashin jarumta yace “da hannuna zan kasheshi don baki farinciki, amma ina rok’onki da kiyi hakuri” shiru tayi kafin tace “Zasu bar k’asan, zasuyi nisa da mu, ba zasu taba dawowa ba har duniya ta nade”

Ya tuna tashin hankalin da ya shiga da tace haka, ya tuna yanda ta daka mai tsawa tace

“Ko ka fi son a kashesu?”

Ya tuna yanda ya girgiza kai da sauri yace

“a saka su suyi nisa damu”

Ya tuna yanda ya durkusa har k’asa yana mata Godia kan amincewarta na ba zata kashe su ba. Ya tuna Komai, Ya tuna Wallahi, Maryam ta dadw tana zaluntarshi, Maryam ta shiga tsakaninshi da k’aninshi, wai kuma sai gashi bayan kwana biyu a ka kawo Gawarwaki guda biyu wai Yesmeen da Sada, Anya sun mutu? a baiyane yace “aa ba su mutu ba”.

 

Maryam ta ha’ince ni, maryam ta zalunce ni, Kuka yakeyi sosai, be sama ma Yaranshi Uwa ta gari ba, k’arshen zamanshi da Maryam yazo, ba zai iya ba, a hankali ya tashi ya na dafe da bango ya fita waje, besan yanda zaiyi ba, amma yasan ba zai iya cigaba da zama dashi ba, don albarkacin yaransu, da ya maka ta Kotu.

A waje AbdulMajeed ya ga Daddy, yayi saurin karasawa gunshi yace “Daddy, ka bar jin jirin ne? Ka koma ka kwanta”

Mommy ta fito da sauri jin muryarsu, Duk yaran suka biyo bayanta har Hajjo, Mummy tace “Ah Daddy, har kaji sauki ne? Ta karaso gunshi zata taba shi yayi saurin janyewa, yace “kar ki sake ki tabani, muguwa Azzaluma” yaran suka kalleshi da mamaki, Abdulmajeed ya shiga rudu a hankali yace “Daddy…” Mairo bakinta a bude ta kasa magana, be taba mata haka gaban yara ba, ga mamakinsu sai ganin Daddy ya fashe da kuka ya zube kasa “Kuyi hakuri ku yafe min Yarana, ban zaba muku uwa ta gari ba, ku yi hakuri, na zaba muku jahila cikin jahilai a matsayin Mahaifiyarku” Ziyada ta fashe da Kuka, Zaineema da sauran Yaran ma suka fashe da kuka, AbdulMajeed ya rik’e Daddy yace “Daddy donAllah in Laifi ta maka ku shirya kanku, ku mahaifanmu ne, muna son ku duka, kuyi hakuri ku shirya kanku” Daddy cikin dan tsawa yace “In shirya da wannan hatsabibiyar? Tsakanina da Maryama Allah ya isa, ta shiga da tsakanina da

danuwana Sada, ta salwantar mun dasu” cikin Zafin Nama ya makuro Wuyanta “Ina kika kaimin Sada da Yesmin? Ina kika kai min su? Ina kikace su tafi? Ina Maryam?” a duk zatonta Zuciyarta ya fito daga Kirjinta, kasa motsi tayi, ganin komai take kamar a film, ta gama tsorata iyakan tsorata, karyarta ya kare, Asirinta ya tonu, Ajalinta yazo” Hajjo ta matso kusa dashi ta dafa tace “Haba Abba, me ya sameka haka? ina zata kai Sada? Ka manta Sada da Matarshi sun Mutu? Ka manta da hannunka ka rufesu? ” da sauri yace “Wallahi basu mutu ba, basu bane, cikin makircinta ne tace sune, Wallahi ita ta salwantar dasu, Umurnin ta suka bi suka shiga dunia” Hajjo ta durkushe a gun tana kuka me tsuma rai, su Ziyada da Zaineema Kukan suke, Najwa da ta gama fahimtar komai ta fashe da wani irin dariyan da ya juyo hankalinsu, a baiyane tace “Alhamdulilah”, duk da suna cikin tashin hankali kacokam suka bi ta da ido, da sauri ta isa gun Baba Abba ta rungumeshi tare da kwantawa kan kafadunshi, Baba Abba be da wani kuzari a kunne tace “Babana, kace Alhamdulilah” be san dalilin da ya sa ya biye mata yace “Alhamdulilah” daidai Sallaman Mutanen da ba zai taba Mance Muryarsu ba, gabaki daya suka juya ga k’ofar shigowa, Hajjo da tayi zumbur ta tashi, ita da Daddy sukace “SADA” Najwa tace “MAAMA” daidai da fitowar fitsari daga jikin Mairo luuuu ta ta fadi kasa sumammiya.

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa.

 

 

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣7⃣

 

Zaid ya kai hannunshi kan fuskarshi ya shafa sajensa kamar yana goge zufa a jiki, ranshi ya 6aci, ya k’ara isa gurinta yace “Ziyaada, listen” ta waigo ta kalleshi rai a 6ace tace “Me zaka ce min? Kalaman Yaudara zaka sake watso min?” ranshi ya 6aci, inda ta san girman Laifin da tayi, inda ta san girman laifin daukar hannu ta mareshi cikin baiyanar Jamaa, da bata fara ba, ya rantse inda Armstrong na nan, ya ga Marin nan, ba zai damu in Ziyada matarshi bace zai mata ligiligi runtse ido yayi ya bude a hankali, murya cike da Umurni yace “Shiga Mota ki jirani” be bata damar gardama ba ya juya inda Amjad ke tsaye ya k’arasa yana kaiwa kusa dashi ya dunk’ule hannu ya kai fuskar Amjad wanda ke tsaye yana murmushi, beyi zaton hannun Zaid a fuskarshi ba, taba gefen bakinshi yayi cikin jin zafin, har ya fitar mai da Jini, ya yunk’uro don ramawa, yaji an rik’eshi ta baya, Odilen Zaid ne, Zaid ya kalleshi yace “Ziyada Mayata ce, kar ka sake ganinta a ko ina ka mata magana, ba ruwanka da ita, kasan meyasa baka aureta ba? Saboda kai banza ne me gajeren tunani, kuma Ziyaa,, ta fi karfin Banza mai gajeren tunani” har ya juya zai tafi ya kuma sake juyowa yace “Ehen hak’ar dama don kar ka aureta ne, kuma ba ka aureta ba, so kaga hakana ta cimma ruwa, what i’m saying is, inka sake mata kallon Yariska ko wani abu, zan sani kuma zan nemeka, kuma kasan abunda zan iyayi, so ka kula”

“Oga What do i do with him?” cewaar Odilen da me rike da Amjad, Zaid ya juya, ba tare da ya sake kallonsu ba yace “let him go, he is Stupid” ya wuce inda sukayi parking Motoci Faisal na take mishi baya, nan aka zubar da Amjad a k’asa kamar wani kayan wanki yana nadaman tsautsayin da ya kawo shi Bauchi.

 

Mota ya shiga ya ganta zaune ta hade kai da bango, ba zai mata magana ba yanzu ransu bace yake, in ta sake mishi wani abu, ba zai iya dauka ba, shi yana ma iya bugeta in ta tunzurashi, dukkansu sai huci suke kamar Zaki, ganin yayi sun dau hanyar Hotel din, ba zai iya sake kwana a hotel din ba.. A Bauchin ma gabaki daya, ji yayi garin ya fitar mai akai, ya kalli Faisal yace “Kano” Faisal ya kalli driver yace “to the Airport” Driver ya cika umurni ya dauke hanya, Ziyada sai sheshekan Kuka take, shi ko yayi banza da ita..

Suna isa Airport Faisal ya siyan musu Ticket, suka tashi Faisal ya musu fatan a sauka lafiya kafin ya kira Idi yace “su shirya, Oga na nan zuwa Kano cikin 45mins”.

A cikin Jirgin ba me kula wani, har suka iso Kano ta bar kukan amma ta cigaba da kumburi, be mata magana ba ya fita tana binshi a baya, har inda ya ke ganin Motocinshi, na tsakiyar ya shiga, bata da wani zabin da ya wuce ta shiga wannan, be damu da masu musu sannu da zuwa ba, yayi banza dasu, itace ma ke amsa su, yanda taga yayi mugun dauke kai ya sa ta shan jinin jikinta, tunaninka kala kala har suka iso Gida, be bari anyi Parking ba ya fito ya mata slamming door a fuska, binshi tayi da kallo, “wai ai maka laifi a fika zucia” ta fada fili, ta dauki jakkarta ta shiga gida.

 

Yana shiga daki ya buga kanshi da bango don ya san ba zai iya shan Giya ba, so yake yayi ihu, takaici goma da ashirin, ga Rigimar Ziyada, ga Gidan Marayunshi anyi gobara, dafe kanshi yayi a baiyane yace”Ya Illahi, have mercy” shi din me Laifi ne, shi din me zunubai ne, shi yasan ba zai iya gyara abunda yayi ba, abu daya ya sani, bazai sake maimaita mistakes dinshi ba, abu daya ya sani ba zai kara yin abunda zaiyi hurting Ziyarshi ba, zuciyarshi ta dinga mai sake sake “Least abunda yayi musu kenan, to ina ga taji manyan laifukanshi? me zai faru in taji shine sanadiyar duk wani bakincinsu?” tsoro ya kamashi sosai, be son fita balle su hadu ta tambayeshi takkadar saki, be san ya rayuwa zata kasance mai ba tare da Ziya a ciki ba, be san me zaiyi da kanshi ba in ta rabu dashi, ba zai kara hurting dinta ba, meyasa ba zata yarda da hakan ba? A shirye yake ya zama abunda take so ya zama, sosai yayi nadama, toilet ya fada don watsa ruwa, ko da ya fito kin zuwa gunta yayi don karta tada mai hankali da maganar Saki, sai ya kwanta lamo yana waya kamar munafuki duk dai don kar taji muryarshi ta san cewa yana ciki.

 

“Tun tana sa rai zai biyota daki, har dai tagaji ta fito ta shiga Kitchen don daura abincin dare, tazo fita daga kitchen shi kuna ya fito daga daki, wuceta yayi ya bar parlo da alamu fita zaiyi, kar fa ya tafi wani gari ya barta ita kadai fa kamar randa aka kawota, nadama abunda tayi ya fara shigarta, ko zatayi fushi dashi, be kamata ta daga hannu ta Mareshi a gaban yaranshi ba, be kamata ta tsinkashi haka ba, ko bakomai Mijinta ne fa, tsoro ya kamata, kar ta kasance cikin Matayen da wutansu ke daban saboda rashin kyautata ma Miji, kitchen ta shiga ta kashe gas din, jikinta yayi sanyi, yunwa takeji amma bata da karfin dafa wani abu, daki ta koma ta rafka uban tagumi, tana ji aka kira Sallahr Maghrib, ta tashi ta dauro Alwala tayi Sallah. Tana idar wa ta daura kanta kan Gado ta shiga tunani, they were happy, yau ne karon farkon da taga Soyayya ingantacciya a idon Zaid, na Awannin da sukayi suna nuna ma juna So, taji wani irin dadi mara Misaltuwa, ko ba shi bane ya roketa da ta manta da komai shima ya manta kuma don ita? Meyasa taki mai uzuri? Meyasa ta watsa shi gaban mutane? Hawaye suka fara gangarowa daga idanunta, haka har aka kira Ishai tana zaune kan dardumarta, tana isha’i tayi shafa’i da wutir.

 

Kamar me tsoron wani abu ya bude k’ofar dakin a hankali yana lekenta, jingine ya ganta da Gado, kar dai fevern tane ya dawo, fitarshi yanzu maganin da suka bari a bauchi yaje ya siyo. Hannunshi dauke ne da Ledan Magani, da Basket bag me dauke da Abinci wanda bansan daga inda Zaid ya samoshi ba, zuciyarsa ya kai nesa ya karasa gareta, murya cikiciki yace “kici Abinci, in kin gama ki sha magani, be jira cewarta ba ya juya da sauri don kar ta mishi maganar da baya so, cikin zafin nama ta mike ta is gareshi ta rungumoshi ta baya kafin ta kwantar da kanta kan bayanshi, runtse idanunshi yayi yana jin hannunta rungume ta kirjinshi, sun dade a tsaye, jin hawayenta a kan bayanshi ya juyota a hankali yana kallon cikin idanunta yana me tsoron abunda zai fito daga bakinta.

 

“Kayi hakuri” ta fada a hankali, sadda kanta kasa tayi yasa yatsun shi biyu ya dago fuskarta, suna masu kallon juna, a hankali ya girgiza kansa yace “I hate fighting you, bana so har raina” da baki ta sake ce mai “i’m Sorry” Murmushi ya sakar mata yace “Na gaya miki abubuwa da yawa sun faru ai? Na gaya miki nayi abubuwa da yawa da ba zan iya gyarawa ba sai dai ba zan sake maimaita su ba, abunda Amjad ya fada gaskia ne, ni na ce mishi haka saboda kar ya aureki, saboda ni nake son Aurenki, amma na rantse miki shine karamin abu daga cikin ayyukana, i was a monster, i did inhuman things, Na gaya miki somethings are better left unsaid saboda kwanciyar hankalinmu duka, rashin fadan shine Alheri, ban san me zai faru ba saboda fadar abubuwan nan, and To God, i’m scared to lose you, i know the curiousity would be there, but for me can you let it go? For me can you forget about everything? For me can you ignore things that are yet to come? Can you forget the past and focus about the future? (Kuma tsakani da Allah ina tsoron na rasakai, na san zaki so kiji menene, amma zaki iya sharewa don ni? Zaki iya share komai, zaki iya dode kunnuwanki ta wasu da zasu baiyana nan gaba? Zaki iya share baya mu maida hankalinmu kan gaba?)”.

 

Be jira ansarta ba ya tallabo duka fuskarta da hanayenshi biyu yace “Wallahi Tallahi na chanza saboda ke, Wallahi na ajiye abubuwa da yawa saboda ke, i want you to trust me, ina so muyi putting komai a gefe, mu biyu kadai ne na junanmu, kin manta me nace miki dazun a bauchi before all that happened? You are my Always and Forever, baki yarda bane? Please believe me, I want you to trust me, ki yarda dani Ziyaa, i’m a changed person”.

Juya kalamanshi takeyi, har ranta ta gasgata kalamanshi, In kafiri ya karbi Musulunci sai a cigaba da kiranshi Arne? In Mazinaci ya tuba ga Allah tsakaninshi da Ubangjinshi ne, wannan kuma tsakaninta da mijinta ne, ba zatayi judging dinshi a laifin da ta kamashi a baya ba, zata dauki hukuncin da zata kamashi a gaba, a hankali ta dauki hannunta ta kai daidai kumatunsa da ta mara, ta shafa a hankali ta hada idanuwansu, tace “I trust you, I trust you with my Life” bude hannayenshi yayi mata tayi sauri ta shige cikin jikinshi kyakyawan runguma ya musu.

 

Daga bisani ya rada mata a kunne cewa “I’m hungry” a hankali ta janye jikinta daga nashi ta tafi kitchen, plates da serving spoon ta dauko musu, lekawa tayi daki yana tsaye inda ta barshi “Oya dauko Lunch Bag din” dauka yayi suka fito daga parlorn suka isa dining area, ta zage zip din ta fiddo da warmers din, ta bude coolern farko Peppersoup din jan nama ne, dayan kuma hadadden Couscous ne wanda ya ji kanya lambu da hanta, ki samun Peppersoup din da yawa, sai abincin kadan, a plate daban daban tayi yanda yace ta tura mishi gabanshi, ita kuma ta zuba Couscous din da dan yawa, ta sa naman a ciki, harta zauna tayi saurin tashi don dauko ruwa a fridge, tana budewa taga Fruits da drinks kala kala, bata ganin sanda ake kawo duk wani abun amfaninsu, babban roban ruwa ta dauko da wasu Orange drinks din daga kallo kasan foreign ne, ta kai kan table, lokacin Zaid cin Couscous dinshi yake cikin kwanciyar hankali, itama ta fara cin nata, kura mai ido tayi yanda yake cin abincinshi ya burgeta, tana kallon ya ture ya janyo plate din peppersoup din, har zai fara ci ya fasa tare da k’ura ma plate din ido, kamar naman zai yi magana, ta lura da yanayin chanjin fuskar shi, ta dan taboshi tace “Yadai? Lafia? ” Murmushi yayi tare da girgiza kai yace “Duk sanda zanci Peppersoup din jan Nama, na kan tuna Babana, yanason Jan Nama, ya san fa yana da Gout amma be fasa ci ba, Doctor ya kirashi ya hanashi, sai yace ya bari ashe in ya dawo Gida yana sa a masu aiki su dafa mishi, da Dr ya gane be daina cin naman ba, sai ya kirani yace in kula da abincin da yake ci, Baba be ji dadi ba da na sani, ina zuwa duk RedMeat din da ke fridge sai da na sa aka fitar dashi a gidan, sai Kaza saboda ban san Kifi shima ya bar ci, wai kinsan me Mutumin nan keyi?” ya tambayeta yana daria, ta girgiza kai itama tana dariar ba wai don tason dariyar me yakeyi ba, ya cigaba yana cewa “Wai sai mutumin nan ya siyo Naman shi ko ya sa Masu aiki su dafa mai amma kar a gaya min, sai yaje bayan k’ofa ya ci abunshi, kullum fa haka yakeyi, har sai da na kamashi redhanded yana ci a bayan kofa, could you imagine, the Whole Alhaji Sadam Audu Gatan Marayu boye bayan kofa yana cin nama a boye?” daria suke gaba daya, bata taba ganin faraarshi ba kamar yau, yanda yake bata labari yana daria tsakaninshi da Allah ita ba wai labarin ya bata daria sosai bane, amma ganinshi cikin annashuwa yasata biye mai tana daria, tace “to ya akayi ya rabu da cin Nama? ” Zaid ya tsagaita darianshi yace “Wa? That stubborn Old Man, ai ba zai bari ba, sai da ya kasance indai ya sa a dafa mai sai dai ni na kwace na ci, kullum haka muke, a dafa mai in cinye sai in sa mishi Kaza, wai sai yace be son Kaza, ji yake kamar Dusa, ke har ranar da zai mutu sai da yaci Parpesun kan rago”.

 

Ziyada tace “Allah Sarki, Allah ya gafarta mai ya sa ya huta” Murmushi Zaid yayi ya cigaba da cin Naman, “Matarshi fa? I mean Mamanka” jimm yayi tare da tsagaita taunar naman da yakeyi kafin daga bisani yace “ban taba ganin Matarshi ba” Ziyada da mamaki tace “Bangane ba” a takaice yace “Matanshi ba donAllah suke son shi ba, yana da wani laluri da Mace ba zata iya zama dashi ba, su kance baya iya haihuwa, to duk wanda kika ga ta aureshi, to ba dan Allah bane sai dai don dukiyarshi da abun da ya tara, to tunda muka hadu be sake wani auren ba” kai ta jinjina bakinta na nauyi zatayi magana yayi saurin katseta don ya san me take son cewa, a takaice yace “i’m only his adopted Son, the son he never had, the son he always wished for(Ni Yaron da ya rika ne, nine yaron da be taba samu ba, Nine yaron da ya dade yana son samu) “.. Ya danyi jim kafin yace “My Parents are Dead”. Allah sarki, sosai ta tausaya mishi, akwai tambayoyin da take so ta mishi, amma zata share, tace “Ubangiji Allah ya gafarta musu duka, ya sa sun huta, ya sa Aljanna ce makomarsu” ya ansa da Amin, ta chigaba da cewa “akwai hikima babba a taimakon maraya, balle shi wannan Marayu sama da dubu ya inganta rayuwarsu, ya dauke su kamar nashi, ai tashi tayi kyau InshaAllah,sai dai mu roki Allah ya inganta k’abarinshi” Sosai aji dadi da adduointa, yace “Ameen, i’m sure da ya ganki da ya soki, sabida yana son duk wani abun da nake So” blushing ta fara yi a hankali tace “Kana sona?” bata san yaji ba yace “Fiye da tunaninki” kallonta ya cigaba dayi kasa kasa, da sauri ta maida kanta kan plate tana cin Abinci, har suka gama ya tashi ya koma daki ita kuma tayi clearing gun da suka ci Abinci ta danyi kallo a ZeeWorld har wurin to 11 kafin ta kashe ta koma Daki don bacci.

 

Har ta hau Gado taji shigowarshi, juyawa tayi da sauri kasancewar duhu ne ta kashe Wuta bata ganshi ba, da fitilar wayara ta haka shi, tsaye ta ganshi cikin fararen shorts da top karama, ta dan muskuta tace “Bakayi bacci ba” cikin mintunan da sukayi kama da har abada yace “Erhm Eh banyi ba” ya karaso kan Gadon ya zauna, ta tashi zaune duk da cikin duhu ne amma tana hangenshi, tace “Lafiya? Kaje daki zan kwanta” da sauri yace mata “ina jin tsoro ne” ido a ware tace “Wani irin tsoro kuma?” yace “ba zan iya kwana ni kadai ba, ina tsoron dodo ne ko me ake cewa?” Ziyada ta fahimci ya ma raina mata wayau, ta juya mai baya tayi kwanciyarta tare da jan bargo.

 

Sosai ya hau kan Gadon, Gabanta ya hau dukkan ukuuku, a bayanta ya kwanta tare da juyo da ita tana fuskantarshi, a kunnenta ya mata rada “Ni Mijinki ne, be kamata ki juya min baya ba kinji?” a hankali ta gyada kai alamun taji, kare matseta yayi yana binta da wasu kauna a jiki, ganin yanda yake matsowa jikinta ne ya sa ta daburcewa jiki na rawa tace “Zanje Makaranta” Murmushi yayi don ya san ta tsorata dashi ne yace “Yanzu zaki makaranta?” da sauri ta gyada kai tace “Gobe” a takaice yace “na cireki” za tayi magana yace “Makarantarki zaki Koma, baze ko? Chan zaki cigaba da karatunki bata iya amsa shi ba, ta mayar da idanunta ta rufe.

A nutse yake nuna mata yanda yake jinta a zuciyarshi, cikin kwanciyar hankali yake nuna mata yanda soyayyarta tai mishi illa batare dayai amfani da kalamai ba. Cikin kwanciyar hankali yake hade zuciyoyinsu da ruhinsu waje daya cikin salon da bazai mantu a wajen su ba har abada.

***

*Bayan Wasu yan Kwanakin da ba su kai Sati ba*

 

Soyayya, Aminci da Shakuwa ta darsu a cikin zuciyoyin masoyan nan biyu, burin daya ya kyautata ma daya, a zaman da sukayi da juna sun fahimci halaiyar junansu, sun sake da junansu, sabida Kwanciyar hankali Zaid ya kashe wayoyinsa don samun hutu, shi fita kasashe bude ido be dameshi ba, niyyarshi ya dauketa su tafi chan Porthacourt su danyi hutu ba tare da hayaniya ba, a yanzu ne Zaid yasan cewa ya dade yana cikin bakin duhu, a yanzu ya san cewa akwai wani abu So, a yanzu ya san cewa mutum na zama da tsana da bakinciki a ranshi in yaso, in ko ya so cirewa zai cire ya musanya da So, Allah ne shaidarshi yana son Ziyada, yana son kyautata mata kamar yanda take kyuatata mishi, shiyasa jiya da daddare da ta zo mai da bukatar suje Gidansu be ce komai ba, amma duk da baya so, ba zai hana ba, dole ya hakura suje Gidan, wurin breakfast ya gaya mata ta shirya anjima su tafi, dadi ya kamata, ta tashi ta rungimeshi tana mai godia breakfast din da basu gama ba kenan.

**

 

Aunty Aynarh ta shigo Gidan da Sallama, duk yaran su ka tashi suka rungumeta, fara’a take tayi, ta zube kasa ta gaida Hajjo, Daddy baki har wuya yaga Masoyiya, a mutunce aka gaisa, Mummy sai famar wurga mata harara take ko a jikinta, ta kalle su tace “Allah ya sa ba ku daura abincin Rana ba, na riga na mana Lunch” Zaineema ta murmusa tace “ba mu daura ba ko” tace “yauwa perfect” Key ta mik’a ma Abdulmajeed tace “Ka dauko Kayan Booth” Abdulmajeed ya karba ya kalli Najwa yace “muje ki tayani dauko kaya” tashi tayi ta bi bayanshi suka bar Parlorn, Mummy ta kalli Daddy tace “bari in daura mana Abinci kafin yara su fara jin yunwa” Daddy yace “Maryam bakiji Hajia Aynarh tace ta yo abinci damu ba?” Galala ta kalleshi, kwana biyun nan tsinkata yakeyi gaban jamaa, kar ya mata haka yanzu ta wayance tace”wai sai a kara ko?” Daddy yace “Aa, am sure Abincin da yawa, ki bari da daddare ayi, yanzu dai muci wannan” zama tayi tana wurgar Hajia Aynarh da harara, ita ko hararar mugunta take mata.

 

“PureHeart, i cant wait naga su Maama don nace su bani ke na aura” Murmushi tayi tace “suna nan tafe cikin kwanaki” yace “Allah ne shaidana, ina sonki dominsa” Murmushi tayi tace “main tumase karta hoon” idonshi ya juya sama cikin salon banji me kikace ba, tayi daria tayi gaba, ya bi bayanta yace “Nidai a bar min magana da Indiyanci” dariya tayi tace “Aunty Aynarh na jira” ya bude Booth ya fiddo kayan ciki duka har su carpet, plates da cups, sai Flask kusan kala uku, suka dau iyakan iyawansu suka kai ciki, suka dawo suka dauka sauran.

 

Carpet din suka shimfida a tsakar Gidan, suka jera komai a kai, sai da sukayi Sallahr Azahar suka fito waje kan Carpet din, daidai nan Ziyada ta shigo Gidan da Sallama, duk sukayi kanta suka yayyabeta suna murnan ganinta, Oyoyo Oyoyo, daga baya Zaid ya shigo, baki Mairo ta washe, shi kuwa kamar an aiko mai da Sakon mutuwa, faraar fusakrshi ya dauke dif, Abdulmajeed a karaso gunshi ya mika mai hannu don suyi musabaha, ba yabo ba fallasa ya karba, tare da dan durkusawa ya gaida da Daddy da Hajjo da Aunty Aynarh da ke zaune kan Carpet, duk ya bi yaran gidan da kallo inda suke gaisheshi, tausayinsu ya kamashi, Zaineema yarinyar da yaso kamar me, be manta kaunar da ke tsakaninsu ba, yarinyan da Mairo ke rankwashinshi in ya dauketa, rashin imaninshi ya sa ya rabata da Mijinta, ya zaiyi ya gyara mistake dinnan? Idonshi ya kaiga Najwa wanda take wurga mishi wani mugun kallon “na san ko waye kai” da sauri ya dauke kai yana me jin tsoronta, kar fa ta ganeshi, kar ta tona mai asiri Ziyada a rabu dashi, Allah sa bata ganeshi ba, ji muryar Mairo yayi tana cewa “Ku shigo Parlo sannunku da zuwa” Ziyada tace “Aa Mummy, bari mu zauna a nan so kike ayi picnic din banda mu?” Mairo ta tabe baki tace “ba wani picnic, dangin yarbawa ce tayi son iyawanta wai ta dafo mana Abinci, kamar munce ba mu da abinci”. Ziyada tace “Yayy, dama nayi missing Abincin Aunty Aynarh” Mairo takaici kamar ya shideta, tace “Alhaji Zaid kai ka shigo Parlo ka zauna” banza yayi da ita, ba wanda ya lura da ko gaishe da Mairo beyi ba, ya samu wuri kusa da AbdulMajeed ya zauna, wanda Hajjo ke gefenshi Najwa na nata gefen, Mairo tace “Lah, Alhaji, zaman kasa be kamace ka na, please ka shigo ciki” ko kallo bata isheshi ba, Daddy yace “Maryam ki barshi ya zauna cikin Yanuwanshi mana”

 

“‘Yanuwanshi” kalmar da Zaid ya fada kenan, ya kalli gefen shi ya ga su Hajjo da Muhsin da Zaineema zaune, dayan gefen Daddy da AbdulMajeed da Zinatu da Ziyada a zaune, sai ya ji shi kamar daya daga cikinsu, ba abunda ya kai bond din Yanuwan jini karfi, ba abunda ya kai feeling din dadi, tabbas yaji wannan connection din, ya ji shi among them, ko yaki ko ya so “they are his Family” yayi Alkawarin gyara laifinshi, “I will fix this , i will fix everything ” ya fada a ranshi..

Daddy yace “Oya a bamu mu ci” Hajia Aynarh tace “ai ga yara na nan, su zuba mana” Mairo kamar ta mutu ganin yanda Hajia Aynarh ke fi’ili gaban Daddy.

Zaineema ta bude kulolin, Faten Wake da Amala, duk wanda kake so sai a sa maka, Miyar Amalan yaji Ganda da Stock fish, Alallen kuwa ya hadu da kwai da kifin Sardine, Faten waken ma yaji dryfish da Ganda.

Tace “Daddy me zaa sa maka? Hajjo me zaki ci?” tace “a zubo min Faten Wake, mun dade bamu hadu ba” akayi daria, Daddy yace “a zuba min Amala” Mummy fa baki ta yatsina tace “Moimoi”.

Ziyada tace “YaMaji me zakici?” ya tashi daga durkuson da yayi yace “Zuzu serve your Husband, ni da kaina zan zuba abinci na” Hajia Aynarh tace “banda abunki Ziyada ana ta Miji wake ta wani YaMaji”.

Ta k’asa ta kalli Zaid din da yayi mugun dauke kai, yana iya cin Abincin Musamman da yaji cewa ba Mairo tayi shi ba, Hajia Aynarh tayi, kuma yana iya cin Amala, don yana son abincin, ita kuma bata yi zaton zaici ba shisa bata tambayeshi ba, a hankali suka hada ido yace mata “Amala” Ziyada ta murmusa, Najwa tace ita kuma a bata irin na Hajjo ba wai don ta san meye ba, amma don yayi kama da wani soup din India, kowa ya fadi abunda zaici akayi serving kowa..

 

Addua Daddy ya umurta ayi, a tare kowa yayi suka fara cin Abinci, kasancewar duk Abinci da busasshen kifi da kuma gasasshen kifi akayi, in ba ci kayi ba ba zaka gane kifi bane, yafi kama da Nama.

Ko Cokali biyu ba suyi ba numfashin Zaid da Najwa ya fara daukewa, sama sama Numfashin ya fara, AbdulMajeed da ya kafa Najwa da ido ya lura da abunda takeyi yayi saurin ajiye spoon yace “PureHeart are You OK?” Zaineema ta kalli Najwa tayi saurin mikewa tsaye Hajia Aynarh ma haka, Najwa me ya faru? Abu takeyi kamar mai neman shidewa, Ziyada ta dan waiga ta kalli Zaid, gabanta ya fadi, irin abun Najwa yakeyi, numfashin shi samasama, fuskarshi yayi ja, da sauri ta karasa gunta “My Forever, lafiya” Hankalin Mairo ya tashi ta mike ta ci kwalar Aunty Aynarh “Munafuka Algunguma, me kika sa ma Abinci? Me kika sa ma sirikina? So kike ya mutu” Aunty Aynarh ta tsure sosai tana girgiza kai tace “Wallahi bansa komai ba, Wallahi ba abunda na sa, mukai su Asibiti” Najwa ta riko hannun Hajjo tana bankarewa kamar zata mutu, Zaid ma hannu ya sa ya rike wuyanshi yana jan numfashin dake fita da kyar, fuskar nan tayi Ja, Daddy yayi saurin fita don taro A daidajta sahu a kaisu Asibiti, yana fita ya ci karo da Convoy din Zaid, Ziyada Hawaye kawai takeyi hankalinta tashe, Abdulmajeed hankali a tashe ya kalli Aunty Aynarh yace “Aunty kinsa Kifi a abincin nan?” da sauri ta gyada kai tace “duka abincin da Kifi nayi shi” Abdulmajeed ya ruga kitchen a guje, Ya shiga bincikar Kayan Miya da ya siyo dazun Tomatoes ya dauko, ko wankewa beyi ba ya fito ya mika ma Ziyada 1 yace ki bashi, lokacin sun fara fita daga hayaccinsu, fasawa yayi da bakinshi ya juye ma Najwa ruwan tumatirin a baki, haka Ziyada ta ma Zaid, a hankali a hankali numfashin su ya fara dawowa daidai, daidai nan Idi da wasu Yaran Zaid suka shigo sukayi kan Zaid wai zasu kaishi Asibiti, daga musu hannu yayi yace “i’m fine” Ziyada tace “me ya faru da kai?” Zaid yace “ina tsammanin Abincin nan akwai Fish, and i’m allergic to Fish” daidai lokacin da Najwa ta ke ce ma Hajia Aynarh “Dama bansan da kifi a cikin Abincin ba, shine naci?” Hajia Aynarh tace “I’m So Sorry, wallahi bansan ba kwa son Kifi ba, Abincin ba wanda ban sa Kifi ciki ba, kuyi hakuri donAllah” Najwa tace “Laah Aunty ba wani abu, ni in na samu irin attack dinnan da na sha tomato zanji normal, ai farkon zuwana Nigeria na taba samun attack din” Abdulmajeed yace “shiyasa na tuna Tomato ne first Aid treatment din” Zaid ya kira Idi ya zo kusa dashi, ya rada mai abu a kunne, da sauri ya fita, Aunty Aynarh duk tayi wani iri, gani take laifinta ne, Zaid ya kalle su Daddy da sukayi cirko cirko suna kallonsu yace “Baba Abba ku zauna ku cigaba da cin Abincinku, Ni kifin ne bana so, yanzu zaa kawo min wani Miyan sai in ci” Daddy ya sage yana kallon Zaid, wani abu ke bin zuciyanshi, dunia Zaidun Sada kadai ke ce mishi “Baba Abba” jiki a sake ya zauna, yace da Muhsin su cigaba daci, Daddy ya kallesu yace “sai kuka tuna min da k’anina Marigayi, kunsan shi ko kanshi Kifi ya ji sai ya fara sheshek’a?” Hajjo ta chabe tace “haka ne, ko abinci nayi da Man kifi in ya fara Amai kamar zai zazzago kayan cikinsa” Zaid ya runtse idonsa yana tausar zuciyarsa. Abincinsu su ka cigaba daci banda su 3, Zaid da Najwa da Mummy, su kadai ne basu cin Abincin, gaban Mairo ke dukan uku uku, ta kalli Najwa a kalli Zaid, tunanin da bata son yi ta fara yi, Sada be cin Kifi, Zaid din Sada be cin Kifi, Wannan dan Sada ne. Da sauri ta girgiza kanta ta tashi kamar mahaukaciya ta shige daki, daidai nan Idi yayi Sallama da Cooler a hanayensa, Gaban Oganshi ya Dire, Ziyada ta bude Miyan Kubewa danya ne da yaji Jan Nama, ta bude wani Amalan ta sa mai da miyan Kubewar, ta kalli Najwa tace “in sa miki ko? ” kai Najwa ta daga, Ziyada ta zuba mata suka cigaba da ci, Hajia Aynarh ta saukar da Ajiyar zucia ganin basuyi zargin ko tayi poisoning dinsu bane.

 

I N D I A

 

Duk wasu Process na tafia sun gama, Jirginsu zai tashi Gobe zuwa Dubai, washegari su tafi Nigeria inda zasu isa Lagos daga nan suyi Kano, Paapa da Maama sunyi Resigning a wuraren Aikinsu, an basu kudin Sallama me tsoka, harta Motocinsu da Gidan da suke zaune sun saida, Paapa ya samu wani Agent dan Kano suna communicating, nan ya tura mishi kudi ya siya mishi dankareren Gida a Tarauni, don shi baya tunanin zai koma Gidanshi na da, yafi karfin ya tada Yayanshi a gidan da yake, ya bar mai Gidan nan har abada, Maama ta dinga shiga Gidajen Neighbors dinsu tana musu sallama, Vijhay Bhaiya yayi kuka sosai, Maama tace “InshaAllah zasu zo wani lokacin” bayan sun mishi Alheri me yawa, ko da ta shiga Gidansu Kaveri nan suka bata lokaci da Maman kaveri suna jimamin rabuwansu, Kaveri kuwa bata fito ba tana daki tana cizgar Kuka.

 

N I G E R I A.

 

Rigima Ziyada ke ta ma Zaid tun tashin su yau da safe don ya sanar da ita Tafiar gaggawa ta kamashi zuwa Taraba, zai biya Kaduna ya ga Gidan Marayu kafin Jirginsu ya tashi zuwa Taraba’s state. Ziyada tace ya tafi da ita, hakuri ya bata cewar tayi hakuri, ya dawo, da ya dawo zai musu processing Visa suje any country of her choice, sannan in sun dawo Gida zasu yi Parking su koma Gidan Babanshi na Asali a Kaduna, dolenta ta hakura amma taso ta bishi don bata son yayi nisa da ita. Alfarma ta rokeshi da ya barta a koma Gida har sai ya dawo, da farko k’i yayi, yace tayi hakuri ta zauna har randa zai dawo, tace “itadai aa, ba zata iya kwana ita kadai ba ” ba yanda ya iya ya amince mata da taje Gidan, a daren da zai tafi, makale suke da juna kamar cingam, baya so ta bishi sabida bussiness zaije yi, da wuya ya samu time dinta. Washegari da kanshi ya rakata har Gida bayan an musu siyayya a Shoprite, sunfi Minti 20 a gaban Gidan cikin Mota suna manne da junansu kamar kar su rabu, shagwaba take ta zuba mai, shi ko yayi ta biye mata, “i’ll miss you i’m My Forever” rungumeta yayi yace “i’ll miss you more” sun dade a haka kafin daga baya ya rakata har Cikin Gidan, suka gaisa da yan Gidan banda Mairo da ba wanda ya lura be gaisheta ba. Daddy ya masa godian Hidiman da yakeyi dasu. Ziyada a boye ta share hawayenta da zai tafi, shima duk yaji ba dadi, ta zama wani bangare na jikinshi.

****

Najwa sunyi waya da Su Maama sun gaya mata Jirginsu zai tashi a ranar da daddare, but zasuyi transit a Dubai washegari su iso lagos, dadi ya ziyarci Najwa, ta musu fatan a iso a lafia.

 

B A Y A N K W A N A B I Y U

 

Tun daga garin Allah ya waye yake jin nauyin jikinsa, ya kanji kunnenshi yayi wani irin Yammm, hannunshi kan mai nauyi wurin dagawa, Da k’yar yaje Sallahr Asuba da taimakon AbdulMajeed ya dawo Gida, duk da shima yace be jin dadin jikin nashi, Hankalin Yaran Gidan ya tashi, Daddy da Ya Maji basu lafia, duk da ya Majin ba kwance yake ba, duk suka zauna suka rafka tagumi suna kallon Daddy. Mummy ta lallabasu suka koma dayan dakin tace “a bar Daddy ya samu bacci” da kyar suka fita suka barshi shi kadai.

kishingida yayi kan Katifarsa yana tunano abubuwa da suka shude shekaru sama da 20, ya tuna Mutuwar kaninshi da Matarshi, gawarsu da ya kasa shaidawa Saboda k’una, ya rufe kaninshi da Matarshi da hannunshi, wani side na kanshi ya buga kamar an kwala mai darma, da sauri ya girgiza kansa, runtse idanunshi yayi ya na son tunano exact abinda ya faru, sai ya gano Me ya faru da Sada da Yesmin in ba mutuwa sukayi ba? A hankali komai ya soma kwaranyo mai,

Kalamanta da abubuwan da suka faru suka so mai sintiri a kwalawa kamar a lokacin ake yinsu

“ina so ka maida sunan duk Takaddun nan daga Sunanka zuwa sunan Abba” ya tuna Sada be mata gardama ba yayi yanda tace yace “nagama” shi karan kanshi yaji mamaki, ya tuna da tsoro ya tambayeta “Meyasa? Don me zaiyi haka?” ya tuna tsawar da ta mishi tace “shuttup, baka son ka mallaka Dukiyoyin Sada?” yace “ai yana bani dukkan abun da na buk’k’ata, hakan yayi” ya tuna yanda ta girgiza kai tace “aa, beyi ba, kana son dukiyan Sada” ya tuna yanda ya maimaita abunda tace kamar karatu” beyi ba, ina son dukiyan Sada” murmushi tayi ta kallo Abba tace “good”.

Ba a kwana ba ya tuna lokacin da ya ganta tayi nisa da tunani, ya tuna tambayarta

“Maryam tunanin me kikeyi haka?”

a takaice ta bashi ansan “tunanin Kashe Sada da Yesmin nikeyi” ya tuna yanda hankalinshi ya tashi cikin rudu yace

“Saboda mene Maryam? Sun ba mu duk abunda muke da burin samu a rayuwa”

“hakane, amma zamansu a doron k’asa barazana ce a rayuwata, shiyasa na yanke hukuncin kashe su”

Ya tuna yanda ya durkusa kan guiwowinshi ya na kuka yana rokonta gafara”Kiyi Hakuri Maryam, ba sai kin kashe su ba DonAllah, Sada danuwa na ne, kuma ina sonshi sosai”

Ya tuna yanda ranta ya baci tace “sai ka za6a ko ni ko shi”

Ya tuna yanda beyi dogon tunani ba yace “ke na za6a uwar ‘yayana, ina sonki, kece farincikina, zan iya rabuwa da kowa don in zauna dake, amma Sada danuwana ne, akwai Babba Alaqa tsakaninmu, ina neman Alfarma da ki barshi raye,in bakya bukatar ganinsu zan sa shi su bar garin,amma kar a kashe su donAllah Maryam”

A kausashe tace? “in kuma hakan zai bani farinciki fa?”

Ya tuna muryarshi me cike da tsoro da rashin jarumta yace “da hannuna zan kasheshi don baki farinciki, amma ina rok’onki da kiyi hakuri” shiru tayi kafin tace “Zasu bar k’asan, zasuyi nisa da mu, ba zasu taba dawowa ba har duniya ta nade”

Ya tuna tashin hankalin da ya shiga da tace haka, ya tuna yanda ta daka mai tsawa tace

“Ko ka fi son a kashesu?”

Ya tuna yanda ya girgiza kai da sauri yace

“a saka su suyi nisa damu”

Ya tuna yanda ya durkusa har k’asa yana mata Godia kan amincewarta na ba zata kashe su ba. Ya tuna Komai, Ya tuna Wallahi, Maryam ta dadw tana zaluntarshi, Maryam ta shiga tsakaninshi da k’aninshi, wai kuma sai gashi bayan kwana biyu a ka kawo Gawarwaki guda biyu wai Yesmeen da Sada, Anya sun mutu? a baiyane yace “aa ba su mutu ba”.

 

Maryam ta ha’ince ni, maryam ta zalunce ni, Kuka yakeyi sosai, be sama ma Yaranshi Uwa ta gari ba, k’arshen zamanshi da Maryam yazo, ba zai iya ba, a hankali ya tashi ya na dafe da bango ya fita waje, besan yanda zaiyi ba, amma yasan ba zai iya cigaba da zama dashi ba, don albarkacin yaransu, da ya maka ta Kotu.

A waje AbdulMajeed ya ga Daddy, yayi saurin karasawa gunshi yace “Daddy, ka bar jin jirin ne? Ka koma ka kwanta”

Mommy ta fito da sauri jin muryarsu, Duk yaran suka biyo bayanta har Hajjo, Mummy tace “Ah Daddy, har kaji sauki ne? Ta karaso gunshi zata taba shi yayi saurin janyewa, yace “kar ki sake ki tabani, muguwa Azzaluma” yaran suka kalleshi da mamaki, Abdulmajeed ya shiga rudu a hankali yace “Daddy…” Mairo bakinta a bude ta kasa magana, be taba mata haka gaban yara ba, ga mamakinsu sai ganin Daddy ya fashe da kuka ya zube kasa “Kuyi hakuri ku yafe min Yarana, ban zaba muku uwa ta gari ba, ku yi hakuri, na zaba muku jahila cikin jahilai a matsayin Mahaifiyarku” Ziyada ta fashe da Kuka, Zaineema da sauran Yaran ma suka fashe da kuka, AbdulMajeed ya rik’e Daddy yace “Daddy donAllah in Laifi ta maka ku shirya kanku, ku mahaifanmu ne, muna son ku duka, kuyi hakuri ku shirya kanku” Daddy cikin dan tsawa yace “In shirya da wannan hatsabibiyar? Tsakanina da Maryama Allah ya isa, ta shiga da tsakanina da

danuwana Sada, ta salwantar mun dasu” cikin Zafin Nama ya makuro Wuyanta “Ina kika kaimin Sada da Yesmin? Ina kika kai min su? Ina kikace su tafi? Ina Maryam?” a duk zatonta Zuciyarta ya fito daga Kirjinta, kasa motsi tayi, ganin komai take kamar a film, ta gama tsorata iyakan tsorata, karyarta ya kare, Asirinta ya tonu, Ajalinta yazo” Hajjo ta matso kusa dashi ta dafa tace “Haba Abba, me ya sameka haka? ina zata kai Sada? Ka manta Sada da Matarshi sun Mutu? Ka manta da hannunka ka rufesu? ” da sauri yace “Wallahi basu mutu ba, basu bane, cikin makircinta ne tace sune, Wallahi ita ta salwantar dasu, Umurnin ta suka bi suka shiga dunia” Hajjo ta durkushe a gun tana kuka me tsuma rai, su Ziyada da Zaineema Kukan suke, Najwa da ta gama fahimtar komai ta fashe da wani irin dariyan da ya juyo hankalinsu, a baiyane tace “Alhamdulilah”, duk da suna cikin tashin hankali kacokam suka bi ta da ido, da sauri ta isa gun Baba Abba ta rungumeshi tare da kwantawa kan kafadunshi, Baba Abba be da wani kuzari a kunne tace “Babana, kace Alhamdulilah” be san dalilin da ya sa ya biye mata yace “Alhamdulilah” daidai Sallaman Mutanen da ba zai taba Mance Mury

 

💭A DADE ANA YI….sai gaskia💭

 

NA

 

Wattpad:@biebeeisa

 

Pg3⃣8⃣

 

Yaran Mairo gabaki daya sukayi kanta, Najwa tayi gun Maamanta a guje, Abba ya matso daf da danuwanshi ya ci burki a gabanshi, kallon kallo suka tsaya yi ma junansu, hawaye tuni ya wanke musu fuskoki, da sauri Sada ya karasa ya rungume Yayanshi, kuka suke a jikin junansu, Abba kamar zai shideta saboda kuka, Sadan ke bubbuga mai baya alamun rarrashi, har sai da ya tsagaita kukan, sake shi yayi ya karasa inda Hajjo ke tsaye tana ganin duk abunda ke faruwa kamar Mafarki, Sada ya tsaya a gabanta, yana hawayen farinciki, a tsorace ya sa hannunshi ya rik’o nata, lumshe idanuwa tayi hawaye na gangarowa kan kumatunta, shine, Sada ne, Autan ta ne, kafadunta ya rik’e, ya sa hannu ya share mata hawaye,  hannunta na rawa ta daga ta kai kan fuskarsa,  baki na rawa tace “Sada kai ne?” rike hannunta yayi da ke kan fuskanshi yana gyada mata kai,  “nine Umma,  nine Sadanki” “Allahu Akbar”cewar Hajjo, Maama ta matso kusa da ita ta rungumeta,  “Yesmeen,  ashe kuna raye?” wani kukan suka fashe dashi, sai lallashinsu Abba keyi.

 

Tana cikin tashin hankali amma Kukan da Yaranta keyi ya na kara tada mata hankali, bata so ta bude ido taga ba mafarki takeyi ba,  bata so ta tashi daga mafarkin da take,  ta zata ta yarda kwallon Mangoro ta huta da k’uda,  in dawowan zasuyi Meyasa ba su dawo tuntuni ba sai yanzu da ta manta da shafinsu,  meke faruwane? Kukan da su Zaineema da Zinatu keyi na kara sata cikin damuwa,  so take ta bude ido ta lallashesu,  amma in ta bude ido hakan na nufin ta farka daga baccin da take.  Ruwa Ziyada ta yayyafa mata,  amma ko motsi batayi ba,  kukansu ya tsananta “Mummy please ki tashi” Daddy “please kace mata ta tashi” Daddy ya fincike hannunshi daga gun Ziyada,  nan hankalin yan India yayi kansu, Murmushi yayi ya matsa daf da ita,  don yaga idonta na motsi,  tsugunna wa yayi yace “Maman Yarona(kamar yanda ya kan ce mata a da=Abdulmajeed  yake nufi ) , na san kina jina,  ki tashi, kin tada hankalin yaranki” ba kunya ba tsoron Allah ta bude ido a hankali ta saukesu fes kan Sada.

 

Bakin Miyau ta hadiya,  idonta ya ciko,  cikinta ya duri ruwa kamar zata fara gudawa,  a haka ta tashi tsaye tana raba ido,  Mijinta take kallo, Daddy ko kallon gefenta beyi ba, ta kasa kai dubanta gurin Yesmeen,  ta san ta cuci Bayin Allahn nan,  ta san ta ha’incesu,  ta san ta shiga tsakaninsu, Maama daga baya tana kallon Mummy cikin ido,  duk wasu abubuwan da suka faru suka soma kwaranyo mata,  kuka take sosai, da sauri Mummy ta sadda kanta kasa,  itama hawaye take,   tana me kunya hada idanuwa dasu, bata taba jin Nadama ya shigo mata lokaci guda  ba irin na yau,  da na sani k’eya ce,  amma tayi dana sanin duk wasu abubuwa da tayi,  kar su rabata da ‘yayanta,  a hankali ta kai dubansu gunsu,  da gan kan Majeed… Zaineema.. Ziyada.. Zinatu da autanta Muhsin,  cirko cirko sukayi suna son jin bayanin Meke Faruwa, Hannu ta sa a fuska ta fashe da wani irin kukan Nadama, duk wani numfashi da take ja,  da da nasani take janshi,   a hankali suka yo kanta su duka a tare,  da baya da baya take ja,  suna binta,  tana baya,  suna binta har saida ta ci karo da bangon Kitchen, Abdulmajeed ya karasa gunta zai rungumeta, ya bata comfort,  ya gwada mata “koma me tayi,  suna tare da ita, dakatar dashi tayi da hannunta, girgiza mai kai tayi tare da zubewa a k’asa, kukan da yake ta kokarin boyewa ya fashe da, baki na rawa yace “Mummy..” sauran Yaran suka taya shi suna nufar inda Uwar take.

 

A kan guiwowinta ta sauka,  duk yanda taso magana ta kasa,  sai taji harshenta ya mata nauyi, ba abinda take iya yi sai kuka,  nadama fal ranta,  Abdulmajeed ya firgita da yanayin da ya ganta,  takowa yayi kusa da ita ya sauka kan guiwowinshi,  bakinta yayi nauyi bata iya komai sai kuka da girgiza kai, ganin abunda ke faruwa yasa  Zaineema matsowa kusa dashi itama ta kai guiwowinta kasa,  Ziyada ma hakan tayi,  Zinatu da Muhsin ma sukayi hakan, duk abunda sukeyi kan idon Paapa da Maama, Abdulmajeed ya fara magana  yace “Mummynmu akwai taurin rai,  ba abu kadan ke daga mata  hankali ba, ba komai ke sata kuka ba, ba komai ke sata shiga yanayi ba,   bansan me ta muku ba,  bansan meke tsakaninku ba,  amma ina so ku sani,  tun da nake da ita, i’ve never seen her like this,  ban taba ganinta haka ba,  ban taba ganin regrets kwance a kan fuskarta ba, bansan me ta muku ba,  amma ina da tabbacin cewa  tayi nadama,  a kan fuskarta na karanta da tana da yanda zatayi,  da ta koma lokacin baya ta gyara kuskurenta,  donAllah, don Girmansa, kuyi hakuri,  ku yafe mata”.

 

Paapa da zuciyarshi ta gama karaya ya juya ya kalli Yesmin da kukan ta ya tsananta,  ta san bond din da ke tsakani Da da Uwa, ta san cewa  Mairo ce  sanadiar duk wani bakincikinta,  ta san cewa Mairo ta mata farraku da danta, bata tunanin zata iya mance abunda Mairo ta mata, a zatonta zata ji tsanar Mairo da duk wani abunda ya danganceta, a zatonta zata cuzguna ma Mairo da mafiyin abin da ta musu,  amma ga mamakinta,  sai taji sosai  zuciyarta ta karye, sosai taji tausayin Mairo da Yayanta.

A hankali ta gyada ma Paapa kai,  a hankali ya matso kusa dasu, ya na kallonta ya maida dubansu ga Yaran,  Murmushi ya sakar masu wanda ko ba a ce ba ma sun gane danuwan Daddy ne wanda sukayi tsananin kama, Abdulmajeed  ya kala yace “Ku shiga Ciki” kallonshi cikin Ido Abdul keyi yana tuna inda ya sanshi,  Murmushi Papa ya sake,  yace “trust me,  everything is going to be fine” da sauri Majeed ya tashi ya mikar dasu duka, ya hada su gabaki daya ya turasu cikin Daki, Papa ya kalli Najwa,  kallonta kawai yayi tasan abunda yake nufi,  takowa tayi ta shiga Dakin itama,  ko baa gaya mata ba,  tasan cewa “Mummy ce sanadiyar komai” hankalin su duk tashe,  a yanda suke jugumjugum,  irin suna zaman jiran likita yazo ya sanar musu da cewa anyi Tiyata lafia patient bata mutu ba,  ba me cema kowa kala,  kowa da sakesaken da yake a zuciyarshi.

 

Tausayinsu Majeed yaji shiyasa Papa ya tura su daki,  ba zai so Yara suji laifukan Mahaifiyarsu ba, ko wace uwa ana So Yaranta suyi Alfahari da ita a duk inda suke,  suyi koyi da ita , duk da dai uwa uwace ko da uwar banza ce,  wani irin Alfahari zasuyi da ita? Baya so su samu  confusion din Uwa da Yaranta, duk da suna da dalilan musu ramuwar gayya, amma these are his nieces and nephews, suna da Jinin Yayanshi a jikinshi, yana sonsu fiye da zato,  so don su ba zai bari Mahaifiyarsu ta  wulakantu a kam idonsu ba.

Maida idonshi yayi kan Hajia Mairo, a takaice yace “Kinsan kin Cuce mu?” ba bata lokaci ta daga kai da sauri alamun eh, “kin san kin Zalunce mu? Ni,  Yaya,  Umma,  Yesmeen?” sabon kuka ta saka ta na daga kai tace “na sani,  na sani wallahi, zai zama Rainin Wayau in nace ku yafe min, dukkan ku nan na Zalunceku,  na Hainceku,  na cutar da ku,  gabaki dayanku nan, na chancanci duk wani hukuncin da zakuyi min,  amma duk da banda idon kallonku,  banda bakin da zan muku magana nace DonAllah ku yafe min, bansan ta yanda zan gyara laifina amma wallahi na bari,  dama chan hassada ne da bakinciki,  amma ku yafe min”.

 

Sosai ya tausaya mata don shi dama zuciyarshi kamar ta mata yake,  abu kadan yake karya  mai zuciya, jiki ba kwari, yace”Hakkin kowa ne ya yafe miki ko kar ya yafe miki, Ni dai na yafe miki,  sai kije ki rokesu gafara, Ubangiji Allah ya gafarta mana,  kije kiyi ta Istighfari” kamar ta yi me don murna,  ta rarrafa a kasa ta riko kafaffun Yesmin, da sauri ta janye kafarta, ba ta tunanin zata iya jure  maganganun da Mairo zata mata, tasan rokonta yafiya Mairo zatayi,  kuma har ga Allah har yanzu tana jin haushinta, Zata yafe mata,  zata barta taji da nadamanta,  zata barta da kunyar da zai cigaba da addabarta har karshen rayuwarsu,  kuma tasan abunda tayi zai cigaba da damunta in har dai tana da Conscience (hankali ko tunani) “Yesmin,  nasan na miki laifuka,  na san kin san ban taba sonki ba,  nasan kin san abubuwan da nake miki,  ba don ni ba Yesmin, ki yafe min,  don martaban Manzon Allah SAW” Maama ta runtse ido tace “Na yafe miki Mairo” Godia ta shiga yi mata, kamar dazun da rarrafe ta koma gun Hajjo tace “Umma donAllah ki yafe min,  na rabaki da Yayanki,  na zalunceki,  Wallahi duk abunda Abba ya miki na halin ko in kula duk nice, na chanchanci duk wani hukunci,  amma na zabi na roke affuwarku,  na chanchanci komai amma na zabi na tona ma kaina asiri,  ki yafe min donAllah” Hajjo ta share hawayenta,  ta durkusa ta dago Mairo tace “Ya wuce,  na yafe miki, Allah ya yafe mana” godia ta shiga zuba mata tana mata adduoin karin kwana.

 

A hankali ta juya ta kallo Mijinta, a sannu take takawa tana isa gareshi, hannu ya daga mata yace “Maryam,  kar ki sake ki matso kusa dani,  kar ki sake,  wallahi zan 6alla ki” chak ta tsaya ta na cizgar kuka,  Sada ya matso kusa da Yayanshi yace “Yaya…” “dakata Sada,  kar ku yarda da kalaman Yaudaran Matarnan,  kar ku yarda da hawayen munafurcinta,  ta amsa laifinta ne kawai don taga karyarta ta kare,  bata da wani mafita,  shiyasa ta saduda,  bakusan Maryam ba,  bata da mu da komai ba sai kanta,  shes too selfish, wallahi ko ganinta bansan yi “Maryam kije na sakeki” da sauri ta zube k’asa,  a sannu takejin komai na wargaje mata,  duniyarta na rugujewa,  Sada ya dafe Yayanshi,  yace “Yaja hannun yayanshi yayi parlo dashi,  ya zaunar,  ruwa ya gani kan carpet ya dauka ya bashi,  ba musu Abba ya karba yasha,  “Yaya Inallilahi wa ina ilaihir rajiun” a hankali Abba ya fara maimaitawa, ya fita ya basshi zaune, Mairo na nan inda ya barta,  ya matsa daf da ita,  yace “Ki tashi kije,  zan lallashe shi,  yanzu yayi fushi sosai, bayan kwana biyu nasan zai sauko,  ki shiga ki kwantar ma Yaranki da hankali,  ba sai kin sanar da su komai ba,  kinsan yara da rik’o” tashi tayi ta share hawayenta,  ta nufa inda Yaran suke, tana shiga duk suka yi kanta,  k’okarin Murmushi take musu,  ta kalli Najwa,  tace “Ke Diyar Sada ce da Yesmin?” Kuka takeyi tana gyada kai,  Allahu Akbar cewar Mummy,  ta kalli Abdulmajeed tace “Kaga yanda Allah ke abunshi ko?  Ba tare da saninka ba,  ka kawo ‘yaruwarka Gida, Shes your cousin” ba wannan yake son ji ba,  murya a taushashe yace “Mummy..” Mummy ta murmusa cike da karfin hali ta kalli Najwa tace “Zan iya magana dasu?” da sauri Najwa ta gyada kai ta mike ta fita tare da kullo musu dakin.

 

Palor suka shiga inda Baba Abba yake,  Hajjo sai kallon Sada take tana murmushi jin dadi,  shima sai Murmushin suke,  Najwa ta shigo da Sallama,  Paapa yace “Umma ashe har kuen hadu da Jikarki” Umma ta mika ma Najwa hannu,  Najwa ta karasa gareta suka rungumi Juna,  tace “Wallahi ganina na farko da ita naji sonta na shiga na a hankali,  saidai rashin sani yafi dare duhu,  ashe jinin Sadana ne”.

Abba ya mika ma Najwa hannu itama,  ta bar jikin Hajjo ta karasa inda yake zaune yace “Kin san waye ni?” Murmushi tayi,  nan kuma ya bata rai yace “dama ta ya zaki san ko ni waye bayan,  Azzaluma bata bada daman Iyayenki su gaya miki kina da Kawu ba” Najwa ta dora kanta kan kafafunshi,  tace “hakanbe chanza komai ba,  yau na san matsayinka gareni amma ya min kama da na san ka tun asali, abunda yake da muhimmanci yanzu shine,  nasan kai waye,  nasan matsayinka a gurina,  kuma ba wanda zai iya dauke mana hakan kuma” hannu ya daura saman kanta yana shafawa a hankali yace “Allah ya miki Albarka Najwa,  tabbas ke diyar Yesmin ce,  kina hankali da hangen nesa” Maama tayi murmushi, nan suka fara firan yaushe gamo ba tare da sun sako ma Daddy zancen Mummy ba.

**

 

Daya bayan daya take kallonsu, kafin tayi jihadin fara magana kamar haka;

“Yarana, ban san ta inda zan fara muku bayani ba,  amma ina so ku sani cewa i’m truly sorry, i’m truly sorry for not being a good Mother,  ban zame muku Uwa wanda zakuyi Alfahari da ita ba,  amma ku sani ina sonku fiye da rayuwa da kanta,  kuyi hakuri da Uwar da Allah ya baku,  don na san kuna nadamar kasancewa nice Mahaifiyarku,  in kunsan abunda nayi a baya,  You’d wish you had a different Mother–” Abdulmajeed ya katseta da sauri ta hanyar dafe mata fuska da hanayenshi biyu yana kallonta “Haba Mommy, wani irin magana kike haka? Ki sani,  Mu  ‘yayanki ne,  bamu damu da abunda kikayi a baya ba, ba zamu taba da nasanin kasancewar ki Uwar  mu ba, you are our a Mother and we love you,  so ki bar irin wannan maganganun kinji? ”

 

Yaken dole tayi tace “ba ku sani ba,  Shekaru da suka gabata,  Mummy tayi aikin sa6o da yawa, Mummy has wronged too many people  in different ways, Mummy bata damu da kowa ba sai kanta,   kunga wanda suka  shigo dazu ai? Uncle dinku ne da Matarshi,  Iyayen Najwa,  Hardasu a ciki wanda na ma laifi, Sada ya mana komai na rayuwa musamman ma kai boy, ya soka kamar nashi,  a School AbdulMajeed Sada kake bearing kafin naje aka ma change of namez duk don So da Kaunarka da yakeyi, amma na sa kafa na shure na saka sun bar k’asar na rabasu da danginsu na raba Sada da Daddynku saboda wani selfish interest dina, but ina so ku sani Mummy tayi nadaman duk abubuwan da tayi, Mummy has regret everything, zatayi duk yanda zatayi don ta gyara laiffukanta, Daddy yayi fushi sosai,  na mishi laifi babba,  zan tafi,  zan bar gidan  sai ya huce” Idanuwa suka zare.  “No kar ku daga hankalinku, i’ll be back for you,  i promise,  zan tafi for some days, har sai Daddy ya yafe min,  zan dawo,  bana so kusa kan ku a damuwa,  ku kula da junanku,  take care of yourselves har sai na dawo,  Mummy is going to be fine only if she knows you all are fine, kunji?”  rungumeta sukayi banda Abdulmajeed da ya tashi yana share hawaye,  daga abunda ya faru daga abunda ta gaya musu duk da ba straight ta fada ba ya gane abubuwan da ta aikata,  kuka yake yana tunanin “ya zaayi Mamansa ta kasance cikin irin mutanen nan” lallashinsu take tayi har sai da taga zuciyarta zai kare, itama zata fara nata kukan gaban yara ya sa ta  ma Abdul ido,  zuwa yayi shima ya fara lallashinsu Muhsin da Zinatu kafin sukayi shiru, ta tashi tsaye ta bude drawer ta dau mayafinta zata fita daidai kofa Zaineema tace “Mummy,  DonAllah kar ki tafi” bata juyo ba  tace “Daddynku na cike  da bacin rai,  in ya sauko zan dawo  donAllah ku kwantar da hankalin ku kunji?” Ziyada na kuka tace “Mummy to bari muje mu bashi hakuri,  zai yafe miki,  just dont go” Mummy tace “Aa,  ba yanzu ba, please kuyi hakuri,  in ba ku barni ba,  ba zan tafi ba,  kuma Daddy zai cigaba da ganina,  ranshi na baci,  kun taba ganin bacin ranshi? ” AbdulMajeed ya share hawaye yace “Mummy,  ki tafi,  kije” gyada kai tayi tace “ka kula min daku” da sauri ta fita tana kuka.

Maama na jin fitowar Mairo ta fito itama cikin dabara ba tare da su Daddy  sun sani ba,  bakinta na nauyi ta bude da kyar tace, “Hajia Mairo Ina Zaid?” kuka mairo ta fara tana girgiza kai,  gigirgiza kai me maana Biyu “ko Aa,  bansan inda yake ba, ko kuma Aa, ya mutu” ganin bata da abun fada ya sa tayi gaba da sauri ta bar gidan gabaki daya.  Zuciyar Mamma ta fara harbawa, Zaid ya mutu, ba rabon su sake haduwa, Allah ya sa mai ceto ne, hawaye masu zafi ne ki fita daga idanunta, ji tayi an rungumeta ta baya, Najwa ce,  ba tare da ta kalleta ba  tace “He is gone, Zaid baida rai ya mutu” kara rungumar juna sukayi suna kuka,  sai da kusan mintuna7 suna tsaye kafin Maama ta karasa gun Pampon da ke gurin ta wanke fuska, atleast yanzun hankalinta zai kwanta,  tunda ta san Zaid be raye,  ba kamar da da take cikin kokonto ko yana da rai ko babu ba.

 

Da kyar Abdulmajeed ya samu ya lallabi k’anensa da ban baki, Lek’awa Maama da Najwa sukayi dakin, sukaa musu Sallama,  kallon? Maama sukeyi kawai ba su sa wacece ita ba, Maama ta kallesu da Murmushi ta nuna  Abdulmajeed da yatsa tace “AbdulMajeed dina, zaka tuna ni?” a sannu ya girgiza kai, ta murmusa tace “ba zaka gane ni ba,  its been long” ta gefenshi ta kalla, Ziyada,  kallonta takeyi sosai kafin ta dauke idonta ta kalli Zaineema tace “Ga Zaineema nan,  na ga kanku daya da wannan beauty din shiyasa nake son gane wacece Zaineen tsakanin ku biyu, well nasan ba zaki gane ni ba kema,  coz when i left,  you barely talk” kasalaceccen Murmushi Zaineema,  Maama ta kalli Zuzu tace “Ya Sunanki?” a hankali tace “Ziyada” beautiful inji Maama,  ke kuma fa? ta fada tana kallon Zeenatu,  cike da shagwaba tace “Zeenah” Maama tace “inye sunan yan gayu,  come here dan yarona,  zo inji wa ya taba min kai” Autan Mummy ya taso yana matse hawaye, kiris yake jira ya fashe, ta dauke shi tace “ya sunanka?” turo baki yayi yace “Muhsin” tace “Inye, look at my handsome boy,  duk kafisu gaye, yi daria na gani” abunka da yaro ya dare baki yana kyalkyala daria, saukar dashi tayi ta zauna kan bedside drawer.

 

“Sunana Aunty Yesmin, Maama zaku dinga ce min kunji ai?” duk suka gyada kai, “Ni Matar Uncle Sada dinku ne,  kunsan shi?” nan ma suka gyada kai, ta cigaba da cewa “Uncle Sada shine Autan Umma Hajjo,  Kannin Babanku ne,  Immediate Brother dinshi,  lokacin  da muka bar gari,  Abdulmajeed da Zaineema kawai aka haifa, its been long,  ba zasu tuna mu ba,   so bana tunanin ko hoton mu kun gani,  So This is Najwa,  Our  Only Daughter,  cikin ikon Allah ta zo Gidansu ma ba tare da sanin kowa ba,  Rashin Sani yafi dare duhu,  nidai na san ta na gidansu Abdulmajeed da Ziyada, coz labarin su kawai ake ban,  haha,  ta ban labarin yanda kuke kula da ita, unknown to you kuna kula da jininku, Mungode Allah muku Albarka” da Amin suka amsa,  yanda sukeyi ya sa ta gane suna cikin Alhinin tafiyar Uwarsu,  sai ta lura da akwai shakuwa mai girma a tsakaninsu da Uwarsu hakan taji tausayinsu,  ta murza hanayenta biyu tace “kunsan me?” bata jira amsarsu ba tace “Hajia Mairo na burgeni sosai wurin yanda take so ‘Yayanta,  tana sonsu fiye da komai,  lokacin in Abdulmajeed ke  Zaineema basu da lafia,  to zaka ganta cike n damuwa,  har kuka zaku ga tanayi,  in ko Abdul ya dawo Gida yana kuka wai wani yaro ya bugeshi,  to nan fa ake yinta,  nan zata sabi gyale taje gidansu yaron ta bugi uwarshi wai danta ya bugan mata da” daria suka saka gabaki dayansu,  ba su taba kokonta a son da Mummynsu ke musu ba. Ganin sun washe yasa Mummy tace musu “Oya ku tashi muje Kuyi  introducing kanku da Paapa” tashi suka yi suka nufa Parlo inda su Daddy suke.

***

 

AMERICA

Zuciyarsa ke tunzura shi ya bar Course dinna ya koma Nigeria gun Matarshi, ya fi yarda da Sharri aka k’ulla mata,  yafi yarda da Yan Hassada ke son shiga tsakaninsu,  to in ba haka ba,  sunyi waya fa da ita randa ya iso Kaduna,  ya sanar da ita zuwanshi Gida kawai zai karaso,  yana a daidai Kawo sukayi waya, shi da Gidansu ke Unguwan Dosa, amma  don tabewar basira sai ta kawo kwarto dakin? Is not possible,  Kuma in ya tuna clearly, kwarton ya gani kwance kan gado,  ita kuma ta fito daga toilet da alama Wanka tayi, yasan Zaineema tana da Zafi,  amma tana sonshi sosai kamar me,  ba zata ha’inceshi ba,  ba zata ci amanar Aurensu ba,  meyasa be mata uzuri ba? Meyasa ya zabi da ya saketa? Kai Inallilahi  wa ina ilaihir rajiun, she’s Innocent Wallahi,  yanzu haka wasu da ba sa son aurensu ne suka shiga tsakaninsu,  yayi da nasanin yanke hukunci da sauri,American Friend dinshi ya dan zungureshi yayi firgigit ya dawo daga tunani,  “Khaleed,  whats wrong ?  you are lost deep in your thoughts” Khaleed ya sauke numfashi,  a hankali ya ba Abokinshi dan Amerika labarinshi ya karashe yana ganin laifin kanshi,  Abokin ya jinjina kai yace “I’m so sorry, dont blame your self, its not your fault, when this is over,  go back to Nigeria and get your wife back,  i’m sure she’s waiting for you”.  Kansa khaleed ya jinjina tare da kudurin yana isa lagos,  Jirgin Kano zai siya ya wuce ya dauko matarsa.

 

••••NAIJA 4 LIFE••••

Ina zata ta raba har kwana biyu? Wake gareta duk fadin kano? Hajia Aleeya zuciyarta ya gaya mata, da sauri ta samu Keke Napep ta ziyarci Gidan Aminiyarta Hajia Aleeya, Hajia Aleeya na ganinta ta washe hak’ora ta fara so ma mata kirarin da a da ke fasa kan Mairo,  “Hajia Mairo ikon Allah,  suruka ga Gatan Marayu na biyu,  ki taka Naira ki Murza Naira, ki Zubda Naira” Mairo ta zauna,  Hajia Aleeya tace “Yaya ne Tawan?  Ya na ganki haka?” “hmm,  ke dai bari,  Tawa ta k’are,  karya ta takare,  Asiri na ya tonu,  Sada da Yesmin sun dawo,  Abba ya sakeni” wani irin Ashariya Aleeya ta lailayo tace “Hajia Mairo,  ya akayi kikayi wannan Saken?  Tab,  Sada da Yesmin sun dawo?  Sai da nace miki a kar su tuntuni,  kikace ke rashin Imanin ki be kai nan ba,  to gashi nan sun dawo duniyarki ta ruguje, hahah ai yanzu da kike Sirikar gatan Marayu akwai kudi gunki, ki fiddo kudi in kai ki gurin Wani Malami,  aikinshi kamar yanka Wuk’a yake,  yanzu yanzu zaa gyarota, Abba kuma ya dawo tafin hannunki” wani kallo Mairo ta wurga mata,  kafin tace “Hajia Aleeya,  bani ba bin boka da mallam,  wallahi na tuba,  kema ki tuba,  wawa ke maimaita kuskure so biyu,  kema ki tuba mu koma ga Allah,  ai karya fure take bata da ‘ya, nidai zuwa nayi in zauna tare da ke kafin Abba ya sauko”

Hajia Aliya ta zaro ido tace “Wa?  Ki zauna da ni?  A gidan nan? Tabb,  wallahi ba dai ni ba,  yanda fa ba kya so a rabeki da yayanki da mijinki,  nima haka banso a rabeni” Mairo ta marairaice tace “ki taimaka min Aliya,  banda kowa wallahi sai ke,  please ki barni na zauna da ke” Hajia Aliya taga Mairo zata bata mata rai,  ta dage sai ta fitar mata daga gida ko ta sa yan iskan anguwa su fiddata,  Mairo da mamaki tace “Ni zaki juya ma Baya Hajia Aleeya?” Hajia Aliya ta nuna mata hanyar fita tace fita tun muna shaida juna”  Hajia Mairo ta jinjina kai ta dauki jakkarta tace “ba wani abu,  rayuwace” ta fita tana tunanin ina ta dosa?.

**

“Ku matso kusa dani yarana” cewar Pappa bayan ya gama saurarensu,  duk suka matsa kusa dashi, Ya musu addua ya tambayi Abdulmajeed ina yake Aiki?” Abdulmajeed ya sadda kai k’asa yace “ai ba ya aiki” ya akayi haka? Na zata har aure kayi?”Daddy ya chafe da cewa “kwadayin Uwarsa ya ja ta aura mai waa shegiar yarinya,  ta salwantar mishi da Takkardunshi,  shariaa mukayi dasu,  reshe ya juye damu,  muka saida gidanka na GRA Miliyan30, mukayi Asara aka biyo mu aka karbe kudin, sai da wani Sirikin Ziyada ya taimaka muka rabu dasu lafia” yanda Daddy ke magana zaka san cike  yake da bakincikin Mairo, Paapa ya jinjina kai yace “Duk kunyi Aure kenan?” Daddy ya sake chafewa yace “Kaga Zaineema tayi aurenta shekara biyu da suka wuce,  k’addara ya sa suka rabu da Mijinta? Sharri aka kulla mata wai an ga Gardi a dakinta” Maama da Paapa suka ce “Subhanallah” nan Daddy ya musu bayani, suka jajanta ma juna,  ya cigaba da cewa “Zaka tuna Alhaji Sadam Audu dan Senegal? Wanda ake ce ma Gatan Marayu?” Paapa ya dan tsaya alamun yana tunani kafin yace “Me Aurar da mutane dari a rana ya musu kayan daki ya ba mijin gida da sanaa” Daddy yace “Shifa,  to danshi Zaidu ke Auren Ziyada, yanzu ma Aiki yaje Taraba,  shiyasa kaga Ziyadan a gida,  shine Abokin Baban ma ya biya mana kudin da Alhaji Nakowa ke bin mu har Miliyan30″Paapa ya jinjina kai yana cewa “Allah Sarki,  ai gatan Marayu akwai taimako,  Allah ya biyasu” Daddy yace “ai ya Rasu,  shekara na uku kenan” Paapa yace “Allahu Akbar,  Ubangiji Allah ya gafarta mai,  ayyukanshi na gari su bishi” suka amsa da “Amin” nan Daddy ya fara basu labarin Abubuwan da suka faru dasu tun barin su Abuja zuwa yau.

Sosai Maama ke kuka tana tausaya masu,  Paapa yace “shikenan, komai ya zo karshe InshaAllah, muna da junanmu,  zamu taimaki junanmu” Hajjo ta umurce su da suyi adduan daurewan Zaman lafiyansu,  Paapa yace  “SalluAlalNabi’ul karim” suka amsa da “Sallalahu alaihi wa salam”.

***

Gidan Her Excellency Zuciyarta ta kiyasta mata, bari taje chan ta fake har Daddy ya sauko,  Napep ta sake tsaidawa tayi Gidan SSG,  cikin  wani lokaci ta iso gidan SSG, ta biya mai Napep ta fito, bata sha wahalan shiga ba, ta nufa cikin Gidan,  Her Excellency na cikin wani yar Bukka ita da Amjad, Mairo na hangosu ta karasa gunsu da Sallama,  Amjad ya hade rai, haka ma Her Excellency,  Mairo yace “Your Excellency ina wuni?” fuska a hade,  tace “Me kikazo yi a gidana?” Mairo ta marairaice tace “wallahi matsala na dan samu da Maigidana, shine nace bari inzo nan in dan kwana biyu kafin komai ya daidaita” galala Her Excellency ke kallonta kafin tace “Ke har baki da kunya zaki zo gidana? Bayan abunda Sirikin ki ya ma Amjad a gaban mutane?” Mairo ta kalli fuskan Amjad taga ya hade rai tace “Wane? Me ya mishi?” tace “oh tambaya na ma kike?  To bansani ba,  ki fitar min a gida kuma kar na sake ganin kafarki a gidana” Mairo ta durkusa tace “donAllah ki taimakeni banda inda zanje” magiya ta fara mata,  Her Excellency ta kira wani SS,  tace “Release the hounds” OK Ma” yace ya wuce,  Mairo ba ta san me hakan ke nufi ba,  illa magiyan da take ta ma Her Excellency.

Wani abu taji wanda ya sa cikinta kadawa,  kamar  Kukan Kura amma haushin karene,  da sauri ta kalli inda takejin haushin karnunka,  taga karnuka su biyar kosossu,  bakinsu bude alamun sun ga nama sun yo kanta da gudu,  l, haba kafin tayi tunanin wani abu kafa me naci ban baki ba, ta arta a guje tayi hanyar gate,  kafin ta karasa gate din duk wani abu dake hannunta sai da ta wurgar,  hatta mayafin jikinta,  gudu take yi ko da ta fita gidan bata fasa gudun ba,  kamar sabon kamu, haka ta cigaba da gudu sai da ta bar unguwar gabaki daya kafin ta bar gudun. Wani wuri ta samu ta zauna tana maida numfashi hawaye na bin kuncinta,  Wai yau itace a wulakance, ita reshe ya juye da ita,  wannan shi ake kira da k’ikayi koma kan mashekiya. Ina ta dosa? Wani tunani yazo mata,  da sauri ta girgiza kai,  amma bata da wani choice sai nan,  duk yanda  zuciyarta Ke hanata zuwa gidan,  amma bata da wani zabi tunda ba zata kwana a Titi ba,  tuna abunda ya faru kwanaki na ita da mai Napep  ya sa bata tsaida me Napep ba don ta yarda yar pos dinta a gidan her Excellency,  duk nisan gidan haka tayi ta takawa tana tafiya tana hutawa har wurin bayan laasar tana hanya har chan gab da 5:30 ta iso gidan. Sai da ta gama duk wasu adduoin da ta iya kafin ta karasa cikin gidan.

**

Kankana take sha ta ji kwankwasawar kofa,  tashi tayi ta zura takalmanta ta karasa ga k’ofa,  budewa tayi, ga mamakinta sai ganin Hajia Mairo,  nan da nan ta daure fuska tare da fadin “Lafiya?” cikin yanayin da bata taba ganin Hajia Mairo ba tace mata “Alhaji Abba ya sakeni” kamata yayi ace taji dadin batunta,  sai dai ta samu kanta da faduwar gaba amma ta dake tace “To meye ruwana ni?” ga mamakinta sai ganin Mairo ta zube a k’asa tace “Hajia Aynarh,  na san ni da ke bama jituwa,  nasan kinsan bana sonki kamar yanda bakya sona,  amma donAllah ki taimakeni,  ki barni na zauna tare dake har sai Alhaji Abba ya sauko” Hajia Aynarh ta kalleta sama da kasa tace “gwara da kika tuna min ba kya sona, nikam ban k’in kowa a dunia,  amma tunda ba kya So na don me zan barki ki zauna tare dani? Salan ki min wani mugun abun?” da sauri ta girgiza kai tace “wallahi ba abunda zan miki,  ki taimakeni,  ba don ni ba,  donAllah hajia Aynarh” wani tunani tayi na wasu yan seconds kafin ta matsa tace “ki shigo” godia ta tsaya mata,  Hajia Aynarh bata tsaya ji ba ta shigo ciki, Mairo ta biyota a baya” Zama tayi kan kujera Hajia Aynarh tayi banza da ita ta cigaba da shan Kankananta “Sada ya dawo” cewar Mairo,  kamar ba zata tankata ba tace “Waye Sada?” cikin borin kunya tace “Lahh kin manta Sada,  kanin Alhaji Abba?” dakatawa tayi da abunda take sha tace “ba ya rasu ba?” Mairo tayi dan jim kafin tace “Dama ni nace su bar garin kar su sake dawowa” Galala Hajia Aynarh ta kalleta kafin tace “Ki ka daiyi musu Kurciya su bar garin,  amma ke awa ki ce su bar gari? To ni dai mutum ya sani jinina daci gareshi,  nama na kuma taurin tsiya ne dashi,  ba asirin da zai kamani da yardan Ubangiji,  Kainuwa ce ni dashen Allah bata wani katon banza ba ehe” ta dauki plate dinta ta fita daga parlorn ta shige dakinta.  Galala Mairo ta rakata da ido,  tabb,  wai yau ita ake dasa ma magana,  ba wani abu,  duniya ce ke horata,  kuma ba zatayi zuciya ba,  ita din mai laifi ce,  neman Yafiya takeyi.

 

WASHEGARI

 

Bayan Aiki,  Aunty Aynarh tazo Gidan Alhaji Abba,  a tsakar gida suka ci karo da Yesmin,  rungume juna sukayi suna mamakin chanzawan junansu, Yara sun tafi makaranta, suka karasa daga ciki sai da ta gaida Hajjo cike da girmamawa,  kafin su Zaineema da Ziyada suka gaidata, kafin Maama ta mata jagora Parlo inda su Daddy suke,  cikin jin dadi suka ma juna barka, suka gaisa sosai da Alhaji Sada yana tambayanta Iyali,  Murmushi tayi tana kallon Daddy,  Daddy ma kallonta yayi cike da kauna yace “Yo ai Aynarh tawace,  dama kai mu ke jira kaje Kwara neman min Aurenta” Dariya tayi sosai,  Sada yace “Ah haba dai Yaya?  Wai har yanzu akwai k’auna kenan” cike da wasa ta harareshi tace “to me zaa fasa?”  Sukayi daria, Daddy yace “Kai Sada fa dagaske nakeyi, Auren Hajia Aynar nake sonyi” Paapa yace “Ahhh, Hajia Aynar,  are you sure ba akai Yayana gun Babalawo ba?” daria tayi sosai kafin tace “ai baka sani ba,  mu ai bawani babalawo,  Tsantsan Soyayya ce kawai ke tasiri,  kuma kasan ka so a soka shine so, kuma kasan da tsohuwar zuma…] ” daria suka fashe dashi, kafin tace “Yesmin ina yarana?” Yesmin tace “i’m sure kinsan Najwa coz there was a day da take min bayanin an bata wani Amala taci yayi dadi, i’m sure kece” Hajia Aynarh ta zaro ido tace “No way,  kar kice nin Najwa diyata ce,  Ikon Allah”.

Fira suke sosai gwanin ban sha’awa, ba ta tambayesu ya akayi ba,  suma basu gaya mata ba,  bata kuma ce musu Mairo na gidanta ba,  don sosai ta bata tausayi jiya, kwana tayi tana kuka,  yau da safe kuwa tambayanta tayi me zaa mata na gyaran gida sai dai ce mata tayi akwai masu yi.

 

Daddy yace “Sada yaushe zakuje Yola?” Paapa yace “Wai jira muke komai yayi settling ko nan da 2weeks ne” Yesmin ta kalleshi,  Daddy yace “Settling din me? Aa sada,  ba haka akeyi ba,  yanda ka k’agu ka gida haka itama ta k’agu taga Yanuwanta, kasan kawaici irin na Yesmin, ku shirya Gobe mu tafi,  nima ya kamata naje,  don da hannuna na kirasu ta landline na shaida musu mutuwarku,  kuma sukazo” Paapa yace “Allah Sarki,  to goben sai mu tafi gabaki dayanmu,  sai mu bi jirgi,  don in zan tuna da kyau,  Yola nisa ke akwai” Daddy yace “Ahh,  har mu duka? Yara fa na makaranta” Hajia Aynarh tace “Ba Muhsin da Zinatu ba? Ina iya tafia da su Gidana, sai ku tafi da su Ziyada” Daddy yace “kuma da mun dawo sai maganar Auren mu ba” Suka sa daria,  Pappa yace “wai Yaya baka kunya surrikarka?” yace “Yo ni  ai Yesmin kanwata ce” tace “hakane Yayana,  kuma da an daura Aurenka da Hajia Aynarh,  kuma sai na ‘yayanka,  Abdulmajeed da Najwa,  don Soyayya suke maka a cikin Gida” Daddy  ya gyara Zama yace “haba biri yayi kama da mutum, shiyasa in suna tare suyi ta wikiwiki da ido,  Ja irin Pure Heart naji yake ce mata” Dariya sukayi gabaki daya, Paapa yace “Amma naji dadi,  da an dawo Yola sai Biki” duk suka amince da hakan kafin suka fara tautauna yanda tafiar zata kasnace,  mikewa Hajia Aynarh tayi tace “barin karasa Gida daga office,  Allah ya tsare hanya ya dawo daku lafia, sai an kawo min yaran” nan sukayi Sallama Yesmin ta rakota dakin Hajjo, ta mata Sallama “Ziyada,  in Abdulmajeed ya dawo kice mai ya kawo min Muhsin da Zinatu Gida,  ba sai kunce musu tafia zakuyi ba, kunsan ba zasu yarda ba” Zaineema tace “ina zamu?” Maama tace”Yola zamu chan Gidanmu” Ziyada tace “Yayyyy, zamuyi tafiya” Aunty Aynarh ta nunata da bakinta irin yanda yarbawa keyi in zasu nuna mutum da baki,  tace “wa ke maganan ki? Kinsan you are out of the equation,  babanki ba zai yarda ba” turo baki takeyi da alaman Shagwaba,  tace Hajjo “wai haka?” Hajjo tace “Yo Eh,  ai yanzu karkashin wani kike” dura tayi ta karasa parlo gun da su Daddy  suke tace “Paapa wai banda ni zaa Yola?” Paapa yace “inji wa? Ai in ba da ke ba zaa fasa tafiyan” Daddy yace “Kai me hankali,  Ka manta tana da aure ba karkashin mu take ba?to ta bika, in mijin ya sakota sai ta dawo gabanka kuyi ta zuwa garruruwa” Paapa yace “ba ma zaayi haka ba,  Diyata kira Mijinki ki tambayeshi” da sauri ta fita ta wuce daki ta dau wayarta ta latso Zaid tana cewa bari ma na sa Handsfree kuji,  kar ace karya nakeyi. su Maama dai daria suke..

**

A Garin Taraba,  Zaid na Conference Meeting ya ga kiran Ziyada,  ko me ya keyi in kiranta ya shigo sai ya datse ya amsa kira,  kallonsu yayi yace “Excuse Me” Ya daga wayan “Hello My Forever” yana jin muryarta ya san tana cikin jida dadi da annashuwa,  hakan ya sa mai Murmushi a fuska” Yes Hello, Wai dama Yola za a tafi duka gida,  Zaaje chan Family house dinsu Maama,  shine Daddy yace ba zaa je dani ba,  shine Paapa yace in kiraka in tambayeka,  My Forever a tafi dani ko?” yace “My Forever, slow down,  gaya min,  waye Maama?  Waye Paapa? Kuma me zaaje yi Yola?” tace “Paapa Uncle dinmu ne,  jiya suka dawo daga India, Maama kuma Matarshi ce, Maaman Najwa?  Wanda take gidanmu? So Yola zamu chan Family house dinsu Maama din shine aka ce sai na tambayeka” Zaid yace “Ohh Ziyaaa,  kinsan Yola akwai nisa,  kuma ni gaskia bansan yan tafiye tafiyen nan, kuma” da sauri ta katseshi tace “Bazanje ba kenan?  To shikenan” jin yanda muryanta ya chanza lokaci daya,  ba don ya so ba yace “Babe listen,  zakije,  kawai ina ce miki ne you should take care of yourself,  zan sa Idi yazo ya kaiku goben ko? We talk later,  i love you” dadi ya rufeta, sonshi na ratsa shi har ta manta mutanen da ke gabanta tace “thank you,  you are the best,  I love you,  bye.” Aunty Aynarh tace “Iye!!” da sauri Ziyada ta firgita kafin ta turo baki cike da borin kunya ta fita sumsum tana cewa “Kai Aunty Aynarh” duk akayi daria,  Najwa dai tabe baki tayi a ranta tace “twofaced kawai” Maama na lura da Najwa ta tuna labarin da ta bata kan Mijin Ziyada, a ranta tace “Anya Najwa ba tayi mistakening Mijin Ziyada da Nura  Kurman nan ba? Coz wannan kamar akwai Soyayya da shakuwa tsakanin su” kafada ta daga dai.

**

Da Daddare  Abdulmajeed ya hau Adaidaita ya kai su Zinatu da Muhsin Gidan Aunty Aynar,  ga Mamakin shi sukaga Mummy,  da gudu suka karasa gunta suna rungunmanta, Mummy ta daga Zinatu tace ” Yarinya ya kike?” Rungumeta tayi tace “Mummy nayi missing dinki” ta murmusa tace “ba gashi kin ganni ba” Muhsin yace “Mummy ina Aunty Aynarh” tace “tana ciki” da gudu Zinatu da Muhsin suka karasa ciki.  Abdulmajeed ya gaidata ta ansa tana me jin nauyinshi,  duk ta rame,  ya hadiye miyan bakinciki yace “gobe zamuje Yola chan gidansu Maama,  shine Aunty Aynarh tace a kawo mata yaran sabida Makaranta” Mummy tace “Allah Sarki,  Ya Daddynku?” yace “Lafiyansa lau,  kowa lafiya” tace “yaushe zaku dawo?” yace “wallahi bansani ba amma kamar zamuyi “Sati Daya” tace “Allah ya kaimu”  nan Aunty Aynarh ta shigo rike da hannun Zinatu,  Muhsin kuma a jikinta.  Abdulmajeed  ya gaisheta ta amsa cike da Murmushi,  yace “Ashe Mummy  na nan” murmushi tayi bata amsa ba, yace “Mungode Aunty” bata amsa ba tace “dazun nazo ba ka nan” yace “eh wallahi naje chan tarauni na duba Gidan Baba Sada ne, an kawo Furnitures shine naje ganin yanda abubuwan ke tafia” fira sukayi har wurin 9saura ya musu Sallama, har zai fita tace “AbdulMajeed,  ba sai ka gaya musu Mummynku na nan ba” Murmushi yayi yace “ba zan yi maganan ba” kunya Mummy  takeji fa,  saidai Hajiya Aynar ta rakashi, lokacin Muhsin yayi bacci,  Zinatu ke kallo kan cinyar mamanta,  Hajia Aynarh ta dauki Muhsin kan kafadanta zata kaishi daki yayi bacci,  Mummy tace “Hajia Aynarh” ta kallota ba tare da tankata ba,  tace “Nagode Allah ya saka da Alheri” tabe baki tayi tace “Ai Hajia Mairo,  da don ke zaa dinga abu da ba a yi shi ba” ta shige daki da Muhsin ta bar Mummy Zaune.

****

 

WASHEGARI

 

Da Misalin k’arfe 8 na safe, Zaid ya kira Ziyada cewa Idi ya aiko Drivers suna Waje,  ta rasa yanda zata gaya musu Daddy cewa driverna waje,  sai da aka gama shiri suka firfito, wurin 10  Paapa yace “Abdulmajeed,  a samo taxi ko?” Abdulmajeed yace “Ok Paapa” ya fita daga dakin,  Ziyada ta bishi da sauri har tana cin  tuntunbe “YaMaji” ya tsaya,  ta karasa gunshi,  cikin muryar rada tace “YaMaji,  Zaid ya aiko da Motan da zai kaimu Airport fa” yace “Kai Zuzu,  meyasa baki fada ba ko tun dazun?” be jira amsarta ba ya shige ciki,  yace “Oya Ku tashi ga Mota”dama duk sun shirya don tafiya Airport, fita sukayi bayan Majeed ya dauki Akwatin nan ya fitar waje,  Drivers din na ganin ya fito suka fito daga motarsu su ka karba kayan Hannun Majeed suka sa a booth.

Daddy na fitowa yace “Wadannan Motocin fa?” be samu amsa daga gun kowa ba,  Idonshi ya kai ga Plate Number din Motan ansa GATAN MARAYU.  Paapa yayi daria yace “kaga amsanka ko?” sai mu shiga,  a bamu Mota daya ni da Mamana, Paapa ya riko hannun Hajjo suka nufa motan  Farko,  haka yake attimes kamar chali chali,  Daddy ya girgiza kai ya bi bayanshi yace “aidai ba mamarka bace kai kadai” sukayi daria.

Hajjo,  Abba,  Sada da Yesmin suka shiga Mota daya, Driver yazo daidai Zuzu ya bude mata k’ofa ta shiga,  Zaineema da Najwa suka sa daria “Ahh Yayi Matar Gatan Marayu, mu ba zaa bude mana ba? Abdulmajeed yace “nidai barin bude miki PureHeart” ta yi daria Zaineema tace “Allah ya ban hakuri ni Zaineema” Majeed yayi daria yace “Oya shigo” itama ta shiga,  shima ya shiga,  kasancewar Motar babba ce kirar *Range Rover* basu tutse ba.

 

Bayan wasu Mintuna suka iso Airport,  nan suka iske Idi yana jiran zuwansu, cike da girmamawa Idi ya gaidasu,  ya matsa kusa da Ziyada ya mika mata wasu Envelop yace “inji Oga” ta karba tace “tohm nagode ko?” Paapa yace “Oya Abdulmajeed je duba kaga inda ake sayar da Tickets kaje kaga nawa ne na Yola?”Idi yace “Erhm, Tickets din na hannun Madam” Ziyada ta kalli hannunta, Idi yace “karamar Envelop din ta sama” ta zare babban ta mika ma YaMajeed,  ya bude ya ga tickets guda takwas,  ya kalli su Daddy yace “Toh Su Paapa sai ku sama inlaw dinku Albarka,  ya siya tickets din 168k 21k per one” nan suka shiga sama Zaid Albarka,  Ziyada kuwa girman Zaid ya karu a idanunta.

Idi yace “Madam jirginku zai isa 15mins to 12″ Akwai wanda zasu tarbeku da Motan ZSA,  Allah ya kaiku lafiya” godia suka ma Idi,  suka wuce inda Jirginsu zai tashi.

****

 

Y O L A

 

Kamar yanda Idi yace hakan ne,  Motoci uku suka zo don tarbansu Ziyada,  sai da Majeed ya musu magana a tabbatar su din ne kafin  suka shiga Sienna su duka,  Yan tarbansu suna musu sannu da zuwa,  Driver din yace “wani Unguwa zaku?” Paapa yace “bari muga Yesmeenah zaki tuna suna Unguwan naku? ” dariya tayi tace “kai dai kace ka manta,  Mallam Jimeta zamu” ya ja mota suka fara tafiya.

Gaban Maama na ta fadi,  bata san me zata iske a gidan nasu ba,  komai ya chanza na daga da garin,  da aka kara karaso unguwansu kuwa hawaye ta fara yi,  kasancewr gidansu kan hanya ne,  daidai gidan tace “Ya isa,  anzo” Driver ya ci birki,  suka fita,  ba ta jira kowa ba ta isa Gidan da sauri, a Soro suka ci karo da Baffa rike da chasbaha,  da alama masallaci zaije,  tsohon dan fulani amma da karfinshi,  chak ya tsaya yana kallon Matar da ke gabanshi tana haki kamar tayi  gudu,  Inallilahi wa ina ilaihir rajiun yake maimaitawa kamar ya ga fatalwa,  bakinta na rawa tace “Baffa” bakinshi na rawa shima yace “Aisha Yesmin” da sauri ta isa gareshi ta rungume Mahaifinta,  da fullanci yake cewa “kece wallahi,  baki mutu ba” nan su Paapa suka  iso,  Bapha yace “Sada,  Wai ya akayi na ganku raye? ku min bayani?  Sada ya karaso ya dafa Baffa yace “Massalaci zaka ai?” muje duka, muna nan baffa har sai ka gaji da ganin mu,  yace “ku kuma ku karasa ciki,  nan suka shiga sukuma mazan suka bi bayan baffa,  drivers suka shigo da kayyayakinsu,  Yesmin da sauri ta shige cikin babban gidansu tana kwada sallama,  wasu yanmata suka amsa sallaman,  da alama bata san su ba,  su ma kallon su kawai suke,  suna cewa “sannunku da zuwa” yesmin tace “ina mutan Gidan” Nene Asibi ta fito tace “baki ne a gidan namu?  Sannunku da zuwa” Yesmin ta tashi ta rungumeta, “Nene Asibi” ta dagota ta kalleta tace “yau na shiga uku,  jamaa ga fatalwa a gidan Ardo” Maama tace “wallahi ba Fatalwa bace nice, Yesmin dinku,  ban mutu ba” mamaki suka tsayayi,  tace “wai ina Umman Shehu, ko tana Sallah” Nene Asibi tace “hmm,  Yesmin,  saidai hakuri,  Allah ya ma Mahaifiyarki Rasuwa Shekaru 12 kenan” wani irin juyi gidan ke mata,  kamar zata fadi,  gabanta na fadi,  da sauri Naajwa da Zaineema suka riketa,  da kyar a ka zaunar da ita,  kuka takeyi a hankali,  ba rabon su gana da Mahaifiyarta,  nan dai Hajjo ta shiga bata baki, har aka samu ta shiga toilet don yi alwala tayi azahar.

 

A GURGUJE

 

Abu na waya,  tuni aka kira Yanuwa da abokan Azziki aka sanar dasu Yesmin bata mutu ba gashi ta dawo gida da ita da Mijinta da kuma diyarta,  kafin dawowar Masallacin Jumaa,  gidan Baffa cike,  da murna,  da yasa basu santa ba,  lokacin da take nan ba a haifesu ba,  wasu kuma basu da  wayau,  nan aka shiga yi mata ta’aziyar Mahaifiyarta.  Nan fa aka shiga cikasu da abincika kala kala,  da su Ardo suka dawo daga masallaci a ka taru a parlornshi,  Daddy ne ya musu bayanin duk wani abu da ya faru,  kuma be boye musu cewa Matarshi ce sanadi ba,  nan aka jajanta wa juna,  Baffa yace  InshaAllah zai basu maganin kariya.

****

Kwanan su Takwas, suka dawo Kano,  sunji dadin zamansu Yola,  sun saba da mutanen chan. Zaid ma ya dawo Jiya, tun da Idi ya zo taryansu Paapa yace mai “Mijin Ziyada ya dawo ko?” Idi yace “eh ya iso,  yaje dai wani aiki ne” Paapa yace “Oya ka maidata Gidanta” batayi musu ba don tayi kewan Mijinta sosai.

Aka Maida Ziyada Gidanta,  Daddy ya sa su Paapa komawa gidan da ya siya a Tarauni,  Gidan Paapa yayi kyau Sosai,  ba wani katon Gida bane,  3bedrooms ne,  da Zaineema da Najwa suka tafi,  Hajjo ta k’i yarda ta bisu,  ya zamana Gidan su Uku ne daga ita sai Daddy sai Majeed, duk gidan yayi wani iri,  Sada ya ma Abba maganar dawowa da Mairo,  ya nuna mai bacin rai,  ya nuna be son maganarta,  nan yayi shiru,  yace bayan an dan kwana biyu zai sake bijiro mai da maganar.

*

Tana isa gidan ta fada wanka,  ta ci kwalliyarta cikin Riga da Skirt na atamfa ta zanzara kwalliyarta tayi kyau sosai.

Shikuma Ogan Niyyarshi ya gama aikin da yake ya wuce Gidansu Majeed ya dauko matarshi,  don ya mayi kokari da be bita chan yolan ba,  sosai yayi missing dinta,  Idi ne ya sanar dashi cewa matarshi na Gida,  haba kamar jira yake ya ruga da gudu mota yace a kaishi Gida,  dokin ganinta yake,  yayi missing dinta da yawa,  ana isa ya fita da sauri,  tana jin shigiwanshi ta fita itama da gudu,  ba su damu da maaikatan Gidan ba,  ta rungumeshi shi kuma ya dagata sama yana juyi da ita yana jin dadi,  daukarta yayi har cikin dakinsu kafin ya direta,  nan fa suka fara gwada ma junansu yanda sukayi missing din junansu,  ta mishi godian abubuwan  da ya musu tun daga ranar tafiarsu Yola har dawowansu,  nan ya hade bakinsu yana shaida mata cewa su abu daya ne,  ba godia a tsakaninsu.

 

B A Y A N   K W A N A  B I Y U

 

Maama ta dafa Abinci ta zuba a cooler tace ma su Zaineema su tashi su kai ma su Daddy Abinci,  dama sun shirya,  suka dauki Basket din ita da Najwa suka fita bayan ta basu kudin Keke Napep.   Suka fita suka tafi gidan hajjo, Abdulmajeed da Daddy  basa nan ko da suka isa,  Najwa tace “Didi,  kizo muje gidan Zuzu” Zaineema tace “Aa ba zanje ba” “Haba didi, kizo muje please,  ba dadewa zamuyi ba” Zaineema tace “ke ni ki kyaleni,  ina Yaya,  ba zan dinga bin gidan k’anwa ba” Najwa tace “Oh,  nikam na tafi,  tace sai kin dawo” Najwa tama Hajjo Sallama,  ta fita ta tsaida keke Napep don yanzu ta zama yar  gari,  Gidan Ziyada ta nufa.

***

Ziyada na kwance jikinshi Wayarshi yayi k’ara,  tsaki yayi kadan,  ya janyo wayan,  ganin me kiranshi ya sa shi sake buga tsaki,  Ziyada tace “Yadai My Forever?” yace “takura min suke sonyi daga gurin Aiki” yayi karya,  tace “ka dauka mana” ya mike yace “ina zuwa” ya fita rai a bace,  zai bata ma Na’ilah rai,  meye zata ding damunshi?  Salan ta ja mai matsala da Ziyada,  fita yayi daga Parlorn yayi bayan Gida inda da yakanyi waya lokacin yana matsayin Nura.

Shigowanta  Gidan kenan,  da yake Zaid ya janye tsaron nan bata samu wahalan shiga gidan ba,  hango shi tayi yayi baya yana latsa wayar,  a ranta tace “mugu,  muguntan zakayi ko?” ta so ta share ta shiga gun Ziyada, amma sai ta samu kanta da bin bayanhi.

 

“Na’ilah,  whats your problem wai,  meyasa zaki dameni,  na gaya miki ba zan iya aurenki ba, i’ve told you not once not twice cant you get that to your head? Haba!  Naci na meye?” don kin taimakeni nayi achieving goal dina,  ai ban sa ki dole ba,  you chose to help me willingly” bata ji me Nailahn ke cewa ba taji yace “aiko tona min asiri will be the last thing you will do, ba ruwanki da zuwa kusa da Matata balle ki gaya mata abubuwan  da nayi, Na’ilah kar ki sake”

 

Zuciyar  Najwa a dake ta sha gaban Zaid wanda ya sage bakinshi kamar yaga Fatalwa tace “Na’elah ce kanwar Nura Kurma?” Zaid ya kashe wayar dukda ya dan tsorata da ganinta,  be san iyakacin abunda taji ba,  ya hade rai yace “ke meye haka?” tace “Nura kurma, yau kaine a matsayin Gatan Marayu ne ko me ake cewa? And yiu turned out to be Ziyadas husband? Really?  Ka gaya min,  mai me kudi kamar ka zai sa yayi faking identity dinshi ya zama some worthless man? Whay are you upto now? You want to hurt Ziyada and her Family? You want to put a baby in her and divorce her? (Me kake shiryawa yanzu? Kana so ka kuntata ma Ziyada da yan gidansu?  Ciki kake so ka mata kafin ka mata sakin wulakanci?) to wallahi  baka isa ba, a da kana mata abubuwa don bata da mai tsaya mata,  amma a yanzu tana da gata, dole ka rabu da ita” hankalin Zaid ya tashi,  duk da bai fahintar abunda yarinyar ke cewa amma hankalomshi a tashe yake,  balle da yaji tana maganar rabasu da Ziyada, ji yayi tace “yau zan tona ma Asiri,  zan gaya mata duk wani abu da na sani game da kai” ta juya a fusace,  be san me zaiyi ba,  be san iyakan abunda zata ce ma Ziyada ba,  a tsinci kanshi a tsananin tashin hankali, ba zai iya rayuwa ba Ziyaa ba,  da sauri ya fincikota ya galla mata mari,  ya sada ta da bango,  hannunshi a kan wuyanta ya makureta,  be cikin hayyacinshi,  ce maa yake “zan kashe duk wanda zai rabani da Ziyada” ita ko k’ak’ari takeyi na cire hannunshi daga wuyanta dinta don gani take zata iya mutuwa yanda ya makureta,  gyalen ta ya fadi,  Zaid be saketa ba,  kamar me shirin aikata lahira, fuskarta yayi jazur,  ta na cikin tsananin ukuba,  kwatsam idonshi ya kai ga hannunta,  daidai da guiwan hannunta,  dam gabanshi ya fadi, *S* ya gani kwance kan lauluasar fatarta, da sauri ya daga kai zuwa wuyanta kamar me neman wani abu ya ko hango abunda yake nema, *Y* da sauri ya saketa yana ja da baya yana girgiza kai, tuni ta fara murza wuyanta cikin wahala tana kuka,  ganin tayi hanyar wucewa ne ya sashi karasawa gunta ya riko ta da sauri,  kuka takeyi,  mamaki taji ganin hawaye a idonshi yace “Ke,  Ina kika samo wannan abun?” ya fada yana me bankarar mata da hannu har sai da ta gano abunda yake nufi,  banza tayi dashi ta shareshi,  ya sake maimaita mata wannan karan ya nuna na wuyanta,  ba ta tankanshi ba, da sauri ya daga hannun rigarshi yace “ki gaya min donAllah,  ina kika samo wannan *Y and *S din” bin jikinshi tayi da kallo,  a daidai inda nata yake nan nashi yake,  baki na rawa tace “Maama na ta min,  kai ya ka samu?” girgiza kai yake,  komai na zuwa mai tamkar mafarki yace “Nima mama na ta min” wani Murmushi me hade da kuka takeyi,  shine yayanta da take nema, tana sane tace mishi “Meyasa aka maka Mark da Alphabets?” “mainly saboda in naga yanuwana in shaidasu” tayi murmushi tace “me Alphabets dinka suke nufi? Meye Y din”  a tare sukace *”YESMIN”* da sauri ya dago kai ya kalleta kanshi na sarawa,  hawayensa ma kara gudu,  tana matsowa kusa dashi shi kuma yana ja da baya kamar ya ga Aljanni,  tace “Meye S din?” a dan tsorace zai fada ta taya shi a tare suka ce *SADA* a lokacin  Zaid ya fashe da wani irin kuka, itama kukan ta sa mai sauti tace “YOU ARE MY BROTHER” yana Kuka yace “I Am your Brother” da sauri ta rungumeshi,  shi ma ya rungumeta tare da matseta a jikinshi kamar zaa kwace mai ita,  a hankali tace “i’ve found you” shima a hankali yace “You’ve found me”……

 

√√√√

 

*Whats up lovers? Kun bacci?  Sorry,  late night post!*

*Finally dai,  Najwa ta gano Yayanta.*

*So ya kuka ga Page dinnan?*

 

#1love

#ADAY

#bibiliciousfreakingfans

#anatare

#nagode

 

Biebee Isa

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Leave a Reply

Back to top button